Showing 144001 words to 147000 words out of 218311 words
Chapter 49 - AJIYA A DUHU BOOK 2 By Billyn Abdull.txt
Zainab. Ƙasa ta zama kai koyi da Nana Faɗima. Ƙasa ta zama kai koyi da Nana Asiya, ƙasa ta zama mai koyi da ɗabi'un salihan mata bayin ALLAH duka da sauran matan MANZON ALLAH daban ambato ba da jaruman mata da sukai ma addini hidima tako wace fuskar alkairi. Ya rabbi kasa tai koyi da ƙyawawan halaye, haƙuri, juriya, jarumtar Oumna. Ya rabbi ka zama shaida, ita ɗin ta musamman ce a gareni, irin musamman ɗin da baki bazai iya ma furta wa ba.....”
Tsam-tsam Maanal ta sake rungumeshi hawaye na sauka mata. Fin minti uku suna faman sauke ajiyar zuciya sannan ya janyeta da ƙyar ya share mata hawayen ya gyara mata lulluɓin lifaya ɗin ya kama hannunta a jikin nashi yaja suka fice. A haka suka fito daga bedroom ɗin kamar makaho da ɗan jagora har cikin falon. Sai a lokacin Maanal ta fahimci basu kaɗai bane ba. Zaunar da ita yay sannan shima ya zauna kusa da ita. Cike da girmamawa yace ma Yaya Fawzan “Gata”.
Murmushi yaya Fawzan yayi mai faɗi, sai kuma ya kalla Maanal ɗin yace, “Lilly!”.
Jin muryar Yaya Fawzan yasa Maanal amsa masa da “Na'am Yaya F”.
“ALLAH yay miki albarka. ALLAH yay miki albarka! ALLAH yay miki albarka!. Nagode ma UBANGIJI daya kaimu wannan rana cike da lafiya da tsohon rai. Dan gaskiya dana mutu banga wannan ranar ba dole ne ma na dinga muku fatalwa banga ƙarshen movie ɗin ba”.
Murmushi su RK suka shiga yi, Yaya Fawzan ya cigaba da yiwa Maanal da AA nasiha da addu'a yanda ya kamata. Kafin su RK su amsa kowa yay tashi a taƙaice. Daga haka suka miƙe bayan RK yazo gaban AA ɗin ya ajiye wani haɗaɗɗen basket da akai ma wani irin ado da flowers a sama aka kuma rufesa da net. Shine da Nuwaira suka haɗashi, Sai kuɗi da suma akai ma wani irin nannaɗar ado a wata flower ɗin daban, daloli su kuma wai na sayen baki. Daga haka sukai sallama suka fice. AA ya ɗan rakosu wajen sashen. Sai Yaya Fawzan ya maidashi ciki yana faɗin, “Koma ciki mun yafe bama son rakiyar, dan nasan ma badan ALLAH zakayi ba Auta, maybe ma jikake kamar ka koromu waje kawai. Dariya sauran suka sanya sosai. RK ya matso saitin kunnen AA ya raɗa masa, “Adai bi min daughter a hankali yarinya ce dan ALLAH. Dan wannan fitinar dake cikin idanunka ma ta isa firgitata”.
Harararsa AA yayi, RK ya bar wajen yana dariya. Sai kawai yaji an riƙo masa hannu. Dariyar ya tsayar tare da juyowa. Ganin AA ne ya riƙosan ga wani irin kallo da yake masa sai shima ya zuba masa nasa idanun. Tsohon mintuna biyu suna kallon junan, su sauran da basu san mike faruwa ba sunyi gaba abinsu dan komawa sashen baƙi su samu su kwanta suma su huta, gobe kuma in sha ALLAHU Kano tai ɗiba.
Da wani irin hankali AA ya shiga jawo RK baya sannu-sannu harya dawo gabansa gab, cak ya tsayar da shi akan ƙafafunsa suna kallon juna cikin ido. Sai kuma kawai AA ya wani kalar jawo RK ya rungume. A tare suka sauke ajiyar zuciya mai nauyi, RK yay murmushi yana ɗagowa bayan ya ɗan bubbuga bayan sa. Magana AA ya buɗe baki zai yi, amma RK ya hana hakan ta hanyar yimasa zipping a baki yace, “Shiiii karkace komai, oya good night my son. Dan ALLAH karka ɓaro min aiki da safe kaga dai na gaji nima mamanka zan ɗauka mubar gidan nan ta ɗan min tausa”. Daga haka ya barsa anan tsaye. AA ya bisa da kallo harya ɓacema ganinsa, a hankali ya furta, “I love you Uncle. Kai ɗin na daban ne a gareni ƙololuwa”. Sai kuma ya ɗan murmusa tare da lumshe idanu ya buɗe a lokaci guda sannan ya murɗa ƙofar ya koma ciki, key ya sake murzawa daga cikin ya kulle........✍️
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*
*09032345899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_*
🅿️➖7️⃣1️⃣
______________
.........A inda suka barta anan ya sameta. Ya ɗan bi falon da kallo kafin ya cigaba da takawa a hankali inda take. Komai baice ba ya kama lafayan ya yaye, kaɗan ta ɗago ta kallesa ta maida idanun ta rissinar, ya ɗan zubama hannayenta data matse cikin juna ido, sai ya saki guntun murmushi. Duƙowa yay ya kama hannun nata ya miƙar da ita tsaye, ita dai taƙi yarda ta kallesa. Da wata irin murya mai laushi da komawa can cikin maƙoshi ya ce, “Bestie ki kalleni mana”.
Kanta ta girgiza masa alamar a'a. Cikin sake sauke muryar ƙasa sosai ya ce, “Why?”.
Da ƙyar ta iya motsa lips ɗinta, batare da sautin muryarta ya fita ba ta ce, “Ba komai”.
Kaɗan ya wani ɗan laɓe baki da jinjina kansa still yana kallonta. Sai kuma ya furta, “Okay, to ko zaki koma sashen Oum ne?”.
Ai baima gama rufe baki ba ta wani ɗago tana kallonsa. Da ƙyar ya iya gimtse dariyar data taho masa, dan tsoro sosai ya karanto a cikin idanunta. Duk ta koma sanyi-sanyi kamar ba ita ba, “Zaki je kenan?”. Ya faɗa yana riƙo haɓarta dan ƙoƙarin duƙar da kan take. A mamakinsa sai ta girgiza masa kai, idannunta a lumshe. Kafin yay magana ta cigaba da faɗin, “Akwai baƙi sashen Oum. Su Didi Amaal dai sun ce zasu zo su kwana nan suna sashen Oum”.
Nan ma dai sai da abun yaso bashi dariya. A zuciyarsa yace (Childish) a fili kam sai yace, “Okay! Ni kuma fa ina zan kwana?”.
Idannunta ta buɗe ta nuna masa stairs. Kallon wajen yay shima a ransa yace (Da sauki ma tunda za'a bani wajen kwana baza'a korani ba). A fili kam yace, “To ina godiya, yanzu dai kafin dawowar nasu muje ki tayani yin salla, kafin sannan suma sun shigo sai na rakoki ki dawo”.
Kallonsa ta ɗanyi, ganin yana son maidata wata ƙaramar yarinya. Wai ya manta ne takai 20+, tana da ilimin addini dana zamani, tama karance-karance. Tunda aka tsira bikin nan komai buɗe mata shi ake da sunan nasiha. Musamman Hajiya Shuwa sai abinda ta manta ne kawai bata faɗa mata ba a rayuwar aure...
“Miye kuma na tunanin?”.
AA ya faɗa cikin kunnenta. Ajiyar zuciya ta saki a hankali. Batare da ya sake cewa komai ba ya kama hannunta. Sai ta ƙi motsawa. Dawowa yay ya tsaya a gabanta, “Goyo kika so?”. Kai ta girgiza. “Ɗauka?”. Shiru tai dan saƙe-saƙen ta yanda zata zille masa kawai take a cikin zuciya. Shi ko sai ya ce, “Uhhmyimm”. Babbar rigarsa yasa hannu ya zare tare da hular damar duk sun gallebesa, ya dawo ta gabanta kawai, cak ya ɗagata daga ƙasa riƙe a hannunsa. Sai tai saurin kallonsa dan abun yazo mata a bazata. Ido ɗaya ya kashe mata, babu shiri ta kife fuskarta a ƙirjinsa tare da saka hannunta a kafaɗarsa ta dafe. Murmushi yayi kawai ya fara takawa a nutse kai kace ba mutum ya ɗauka ba. Haka ya dinga taka steps ɗin cike da ƙasaita har upstairs. Kai tsaye ɗakin dake matsayin nata ya kaita, duk da shi a ransa ya gama sakawa babu batun raba ɗaki, adai yi a gama kawai zai canja tsarin komai na gidansa. Sosai ɗakin yayi ƙyau, ga wani irin ƙamshin mai saka kasala na tashi a kowacce kusurwa. Wani irin shegen mayataccen royal bed ne aka saka, gashi an bisa da wata irin rumfa mai shegen ƙyau da idan ana sanyi ka shige ciki sai ka manta anayi. Shi kansa ɗakin yay masa ƙyau sosai. Saman gadon yaje ya ajiyeta, batare da yace komai ba ya juya ya fita. Ba'a wani rufa mintuna bakwai cikakku ba sai gashi ya dawo. Basket ɗin nan ne da kuɗin sayen baki a hannunsa. Ajiyesu yay a gabanta saman lallausan carpet ɗin gaban gadon mai kamar gashin mage gashi milk color sai ɗaukar ido yake. Idan ka taka kuwa ƙafarka nitsewa take a ciki.
Kusa da ita ya zauna, ya kamo hannayenta cikin nashi ya rumtse. “Barka da zuwa duniyata a karo na biyu Besty. Gidanki na miki marhababika da shigowarki bayan tsohon shekaru daya ɗauka yana jiranki, da kuma baki zo ɗin ba zai cigaba da jiranki na har abada dan bazai taɓa amsar kowacce mace ba sai ke kaɗai da aka gina domin ke. Yanda UBANGIJI ya nuna mana wannan rana, ina roƙonsa ya sa mu gammu a aljanna tare kamar haka. Maanal kece Ajwaad, idan babu ke shima babu shi har abada......”
Hawayen da take yi ne suka sauka akan hannunsa, ya ɗan zuba ma ruwan hawayen ido sai kuma yay ɗan murmushi tare da matsota jikinsa ya rungume. Bayanta ya shiga shafawa alamar lallashi. Kafin ya ɗagota ya share mata hawayen tas da faɗin, “Tom kuka ya ƙare haka, muje muyi alwala domin godiya ga ALLAH. Dare na ƙara yi kizo ki kwanta ki huta gajiyar biki okay”.
Kanta kawai ta jinjina masa tana sauke ajiyar zuciya. Shine ya miƙar da ita, ya kama hannunta, closet ɗin ɗakin babba shima suka fara shiga kafin toilet. Komai an tsara mata na kayanta abin dole ya birgeka, su Amaal sunyi ƙoƙari. Bayin ma ƙaton gaske ne, sannan ya haɗu da komai na bayi irin na zamani. Sai wani ƙanshi yake dan shima yaji turaren wuta. Da taimakonsa tai alwala, dan tace tana da tsarki, shima dai yana da shi ɗin, dan haka bayan ta kammala shima yayo suka fito. Anan closet ɗin ya ɗauka sallaya da hijjab da yaga an tsarasu suma a nasu ɓangaren sannan suka fito. Shi ya shimfiɗa musu sannan yazo ya gyara mata mayafin lafayar da ƙyau.
Sun gabatar da salla cikin nutsuwa, ya rufe musu da shafa'i da wutri. Sannan ya juyo ya dafa kanta yay addu'a da ya dace ango yayi, ya kuma sake cigaba da wasu addu'oin masu ratsa jiki da zuciya tsawon lokaci. Daga haka ya mata tambayoyi duk da yasan baida haufi a kanta tanan ɓangaren sam. Amma dai yayi ɗin dan yana son yasan a zuwa yanzu wane mataki take a neman ilimin. Yaji daɗi sosai jin bata zauna ba bayan rabuwarsu ma ta cigaba da neman ilimi. Dan haka ya tabbatar mata zasu cigaba da karatu a gida, zai kuma sakata wasu online class na addini suma dan ta ƙara samun sani da ɗammarar bautama UBANGIJI. Kanta a ƙasa tai masa godiya.
Hancinta ya ɗan ja kaɗan, ya ce, “Nima kike ma godiyar?”.
Murmushi tayi kaɗan, sai kuma a hankali ta ce, “Ka cancanci fiye da haka ma a gareni kai dukkan ahalinka. Tun ban san kaina ba kuke nuna min ƙauna. Ni da nawa a halin, kuna mana soyayya irin ta ƴan uwa na jini batare da kallon kun fimu da wani abun duniya ba tun ma a wancan lokaci. Abah ya zame ma iyayena Yaya, Oum ta zame musu aunty. Ku kuka zame mana yayu. Koda hararrarmu akai baƙwa ƙyalewa balle duka. Ku ɗin a garemu babban alkairi ne da baki yayi kaɗan ya furta. Bamu......”
“Shiiiiii!!!” AA ya faɗa a hankali yana ɗaura yatsarsa akan lips ɗinta. Idannunta ta ɗago a hankali ta kallesa, shima kallon nata yake cikin wani irin kasalllalen yanayi. Yanda suke kallon junan a tare tsigar jikinsu ke wani tashi, zukatansu na narkewa a ƙirazansu. AA ne ya fara janye nasa a hankali, batare da yace komai ba ya yunƙura ya miƙe. Sallayar ya ninke, ya ajiye. Saman carpet ɗin nan ya koma ya zauna a ƙasa, a nutse a kwance ɗaurin net ɗin nan da akama basket ɗin. Ya kwashe ledar da aka zuba flowers ɗin saman gaba ɗaya ya ajiye gefe. Kyakkyawar kwali ne ya bayyana, sai milk na kwali guda biyu, sai wani ɗan basket ƙarami da kayan fruits an naɗe samansu da leda suma. da aka zuba a sama gefe. Sai kwalin pizza da shawarma da sandwich suma kowanne an naɗesa daban. Sai wani kwali ɗan babba da bai san miye a ciki ba, da wata leda itama a gefe ƙarama. Juyawa yay ya ɗan kalla Maanal, ganin tana wajen zaune har yanzu ya ce, “Bestie zo kiga”.
Kallonsa ta ɗan yi, sai kuma yanda yay magana babu wasa yasa ta miƙe kamar wadda ƙwai ya fashema a ciki ta naɗe sallayar ta ajiye inda ya ajiye waccan sannan ta nufesa. Hannunta ya kama ya zaunar da ita kusa da shi. Kwalin farko ya fara buɗewa, kaza ce da akaima gashin ƴan gayu na musamman a ciki, sai gasashen naman rago a gefenta shima masha ALLAH. Ɗayan kwalin dabai buɗe ba ya buɗe, a mamakinsa sai yaga kaya ne a ciki na barci, nata da nashi duk da a naɗe suke, maidasu yay ya rufe kawai. Ya maida hankalinsa ga abinci yace wanne take so.
Kanta a ƙasa tace ita ta ƙoshi. Taci abinci ɗazun. Bai takura mata ba dan yaga yau an koma salihai, tashi yay ya fita, babu jimawa ya dawo da kofuna sai ƙaramin plate. Milk ɗin ya zuba a kofi ya miƙa mata. Kanta ta girgiza sai ya ɗan harareta. “Baki so nayi koyi da MANZON ALLAH ne.?”.
A hankali ta ce, “Ina so mana”.
“To bismillah”. Ya faɗa bayan yasha madaran itama ya saka mata kofin a baki. Hannunta ta ɗaura akan nashi tasha a haka. Bai kuma barta ba sai da ta shanye tass. Shi ko ya ɗan ci sandwich ɗin dan yana sonshi sosai, ya ƙara shan madarar ya haɗe komai waje guda ya fita dasu. Babu wani jimawa ya dawo ɗakin. Ganin tana lullumshe idanu ya ce, “Barci?”. Kanta ta jinjina masa. Ya ce, “Okay buɗe kwalin nan muga.”
Kwalin ta buɗe, ganin kaya a ciki sai ta kallesa. Kai ya jinjina mata alamar ta fiddo. Itama sai ta jinjina nata kan, a bisa tsautsayi tana ɗago na saman dake matsayin nata kawai rigar ta warware kanta. Ya subahannallah, ai Maanal bama tasan ta saki rigar ba, sai kuma ta juya da sauri ta kalla inda yake. Ganin yanda tai tsuru-tsuru yasa AA kauda kansa ya fuske kamar bai gani ba kafin ma ta juyo. Aiko sai ta wani sauke ajiyar zuciya, da sauri ta cikuykuye rigar da p ɗinta daya faɗo shima ta maida a kwalin. Miƙewa yay abinsa batare da yace mata komai ba ya nufi closet ɗin ɗakin, bai wani jima ba ya dawo hannunsa da wasu kayan barcin. A saman gadon ya ajiye mata, sannan yazo inda take ya ɗauke kwalin wancan kayan da ledan nan daya buɗe yaga magunguna ne a ciki.........✍️
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*
*09032345899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_*
🅿️➖7️⃣2️⃣
______________
.......Haɓarta ya kamo ya sumbaci lips ɗinya. “Ga wasu kayan nan ki tashi ki canja ki kwanta ki huta goodnight”. Ya sakimmata fuska ya wuce yana ɗan murmushi. Sai da taji ya fice gaba ɗaya ya rufe mata ƙofar sannan ta wani sauke ajiyar zuciya mai nauyin gaske kai kace irin wadda ta kuɓuta daga hannun dodon nan. Kayan daya ajiye ɗin ta juya ta kalla a karo na farko, nan ma sai ta sake sauke ajiyar zuciya ganin su kam na mutunci ne. Amma waccan gantalalliyar riga ai ba'a magana, duk wanda ya saye ta ma ba ƙaramin ƙwallon ɗan is... Bane. Ta jima tana saƙe-saƙen ta kafin ta miƙe ta kwashi kayan ta nufi bayi. Ƙara gyara jikinta tai sosai kamar yanda Hajiya Shuwa ta ɗorata a layi, sannan ta saka riga da wandon na barci masu taushi sosai gasu basu wani kamata ba, duk da dai wandon iyakarsa gwiwar ƙafarta yafi dama-dama akan waccan rigar.. sosai ta sakama jikin wasu turarurruka masu sirrin ƙamshi da Amaal ta sanar mata sun ajiye mata su anan cikin bayin, tana ko buɗe haɗaɗɗen drawer ɗin glass dake bayin da aka cika da kayan gyaran jikin Hajiya Shuwa da turarurruka na wanka da sabulai sai ta gansu. Suma ɗin dai kala-kala ne dama Hajiya Shuwa tace mata sai tana gida kawai ko zata kwanta sannan zata sakasu, haka ma sai in tana sashenta kawai. In har zata fita koda sashen Oum ne kada ta shafa. Ita bata fahimci ma'anarsu ba, ta ɗauka kawai tsarin sakasu kenan shiyyasa ta bajesu a jikinta yanda ya kamata, tsabar rawan kai irin na amare ma kowanne saida ta ɗan taɓa kuma kala-kala ne fin goma sha. Aiko ya arrahaman, bayin kansa yasan amarya tayi shirin barci....