Showing 96001 words to 99000 words out of 467220 words

Chapter 33 - MATAR MUTUM COMPLETED 1-3 BY MARYAM FARUK.doc

23 Sep 2025

12197

yayiwa Zubaida da zamanta a gidansa zuwa yanzun data haihu be rage komai a ciki ba. Malam Hassan yayi shiru cikin tsantsar jimami kafin yace

"Tabbas nayi zargin wani abu ya faru saboda irin zaryar da dan uwanka ya ringayi a gidan nan kuma alamu na rashin gaskiya sun bayyana tattare dashi sedai na kyautata masa zato na cewar koma menene nasan baze cutar mun da Zubaida ba na saka a raina dai wata matsala ce qila da yake jin nauyin sanar dani. Hatta zuwan da zayya tayi ni na turata domin taje ta ga halin da suke ciki qila mu iya gano bakin zare sedai ya tabbatar mata da cewar ya tura Zubaidan can garinku, tabbas wannan maganar ta tayar mana da hankali hat shaidan yaso yayi wasa da zuciyata ya darsa mun zargin wani al'amari na daban amma na yaqe shi da qarfin addu'a ban kuma gusa ba kullum cikin yinta nakeyi ina roqon ubangiji da koma menene yake faruwa ya bayyana mana ya kuma sauqaqa mana.

Na godewa Allah da Jarabawar ta tsaya iyakar haka, na kuma gode maka da kayi mun wannan arziqin na riqe Zubaida a hannunka harta haihu ubangiji ya wanketa daga zargin da dan uwanka yakeyi mata na taje masa gida da Dan da ba nasa ba. Yanzu data haihu a hannunka ze iya tantance kamanceceniyar da take tsakaninsa da abinda aka samu kuma ya iya nutsuwa yayi lissafi na kwarai sabanin idan ana nan ta haihu tunda har ya rigada ya yarda da cewar Boka ko Malamin tsubbu na iya aikata komai la shakka yace itama kamannin dake tsakaninsa da abinda aka haifa qirqirarta akayi".

"Hakane Baba ina kuma qara baku haquri akan abinda ya faru In sha Allahu ma komai ze daidaita base har Zubaida ta dawo gida ba daga can gurina zata sake komawa dakinta da yardar Allah kuma abinda yasa nazo na sanar muku da abinda ake ciki saboda ku mahaifantane kuna da haqqi akanta be kamata kuma ace mun rufeku akan babban Al'amari irin wannan ba" Yakubu ya sake fada. Malam Hassan yayi murmushin daya fi kuka ciwo yace

"Kayya yaro dena wannan magana kuma ai zancen kome babu shi Aure ya qare sedai muyi fatan ubangiji ya musanyawa kowannensu da Mafi Alkhairi a gareshi. Kamar yanda rayuwar data faru a baya ta shude muka yarda da qaddara wannan ma mun dauka, rabon wadannan bayin Allah yayi sanadiyyar wannan Auran, tsakaninmu da Abdullahi kuma har abada babu abinda zamu ce masa sedai fatan Allah ya dubeshi ya saka masa da Alkhairi kwatankwacin wanda yayi mana. Maidomun da Zubaida gida da yayi ya isheni komai a duniya wlh kuma wannan al'amari daya faru baze goge tarin Alkhairinsa na baya a idona ba, wata Jarabaqar ce daga ubangiji kuma idan munyi haquri zamu cinyeta".

Yakubu be ja maganar da nisa ba yayi masa sallama bayan ya roqi Baba Zayya data shirya su tafi Asibiti tare ya kuma sake roqar Malam din da maganar ta zama sirri tsakaninsu. A hanya Baba Zayya ta samu bakin zazzage masa buhun bala'in da bata iyayi gaban Malam Hassan ba kai kace shine Audun, shidai be tanka mata ba domin sunada duk wata dama ta suyi fada dan an bata musu.


*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*

*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*S'

*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*


*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*

*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*

*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*

*Kutuntube mu ta wannan number =???08129249549*
*=???07011401314*

AUDU

Shirye shirye suke tayi saboda a daren ranar suke saka ran tashin su Binta. Gaba baya ta hargitse gidan ta hada faggon jakunkuna tamkar me zuwa yawon bude ido ba Ibadah ba. Addaba masa tayi akan seya qara mata kudi,

"Kaga fa a can nake so nayi siyayyar kayan haihuwar nan, dan abinda ka bani me naci a ciki me nayo tsaraba sannan duk ciki kake so nayi siyayyar kayan jaririn?" Binta ta fada tana matse fuska sanda yake jaddada mata sisi baze qara mata ba.

Kudade masu kauri ta karba a hannunsa, banda guzurinta ga wanda Babanta ya bata amma a haka take hanqoron se ta sake waftar wasu a hannunsa ya rasa bala'in son kudi irin na Binta kuma ba abin Mamaki bane taje ta dawo daga ita se jakar hannunta dan ya dade da gane Binta bata iya tsinanawa kanta ko waninta da komai a zamansu daga kan sutura zuwa wani abin amfani na gida sabo sedai idan shi ya siyo ko kuma aka mata daga gidansu amma a karan kanta batayi ya kan tuna Bara'atu zamansu duk Azumi zatayi yan kaye kaye ta fitar da tsoffin kayan amfaninta ta maida sababbi banda Bintan.

Data ishe shi da surutu shi kuma ya rantse sile baze qara mata ba se kawai ya shirya ya fita, Gidan Mai ya tafi, mamaki ya kamashi yanda yaransa suke ta yi masa barka da Arziqi Allah ya raya bayan sun gaisa haka ya shige ofishinsa ransa fal da mamakin barkar me ake masa.

Sallama Musbahu yayi ya bashi izinin shiga bakin nan nasa kamar ze taage saboda fara'a ya gaida Audun kana yace
"Yanzu naje na gano yan tagwaye, wlh Baba kamar kayi kaki ka ajiye, duk yaran gidan nan ni banga wanda ma yayi kama da kai kwabo da kwabo kamar su ba".

Kallon Musbahun ya ringayi kamar be fahimci abinda yake fadi ba, so yakeyi ya tambayeshi waya haihu amma kuma ya qiyin hakan a maimakon haka seya miqe yana cewa
"Muje na gano su"
Maganar tasa ta bawa Musbahu mamaki dukda daman yanda ya ganshi tamkar be san da zancen haihuwar ba ya bashi mamaki sannan ya sake shiga duhu akan lamarin, tabbas akwai abinda yake faruwa tun daga daukarsa da Baba Yakubu yayi sukaje can gidan Malam Hassan bayan nan sukaje Asibiti a can din yayi tsammanin tarar da Baba Audun ko matarsa amma yaga akasin haka Inna Balaraba ce kadai se Baba Zayya da suka tafi da ita tare.

Shidai bece komai ba har suka isa Asibitin wanda shi yake tuqi yana gaba Audu na biye dashi a baya har suka isa dakin da aka kwantar Zubaidan tana hutawa. Wani tsalle zuciyar Audu ta buga lokacin da idonsa yayi arba da jinjiri a hannun Baba Zayya tana jujjuyashi, idonsa fes akan yaron ya shiga cikin dakin sosai se ganin mutum sukayi sangangan akan su. Balaraba ta buga tsaki kamar zata tsinke harshenta kafin ta miqe tana cewa Baba Zayyan
"Bari na zagaya"
"Nima bari na biki nasha iska warin magani duk ya cika mun ciki" daga haka ta ajiye jaririn hannunta Musbahu yayi zuruf ya daukeshi suka fice suka barsu a dakin.

Idanu Zubaidan ta rufe tana qara gyarawa yaron data gama shayarwa kwanciya a jikinta, Audu na tsaye tamkar wanda aka sarewa guiwoyi ya kasa gaba ya kasa baya jinin jikinsa ya tsinke haka bugun zuciyarsa ya qaru kamar wanda yake kusa dashi ze iya sauraro. Musbahu ya ajiye yaron hannunsa bayan daya gaka jujjuyashi bakin nan yaqi rufuwa ya fita ganin kamar suna da buqatar sirri. Fitar Musbahun ta dan saukar masa da qwarin guiwa har ya qara taku biyu ya isa gaban gadon sosai yana kallonta tareda yaran da kunyarsu tayi masa lullubi.

Ko a rufa ido aka shafa fuskarsa aka shafa ta yaran an sana halitta dayace balle a kalle su ido biyu, bayan kamannin fuska qirar jiki da kammani na jini duk sun bayyana tattare dasu, ya kai hannu ze sauki wanda Musbahu ya ajiye a ba zata yaji ta daka masa tsawa tace

"Akul ka tabamun yara" ta fada har tana nuna shi da yatsa. Yanda tayi maganar cikin sauti me nuna bacin rai matuqa hakan kuma ya nuna a idanunta tilas ya janye hannunsa daga daukar yaron da ya bude ido yana kallonsa tamkar ya sanshi. A sanyaye kai a qasa tamkar ba Audu uban yan Izza ba ya matsa dab da ita cikin karyayyen sauti yace

"Kiyi haquri ki yafe mun, wlh sharrin shaidan ne".
"Babu wani shaidan face kai da Annamimiyar matarka, ni yanzu babu wani abu daya rage tsakanina dakai ubangiji ya gama mun komai daya wankeni daga zargin da kake neman laqabamun, ciki dai gashi na haifeshi watanni goma sha daya a gidanka cikin qudura ta ubangiji kuma ya bani Yaya masu kama da kai kaga duk iya sharrinku da kaida matarka baku isa ku barranta wadannan yayan da Ahalinku ba, fatana kar Allah yasa su gado mugun hali irin naka. Wlh nayi dana sanin Auranka Audu, da ace na san haka can cikin zuciyarka yake baqiqqirin da ban amince da kai ba.

Ka gwada mun hali me kyau, ka yaudareni da Kyakykyawar Dabi'a. Nayi tsammanin na samu Bangon da zan jingina, jigon da ze tallafi rayuwata ya gyarani ashe kai kayi shirin qarasa tarwatsa rayuwa tane. Rayuwata ta baya ta zama tariyi kai kuma ka niyyati shafamun baqin fentin daya fi na baya muni, shin bakayi tunanin halin da mahaifina ze shiga ba idan yaji wannan mummunan abun daka zargeni dashi?
Anya kai ko da zuciya a qirjinka Audu? Me yasa baka tunani da kwakwalwarka ka sakarwa zuciyarka Linzami?
To wlh ka farka tun kafin lokaci ya qure maka, wannan rayuwar da ka dauka ta rashin tunani babu inda zata kai ka illah Nadama da dana sani mara amfani.

Ita kuma matarka ka gaya mata tabi a sannu, ina tausayawa rayuwar da zatayi a gaba haqqi dabaibaye da ita. Se yanzu na fahimci yanda kuka taru kaka kassara rayuwar Bara'atu kuka laqa mata mata mugun qazafi to wlh haqqinta kadai ya isheku a duniya idan har baku nemi yafiyarta ba ina kuma fatan yanda Ubangiji ya wankeni itama ya wanketa ya bayyana gaskiyar duk wani mugun qulli da kukayi akanta" tana gama fadar haka ta gyara kwanciya ta jera yaranta a gabanta bayan ta bashi baya ta rufe ido zuciyarta na tafarfasa tsanar Audu me tsanani tana hudata.

Badan kar tayiwa Allah butulci ba da tace inama ya jinkirta bata wannan gwalalon kyauta a wani gidan inda yafi na Audu Alkhairi? Amma dukda haka ta godewa Allah ta sake gode masa bisa ni'imar da yayi mata.

Tamkar wanda lakarsa ta tsiyaye haka ya ringa jefa qafafu harya fice daga Asibitin, ya manta da Musbahu sukaje hakanan beyi tunanin mota ba ya ringa taka qafafunsa bude ido kawai yayi ya ganshi a qofar gidansa tundaga Asibitin Murtala, tafiya yayi wadda rabon da yayi irinta a qafa dai ze iya cewa tun Zamanin yana Audu qolo. Binta na zaune a tsakar gida da jama'arta da suka zo yi mata Sallama makwafta da kuma Turai da Mardiyya Wata sabuwar qawa da tayi babu dadewa.

Yanda Audun ya shigo ya saka duk matan binsa da kallo kamar ma be lura dasu ba haka ya tsallaka ta tsakaninsu ya wuce sama, Turai ta kalli Binta kafin tayi mata alama da ta bishi ta miqe tana murmushin yaqe ta sallami maqwaftan ya rage Turai da Mardiyya kafin ta haye sama gurin Audu.

Yana zaune akan kujera yayi irin zaman nan na balance ya bude qafafu da hannayensa kana kallonsa kasan da akwai abinda yake damunsa. Cikin salo da kissa ta bude firji ta dakko ruwan sanyi ta matsa gabansa ta tsiyaya masa tana cewa
"Lafiya dai ka shigo kamar baka cikin hayyacinka?"

Seda ya kwalwale ruwan ya miqa mata kofin kafin ya yunqura ya gyara zamansa yana kallonta dakyau yace
"Zubaida ta haihu"
"An ganta kenan, a ina? To mema ya shafemu da ita ko haihuwar ta? Halan gurin farkan nata ta je ta haihu acan ko?" Ta yi maganar tana yatsina fuska. Miqewa yayi ya nufi daki yana tafiya a hankali yace
"Ta haifi tagwaye duka maza, kamanninsu daya dani"

"Me kake nufi?" Ta miqe a zabure qirjinta na dukan dubu dubu kunnenta na mata amsa kuwwar Tagwaye Maza da ya fada, se ya waiwaya ya kalleta yace
"Karmu fara wannan maganar ma. Kin cuceni kin rabani da matata, waima meye dalilinki na sheganta mun Yaya Binta? Me yasa kikayi haka?"

"Ni na sheganta maka yaya? A yaushe akayi haka? Tsakaninka da Allah ni da kai mun taba magana nace maka cikin Zubaida shegene? Hasashena nayi na fada kai kuma tunda kasan da walakin goro a miya ka tabbatar haka ne to kuma se kazo kace na cuce ka dana maka me? Da kake wannan babatun ma me kake nufi ka karbi cikin kenan ko Yaya?"

"Ciki daman nawane" ya bata amsa yana shigewa ciki dan in ya tsaya din be san me zece mata ba. Gaskiya ta fada magana tayi me harshen damo shi kuma ya hau ya zauna daram wato ta tabbata ya zama wawa kamar yanda Yakubu ya fada Bintan ta karanci rashin tunani irin nasa shiyasa tayi amfani da wannan ta cusa masa tunani a kwakwalwarsa harta kaishi ga yanke danyan hukunci yanzu gashi tun ba'aje ko ina ba ya dawo yana dana sani mara amfani dan yasan ya rasa Zubaida ba zata sake yarda ta komo gidansa a matsayin matar aurensa ba.

Daren ranar Binta ta wuce Saudiyya cikin tashin hankali bayan sun rakaya dasu Turai sunje Asibiti sun ganewa idanunsu Tagwayen da akace Zubaidan ta haifa. Kuka wiwi ta ringayi kamar wadda kanta ya kwance wai ya za'ayi tazo a bayanta ta haifi tagwaye kuma Maza kenan yanzu ta fita kasafi cikin dukiyar Audu kenan. A Saudiyyan haka tayi Ibadar rabin Addu'arta ta Allah ya sa tayita haifar Yan biyu Maza ne bayiwa kanta wata kwakwkwarar Addu'a ba balle Yayan da take roqon a bata haka aka sauke Hajji ta dawo kamar yanda Audun yayi tunani daga ita se Kayan data tafi dasu yar tsarabar data yiwo bata kai kota kashi goma cikin uban kudin data tafi dasu ba.

Bayan dawowarta ta tarar da an kwashe kayan Zubaida wannan ya dan rangwanta mata damuqar data saka kanta a ciki. Daman daga Asibiti Zubaidan gidansu ta wuce kamar yanda Mahaifinta ya buqata Yakubu yayi iyakar roqon da ze iya amma Malam Hassan yace yayi haquri kawai. Ran Yakubun ya sake baci matuqa ya dauka Audun zeyi Nadama ya kuma nemi su sasanta ta koma dakinta amma seyaga akasin haka. Ya dai siyawa Jarirai kayan na Alfarma haka itama Maijegon ya hada da ita da Manya manyan Ragunan suna dana Qauri ranar kwana biyar da Yan Bechi suka zo wanda suma Yakubu ne yaje ya sanar dasu suka kai kayan Barkar.

Da aka kwana biyu har ya koma Ikko ya sake dawowa wata daya bayan haihuwar kenan ya sake tarar Audu da zancen ya suke ciki sun daidaita zata dawo idan ta yada wanka ko kuwa kai tsaye babu boye boye yace masa

"A gaskiya ni bazan iya zuwa nayi bikon wata mace ba, zan bata lokaci harta huce daga fushin da takeyi, idan ta nuna buqatar cigaba da zama a gidana se mu daidaita".

Yakubu ya rasa abin fada ya ringa kallon Audu kawai yana jin kamar ya rufeshi da duka. Ya dade yana ganin marasa hankalin mutane amma Audu leader ne, cikin tsantsar takaici yace

"Abinda ya hanaka ka maido da Bara'atu kenan tunda bata furta da bakinta tana so ta dawo ba ko?"

"Ka gane ashe, ai Allah ya kallo duk wani abu daya kamata ace nayi da ze nunawa Bara'atu ta dawo dakinta nayi. Kana kallo dawainiyar gidansu kaf har abinda be zama dole na ba yi musu nakeyi, duk wata se nayi mata aiken kudi da kayan abinci kuma idan naje Bechi ina zuwa naga Yaran to me kuma ya rage da zanyi ya nuna mata Biko nakeyi? Sena zubarda girmana na roqeta ta dawo bayan Alfarma zanyi mata naci gaba da zama da ita bayan laifin data aikata mun?

Itama Zubaidan ai koda ina da laifi nata yafi yawa a ciki, me yasa bata tsaya tayi mun bayani yanda zan fahimce ta ba amaimakon haka seta ringayin abubuwan da zasu qara tabbatar mun da zargina akanta ni kuma shine ya tunzurani na yanke hukunci. Kuma ai ita har haquri na bata da naje Asibiti tace babu ita babu ni kuma ta hanani taba Yayana shine kake so naje gidansu nace ta dawo salon ta samu damar rainani ko to ni bazan iya wannan aikin zubarda mutunchin ba" Audun ya fada cikin dagawa.

Mamaki, takaici hade da baqin ciki sukayiwa Yakubu rubdugu lokaci daya amma ya rasa kalmar da zeyi amfani da ita gurin zagin Audun dan haka ya kada kai kawai ya wuce ya barshi yana jinsa yana masa magana akan ya tsaya mana ina zashi be ko waiwaya ba. Duniya dai akace tafi bagaruwa iya jima, tabbas yana jiyewa dan uwansa randa muguwar Ta'adarsa zata bibiyi rayuwarsa.

https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG

*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*

*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login