Showing 114001 words to 117000 words out of 124668 words
Chapter 39 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
Koma waye aka bawa MT duk dai y’ay’an mu ne..
Kuma daman ni na dad’e da fahimtar Aslam d’in yake son bawa ko duba da d’umbin soyayyarshi a zuciyarsa da kuma tausayinshi…
Auwal ya rainaki amman still mu muka haifeshi!
Lokaci yayi da zaki fara nuna mishi dai dai duk d’acin ta da kuma akasin haka. Idan muka zuba ido a kansa especially yanzu da yaga Aslam ya dawo
Ina jiye mishi kar yaje yayi wani shirmen da za a kwace gaba d’aya shares d’insa a duk k’ananan company’s d’in sannan kuma a koreshi gaba d’aya! Kina gani dai irin tarin soyayyar da Granpa ke yiwa Abba! Na san duk da abunda ya shiga tsakaninsu har yanzu yanajin shi a rai amma ki duba kiga yadda ya rufe ido ya tsameshi a kan komai yanzu..
Tou har gara Abba dan yanzu shirin ma bud’e construction company suke yi shi da Aslam
Kisa a ranki Auwal aka yiwa abunda aka yi wa Abba
Shin wacce sana a kike tunanin zai yi??
Gashi girma ya zo mishi,
lokacin tara Iyali yayi.”
Shiruuu, Mom tayi ta nutsu ta bama Daddy dukkan hankalinta tana sauraronshi..
Ba k’aramin dad’i hakan yayi mishi ba kuwa, dan haka ya gyara zama yaci gaba da yi mata nuni da abinda ya dace da wanda bai dace ba da kuma yadda zasu had’u su gyara d’ansu tare da neman had’in kanta…
Sun dad’e suna tattaunawa ganin ta aminta da hakan ga kuma nadama k’arara a kan fuskarta dan har hak’uri ta bashi tare da alk’awarin yin amfani da shawarwarinshi..
Hakan yasa ya janyo ta yayi hugging d’inta zuciyarshi fes! Cike da farin ciki, ba abunda yake buri a yanzu sama da ya ga Auwal d’insa ya nutsu ya zama kamar su Aslam shima.
A haka ya jata suka kwanta yana mai karanto addu’o’in bacci ya shafe jikinsu dashi, yana d’an shafa gashin kanta
har bacci yayi awon gaba da shi.
Ganin da Mom tayi yayi bacci yasa ta share hawayen da suka zubo mata sannan ta mik’e ta zauna ta galla mishi wata uwar harara a ranta tace “Sakarai kawai!
Ana nuna maka Annabi kana runtse ido, ko su y’an uwan naka dakake ta tak’ama kana nuna y’ay’ansu nakane bari kaga ranar da za a bawa wani Mai Turare a nan zaka sha mamaki!
Infact shekaru ma suna ja nan zaka fahimci da mai shi ake yi!”.
Pillow taja ta saka a bayanta sannan ta kishing’ida a kan gadon dan ita bata ga ta bacc ba!
Ai kuwa bata yi minti talatin ba idea ta fad’o mata!
Murmushi kawai tayi sannan tace “Alhamdulillah”
Tana mai ayyanawa a ranta ‘Gobe! Zata je ta samu Maman Aslam ta sanar da ita Aslam ya dawo! Bayan ta san yadda tayi ko ta halin k’ak’a ne ta d’auki video d’in Aslam da Arshaad ko dai wani a cikin estate d’in ba tare da an farga ba, ta yadda Maman nasa zata fi yarda idan ta gani.’
Juyowa tayi tana kallon Daddy wanda yake ta baccinshi..
Murmushi tayi tace
“Yi baccinka Mijina! Auwal shi ke da Mai Turare, Bi‘izinillahi Ta ala.”
Auwal, shi kam yana chan abun duniya yayi mishi zafi!
Ya rasa ta Ina ma zai fara.
Wayarshi ya zaro ya hau online wai ko zai d’an samu ya rage zafi!
Sai dai yana hawa yaci karo da message d’in Jalila a sama sama da alamun yanzu ta turo..
Tsaki yayi ya jefar da wayar dan kwata kwata ya kasa fahimtar spelling d’in nata sannan ya gaza ganewa shin da Hausa tayi mishi magana ko da turanci!.
Shifa ya kasa fahimtar alak’arta da Arshaad kwata kwata!
Ya bugi cikinta shekaran jiya amman bai fahimci komai ba..
Ganin she’s not worth his time ya sanya kawai ya kawar da tunaninta gefe ya fara wanda ya san zai fishshe shi…..
Gandun Albasa !
Yau kwana uku kenan rabon Jalila da Auwal
Tun ranar da ya kirata a waya bata d’auka ba bai sake nemanta ba!
Umma tana ankare da ita
shiyasa da taga kamar basa waya kuma bataji tace mata zai zo ba ta tambayeta..
Jalila bata b’oyewa Umman komai ba, tace mata
“Tun ranar da suka je shopping da ya kirata bata d’auka ba har yau ba suyi magana ba.”
“Innalillahi wa innailaihirrajiun!!”
Shine abunda Umman tace tana dafe kanta.
Da sauri Jalila tace
“Umma mai ya faru??”
Cike da takaici tace mata
“Ke kika faru!
Mahaukaciya dak’ik’iya irin ki, banza kawai!.”
Tura baki tayi ta koma gefe tana gunaguni dan sai yanzu ta fahimci dalilin salatin nata
Cikin gunagunin nata tace
“Umma nayi mishi magana fa a watsapp bai ce min komai ba.”
Cikin tsananin b’acin rai Umman tace
“Wallahi ko nice ba zan kulaki ba!
Anya Yarinyar nan kin san ciwon kanki kuwa?”
Tsabar bak’in ciki Umma kasa ma ci gaba da yi mata magana tayi, dan haka kawai ta mik’e ta fice a d’akin ta zauna a tsakar gida.
Ganin yadda ran Umma ya b’aci sosai ne ya sanya kawai ta d’auki waya ta kirashi…
A na farkon bai d’auka ba
sai ana biyun!
Shiru, yayi bai ce komai ba!
Jin yayi shiru yasa tace
“Ina wuni”
“Lafiya” kawai yace mata.
A hankali tace
“Kwana biyu”.
“Umm”
Kawai ya sake cewa.
Jin tayi shiru yasa yace
“Kina da abun fad’a ne?”.
Taji zafin tambayar amman kawai ta daure tace
“A’a kawai dai na kira mu gaisa ne.”
“Hmm”
Kawai yace
daganan duk suka yi shiru.
Kamar ba zai ce wani abun ba
chaan! Kuma ya sauk’e ajiyar zuciya yace
“Shekaran jiya baki ga miscall d’ina ba??”
A hankali tace
“Na gani.”
“So?”
Yayi mata tambayar a gajarce.
Dabara ce ta fad’o mata dan haka tayi saurin cewa
“Bani da kati ne, sai yau Umma ta saka min.”
A hankali taji ya sauk’e ajiyar zuciya
“Na d’auka kyaliya ce ai, shiyasa daa har nayi fushi.”
Murmushi tayi sannan tace
“Kayi hak’uri”
Shima murmushin yayi daga nan yace
“Ina aiki, zamu yi magana anjima.”
“Allah ya taimaka”
tace mishi.
Daganan ya yanke kiran.
Bai sake kiran taba har
bayan kwana biyu…
Yau ma Ummance ta tusa ta a gaba sai da taga ta kirashi ya amsa a kira a hud’u! Tukunna ta fita daga d’akin.
Ya d’an sake yau ba kamar ranar ba…har d’an janta da hira ma ya dinga yi!
Amman wata maganar idan ya fad’a sai taji kamar k’asa ta tsage ta shige ciki…
Sai da suka kusan k’are wayar tukunna yace mata
“ta shirya gobe zai zo da safe
zata rakashi unguwa!
Tunda weekend ne.”
Sai da ya maimaita mata tukunna tace
“Allah ya kaimu”
Daganan sukayi sallama.
Sun gama wayar kenan Umma ta shigo.
Ganinta tayi zaune da waya a kunnenta amma kamar ba wayar take yi ba, da alamun tunani ta tafi…
Sunanta ta kira dan haka tayi firgigit! Ta juyo tana kallonta kafin ta sauk’e wayar daga kunnanta tana mai sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya.
A hankali Umman ta k’araso ta zauna a kusa da ita kafin ta dubeta tace
“Tunanin ne yau ma?”
Wata ajiyar zuciyar Jalila ta sauk’e kafin tace
“Wai cewa yayi zai zo in rakashi unguwa gobe!
Da safe.”
Murmushi Umma tayi sannan tace
“kice kar inci d’umame da abinci rana gobe, ke har ma na dare ba zan ci ba.”
Tana gama fad’in haka ta mik’e ta isa bakin wardrobe ta sunkuya ta d’auko ledar da su Huda suka kawo mata kwanaki ta zaro dandatsetsiyar riga tace “ungonan ajjiye ta a gefe ita zaki saka gobe.”
Cikin rashin jin dad’i Jalila tace
“Haba Umma!
Daga yace in zo ni kuma sai kawai in bishi zungui zungui?
Sati d’aya fa kenan yau d’in da had’uwa ta fa dashi.
Sannan, kin ga dai bai gaya min inda za muje ba ko?
Amman wallahi tunani na ya bani!
A yanayin maganarshi da hirarshi ta yau sarai na
fahimci inda ya dosa!
Saboda haka
gaskiya ni babu inda zan je!!”.
Tayi maganar tana had’e rai sannan ta gyara ta kwanta a kan gadon rigin gine.
Takowa inda take Umma tayi
bayan ta ajjiye rigar a kan kujera
Tana zuwa tace
“Kin san Allah Jalila Wallahi sai kin je!!”
A zabure da d’an mamaki a kan fuskarta ta mik’e ta zauna tana kallonta
“Kwarai kuwa!
Kin jini da kyau!
Cewa nayi wallahi sai kin je!
Idan ta kama in jaaa ki ne
To ina iyawa In fitar dake!Muddin ya zo gobe kika yi taurin kai. Tunda na lura so kike ki kasheni da raina
y’ar bak’in ciki
Yarinyar da bata san ciwon kanta ba!
Ana nuna mata Annabi tana runtse ido!.”
Tana gama fad’in haka ta juya ta fice fuuu kamar zata tashi sama.
Har dare Umma k’in kula Jalila tayi.
Washegari da safe ma k’in kulata tayi…
Ko tayi mata magana sai dai ta d’auke kai ta fara wak’a!
Sanin abunda ya had’asu fad’a da Umman nata ne ya sanya kawai ta mik’e ta shiga wanka ta fito ta tsantsara kwalliya ta sanya doguwar rigar da Umman ta zab’a mata jiya..
Tayi masifar yin kyau kuwa
kamar ka saceta ka gudu!
Tana cikin rolling Umman ta shigo, tana ganinta a shirye ta hau Fara’a! Sai a lokacin taga tayi murmushi tun jiya.
“Hmm” Kawai Jalilan tace
daganan ta koma kan kujerar d’akin inda ta ajjiye purse d’inta ta d’auka da wayarta tace
“Bara inje yana waje.”
“To d’an yi dariya mana Autata!
Haba mana..
Haka zaki fita kina fushi da ni?”.
Umma ta fad’a cikin sigar zolaya.
Murmushi kawai Jalilan ta iya yi daga haka ta sa kai ta fice daga d’akin......
A hargitse Anty Zainab ta shigo gidan sakamokon abunda Umman ta gaya mata a waya tana kuka…
Bata bi ta kan Hudan wadda ke sharar tsakar gidan ba ta shige ciki kamar zata hantsila, kai
kana ganinta ka san ba lafiya ba!
Tana shiga d’akin ta hango Umma zaune akan kujera tanata faman sharb’ar kuka!
Kamar jira take yi suna had’a ido da Anty Zainab ta sake sakin kukan da k’arfi.
Da sauri ta k’arasa inda take kafin tace “Haba mana Sadiya,
ba kuka za kiyi ba!
Tashi za kiyi a fara nemanta
In ta kama har gidansu shi Yaron sai aje.”
Cikin kuka Umma tace
“Ina na san gidan su Yaron?
Sai dai In Huda za a kira ta fad’i inda gidansu Arshaad d’in yake sai aje
Na san za a samu Jalila a wajen”
Gaba d’aya kan Huda d’aurewa yayi lokacin guda!
…Parker take nema a tsakar gidan bata samu ba
Chan ta hango wata a bakin k’ofar dakin Umman
dan haka ta k’arasa don ta d’auka!
Ba abunda kunnuwanta suka jiyo mata sai
“Inda gidansu Arshaad d’in yake sai aje
Na san za a samu Jalila a wajen.”
Da mugun sauri ta bar wajen kanta a d’aure..
Har ta kwashe sharar ta zubar ta wuce d’aki hankalinta sam baya jikinta…
A Chan d’aki kuwa cikin rashin fahimta Anty Zainab tace
“Arshaad dai saurayin Huda?”
Da sauri Umma tace “eh,
ai Yaron k’aninsa ne.”
Ajiyar zuciya Anty Zainab ta sauk’e kafin tace
“D’an gwada sake kiranta muji
ko zata d’auka!”
Cikin kuka Umma tace
“Tun shekaran jiya fa wayar a kashe!
Yau kuma da safe a kunne amman nayi mata miss call yafi dari biyu bata d’auka ba.”
A hankali Anty Zainab tace
“Tou ko Baba zamu gayawa?
Lamarin nan bafa lalle mu iya handling d’inshi mu kad’ai ba.”
Cikin firgici Umma tace
“Ki rufamin asiri Zainab!
Tun a jiyan ya fara sintirin nemanta..
Babban abunda yafi d’aga min hankali shine
‘Nace mishi yau zara dawo daga gidan Hansai!
Dan ce mishi nayi nan taje sai kuma aka yi rashin sa a Hansai d’in ba lafiya shine nace ta d’an zauna tunda Yaranta ita duk maza ne ba zasu iya jinya ba!’
Wallahi Zainab In kinga yadda mutumin nan yayi min fata fata d’azu da safe za ki sha mamaki
Kin sanshi a kan Jalila da Ja’afar..
To yanzu kafin ya fita kasuwa sai da yayimin gargad’in ‘In tafi gidan Hansai da kaina In d’auko mishi y’arsa idan ba hakaba na bari ya dawo babu Jalila a gidannan duk abunda yayi mini in kuka da kaina!’
Har kud’in mota ya bani
Yanzu gashi yamma tayi na san duk inda isha tayi ya dawo gidannan
Ta Ina zan fara?
Ya zan yi?
Ina zan ga Jalila ni Halimatu!!”.
Ta k’arashe maganar tana fashewa da kuka.
Da kyar Anty Zainab ta samu ta lallasheta.
Sun jima suna tattaunawa daga k’arshe suka yanke shawarar fad’awa kowa ba a san inda take ba!
Tasan su Kaka zasu san abun yi kuma in sha Allah za a ganta ba tare da asirinsu ya tonu ba!
Amman muddin suka tunkari su Ummu da Huda da zancen aka tambayi Arshaad to sai gaskiya ta fito
Sukuma ba zasu so a san asalin dalilin b’atan nata ba.
Umma tana kuka wiwi da majina suka nufi k’ofar fita daga d’akin dan zuwa wajen su Kaka.
Anty Zainab ce a gaba Umma a baya
Kicib’is!! Haka taja ta tsaya tana kallon Jalila wadda ta shigo yanzun nan..
Da sauri Umma ta ture Anty Zainab d’in tayi kan Jalilan ta hau duddubata kafin ta jawota jikinta ta rungume ta sa kuka
Ga mamakinsu sai sukaga Jalilan itama ta fashe da kuka!!
Shiruuu, Umman tayi ta hau lallashinta tana tambayarta amman tak’i kulata!
Nan suka jata suka kaita bakin gado suka zaunar da ita suka hau tambayarta suna lallashinta…
Bata ce dasu k’ala ba
in banda kukan da take yi kamar ranta zai fita!
Da kyar da sid’in goshi bayan kamar awa d’aya aka samu tayi shiru..
Bata ko kalli inda suke ba ta ja pillow ta kwanta ta juya musu baya
Tanaji Umma tana yi mata magana tayi banza da ita!
Ko minti biyar bata yi da kwanciyaba baccin wahala yayi gaba da ita…
Bata san lokacin da Anty Zainab ta tafi ba
Ta dai ji lokacin da Baba ya haska ta da tochila yana cewa
“Ya naga fuskarta duk a kumbure?”
Tanajin Umma tana yi mishi magana bata gama fahimtar zancen nata ba wani baccin ya sake kwasheta…..
Ba ita ta tashi ba sai washegari wajajen 10:00pm
Da Umma ta fara yin tozali dan haka tayi saurin kawar da fuskarta ta mik’e ta zauna.
Bata kalletaba ta sauk’o daga kan gadon ta duba wardrobe d’inta ta d’auka brush da makilin tayi hanyar waje
“Jalila zo nan!”
Taji muryar Umman.
Sai da ta juyo ta kalleta tukunnan ta d’auke kai ta fice daga d’akin, ta bar Umman nan zaune da baki a sake.
Umman ji take kamar ta bita har wajen sai kuma ta tuna ba su kad’ai bane a gidan dan haka ta hak’ura ta zauna tana zaman jiranta a d’akin!
Bata dawo d’akin ba sai da tayi wanka!
Tana shigowa, ko gama ajjiye kayan jikinta data fita da su waenda yanzun ta cire ta ruk’o a hannunta bata yi ba
Umma ta hau ta da fad’a!
kamar zata had’iyi harshenta
ta inda take shiga bata nan take fita ba..
Ko kallon inda take Jalilan bata yi ba…shirinta kawai take yi cikin nutsuwa..
Hakan kuwa ba k’aramin sake fusata Umman yayi ba
Dan haka ta fincikota cikin b’acin rai tace
“Wai aljanun rainin wayo kika je Auwal d’in ya saka miki?
Wacce sabuwar d’abi’a kika d’ebo ne?
Ya Ina yi miki magana tun jiya kin banzatar dani kamar ba uwar da ta tsugunna ta haifeki ba??”
Ta k’arashe maganar cikin d’aga murya.
Wasu zafafan hawayene suka zubo a kan kumatun Jalila!
Cikin tsananin d’acin zuciya tace
“Umma abunda nima nake ta so in tambayeki kenan
‘Anya kuwa kece uwar da kika haife ne?’
Kece uwar da kika reneni a jikinki?”
Bata damu da yadda kalamanta suka sake b’ata ran Umman ba taci gaba da magana “Umma da na nuna miki bana son alak’a ta da Auwal ya kamata ace kin fahimceni a matsayin ki na Mahaifiyata!
Ban tashi sanin na tafka babban kuskuren biyewa son zuciyarki da nayi ba sai shekaran jiya da kika kasa kwata ta kika kasa cetona!
Sai a lokacin na lura da yadda ni da ke muka taru muka jefe rayuwata a cikin tsanannin tashin hankali!”
Kuka mai k’arfi ne ya kwace mata, cikin kukan tace
“Umma yanzu wa kike tunanin zai aureni a haka?
Me kikaso In cewa Mijin da zan aura?
Bari kiji in gaya miki, Auwal har fyade sai da yayimin da na k’i in bashi had’in kai a farko!
Sannan yau ya ce mini ‘ko kiransa Idan nayi raina sai ya b’aci!’
A kan kawai ya tambayeni in fad’a mishi alak’a ta da Arshaad nace mishi ‘ba komai’
Kuma ya tabbatar mini da ba aurena zai yi ba!
Yace kawai ya fad’amin haka ne saboda In saki jiki da shi
sannan maganar auren da yace Arshaad zai yi
Wannan itama k’arya ce!.
Umma har ‘Akuya’ ya ce mini!
Yace bai tab’a ganin macen da aka yi winning d’inta a cikin sati daya tak ba
Sai ni.
A cikin sati d’aya kika tunzura ni na bi wanda ban sani ba kika jefa rayuwata cikin tashin hankali da rud’ani!
Duk ata dalilin
burin ki wanda na tabbatar yanzu bazai tab’a cika ba!.
Umma ni kinga rayuwata ta riga ta lalace ko?
To ki zuba ido ki gani!
Muna nan zaune a cikin gidan nan Arshaad zai zo a d’aura mishi aure da Huda ya d’auketa ya kaita gidanshi taji dad’i ta huta tayi rayuwarta cikin kwanciyar hankali!
Saboda ita Mama ta bata tarbiyyar data kamata, ta kama kanta ta kama mutuncin ta...........”
Mahaukacin marin da Umman ta d’auketa da shi ne ya sanyata had’iye ragowar maganganun ta!
A take ta durk’ushe a wajen ta fashe da wani matsanancin kuka…
Umma kanta bata san lokacin da hawayen tashin hankali suka zubo mata ba!
Kasa magana tayi kawai ta suri mayafinta tayi gida wajen Baaba Laraba.
Ita kanta Baaba Laraban ba k’aramin tashin hankali ta shiga ba daga jin labarin da Umman ta zo mata dashi..
Tabbas Yaron nan shak’iyi ne!
Amman ko d’an shed’an ne shi
wallahi sai ya dawo ya auri Jalila
Ko da kuwa ace za suyi yawo tsirarane!
Sanann sai sun raba Huda da Arshaad rabuwa ta har abada!!
Kamar mahaukata haka suka zama….a iya ranar kad’ai sai da suka je wajen mutane uku!!
Sannan suka hak’ura suka koma gida
Shima dan sunga dare yayi.
Haka nan duk a gajiye suka nufi gidajensu da niyyar fitar sassafe washegari idan Allah ya kaimu............
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
35
Washegari Kamar yadda Mom ta yi niyya…
Haka nan ta d’auki video d’in da ta shiryawa!
Ta saman balcony d’in d’akin Mammy ta d’auki video d’in Aslam da Arshaad lokacin suna shirin fita..
Ko ta kan Mammy wadda take ta faman tambayarta “me za tayi?” Bata bi ba, ta fice abunta