Showing 81001 words to 84000 words out of 467220 words

Chapter 28 - MATAR MUTUM COMPLETED 1-3 BY MARYAM FARUK.doc

23 Sep 2025

12399

ya bita da kallo yana tuna lokutan baya a zamanin Amarcin Binta. Kullun ta Allah se sunci Gasashshiyar Kaza da tsire da wani damun fura me shegen dadi da yake siyo musu suci su biyu ko takardar Naman Bara'atu da Yaranta basa gani balle suji qamshi. A sannan ma yakan siyo hardasu amma indai ya fara shiga bangaren Binta dashi to ya zama haramiyarsu daga baya ma ya dena siyowa dasu ta cusa masa ra'ayin ai suna ci a Miya kuma sanda tana Amarya itama an mata dan haka yanzun lokacinta ne taci ita kadai shiyasa yanzun yayi amfani da maganarta ya siyo musu shida Zubaida kadai itace Amarya ai itama tana ci a Miya.

Zubaida kuwa a qofar dakin Binta ta tsaya ta rafka sallama, Bintan na zaune ta zabga Tagumi, abin duniya ya isheta taji sallama, bata dauka Zubaidan bace ta amsa harda bada izinin a shiga. Ta shiga tana qara wata qaramar sallamar ganin itace ya saka Binta zabura tana binta da kallo tundaga sama har qasa, dukda kyashi da hassadarta daya cika mata zuciya seda ta yabi kyan da shigarta tayi to ina ga Audu?

"Ke bakida hankali koM meya kawoki dakina? Da izinin ubanwa kika shogo?" Ta fada cikin hargowar data zame mata jiki, Zubaidan tayi murmushi tace
"Seda nayi sallama fa kika amsa kafin na shigo, kuma ba wani abu ya kawoni ba, kazar Amarci Mijinmu ya sake siyomun shine nace bazanci ni kadai na na raba na kawowa Dana" ta dangwarar mata da Farantin a qasa ta juya tana tafiyar yanga Binta tayi kukan kura ta kai mata cafka, a yanda ta cakumeta Allah ya dubeta kamar jifa sega Audu ya fado dakin badan haka ba ta tabbatar da tace seta ballata ta zuba a wilbaro tabbas abinda tayi niyya kenan.

"Baki da hankali Binta meye haka zaki kamata da dambe?" Ya fada yana janye Zubaida da zuciyarta ke buga tsalle daga hannunta. Bata dauka jarabar Matar nan takai haka ba, ita ko doguwar cacar baki ba iyawa tayi ba ina dmga yar bawa hammata iska kuma ace da wannan qansamemiyar basamudiyar ai wata rana murus zata kasheta idan akace suyi dambe.

"Dole kace bani da hankali mana wato kai ka aikota tazo tamun cinikinta Abinda aka saba ko? Ni zaka wulaqanta Audu da abinda zaka sakawa ubana kenan bayan duk halaccin da yayi maka a duniya? Karka manta mahaifina shi yayi maka rigar da har ka ringa yawo a gari ka kwaso wannan karuwar, to wlh bazan zauna baqin ciki ya kasheni ba tattarawa zanyi na bar maka gidan ka idan yaso ka auro irinta goma ka ajiye gara na koma gidanmu inda ake sona" tayi bal da farantin kazar da aka kai mata ta shige daki tana kuka wiwiwi, diri diri yayi ya rasa me zeyi, ya bita ne ko kuma su fita su bar mata dakin?

"Ka bita mana karfa ta jiwa kanta ciwo kamar watsi take da kaya" Zubaida ta fada jin Binta na zubar da kaya a qasa se ya tafi solo solo ya shiga dakin ita dai Zubaida ta juya ta fice har sannan jikinta be dawo daidai ba daga tsoron shan suburbuda a hannun Binta. Bata san ya suka qare ba dan har bacci ya fara fizgarta kafin ya shigo ransa duk babu dadi ganin haka yasa daman tayi shirin bacci a kwance take tana jiransa se kawai ta gyara kwanciya dakyau tayi baccinta shima ya gama abinda zeyi be nemeta na duk yanda yake cike da zumudin kebewarsu amma ya gagara yin komai, yanda Bintan ta ringa kuka tana fadin zata tafi kawai ta shiga duniya yana wulaqantata ne saboda yaga Dadynta ya goyi bayansa sanda ta koma gida ita kawai gara ta tafi koma inane tunda babu me qaunarta ya shiga tsakaninta da Iyayenta kuma yazo yana wulaqantata akan Matar daya hadu da ita daga baya tasan baya qaunarta tun sanda aka kashe mata Da amma be dauki matakin komai ba.

Haka ya kwanta ransa duk babu dadi sedai da Asubahi da yar dagwas ta kaishi gari me nisa tuni ya manta da wata Binta da Emotional blackmail dinta. Tana can ta saki baki tana jiran ya bugo Asubanci yaci gaba da rarrashinta dan jiyan Data gama surutai bandaki ta shiga ta kulle yayi yayi ta fito taqi tace ya fitar mata a daki in ba haka ba zata kwana a ciki sannan ya tafi to ta dauka daya dawo masallaci ko kafin ma ya fita se shiga ya dubata amma taji muqus har gari ya waye tarwai se Tara saura na safe suka fito da Amarya yayi shirin fita, tana zaune kan barander dakinta Lantana na share tsakar gidan suka fito ta zube tana gaishe su.

Kamar jiya yauma harda dan risinawar Zubaida ta mata ta gaidata, bata tanka ba ta zabga tsaki bata dai yi masifar data sababa shirun nata kuma se yaji babu dadi dan haka yacewa Zubaida yana zuwa.

Falon Bintan ya shiga ya tsaya a tunaninsa zata bi bayansa amma shiru, ya leqo ya mata magana nan ma ci kanka bata ce masa ba wannan ya hasalashi ta wulaqantashi gaban me aiki dan haka ya fice fuu ko Adawo lafiyar da Zubaida take masa be amsa ba.

"Zaki san ni ba sa'ar wasanki bace wlh yau se kin gane kurenki badai jiya ya ceceki ba? Yau naga ubanda ze kwaceki a hannuna" Binta ta fada tana miqewa bayan data tabbatar Audu ya fice daga gidan tabi bayan Zubaida data qarawa tafiyarta sauri jin abinda take fada, gudu ta saka ganin dagaske kamata take shirinyi tana fadawa daki ta turo qofa Binta ta saka hannu zata dannata ciki bisa tsautsayi ta datse mata yatsa da qarfi take ya fashe ya fara jini.

*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*

*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*

*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*

*PAGE 20*

"Akan me zaki kulle qofa? Dukanki zatayi ko cizo da ze saka ki kulle qofa har ki hada da hannunta ki matse?" Audu ya fada cikin kaushi yana duban Zubaida dake durqushe gabansa kanta a Qasa Binta kuma na daga gefe tana yarfe hannu yatsanta data datse da qofa ya kumbura idanun nan sunyi fici fici da alamun tasha kuka ba kadan ba yau din. Audu na yin sallama Lantana da bata tafi ba ta zube a gabansa tana fada masa uwar dakin nata babu yanda take tana daki, hankali tashe ya doshi Dakota n nata can ya tarar da ita tayi zaman dirshan a qasa tana yarfe hannu tana kuka harda majina, shiri sukayi da Bintan akan hakan dukda dagaske take jin azabar ciwon yatsan amma tuggun da take so ta hada da faruwar hakan shi ya saka ta sake rakwarkwabewa ba iyakar zafin ciwon ba.

Daya tambayeta ya akayi taji ciwon take ta gaya masa Zubaida ce, akan ta bita daki su sulhunta kamar yanda ya roqeta jiya akan tayi haquri ta kwantar da hankalinta su zauna lafiya to bayan tafiyarsa tayi tunani akan hakan kuma taga ya kamata ace tayi shine yau taje dakinta da niyyar ta bata haquri akan abinda tayi mata jiya a maimakon ta saurareta se kawai ta hau zaginta tace ta fitar mata a daki, data tsaya ta dafa qofar shine ta hada harda hannuta ta datse shi kuma kamar fulawar da aka zubawa Yeast ya shiga kumbura ya tafi fuuu ya kira Zubaidan nan gaban Binta ya titsiyeta yana tambayarta ba'asin dalilin rufe qofa.

"Ni ba a sanina na bigeta ba kuskure ne" ta fada cikin sanyin murya, Binta ta zabura tace
"Wlh qarya takeyi tana sane ai Lantana na gurin ka tambayeta kaji"

"To a tambayi Lantanar mana in har zata fadi tsananinta da Allah ko ita ta san ba ina sane na bige miki hannu ba, sannan ni bani na nace ki shigar mun daki ba bare har ki saka hannunki qofa ta datse ki" Itama Zubaidan ta katseta

"Ke! A gaban nawa ma rashin kunya zaki mata? To bari kiji daga yau koda wasa karki sake kullemun qofa tunda dai gida nawane ba na wani ba, sannan dukanku matana ne babu wadda nayiwa shamaki daga shiga dakin wata a cikinku, yanzu kalli ciwon da kikaji mata ji yanda hannun ya kumbura fisabilillahi hakan da kikayi yayi kyau?" Audu fada yana zare mata ido, Zubaida sadda kai qasa saboda kukan dake shirin bada ita tace

"Amma dai tsakani da Allah ba haka ya kamata kayi ba, seka tambayeni abinda ya hadamu tunda dai kaji daga bangarenta"

"Ke zaki tsara mun abinda zanyi a cikin gidana? To banyi hakan ba nace banga damar yin hakan ba koda abinda zakiyi?" Ya hayayyaqo mata seta fashe da kuka saboda takaici tama rasa abinda zata kuma ce masa

"Tashi kije" ya???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? bata umarni yana wani dauke kai dan kukan nata ya tabashi amma shi a dole ta masa laifi shiyasa ya dauke kai. Cikin kuka guiwoyinta a sanyaye ta wuce dakinta. Zubaidan na fita itama Binta ta fashe masa da kuka tana cewa
"Yanzu shikenan ta jimun ciwo taci bulus iyakar abinda zaka ce mata kenan sannan saboda makirci ta fita tana kuka kamar ita aka zalunta?"

"To ya kike so nayi, so kike na rufeta da duka ko kuma na riqe hannunta ki rama abinda tayi miki? Ina kinji dai tace kuskurene?" Audun yayi kanta a fusace, yanda yayin yasa tayi shiru bata kuma cewa komai ba wato tuggunta be samu shiga ba so tayi ya rufe Zubaidan da fadan koma ya falla mata mari koya rufeta ma da duka amma dai ko banza hakan ma babu laifi tunda ya sakata kuka a gabanta da haka zata cigaba da nunawa Zubaidan ita din ba kowa bace a gurinsa Audu, kuma duk yanda ta dama haka za'a sha. Qarawa kukanta volum tayi babu ko dadin sauraro Audu yaja tsaki yace ta tashi suje gurin wani wanzami dake qasansu a duba hannun.

"Wlh ba zani ba idan ba zaka kaini Asibiti ba sedai na zauna da hannun haka kuma gobe karka saka ran zaka fito ka tarar dani a gidan nan Kaduna zan wuce" ta fada cikin kuka. Wannan tasa ya kaita Asibitin suka bata magu gunan rage radadi bayan an mata allurar kashe kwayoyin cuta sannan suka dawo gida lokacin goma harta gota, seda taci abinci tasha magani kafin ya wuce dakin Zubaida.

Tana zaune a falo ta kunna Tv amma hankalinta baya ga abinda ake nunawar tayi nisa cikin tunanin da tunda ta baro dakin Binta takeyinsa. Se taga kamar shari'ar ta Audu ba haka ya kamata ya gudanar da ita ba, tambayarta ya kamata yayi abinda ya hadata da Binta har wannan tsautsayin ya faru bawai ya dora mata laifin matsewa matarsa hannu haka nan ba kuma da yake maganar kowa tana iya shigar dakin yar uwarta babu shamaki a ina ake haka fusabilillahi?

Yanda ya shiga fuska a daure haka tayi masa sannu da zuwa jiki babu karsashi guiwoyinta suka sake sanyi da Al'amarin Audun, to fushin na menene kuma? Ba an gama magana ta wuce ba? Ya gama uzurirrikansa data bashi abinci yace ya qoshi, bata sake tsinkewa da lamarin ba seda ya juya mata baya da sukaje kwanciya a ranta tace lallai abin babbane.

"Kayi haquri in dai akan abinda ya faru jiya ne kake fushi wlh ba ina sane na matse mata hannu ba ita ta biyo ni tana zagina tace zata dokeni ni kuma tsoron haka yasa na shigo na tura qofar bansan ta saka hannunta a ciki ba" Zubaidan ta fada hawaye na saukar mata sanda Audu ke shirin fita da safe ba tareda ya ko kalli kayan karin data jera masa ba.

"Oh, bayan abinda kikayi shine kina da bakin sake magana harda sharri zaki mata a yaushe ta zageki harta biyoki zata dokeki?" Ya fada yana dakatawa daga fitar dayayi niyya. Hawaye suka balle mata na takaici, wato sharri tayi mata? Ita Bintan Allah kadai yasan abinda ta fada masa wato natane gaskiya se ita data fadi ainihin abinda ya faru shine zece ta mata sharri?

Muryarta na rawar kuka tace
"Akan me zan mata sharri? Sannan ai kaima zaka iya bada shaida akai dan ba shibe karo na farko data zageni ba ko tayi yunqurin dukana a gabanka ma anyi shekaran jiya ba kai ka kwaceni daga hannunta ba?" Ta fada tana tsare shi da ido. Yayi jummm alamar ya gasgata abinda ta fada din amma saboda qi fadi da rashin son gaskiya irin nasa se ya murje yace

"Rashin kunya zakiyi mun har kina tsareni da ido kamar wani sa'anki? To bari kiji muddin kina neman zaman lafiya a gidan nan dole ki zauna lafiya dani da kuma matata. Mu bamu saba fadace fadace da kuka iya har ana fidda jini ba a gidan nan dan haka ki san a inda kike" daga nan yasa kai ya fita ya barta tsaye kamar ya dasata tana juya kalamansa.

Ita da suwa suka saba fadace fadacen da zubar da jini?
"A bariki mana yake nufi" zuciyarta ta bata amsa, dabas ta zauna dafe da kunci hawaye suka shiga mata tsere, wato abinda yake nufi kenan, a fakaice yana gaya mata cewar nan ba irin gidan daya dakkota bane kenan da suka saba Fada kamar Kaji suna jiwa junansu rauni Yau Audu da kansa yae goranta mata wani al'amari daya shude a rayuwarta kenan.

Wannan abu yasa gaba daya jiki ta yayi sanyi, sararin data samu ta fara baje kolin sharholiyarta duk karsashin ya barta shima kuma be bi takanta ba yana ta tattalin Binta da hannu ya saka a gaba har ya saukar mata da zazzabi me zafin gaske seda ta kwana uku a kwance kullum kuma is Zubaidan ta shiga ta dubata safe da dare idan yana nan zata amsa cikin sakin fuska idan baya nan kuwa har Lantana samun damar yaba mata magana take suce mata mayya wai ta kama mata hannu to kurwarta kur. Ita Binta ko abinda take mata ma sam be dameta ba irin na Audun, qiri qiri yaba ganin gaskiya amma ya take yabi qarya shin wane irin mutum ne shi haka?

Ya za'ayi rayuwa ta yuwu a haka ace duk abinda aka gayawa mutum walau shine gaskiya walau qaryane se ya hau ya zauna kuma idan ya gano gaskiyar daga baya girkan kai da izza su hana shi karbar kuskurensa ai ko baze furta da baki ya karbi gyara ba se ya nuna hakan a aikace amma shi babu daya daga ciki da yakeyi sedai ya dora fushi wannan ai ba daidai bane. Data lura da gaske fushi yake da ita kuma bashi da alamar sakkowa dan har ranakun girkinta da suka zagayo bacci ke shigar dashi dakinta safiya nayi ze fice dole ta sauke nata fushin ta sake samunsa ranar ta tattara duk wata wayo da dabarar da take dasu ta wanke kanta a gurinsa ta hanyar karban laifin da bata aikata cikin sani ba ta kuma tabbatar masa da ba za'a sake ba har da kukanta tace kuma ya rakata a gabansa ta baiwa Bintan haquri sukaje ta bata haqurin ganin idonsa yasa Binta tace ta haqura ai ita komai ya dade da wucewa a gurinta daman wannan tasa ya sakko daga fushin da yake suka koma zamansu lafiya abinda yayi mugun batawa Binta rai.

A zaman tsamar da sukayi ba qaramin qara samun kan Audun tayi ba, a wayo da dabara take dada kwarkwarashi shi kuma dake kan keke ne ya hau daram ya zauna. Shiryawarsu da Zubaidan se ya zama silar warewar nata shirin musamman da taga kamar Zubaidan ta ganota duk irin tuggun data hada mata a gurin Audun ta dena musawa zata amsa laifinta ta durqusa har qasa ta bashi haquri tana hawayen munafunci a cewar Bintan shi kuma me son girma kansa ya sake fasuwa shikenan kome ta shirya ya wargaje.

Tun daga wannan kuma Zubaidan ta hankaltu duk laifin da Binta ta dora mata zata amsa ta bashi haquri tunda ta fahimci abinda yake so kenan babu ruwansa da jin ainihin magana yanda take hakan kuwa da takeyi ya sama musu zaman lafiya se a dade ba'aji kansu ba idan ba kuma Bintan ta shammaceta ta tunzuro shi ta yanda harta gaza kare kanta ba.

A haka aka kwashi watanni biyar da Auro Zubaida a kuma wannan yanayi ta fara laulayi wanda yazo mata da zafin gaske ga Amai ga Zazzabi lalurori dai iri iri ba qaramin Jiki take ji ba, wannan cikin ya sake gigita Binta, wato Zubaida zama tazoyi ma kenan tunda gashi har tayi ciki ita tana me haka ta faru yama za'ayi Mata suyita haihuwa a gidan Audu Bara'atu tayi biyu ita tana da daya kamar rai kuma a auro wata a bayanta tazo ta goga da ita wannan baze yuwu ba ta shiga takalar masifa kala kala fatanta Zubaida ta tanka mata ta samu dalilin lakada mata na jaki ta yanda cikin zebi rariya tun be gama samun gurin zama dakyau ba sedai bata samu hakan ba, Zubaida da ko a baya bata biye mata ba balle yanzun da take ta kanta.

Abin ya hadewa Binta biyu dan Audun shima yanzu duk ya maida hankali kan Zubaidan sosai wannan yasa ta kasa jurewa ta fiddo haukarta fili take baje musu ita watarana ya tanka mata wata rana kuma ya qyaleta a haka abinda ya sassuta lamarin ganewar da tayi itama tana da shigar ciki saboda batan wata da tayi amma tayi shiru bata gayawa Audu ba sannan kuma cikin Zubaida yayi watanni uku a lissafinsu na daga sanda ta fara laulayi kenan ita kuma nata yana wata daya.

Koda Zubaida sukaje Asibiti likita ya tambayeta yaushe rabon da tayi Al'ada ce masa tayi watanni uku, tayi lissafi da watan data fara laulayi dukda maganar gaskiya ba zata iya cewa ga lokacin da tayi al'ada ta qarshe ba tun zuwanta gidan sau daya tayi watanninbaya da suka biyo idan Al'adar tazo kwana daya ne kuma dan kadan ba kamar yanda ta sabayin kwanaki Bakwai ba kuma ba se qarshen wata ba ko yaushe tana iya ganinsa kuma ya dauke har ta fara zaton

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login