Showing 51001 words to 54000 words out of 467220 words

Chapter 18 - MATAR MUTUM COMPLETED 1-3 BY MARYAM FARUK.doc

23 Sep 2025

12247

qafa ta dawo dan ba zata barsu a gida suka kadai da daddare ba.

Kan jiki kan qarfi ta ringa hidima da Bintan da Jaririnta kyara da hantara kuwa babu wanda bata gani. Abinda yafi damunta yanda Audu ya shareta, ko magana ta masa a ciki yake amsawa hidima yake tayi da Matarsa da Jaririnsa kayan fitar suna ma ana saura kwana biyu Abdullahi ya shiga da qatuwar leda ta zazzage taga kayansu ne shida su Babangida ko dan kunne babu nata a ciki. Suna duba kayan ya shigo fuskar nan kamar hadari ya wuce dakinsa ta tashi ta bishi. Seda ta kai masa abincin dare ya gama ci kafin tayi masa godiyar kayansu Babangida da ya bayar ta qara da cewa

"Dan girman Allah idan wani laifi nayi maka kayi haquribka sanar dani na gaji da wannan zaman gabar da mukeyi" ta tattara qarfin hali ta fada wanda Sadiya maqociyarta kuma qawarta guda dayace ta bata wannan shawarar ta cewa ta dena shiru, duk idan taga canji a gurinsa ta tuntubeshi suyi magana tunda tasan halin Binta baze wuce ta qulla mata wani abun a gurinsa bane koda ace baze yarda da ita ba in har ya gaya mata laifinta ta kare kanta shikenan ai ba makaho bane kuma ba kurma ba qin Allah ne ya saka idan an gaya masa abu yake hawa ya zauna ba tareda yayi bincike akai ba.

Seda ya mula kafin ya fara magana yana cewa
"Wato badan Allah ya kawoni ba so kikayi ki bar Binta ta mutu ba zaki fita ki taimaka mata ba? Koda yake dama tasha fadamun kince se kinyi Ajalinta da ita da abinda yake cikinta ba zata haifeshi ba. Wlh mamakinki nake Bara'atu, yaushe kika zama haka? Ko kuwa dama hakan kike kin lullubeni ne baki fito da ainihin kalarki ba is yanzu?"

"Ni ya kamata nayi maka wannan tambayar yaushe ka zama haka Audu? A zatona kaine mutum na farko da zaka fara bayarda shaida akaina amma kuma se zaton nawa ya zama ba gaskiya ba, koda ace ba zaka shaideni ba Audu yaci ace kasan me zanyi da wanda bazan aikata ba. A Bechi tace na nufeta da wuqa ka yarda yanzu kuma tace ni nace zan kasheta da dan cikinta shima ka yarda wane mugun abu na aikata maka daya janyo irin wannan rashin yardar a tsakaninmu har takai ayi mun qazafin zanyi kisan kai kuma ka hau ka zauna? Nayi tsammanin ko Qadangarenta tace nace zan kashe zaka qaryata balle ran mutum ba dYa ba harda na Jaririn dabe iso duniya bama" Bara'atu ta fada cikinmatuqar qarfin hali hawaye masu dumi suna sakko mata.


https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG

*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*

*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*

*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 400 (PROMO PRICE BAYAN KAMMALA FREE PAGES ZE KOMA 500) A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*

*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*

*FREE PAGE 14 (LAST FREE PAGE)*

Hawayen ta suka qara gudu lokacin daya miqe ya fice daga dakin bayan daya antaya mata tsaki me qarfi. Ta dade zaune a gurin tana kuka, meta tsarewa Binta? Ita data shigo ta tarar batayi kishi ta tayar da hankalinta ba se itace zata yita hada mata tuggu da makirci a gurin Miji shi kuma sam babu bincike ya ringa zama kan magana da an gaya masa? Tana tsaka da wannan kukan Hadiza ta kwankwasa mata qofa, seda ta gyara fuskarta ta fita Hadizan ta gane tayi kuka amna tayi shiru bata tambayeta dalili ba kuka kuma ta gaya mata ta daura aure dashi tunda ba zata tashi tsaye akan wannan Kishiyar tata makira ba se ta zauna tayi musu kuka har hawayenta ya qare.

"Yace kije ga naman qauri can an kawo a gyara, banda rainin wayo ke zakiyi mata suyar qaurin ma ina yan uwanta sunzo? Dama ace zaman mutunchi kukeyi da sauqi amma keda bola banbanci kadan ne a gidan nan sann.."
"Ya isa Hadiza, muje ki kama min" Bara'atu ta katseta daga mitar data kwaso.

"Allah ya sauwaqe kedai da zaki iya bismillah" Hadizan ta fada tana zama akan kujera, tasan ba zatayi ba tunda ta fada dan haka ta fita rai babu dadi zuwa gurin gyaran Qaurin. Ta tarar da Mairo na hura ta dora yan ciki lantana kuma tana ware nama da qashi da alama hadosu masu gyaran naman sukayi.

"Barka da Rana Hajiya" Mairo ta gaisheta, fuska babu walwala sosai dalilin quncin zuciya ta amsa mata, Lantana kuwa ko kallon arziqi bata mata ba sema tahau waqar Habaici daga Mairon har Bara'atun babu wanda ya tanka mata daga qarshe ta nemi guri ta zauna dan Mairo tace ta bari zasuyi tana kallon Lantana nata jan qwafa da alama zataje tayi abinda ta saba na hadin masifa.

Suna kaskon qarshe yan uwan Binta biyu suka zo gurin ta gane Babbar ita tana dan zuwa dalilin akwai yan uwan Mijinta a nan Kanon me bi matan dai sau daya ta taba ganinta se yau na biyu. Dazu da suka sauka har ta fita zataje ta gaishe su suka hadu da Binta a tsakar gida tace ko barandarta ta taka seta mata rashin mutunchi shiyasa ta fasa dan hakan yanzun ta gaishe su suka amsa kadaran kadahan. Robar da aka zuba Nama suka dauke suna barwa Lantana sallahun idan ankwashe sauran a kai musu.

"Ko me zasuyi dashi se Allah, a irin arziqinsu ai wlh nama dai yaci ya gunduresu yanzu amma Allah sa suma ba jida zasuyi su tafi dashi su aje qulli qulli a firiza yanda Hajiyar nan takeyi ba su basu ci ba su basu bawa wani yaci ya musu addu'a ba kai Hajiya Binta fa akwai Rowa alqur'an" Lantana ta shiga jero zance babu kai babu qafa. Yanda Bara'atu bata tanka ba haka Mairo kamar bata gurin, wannan nadaga abinda yasa take qara ganin girman matar. Ba ruwanta ta shiga sabgar da bata shafeta ba, aikin daya kawota gidan kawai take yi idan tazo da safe ta gama musu kalaci da wuri take dora na rana wata rana ma sha biyu ta gama data gama ta karbi rabonta zata tafi se kuma gurin qarfe uku ta dawo ta dora na dare shima tana saukewa zata tafi se kuma gobe da safe musamman yanzu da Binta tasa aka hade girkin tun zuwan Hadiza a yanda ta cewa Bara'atu ta dena girki da kanta, kwadayin Nama da Kazar daya kawo qanwar tata seta koma haka idan anyi girkin zata tsaya a raba ta kwashe duk abin arziqi ta hadasu da qasan tukunya ita bata ci ba ita bata bari wani yaci ba ta bakin Lantanar, ba kamar Mairo ba ita lantana idan tazo tun safe seta kai Taran dare har se Audu ya dawo Bintan ta fatattaketa sannan zata tafi yanda kasan bata da Miji balle Yara.

Haka suka gama suyar ko dandanon gishiri a harshenta ta koma daki. Washe gari tun sassafe aka ringa shigo da kayan cefane, guraren Goma Binta ta aiko kiranta, A falon Audu na sama ta sameta tasha kwalliya abinta ba zakace jego take ba. Ta gaidasu ta zauna tana satar kallon Audu da tun maganar jiya be sake ce mata komai a gidan ba dubasun da yake da Asuba ma beje ba yau. Kudi ya tura mata murya a daure yace
"Gashi nan, ki duba cefanen da aka kawo, abinda babu se a siya sannan su Bilki suna hanya bansan ko su nawa bane ki gayawa Mairo a saka abinci da yawa"

Tayi shiru a ranta tana mamakin yau kuma ita aka bawa kudin cefane sannan ita ake cewa ta fadawa Mairo a qara abinci abinda ko ran girkinta Binta ke fadar abinda za'a dafa.
"Shikenan na sallameki" ya sake fada seta miqe ta dauki kudin tana jin Binta cikin kissa murya qasa qasa tana ce masa
"Ko kaifa, ai ya kamata dai itama ta ringa jin matar gida ce ba wai ace komai sedai taga anayi ba kaga kar suzo a qara tafiya dani a baki ace na kankane komai"

Ta tafi tana mamakin Bintan a ranta, wato matar nan ko wagainiya Albarka shiyasa wani sa'ilin bata ganin laifin Audu saboda Bintan tamkar me rufa ido take. Bata taba mata Tijara ko cin mutunchi a gabansa ba, idan yana nan nunawa take nan dunita tafi kowa son su zauna lafiya da Bara'atu amma ita taqi bata hadin kai, da hakan take kanainayeshi kullum tana nuna masa laifin Bara'atu ne ita ce bata so su zauna lafiya, Bara'atu ce take fadawa yan uwansa mugun abu akanta shiyasa kowa baya sonta, Bara'atu ta tsaneta bata da buri illa na taga bayanta sannan ita kuma tayi ta nuna bajintarta da son jan Bara'atun da yayanta a jiki a gaban idonsa idan yana nan har kyautar abubuwa take kai mata ko yara yana fita tabi ta karbo abinta ta dora da Tijara shiyasa baze taba ganin cutar da take mata ba.

Maganar girkin kanta da farko ta hana ko gaidata masu aikin suyi da kuna ta canza ra'ayi ta karbe girki ita ta gaya mata ainin dalili amma shi se tace masa saboda Bara'atun ta huta ne hidima tayi mata yawa ga yara ga girki gara Mairo ta ringayi gaba daya tubda dai biyanta akeyi kuma dama kullum se tazo ko ba rabar girkin Bintan bane ire iren abubuwan da suke qara dagula zamansu kenan, shi tunda kunnene kawai se abinda yaji ba ruwansa da bin ba'asin ya akayi cikin kissa zata tunzuro shi ya dauki fushi da ita yanzu kuma da taso qulla wani abun shine zatace ya bata kudin cefanen abincin suna dan ta tabbata ba Alkhairi ya saka Bintan yin hakan ba.

Mairo taje ta samu tace ta duba kayan, data tambayeta me za'a dafa toh tilas ta koma ta sake tambayo Bintan tace mata Shinlafa da tuwo kawai zasuyi sauran abubuwan ta bayar da aikatau wannan yasa ta dan samu nutsuwa qila abincin iya jama'ar Bechi za'a bawa shiyasa ta barshi a hannunta. Tun rana suka fara rage aiki, su Bilki da Aisha da matansu Aminu ne suka yo gaba sauran dangi se gobe suna haka suka tasata gaba da tsiya harta rasa inda zata tsoma ranta wai daga dawowa harta tsomare a qauyen ma tafi kyan gani ta bari tsoron kishiya yayi tasiri a ranta.

Har an idar da Isha suka karbi baquncin mutanen Ikko, Yakubu da iyalansa Bara'atu ta rasa ina zata tsoma ranta saboda murnar ganin Balaraba. Suka rungume juna cike da kewa, Balaraba tayi kyau ta qara zama wata babbar Mace fata se walwali takeyi ita kuwa Bara'atu abin se godiyar Allah kawai. Daga gefe Aisha dake kallonsu tace
"Wato kwanciyar hankali duniyace, ku kalli dai idan daula da jin dadi ne Yaya Bara'atu tafi Yaya Balaraba samunsu amma kalle su ki gani banbancin kamar sama da qasa kowacce da ka ganta base an gaya maka matsayin da take a cikin gidanta ba"

"Aisha kenan kedai da Allah yasa kike ke kadai a gun Mijinki kici gaba da gode masa domin ba zaki gane qalubalen me Kishiya ba se kina da ita duk abinda zaki fada ko ki bada shawara akai hasashe ne kawai tunda baki san ya ainihin matsalar take ba" Sauda Amaryar Aminu ta bata amsa.

Bara'atu kuwa a dakin Audu ta sauki Balaraba, ta fita ta kawo mata ruwa da abin tabawa tace
"Bari na dora muku abinci wannan bazata haka ace zakuzo ko Yaya Audu be sani ba"
"Wai injiwa? Audun da shi yaje ya dauko mu daga filin jirgi" Balaraba ta fada. Bara'atu ta gwale ido tace
"Filin jirgi? A jirgi kuka zo?"
Balaraba ta harareta tana dariya tace
"Ji yanda kika gigice kamar wnada nace miki da fiffike mukazo, jirgi muka hawo mana abin Allah in gaya miki yau se ga Balaraba a jirgi qiris ya rage na haihu saboda tsoro" suka kwashe da dariya gaba daya. Bara'atu ta sake cewa

"Amma shine be gaya mun zaku zo ba?"
"Ba zata yayi miki gashi ai kinfi yin murna da muka zo yanzun, ke ni ba wannan ba ya naganki gaka qashi da fata ko laulayi kikeyi?" Balaraba ta fada tana kallon Bara'atun, seta miqe kawai tana cewa
"Bari naje na dora abincin"
"Karki wahalar da kanki seda muka ci abinci muka taho tafiya a jirgi kamar wanda Aljanu suka ragewa hanya? Ni ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????banma san minti nawa mukayi ba kedau Allah ya qara mana arziqi me amfani Allah kuma yasa badi mu lula muyi tafiya me nisa a Jirgin muje mu sauke farali" cewar Balaraba.

Dukda haka Bara'atu taqi zama tace to bari taje su gaisa da Yaya Yakubu daga haka ta tsere, bata so ta zauna tunda Balaraba ta fara zancen ta rame ko ciki ne da ita tasan yanzu magana zata sake dagulewa sedai tana fita Bilki ta shige ta samu Balaraban ko kyakykyawar gaisawa basuyi ba dan tana sallah suka shigo yanzun taje ta gaida Yakubun kuma jira taje Audu ya matsa ra kwashe duk abinda ya faru da wanda yake faruwa ta gaya masa amma bari ta fara da Balaraban.

Tas ta labarta mata komai daya faru basa nan,
"Yanda kika san sallamammiya Bara'atu, na fada mata da nice wlh tun daga kan ginin nan gayyar zata watse. Hauka ma akeyi suci Talauci tare sannan dadi yazo ace ta zama yar kallo itafa da Boyi boyin gida babu banbanci. Idan anyi magana tace to ya zatayi? Na gaya mata taci abu ta kazan Yaya Audun tunda shi yake daurewa Bintan qugu tana mata iskanci kafin ta gangara kanta, ko Iskar qarya tayi ta musu rotse wlh duk zasu kiyayeta amma mata kamar Kazar da ruwa ya daka salaf salaf sedai tayita kuka in sun mata abu tana rama a haka fa kin ganta da kyan gani dalilin tajr Bechi kusan watanta biyar a can da ana gyaran gidan dawoqarta ne tayi wannan zabgewar to in aka cigaba a haka wata rana sedai azo a kwashi sauran qasusuwanta ai damuwa ta cinye tsokar tasa" Bilki ta fada cikin kumfar Baki.

Tsabar baqin ciki da takaici Balaraba kasa cewa komai tayi se qafa da take girgizawa, a haka Bara'atu ta dawo ta tarar dasu tana ganin Bilkin kuma ta tabbata ta gama kwaza komai. Fada Balaraba ta ringa mata kamar zata daketa da tayi tayi kuma seta koma banbaki da lallami dan lamarin Bara'atun ta rasa wannene ma zeyi amfani a ciki.
Banda kuka babu abinda takeyi ita kuma, haka suka kwana ko baccin kirki Balaraba bata iyayi ba, data rufe ido abin ze mintsineta ta tashi ta fara surfawa Bara'atun masifa can kuma tayi qasa tana lallashinta tareda bata dabarun kwatar yanci.

"Audu yana sonki, da ace baya sonki a yanda take wannan abun da ba zakiyi qarkon kawowa yanzu a gidannan ba. Wayo da dabara ne baki dasu, idan ta nuna miki wayewar Birni seki nuna mata ta qauye, akan me zaki ringa yiwa Kishiya kuka kin nuna mata kina tsoronta a fili ba dole ta takaki yanda taga dama ba, ai ko a ranki kina tsoronta ki dake idan ta fada ki mayar mata kar ki ganta wata zabgegiya kiji tsoron karta dake ki ai qarfi ba'a jiki bane idan kika qarfafa zuciyarki tsaf wlh zaki kaita qasa idan ma ta kaiku da dokuwa sannan shima karki raga masa tunda be dauki tsagin gaskiya ba. Wlh ki tashi ki kwatarwa kanki yanci idan ba so kike ki bata quruciyarki ki kashe kanki da kanki ba".

*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*

*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*S'

*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*


*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*

*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*

*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*

*Kutuntube mu ta wannan number =???08129249549*
*=???07011401314*

Washe gari.

"Nifa wlh Ji nake kamar na rufeki da duka Bara'atu" Balaraba ta fada kafin taci gaba da cewa
"Banda tsabagen abin haushi Bintar me? Me akayi akayi wata Binta da zaki zauna ta shigo gidanki ta mayar dake yar kallo bayan ke kika ci wuyar Audun kika zauna dashi tun bashi da ko sisi har ya zama mutum ta ganshi ta aura na tabbata wlh a rayuwar da kikayi dashi Binta ko a me wanke mata kaya ba zata dauke shi ba. Amma shine kika zauna kika barta take zuba miki mulki a gida kin zama yar kallo jibeki dan Allah yanda kika qwanjale kika fita hayyacinki tamkar me wani ciwo ita kuwa tana walwala da farin ciki Miji na hannunta wlh tun wuri idan zaki farka gara, ki amshi Mijinki da matsayinki, ke kika sha wuya dashi dan haka yanzu kamata yayi duk wadda zataji dadinsa to a bayanki take".

"Kema dai kya fada Yaya Balaraba" Aisha ta tsoma

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login