Showing 207001 words to 210000 words out of 218311 words

Chapter 70 - AJIYA A DUHU BOOK 2 By Billyn Abdull.txt

suka faɗa masa addu'ar yayi. Dan daga shi har Oum ɗin ƴan ba ruwa na ne.
Haka kuwa suka shirya suka tafi, suka bar su Oum kuma anan Nigeria suna shirin fara gyara amare ita da Hajiya Shuwa. Sai dai ita Najma ma can wajen Ammie zata zauna nata gyaran. (Kun san dai itama Ammie tsohuwar mai gyaran jiki ce) Dan haka Hajiya Shuwa data haɗa duk abinda ake buƙata aka aikama Ammien, itama kuma daga can Ammien ta aiko musu da tata basirar da za'ama Ameerah da Maimoon da itama ta dawo nan Abujan amma a sashen Oum zata zauna dan ba'ayi abin kunya suruka Hajiya Shuwa tayi gyara ba..
Babban Yaya da Yaya Fawzan kuma sai suka maida hankali a gyaran sassan nasu. Amaren zasu zauna a downstairs kafin a gama musu nasu ginin. Amma duk da haka sai da aka gyara duka sashen biyu. Hakan yasa Nibras komawa sashen Oum da zama. Saheeba dama har yanzu tana a sashen Mamy. Duk da dai sunata zuba rikici ita da Mamyn, dan kota sakata abu yanzu batayi. Mamanta da itama ta tadama Mamy hankali tace Saheeba ta taho gida amma Saheeban tace babu inda zataje, dan Babban Yaya ya rantse mata indai ta fita a gidan ta fita kenan na har abada.
Hajiya Turai ce da ƙyar ta sasanta Mamy da Maman Saheeban. Ta kuma nuna musu illar bari kan nasu ya rabu. Acewarta a yanzu ne ma ya kamata kansu ya haɗu suyi yaƙi na gaske dan abaya wasan yara sukayi. Fargarwar tata ta shigesu, dan haka suka sasanta ɗin itama Saheeban mamanta ta ƙwaɓeta. Ita kuma ta bazama gidan bokaye da malamai neman sa'a...


_______★


Rayuwa a Dubai ta sati ɗaya kacal rayuwa ce mai tsayawa a zuciya da ɓargon jiki tsakanin Maanal da AA. Hakama Nuwaira da RK ba'a barsu a baya ba. Ƙara'in amarci akai sosai mai kuma ƙayatarwa. Sunyi wani fresh abinsu musamman Maanal data fara shiga wani yanayi na biyema fitinar AA. Shi kanshi har mamaki abin ya fara bashi. Tana shan wahalar amma tana nane da shi yanzu ba kamar da ba. Takai wani lokacin ma ita da kanta take takaloshi koda zatai masa rakin daga baya. Ranar dai suna hira shi da RK Maanal da Nuwaira kuwa sun fita kasuwa dan yau su AA ɗin sunce sun gaji sukam, sai AA ke ɗan yima RK tambaya akan hakan. Murmushi RK yayi dan shikam tun a Nigeria ya fahimci Maanal nada shigar ciki. Amma rashin tabbas ya sashi yin shiru tunda mata nada abubuwan ban mamaki a tattare da su.
Cikin nuna rashin tabbas RK ya ce, “Ciki zai iya saka mace hakan, dan wani lokacin idan suna da ƙaramin ciki sukan buƙacemu a kusa da su fiye da ko yaushe. Dan a farkon aure gaskiya mune zaka samu muna zalamarsu amma su ba sa jin daɗin yanayin gaba ɗaya wahala tafi yawa. Shiyyasa sukafi son a tsaya iya romancing kawai. Wata macen zata iya maka haihuwa uku sannan ta fara sanin muhimmancin yanayin. Wata ɗaya, wata biyu wata ma har biyar. Idan kuma ba'a haihu da wuri ba zakaga an ɗauki shekaru, bawai basa so bane gaba ɗaya, a'a badai kamar mu ba, doke zaka ga dai sai sunja shekarun nan sannan komai me daidaita musu. Sai dai idan suna shan ƙwayoyin saka ƙarfin sha'awa ne ko wannan kayan nasu na mata”
Cikin gamsuwa AA yake jinjina kansa. A ƙasan zuciyarsa kuwa wani irin farin ciki yake ji da fatan ALLAH ya tabbatar da hasashen RK ɗin na batun cikin ne bawai shan maganin Maanal keyi ba duk da dai bai taɓa gani ba. RK da duk ke lure da shi ya ce, “To amma fa kaima sai ka ɗan sassauta a irin wannan yanayin. Dan in har hasashenmu ya zama gaskiya cikin ne ALLAH zaka iya ɓaro shi. Ka aikata hakan kuma ba yafe maka zamuyi ba”.
Harararsa AA yayi, sai kuma ya ɗauke kai gefe da faɗin, “Shiyyasa bazan taɓa Kawu da kai ba dan kawun banza ne anan”.
Dariya RK ya shiga yi. Dole AA ɗin ya tayashi da murmushi.


★ Satinsu ɗaya suka dawo Nigeria, a kallo ɗaya kuma Oum ta tabbatar da hasashenta akan Maanal. Dan komai na jikinta ya ƙara canjawa a sati ɗayan nan. Sai wani mahaukacin ƙyau takeyi da haske. Sai murmushi ya kasa barin fuskar Oum, duk motsinta addu'a take na ALLAH ya tabbatar da hakan. Da ƙyar ta iya danne zuciyarta bata gumtsawa Abah ba........✍️










*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*


*09032345899*






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*
















*_💞AJIYA A DUHU....💞_*








*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*




*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._


*_My TikTok account 👇_*


https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1


*_Instagram👇🏻_*


https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv


*_Arewabooks_*


Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30


*_WhatsApp channel_*


https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R




_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


*_BOOK 2_*
🅿️➖1️⃣0️⃣2️⃣




______________




....Washe garin da suka dawo wasu cikin ƴan Kano suka iso Abuja. Dan za'a kai lefen Najma Zaria. Koda Maanal ta nuna zataje AA yace bai yarda ba. Dan tunda RK ya masa kanta farga yake wani kaffa-kaffa da al'amarin Maanal ɗin duk da ba tabbas. Koyaya yaga zatai wani aikin da zai jijjiga mata jiki yanzu zai amshe gara shi yayi. Tunma yana yi a su kaɗai harya kasa daurewa bai iya kawaicin hakan ko a gaban Oum. Ita ko Oum babu ruwanta, irin wannan abubuwan kawaicema yaran nata take tayi kamar bata gani ba. Dan farin ciki hakan ke bata akan kulawar da suke bama matan nasu.
Kamar wasa rigima ta kacame akan zuwa Zaria. Dan AA ya dage kuma ya ɓata rai a yanda Maanal ɗin bata taɓa gani ba. Ita kuma ta rigime akan sai taje sai masifa take masa kamar dama jiranshi take yi. Kuma tana masifar tana kuka. Takaici ya sashi yinƙurin baro mata sashen gaba ɗaya. Amma sai ta biyoshi yana gab da fita ta riƙeshi wai wlhy bazai fita ba.
Tsayawa yay yana kallonta, fuskarsa babu alamar wasa ya ce, “Sakeni”.
“Anƙi ɗin”.
Ya faɗa a fusace. Sai ma ya rasa mi kuma zai yi. Dan kallon ma abin yake a matsayin rainashi ta farayi ne ko mi bai san yazai fassara ba. A wani kuma gefe na zuciyarsa yana ƙara yarda lallai mata zuma ne ga zaƙi ga harbi. Duk yanda kake da su idan suka kuma maka wani takaicin sai kaga kamar basu taɓa ma saninka ba. Wannan yanayin dakan gitta lokaci zuwa lokaci shine iyaye kullum ke tisa mana kalmar haƙuri a kansa, sai anyi haƙuri da mata sai anyi haƙuri da mata. Idan ka fusata ka zafafa su kuma matan su kalleka a matsayin namiji ba ɗan goyo ba. Jiba fa ƴar ficiciyar yarinyar nan daya raina da hannunsa ce yau take neman birkita masa lissafi gaba ɗaya. Ƙiri da muzu yace baza'ai abu ba tace sai tayi. Yayi yunƙurin bar mata gidan yaje ya ɗan huce ta masa ɗaurin goro tana mazurai wai bazai fita ba kai kace itace Oum. Oh shi ɗan Aliyu da Fateema yau yaga takansa.
Kallonta ya sake yi, yanda take hura hanci wlhy saika ɗauka duka zata lakaɗa masa. Anya a duniyar nan akwai wanda yakai mata ƙarfin hali kuwa. Ka gansu abu ba abu ba amma fitinarsu da rikicinsu yafi na yaƙin basasa girma. Nan kuma anjima fa idan ta huce sai ta rungumeshi ta masa kiss ƙauna ruwa-ruwa. Nisa'u na rijalu kenan.....
“Ni ka daina kallona”.
Maanal ta faɗa tana fashewa da kuka. Ajiyar zuciya ya sauke, cikin daidaita nashi yanayin ya kama hannun nata ya jata suka koma cikin falon, zaunar da ita yay shima ya zauna. Idanunsa na binta da kallo mai tausasawa ya ce, “Na zauna yanzu mi kike so ayi?”.
Sai da ta share hawayenta sannan tace, “Ni ka barni naje”.
“Besty kima daina ɓatawa kanki rai da batun tafiyar nan dan bayinta za'ai dake ba. In da ace jirgi ne sai na barki, amma tafiyar mota daga nan Abuja har Zaria badani ba wlhy. Ban shirya asara ba gaskiya. Zaɓi dai wani abun”.
“Ni ba abinda nake so, Zaria kawai nake son zuwa. Da da nake tafiya a motar miya saman, sai yanzu zakace wani bazanje ba bayan kuma kowa zaije. A can Dubai wane irin yawo ne bamuyi a mota ba sai anan da yake kana jin mugunta..”
Wai yana jin mugunta abin dariya. Dannewa yay cikin lallashi ya ce, “Ki gane mana Besty, titin Nigeria dana Dubai ai ba ɗaya bane b.....”
Baima gama ba ta sake fashe masa da kuka tana faɗin, “Ni ban yarda ba! Ni ban yarda ba. Kawai sai naje! Sai naje”.
Shi kam yau AA yaga bala'i ai ganin idonsa. Wlhy ta birkice masa gaba ɗaya kamar ba Maanal ɗin ba. Sai kawai ya zuba mata ido ma yana kallon ta. To sai kuma sabon masifa, ita dan mi zaiyi banza da ita. Dan mi tana magana zai yi shiru. Ita bazata yarda ba, ita miye-miye.”
Da yaga abin bana ƙare bane sai ya fara tunanin hanyar da zai gudu. Can dabara ta faɗo masa. Sai yay ɗan gyaran murya yana miƙewa da faɗin, “Bari na kawo miki ruwa ki sha sai muyi magana naga yanda za'ai tafiyar ta yiwu, in ma ni zan kaiki sai na kaiki da kaina”.
Da farko riƙeshi tayi, sai kuma ta sake shi tana share hawaye ta ce, “Kuma mara sanyi nake so, ka haɗo da fresh milk mai sanyi ka saka min inibi da dabino a ciki”.
“An gama Aunty”.
Ya faɗa yana nufar hanyar kitchen. Haɗa mata duk abinda tace tana so yayi, ya buɗe back door ya gudu. A can compound ya samu su Naufal na ball da yaran maƙwafta, sai ya kirashi yace yabi ta back door ya ɗauka abu nan akan work table ya kaima Auntynsu falo tana jira. Shi kuma ya shige mota yabar gidan. Gara yaje ko zagaye gari yayi idan ta huce ya dawo.

🤣🤣AA bawan ALLAH yau Nisa'u sun nuna maka hali kenan😂? Maanal karfa kisa mu Aurama brozan su o'e Nuratu fa. Koda yake ki kiyayi ranar da suka Rijalu zasu murɗa nasu kambun rigimar tommm😂.


________★


A lokacin da AA ke fita anan ɓangaren Mamy ta fito wanka ne ta samu wayarta na ringing. Koda ta duba taga number ce kawai babu suna ajiyewa tai tana jan ƙaramin tsaki. Sai dai me kiran sai ya cigaba da shigowa babu ƙaƙƙautawa harta ji haushi ta ɗaga a fusace. Tana fara masifa Sille ya wani kwashe da dariya daga can. Sai tai tsai tana saurarensa zuciyarta na bugawa dan ta gane sa. A ranta tace ubanwa kuma ya bama wanan ɗan iskan number ta. A fili kam cikin ƙarfin hali ta ce, “Malam waye kai?”.
“Ai kin san waye ni Mrs Darma. Karki wani yi pretending. A tunaninki kin kashe waccan wayar kin tosheni ke nan. To ai abinda baki sani ba ni kamar kurege nake bana hanya ɗaya. Hanyoyine dani kashi-kashi harta inda bakiyi zaton zan fasa ba. Ina muka kwana ina muka tashi? Bake ba kuɗina mike faruwa?”.
Tsaki mai kauri Mamy taja. Cikin dakiya ta ce, “Kai bari kaji na fika iskanci wlhy, kai ubanwaye daka isa ka sani yin abinda banyi niyyar yi ba. Anƙi a baka kuɗin, kuma anƙi a yarda a ganka ɗin yi duk abinda kaga zakayi”.
Wata irin mahaukaciyar dariya Sille ya sanya daga can. Tare da faɗin, “Oh haka kikace? Shike nan zanko baki mamaki. Amma bisa wasu dalilai zan baki dama ta mintuna talatin yanzun nan kacal. Koki fito yanzu ki sameni a bayan gidanku da kuɗina 10m, ko kuma yanzu na nuna miki ni bana magana biyu, dan zaki ganni har cikin ɗakin barcin ki, sai ki fara ƙirga lokaci.....”
Ƙittt ya yake kiran. Ba ƙaramin bugawa zuciyar Mamy tayi ba. Tai shiru kamar mai nazari tsahon sakanni sai kuma ta taɓe baki da faɗin, “Ɗan iskan banza, su masu gadin dake gate ɗin wawayene irinka da zasu barka ka shigo har nan”. Hankali kwance ta shiga shafa manta. Kafin ta miƙe ta nufi closet ɗinta dan saka kaya. Harda su kallon agogo kuwa tana sake jan tsaki. Ta gama shirinta tsaff ta fito dan gidan wata tsohuwar aminiyarta take son zuwa. Da bala'in sauri tai baya zata fasa ihu jikinta na rawa saboda ganin mutum zaune a bakin gadonta.
Sille dake kallonta yay wata shegiyar dariya da faɗin, “Haba relax mana Mrs Darma. Sai kace bake ɗin ba.”
A rikice matuƙa Mamy ta nufi ƙofa, ta danna mata key sannan ta dawo inda yake. Bakinta har rawa yake ta ce, “Ubanwa ya shigo da kai har nan?”.
“A ƙafafuna mana. Ai na faɗa miki ni bana magana biyu kamar ubana nake.”
“Waye uban naka? Kai wanene ma kai? Mi kake so a wajena?”.
“Tofa irin wannan tambayoyi haka wacce zan amsa a ciki”. Sai kuma ya zame hular rigarsa data rufe masa fuska yana cigaba da faɗin, “Kalla fuskar baƙya buƙatar bayani”.
Kaɗan ya rage Mamy kuwa ta zube ƙasa tsabar razana. Junaid fa take gani, Junaid dai Junaid. Amma taya Junaid zai cigaba da zama a iya wannan shekarun har yanzu. Wannan fa bazai wuce talatin da tara ba haka. Dan zai girmi Fadeel gaskiya kamar da shekara biyu ma. Jiri ke neman ɗibarta ga numfashinta sai wani fisga yake da ƙyar. Shi dai Sille kallonta kawai yake. Sai da yaga kamar zata sume sannan ya miƙe zai kamata. Hannunsa ta bige tare da faɗin, “Karka taɓa ni”. Hannayensa ya ɗaga sama tare da ja baya ya koma ya zauna inda ya tashi, itama ta daddafa ta kai zaune cikin sofa, ruwan dake a saman table ta ɗauka tasha tana hakki ga idanunta sunyi jazur. Da ƙyar ta iya sake furta, “Wanene kai? Miya kawoka waje na?”.
Murmushi Sille yayi mai haɗe da dariya. Sai kuma ya taɓe baki da faɗin,.....✍️












*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*


*09032345899*






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*
















*_💞AJIYA A DUHU....💞_*








*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*




*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._


*_My TikTok account 👇_*


https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1


*_Instagram👇🏻_*


https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv


*_Arewabooks_*


Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30


*_WhatsApp channel_*


https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R




_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


*_BOOK 2_*
🅿️➖1️⃣0️⃣3️⃣




______________




.......“Zuwa yanzu ko baki san wanene ni ba kin san daga ina na fito. Kin kuma fahimci zan iya aikata komai idan baki min yanda nake so ba. Sunana Junaid ibn Junaid, kuma ɗan Kamila”.
Da wani irin razani Mamy ta kallesa yanzu ma har yawu na neman sarƙeta ta ce, “Wace Kamilar?”.
“Bayan ke akwai wata Kamila anan ne? Ki maida tunaninki baya, 39years da suka wuce, ranar lahadi ƙarfe sha ɗaya da arba'in na daren litinin, cikin kangon jikin makarantar allon Malam Bello ɗan Bichi dake bayan anguwarku. Budurwa ƴar kimanin shekaru goma sha bakwai, ana ruwan sama mai yawan gaske, ita kuma tana durƙushe tana naƙudar haihuwa data fara tun yammaci, fahimtar haihuwa zatai ya sata zuwa wannan kangon ta ɓuya, bata sha wata wahala ba ta haihu, tsabar taurin zuciya ta yanke cibin jinjirin da kanta sannan ta naɗeshi a zani ta koma gefe ta huta batare da ko kallonsa tayi a matsayin sa na wanda ya fito a jikinta ba, kafin ta tashi ta sake ɗaukar jaririn ta fita a cikin dai wannan ruwan ta tafi can bayan layinsu a ƙafa ko tsoro bata ji ta tona bola ta ajiye shi. Babu ko tausayi balle imani a tare da iya ta zuba tarin bolar nan a kansa ta rufe ta juya tabar wajen ranta ko gezau babu na nadama balle jin tausayi ta koma gidansu. A zatonta shike nan shike nan tayi AJIYA A DUHU na har abada, sai dai kuma shi ALLAH babu ruwansa, yayi alƙawarin saina more wannan duniyar, harna taka ƙasa nazo inda take da ƙafafuna a yau a yanzu..”
Tunda Sille ya fara wannan bayanin jikin Mamy ke mazari. Zufa kam ba'a magana tai mata sharkaf. So take tai magana amma ta kasa, dan gaba ɗaya lissafinta ya birkice... Sille dake kallonta ya wani kwashe da dariyar ƙeta yana miƙewa. “Bara na barki haka, dan na fahimci ƙwaƙwalwarki na buƙatar yin cikakken tunanin daya fi wannan bayanin nawa. Kuɗina kuma daga yanzu zuwa safiyar gobe ki tabbatar kin haɗa min su. Idan ba haka ba zan sake dawowa na amsa da kaina, idan na dawo kuma zan fara ganawa da Alhaji Aliyu Darma ne kafin ke. Dan ya kamata shima fa ya tuna da abokinsa na yarinta Junaid,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login