Showing 93001 words to 96000 words out of 467220 words

Chapter 32 - MATAR MUTUM COMPLETED 1-3 BY MARYAM FARUK.doc

23 Sep 2025

12403

dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*


*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*

*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*

*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*

*Kutuntube mu ta wannan number =???08129249549*
*=???07011401314*

Seda suka gaisa kafin ta zaro takardar da Audu ya bata ta miqa masa ba tareda tace komai ba, ya bude ya karanta yayi shiru kamar ruwa ya cinye shi kafin ya ninketa yana sauke ajiyar zuciya ya miqe tsaye.
"Ki gyara mata dakinki seta zauna ciki kafin muga abinda Allah zeyi" ya fadawa Balaraba ya shige ciki. Balaraban ta miqe a sanyaye tabi bayansa ita kuwa Zubaida Fulas taja ta shiga hada shayi daidai wanda ze isheta ta tabbata dai saki ne a cikin takardar, ita kuma a kullum ta tashi Addu'a bata mantawa da neman zabin Allah a dukkan lamuran rayuwarta dan haka duk abinda ya sameta zata karbeshi da kyakykyawan Ikilasi.

A dakin Balaraba tayi masauki tana ta jaddada mata ta saki jikinta tamkar tana gida. Bayan da su Dada da qannenta biyu suka tashi daga bacci su suka ringa debe mata kewa harta manta da damuwar data kawota gidansu ta ringa jin zumudin itama dan cikinta ya fito duniya ta tabbatar koshi ya isa ya ringa bata nishadi yana debe mata kewa. Ta tuna sanda tayi cikin da bayan zubar dashi Audu ya maidota gida a lokacin taso ta bar cikin ta haifeshi saboda ta shirya barin rayuwar Bariki. Ta so ta haife dan ta raineshi da yaqinin wannan abin ya saka ta samu rangwame a gurin ubangiji na daga tarin zunuban data dibarwa kanta sedai daga baya tunanin irin rayuwar da Da ko yar da zata haifa da qalubalen da zasu fuskanta yasa ta kasa idar da qudurinta.

Sanda wannan cikin ya bayyanar mata tayi murna kwarai musamman dataga irin tarin murna da Zumudin da Audun ya ringayi shima ta ringa hasaso yanda zasu raini abinda zata haifa tare ashe duk mafarki takeyi zanen qaddararta daban abinda take tsarawa a zuciyarta daban.

Bayan fitar Yakubu har ya dauki niyyar zuwa gidan Audu se kuma wani tunani yasa ya fasa hakan, a karo na biyu kenan daya sake yanke danyan hukuncin da yake ganin hakan daidai ne a rayuwarsa.

A bangaren Audu seda hantsi ya daga kafin ya shirya ya fito ya nufin dakin Zubaida dan ya karbo takardar jiya. Ya tura qofar dake a bude ta sakayata yana sallama ciki ciki shiru babu motsi Tv da Radio da take yawan kunnawa duk a kashe dan haka ya dauka bacci takeyi seya wuce uwar daki nan ma qwalam bata nan. Tsaf ya bincike ko ina be ganta ba kuma bega takardar ba, yanayin dakin da be nuna alamar an dauki wani abu ko an hada kaya ba yasa yayi tunanin ko maqota ta leqa amma wannan ba halinta bane musamman da duk maqotan yan fadar Binta ne dukda haka ya qaddara wani gurin ta leqa seya koma daki da niyyar kafin ya gama shiryawa ta dawo.

Binta ta kawo masa abin kari yau din jinta take kamar wadda akawa Bishara da Aljanna. Lantana ce tayi mata albishir din taga Zubaida a hanya da jaka sanda take tahowa ta gaji kenan ta tafi ba kuma zata dawo ba. Tana so ta zungureshi da maganar taji ko ya sani amma dai tayi shiru harya karya ya fito ta rakoshi ta ringa dariya qasa qasa ganin ya doshi dakin Zubaidan yana kwazara mata kira nan ma shiru bata amsa ba.
"Wai ina wannan yarinyar ta tafi?" Ya jefawa Binta tambayar ta watsa hannu tace
"Yo ka bani ajiyarta ne da zan san inda zataje?"
"Shikenan sena dawo" ya fada daga nan ya fice yana mamakin ina zataje dan sam be kawo gida ta tafi ba tunda ai bata san abinda takardar daya bata ta qunsa ba, haka ya dawo gida da yaqinin ze tarar da ita amma wayam bata nan, ya diririce, ta tabbata gidansu ta tafi kenan amma me yasa zata tafi to? Ya jefawa kansa tambayar rainin wayo.

Bayan Isha ya shirya tsaf ya cewa Binta zeje wata unguwa, gidansu Zubaidan ya tafi zuciyarsa ta ringa tuhumarsa me ze kaishi gidan amma hakan nan ya zungura kai yaje. Malam Hassan ya rasa ina ze sakashi saboda murna bayan sun gaisa ya tambayeshi Iyali yace
"Dazun Babarsu take cewa gobe In Allah ya kaimu zata leqa ta ganota kuwa jiki yayi nauyi har tana cewa ko zata dakkota tazo gida tunda haka akeyi a Al'ada haihuwar fari"

Cikinsa ya bada wani sauti quuuu, bata zo nan ba kenan? To ina yarinyar nan ta tafi kardai fa ta hefashi a masifa in duniya ta sake shiga ai da seta bari seta zo gidansu ta gayawa Mahaifinta komai sannan seta tafi amma yanzun ta ina ze fara yi masa bayanin shima nemanta yazo?

"Aa bafa abin dole bane idan baka so ta dawo gidan se tayi zamanta dan naga fuskarka ta canza daman matane da Al'ada kasansu basa wasa da ita" Mala Hassan ya katse masa tunani a zatonsa zancen dawowarta gida ne ya canza fuskar Audun besan Al'amarin yafi gaban haka ba. Tilas ya masa sallama a gurguje ya taho bayan ya ajiye masa na goro.

A gida ma rkicewa Binta yayi da tambayar ina zasu nemo Zubaida ina ta tafi?

"Ya wuce ta koma inda ta fito ne, wai kai meye ma naka na damuwa ina ka saketa duk ma inda zataje taje mana kana da matsala da ita ne?" Ta fada cikin jin haushin yanda yake ta safa da marwa cikin damuwa. Washe gari da farar safiya ya tafi gidan Yakubu ya ringa buga musu qofa kamar za'a tashi duniya Yakubun ya fito yana ganin shine ya shiga surfa masa fada shima yana tambayar ba'asin wannan bugu kamar ya masa sata. Daya masa bayanin abinda ya kawoshi qiris ya rage Yakubun yayi dariya amma ya kanne a ransa yayiwa Allah tasbihi wato tun ba'aje ko ina ba aiko ze gane kuskurensa domin baze fada masa tana gidan ba.

"Ni meye nawa a ciki yanzu Audu? Kashedi nawa kamun akan na fita daga sabgar gidanka? Ashe da nace kayi haquri ka bar maganar nan baka daddara ba to ka saketa ta bar maka gida meye kuma abin damuwa a ciki ko daman ka dauka zata zauna ne kuci gaba da ci mata mutunchi kuna aibatata kaida matarka?" Yakubun ya fada yana tsareshi da ido. Audu yaja tsaki yace

"Ni bance ta zauna ba amma data tashi tafiya ai seta tafi gidansu ko amma yanU naje jiya bata can yanzu me take so na gayawa mahaifinta idan suka zo ganinta basu sameta ba?"

"Se ka gaya musu ka saketa ita kuma tana tsoron ta tayarwa da mahaifinta hankali idan ta koma gida ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?shine ta sake shiga duniya, ni dana san wannan shirmen ne ya kawoka wlh bazan bude qofata ba haka nan ina bacci na me dadi ka daga mun hankali da bugu. Ka tafi ka nemo yarinyar mutane dai kafin iyayenta su farga, kaga daman ba'a jima nayi wani case Mata ta bata Iyayenta sukace Mijin ne ya siyar da ita yayi kudin jini AAllah ya tsareka kaima kar suce kayi kudin jinin da ita daman an fiyi da masu ciki" yana gama fada masa hakan ya maida qofarsa ya rufe ya bar Audu cikin tashin hankalin daya ninka na farko akan maganar da yayi ta karshe.

Daman a Bechi ana rade radin qungiyar Asiri ya shiga yayi kudi farat daya da yawa sun qaryata cewar wai sirikinsa kuma ubangidansa ne ya buda masa yake samun kudi haka? Su kance shi din har nawa ya mallka da yake bawa Audun kudi haka? Zancen da akeyi yanzu rabi da kwatan Gonaki da filayen da suke a Bechi mallakinsa ne saboda duk wanda ya daga fili ko gona ze siyar da an tallata masa ze siya a farashi me daraja kuma shiyasa wasu ma haka nan suke siyar masa suje wani gurin su sake siya ragowar kudinsu susha shagali yanzu idan wannan magana taje Bechi ace matarsa ta bata da tsohon ciki la shakka cewa zasuyi yayi tsafi da ita kawai.

https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG


*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*

*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*

*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*

*PAGE 23*

Sati guda ya shude Audu na bulayin neman Zubaida sedai sama ko qasa babu ita babu kuma wanda ya ganta bare asan labarin inda tayi. Har Zariya sukaje da Bashir gidan daya dakkota suka tarar an tashi gidan ma gaba daya titi ya biyo ta kan hanyar haka suka juyo Kano babban abinda ya qara daga masa hankali ya bazama nemanta zuwan da Baba Zayya tayi akan taje duba Zubaidan Allah ya taimake shi yana gida ranar, daya rasa abin fada mata dole ya rangada mata qaryar Zubaidan tana Bechi, kuma daman yaso yaje ya sanar dasu tana can har se bayan ta haihu zata dawo Kano to Allah be nufa ba. Dake akwai yarda da Amana sam Baba Zayya bata kawo komai a ranta ba tunda ana hakan mace ta tafi garin su Miji haihuwa dan haka tayi musu sallama ta koma gida ta shaidawa Malam Hassan yanda akayi.

Wannan dalili ya qara zaburar da Audu ga neman Zubaidan, nadama mara amfani ta dirar masa biya hukuncin daya yanke ba tareda zurfin tunani ba. Haka ya ringa raba kudi wa malamai akan ayi masa Addu'a Allah ya bayyana Zubaidan ya kuma kareta a duk inda take. Cikin wannan yanayi Alhazai suka fara tashi, Binta taje gida tayi sallama da danginta ta dawo tana ta shirin tafiya sauke farali bacci ragagge takeyi saboda jiran ace su fito. Ita sam ta manta ma da wata Zubaida balle batun ba'a ganta ba, yanda Audun be cika nutsuwa ba a lokacin yasa ta tsahirta masa, ita kadai take ta shirinta tunda dai ya sallameta ya bata Guzuri me auki ita kam ya gama da ita se jiran ranar tashi kawai takeyi.

Acan gidan Yakubu kuwa hankali kwance Zubaida ke zamanta, tsakanin Balaraba da Yakubun ba zata tantance wanda yafi tattalinta ba. Duk wani abu da zata buqata suna mata haka nan basu barinta ta zauna shiru balle ta fada tunani ko wata damuwa a koda yaushe cikin hikima sukanyi mata nasiha akan rayuwa da qalubalen da yake tattare da ita. A dan taqin zaman ta fahimci banbance banbance masu tarin yawa da suke cikin rayuwar Haske data duhu ma'ana rayuwar da akeyinta cikin sani da wayewa ta Addini da kuma rayuwar Bidin bidima irin wadda tayi a baya ta koma dora yinta a gidan Audu.

Yakubun jajirtaccen Namiji ne wanda yake tsaye akan lamuransa dana iyalinsa. Ga daishi be tara dukiya tamkar dan uwansa ba amma rayuwar gidansa ta zamo abar sha'awa wadda duk me hankali idan aka bashi zabin kudi ko nutsuwa irin ta gidan Yakubun tabbas baze tsallaketa ba.

A kullum da Asuba seya dorawa matarsa da Yayansa karatu haka bayan sallar Isha'i idan sun zauna a maimakon hirarrakin banza na duniya sukan yi tasu hirar ne akan karatuttukan da sukayi. Ya tambayesu su tambayeshi, hatta da Qaramin dansu Tijjani me shekaru uku a sannan Alqur'ani ya fara zama a bakinsa, haka qananan Hadisai da ake dorawa Yayinsa yana tsinta har idan Yakubun yana tambayarsu sukayi kuskure Tijjanin da suke kira da Alhaji ze gyara musu ga wayewa ta boko turanci yafi hausa Nuna a bakinsu kodan inda suke zaune yaren da suka fi amfani dashi kenan? wannan abin ya matuqar birgeta ya kuma zaburar da ita kan cewar itama bata makara ba tana da damar da zata nemi ilimi tana kuma burin abinda zata haifa ya tashi cikin irin wannan rayuwar ta ilimi ba irin ta gidan ubansa ba.

Zata iya bada shaidar Audun yana salloli na farilla kuma yana qoqarin yinsu akan lokaci kuma cikin jam'i, a zamansu daya tasamma shekara a watan Azumi kadai zata bada shaidar yana zuwa sallar Tarawi da kuma Qiyamullaili tun bayan daya shude kuma a ranakun girkinta dai bata sake ganin yayi ba bata sani ba ko idan yana dakin Binta. Dama shi bame jurar Ibadar Azumi bane domin Ramadanan ma da qyar yake kaishi, bayan Alqur'ani bata tsammaci ya karanta wani littafi ba bata taba ganinsa dashi ba haka ko a magana ba zatace ga inda ya kawo misali daga cikin Hadisi ko wani littafi na Addini ba. Ba zata manta ba akwai sanda ta taba shawartarsa shiga karatun Asuba da akeyi a masallacin dake cikin layinsu wani baqon babban Malami ne yazo yake bada karatun Fiqhu da Hadisi se Tauhidi take yace mata ai ya gama karatu, seda ya shekara biyar yana qolanta to wane karatu ya rage masa da beyi ba kuma?
Da tace ita zata ringa zuwa gurin matar Malamin da take karantar da Mata a cikin gida harya yarda bata san ya akayi ba ya dawo yace babu maganar ta tambayi dalili kuma yace babu dole ta haqura badan taso ba domin Allah ya sani tana sha'awar ta nemi ilimi shiyasa yanzun data samu wannan damar tayi amfani da ita.

Dada take ja tana biya mata karatun, dayake tasan baqi dan haka karatimu da takardar Alqur'ni be bata wahala sosai ba dukda tafi gane rubutun warshu amma da yake ta saka kanta se gashi tana ganewar in ta biya mata kuma ta ringa nanatawa kenan har seta haddace. Balaraba ce ta sameta akan ta ringa fitowa suna daukar karatun tare bayan da Dada ta sanar mata tana yiwa Inna Zubaidan qarin karatu, daga nan itama ta zama yar Aji ta kuma maida hankali sosai akan abinda ake koya mata. Irin nutsuwar da take tsintar kanta a ciki ta qara tabbatar mata da cewar tabbas akwai banbanci me tarin girma tsakanin rayuwar da akeyinta cikin sani da kuma ta jahilci.

Satinta uku a gidan wata safiya ta tashi da naquda, kafin nan sunje Asibiti har sau biyu Yakubu da kansa ya kaisu tareda Balaraba an dubata an kuma tabbatar da lafiyarta data abinda yake cikinta suka basu kwana goma daya zagayo suka koma kwanaki biyu kenan da zuwan nasu da safiyar ranar Laraba ta tashi da naquda nan da nan suka wuce Asibiti da ita, daman Yakubu yana nan ya jinkirta komawarsa Ikko saboda yana taraddadin ya zasuyi idan haihuwr tazo mata cikin dare gida babu Namiji daga ita se Balaraban dalilin daya saka ya daga tafiyarsa kenan saboda a Asibiti zuwansu na farko sun bashi tabbacin ba zata qara sati biyu nan gaba bata haihu ba gashi kuwa kwanaki goma sha biyu kenan da wanacn zuwan haihuwar tazo.

Cikin taimakon Allah bata dauki lokaci mai tsaho ba ta sauka, ta haifo wasu runtuma runtuman tagwaye wanda ko a Da guda daya aka haifi wannan tabbas se an jinjinawa wadda ta santaloshi se gashi har biyu ubangiji ya bata a sauqaqe cikin Aminci. Lokacin da aka nunawa Yakubu yaran kasa cewa komai yayi se tasbihi daya ringayi a zuciyarsa. Duk wanda yasan Ahalin gidansu baya buqatar a fada masa yaran tsatsonsu ne ze iya cewa ma ba'a taba haifar Jarirai masu kama da Mahaifinsu Malam Tijjani Kwabo da kwabo irin wadannan ba har hasken fatarsa basu bari ba abinda ya banbantasu da Audu kenan saboda shi yana da duhu kadan.

Ya rasa ta ina ze fara ma, Balaraba nata murna ta kasa tsayuwa guri daya shi kuwa tunanin waze fara shaidawa zancen haihuwar yake tayi. Gadai Arziqi Allah ya basu wadannan ne tagwaye na farkoba zuri'ar gidansu amma haihuwar su tazo cikin rudani. Seda ya tabbatar babu abinda ake da buqata a Asibitin kafin yacewa Balaraba zeje ya dawo.

Can kamfanin da Audu yake ginawa inda kuma nan su Musbahu suke zama ya nufa. Yaci sa'ar tarar da Musbahun be tafi gidan Mai ba, bayan sun gaisa yace yazo ya rakashi gidansu Zubaida Amaryar Audu babu musu ya hau mota suka tafi a ransa yana mamakin meyake faruwane domin a kwanakin nan gaba daya sun lura da Baba Audu baya cikin hayyacinsa dukda be fada musu komai da yake damunsa ba amma ko gidan Mai seya kwana biyu be fito ba aikin Kamfanin ma an dakatar dayi kamar yanda ya fada yana cikin wani dan uzuri ne.

Da suka isa gidan a Mota ya bar Musbahu ya qara qofar daya nuna masa a mazaunin ta gidan Malam Hassan. Yayi sallama cikin sa'a Malam din ya fito ya amsa a shirye yake da alama wani gurin zashi, be taba ganin Yakubu ba amma jini da kamannin fuska yasa ya gane dan uwan Audu ne dan haka yayi masa iso cikin gida bayan ya saka Baba Zayya tayi musu shimfida ta kawo masa ruwa a mutunce suka gaisa suna tambayarsa iyali.

Cikin nutsuwa da kuma sanin makamar aiki irin nasa ya warwarewa Malam Hassan duk abinda ake ciki be boye masa komai ba hatta da sakin da Audun

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login