Showing 81001 words to 84000 words out of 124668 words

Chapter 28 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt

25 Sep 2025

2302

tsaurin ido!
Wata zuciyar ce ta hau tunzurata ta fad’awa Mammy halinda ake ciki, sai kuma ta tuna da Anty Adama, da kuma yadda shima Ya Arshaad d’in yayi shiru yana hoping a yi settling case d’in b4 Monday..kar taje ta had’a gurmi kuma azo case d’in ya mutu amman fad’a tsakanin iyayensu bai mutu ba….

Muryar Mammy ce ta dawo da ita daga wannan tunanin
jin tana cewa
“Auwal gaskiya tou akwai matsala tattare da Aaima, bafa jin ka takeyi ba, ke wai me yake damunki ne? Ina Arshaad d’in yake? Daga fitowa daga wajenshi duk kin yi sanyi haka sai tunani?
lafiya dai yake ko?
Umm bara dai inje In ganshi kawai.”
Mammy ta k’arshe maganar tana mik’ewa direct ta nufi hanyar side d’in Arshaad, ko Aaima wadda take ce mata “he’s fyn” bata tsaya sauraraba.

Mammy tana shigewa Auwal ya taso ya zo kan handle d’in 1 seater n da Aaima ta ke zaune a kai, ya zauna.
Yana zama tana mik’ewa da sauri ko bi ta kanshi bata yi ba ta wuce tayi hanyar sama…
Da sauri ya sha gabanta yana k’ok’arin kallon kwayar idanunta amman tak’i bashi had’in kai.

Hab’arta ya kama da k’arfi ya d’ago fuskarta har sai da tayi Kara kafin yace
“Ban son raini, wannan attitude d’in fa?”

Dukkan k’arfinta ta saka ta buge mishi hannu itama
sannan tace
“Out of my way, zan je d’aki, i have better things to do!!”

K’ura mata ido yayi na y’an mintuna chan taga ya fashe da dariya har da d’an rik’e ciki. Sai da ya d’an tsagaita sannan ya d’ago yana kallon hanyar side d’in Arshaad yana murmushi yana shafa lallausan sajenshi a hankali yace
“Arshaad! Arshaad!! hmm..”

Kafin ya juyo ya ce mata
“ya min spilling beans ko? Me yace?”

“Ban sani ba!”
Shine abunda Aaima tace sannan ta yunk’ura zata wuce…
Da k’arfi yasa hannu ya fisgota ta dawo gaban shi kafin yace
“bamu gama maganaba dan haka you are going nowhere, idan kina so ki tafi you better drop this attitude and talk!!”.
Ya k’arashe maganar yana mai had’e rai.

Mamaki kawai take yi yadda ya juye mata lokaci d’aya kamar ba Auwal d’inta mai lallab’ata ba.
Tabbas ta kusan tafka babban kuskure a rayuwar ta, Allah ya taimaketa data farga da wuri!
Kwallar da taji tana shirin zubo mata yasa ta ja vail d’in doguwar rigarta ta hau k’ok’arin sharewa.

Binta ya fara yi da kallo from head to toe… chaaan! Ya ja
akiyar zuciya ya sauk’e
sannan a hankali ya matso ya dafa kafaf’unta yace
“Baby this is all your fault…kiyi hak’uri to na fisgo ki kinji don’t cry, unhm?”

D’aga kai kawai tayi
ba tare da tace komai ba.

Ahankali ya saki wani killer smile sannan yace “yauwa dear.
To yanzu about that kiss”
Ya fad’a yana kallonta da murmushi a kan fuskarsa.”

Da sauri ta d’ago tana kallon shi, a zuciyarta taji tabbas it’s about time da ya kamata ta yiwa Auwal wankin babban bargo dan ta lura bayan mugayen halayenshi har da tab’un hankali ma yana damunshi.

Sai da tayi murmushi sannan tace “It’s clear abunda kake so daga wajena, Auwal ya kamata ka farka ka daina deceiving d’in kanka, dan ba sona kake yi ba wallahi!! Kuma abunda kake buk’ata daga wajeni ni Aaima ba da niba!
Mai zai hana ka tafi wajen y’an matan ka, i’m pretty sure za suyi maka wanda yafi wannan without any hasitation, and please kar ka sake shigowa gidan mu, tunda har zaka iya yiwa Ya Arshaad abunda kayi to i don’t think kayi deserving any love or kindness from his family, and yes Allah zai fitar dashi daga tuggun daka had’a mishi…
Ka sani mai gaskiya kullum shine a sama!!
Look at u, akan abun duniya
you have turned into a monster, baka da aikin daya wuce ka had’a wannan da wannan ka had’a wanchan da wanchan duk saboda kud’i!
Alhamdulillah! Mu ba wannan ne a gaban mu ba.
And one more thing Allah ya isa na deceiving d’ina daka dinga yi, i tot you love me truly ashe kai chan wani shirme ka kake tunani…
I’m like a sister to you, so ba zan ce maka na tsaneka ba but inaso ka ajjiye wannan at the back of your mind ‘ko ni da kai kad’ai muka rage a duniyar nan ba zan had’a ko wanne irin relationship da kai ba!’.”
Tana kaiwa nan ta watsa mishi harara sannan ta ce
“Humanizer irin ka.”

Da mamaki yaketa kallonta
tun lokacin data fara magana
tana dasa aya ya hau tafi!!
yayi kusan sau hud’u sannan yace
“What a great speech, Aaima.
Hope you are done saboda now it’s my turn.

Abu biyu kawai zan iya fad’a miki yanzu
First
You are right, bana sonki, you are not my type, sometimes idan muna zance ji nake kamar inyi kuka tsabar takaici, kawai daurewa nake yi, ke to be sincere ni ko irin soyayyar y’an uwan takan nan ma bana yi miki!!
Dan haka don’t even think of wai kinyi rejecting d’ina ne Aaima i never loved u you day one….kuma kin da wayo fa for that i salute u sannan Allah ya taimakeki da kika gano gaskiyar lamari, and Yayanki shima yayi playing role wajen ceton rayuwarki because i was planning in yi using naki ne sannan nai dumping saboda Ina so in koyawa Yayanki hankali akan takura min d’in da yake yi.
Abu na biyu
Kinga ba sonki nake yi ba ko? But abunda Arshaad yayi min ya min ciwo, so ga sak’o inaso ki bashi from me to him, yadda ya rabani dake to kar ya bari in had’u da girl d’insa.”
Yana gama fad’an haka ya juya fuuu, ya fice kamar zai tashi sama.

Aaima a wajen ta tsugunna ta fashe da kuka, so kawai all this time yana kallontane as a fool?!
Sai kuma ta fara maimaita ‘Alhamdulillah’ da Allah ya tseratar da ita.
Gabanta ne ya fad’i da ta tuna da abunda ya gama fad’a a kan Huda yanzun, a hankali tace “Allah yasa kar ya yiwa Huda komai.”
Tana gama fad’in haka ta mik’e tana goge hawayenta wanda hakan yayi dai dai da fitowar Mammy daga side d’in Arshaad.

Salati Mammyn ta saka sannan ta k’araso wajen Aaima ta rik’eta tana
“Me yake damunki? wani abun ne ya had’a ki fad’a da Auwal d’in? Mai ya faru???”
Murmushi kawai Aaiima tayi kafin tace
“ba komai Mammy abune fa ya fad’a mini cikin ido.”

Cikata Mammy tayi sannan tace “ke wallahi zan ci Uban ku! Daga ke har Arshaad d’in
shima tun d’azu nake ta fama dashi akan ya fad’a min damuwarsa sai k’arya ba komai yake min kuma kina ganinshi kin san yanada matsala!
Sannan kema yanzu kin ce min ba komai, kunada wata uwar da ta fini ne??”

Share hawaye Aaima tayi tace “Mammy ba komai fa, dan Allah kiyi hak’uri, zan je in kwanta kaina ke ciwo.”

“Ba fa inda zaki je sai kin gaya min matsalarki yanzun nan!”
Mammyn ta fad’a tana sake rik’o Aaima wadda take k’ok’arin wucewa.

Ahankali Aaima tace
“Tou shikenan Mammy i promise zan fad’a miki, amman sai gobe da safe plss Dan Allah yanzu kaina ke ciwo.”
Cika ta kawai Mammy tayi tace
“Allah ya kaimu.”
Da alama ranta ya baci dan fuuu ta juya ta nufi nasu hanyar staircase d’in.

Sai da Aaima taga shigewarta sannan itama ta kama hanya tayi sama….
Dank’areren parlournta ta wuce ta shige bedroom wanda shima girman sa ya kusan parlour d’in, a hankali ta k’arasa k’ofar toilet ta kama handle dinner ta bud’e, sannan ta shiga…had’add’en band’akin ne mai d’auke da different wajen wanka har uku, shower
normal bathtub da wani makeken jacuzzi sai wani had’add’en closet da aka warewa waje shima daban kana hangowa ta toilet d’in.
Wayar ta kawai ta ajjiye a kan doguwar drawer gaban k’aton mirror d’in dake cikin toilet d’in sannan ta nufi bathtub ta fad’a ko bathroom slippers d’in dake a k’afarta bata cireba…
Ajiyar zuciya ta sauk’e sannan ta sakarwa kanta showern saman bathtub d’in.
Ta dad’e a haka jin mura har ya kama ta yasa ta mik’e ta fito tana d’igar ruwa, da kyar ta iya cire kayan jikinta ta d’aura towel ta fad’a gado, tana yin addua ko minti goma ba’ayi ba baccin takaici yayi awon gaba da ita.......


Washegari tana fitowa zata yi breakfast a main parlour Mammy ta hau tambayarta.

Gaba d’aya ta rasa ya zata yi mata, suna a haka sai ga Arshaad shima ya fito nan ta had’a su tayi ta tambaya..
Aaima ce tace
“Mammy bafa wani abun bane ba, kinga shi Yaya wani d’an fad’a suka yi da budurwarshi, shiyasa kika ganshi a haka kuma k’awata ce, shine nima ya had’a dani ya min fad’a wai ai laifi nane.”

Da sauri Mammy tace
“Wacece wannan d’in? a ina take?”

“Huda”
Shine abunda Arshaad yace yana mai k’ok’arin b’alle cuff links d’inshi sannan ya k’araso yazo ya kama hannunta yayi kissing kafin yace
“Good morning Mammy”

“Morning, wait Arshaad Hudan dai wannan d’ayar Yarinyar da Aaima ta tab’a bani labarin an kaisu school d’insu a scholarship har tana yi musu lesson??”

“Yep”
Shine abunda Arshaad yace yana mai k’arasawa dining table yana cewa Aaima
“hurry kin san zamu fita Ina so mu k’arasa b4 12 dan zan je kd a yau.”

“Ok”
Aaima tace, itama tana k’arasowa dining dan yin break fast d’in.

Da sauri Mammy ta k’araso tace “Arshaad wai me yake damunka? Ka san dai ba zan tab’a bari ka auro mini Yarinyar nan ba ko??
Ke kuma Aaima munafuka ai kin san da zancen amma shine baki tab’a gaya min ba!! To bari in gaya maka!! Ka san senator Bashir ai ko? To akwai dota d’inshi takwara tace tun kuna Yara idan zaka tuna Mamanta da sirikina take kiranka, ni a tunani na you are not ready for marriage shiyasa ban fara maganar ba ashe kai kana chan ka lik’ewa y’ar da ubanta ba kowan kowa ba!! Har da wani rashin lafiya jiya a kanta saboda kun yi fad’a!! Tou wallahi ka fita a idona in ba haka ba ranka zaiyi mugun b’aci dan ba zan had’a iri da talakawa ba wallahi!!!.”

Murmushi Arshaad yayi sannan ya ajjiye spoon d’in ya mike yace “Mammy Hudan is not poor, ok?
She’s is very rich! Kawai dai ban san dalilin da ya sanya iyayenta suka zab’i ta tafi a scholarship ba.
Please Mammy dan Allah kar muyi haka dake mana! I luv her a lot so dan Allah kar problems su fara rising daga wajenki plsss.
In kikai min auren dole da wanchan Yarinyar da kike magana akai tabbas zaku samu matsala ne dake da friend d’in taki, saboda I cant take care of her daughter tunda ba son ta nake yi ba!.

I need your support a kan Hudan please Mammy dan Allah.”

Kallonshi ta tsaya tana yi hakan yasa ya sakar mata murmushi yace “thanks, you are the best!!”
Bai jira jin mai zata ce ba ya fice yana cewa Aaima “ta sameshi a mota da wuri!”.

Da ido Mammy ta bisa har ya fice! Kwafa tayi sannan ta juyo kan Aaima….
Aaima tana ganin haka ta mik’e da gudu tayi hanyar sama tana cewa “Mammy bara in shirya In je kar Ya Arshaad yayi fad’a yace na shanyashi.”
Bata wani dad’e ba ta sauk’o,
ta d’auro abaya da vail akan English wears d’in jikinta..
Nan ma da gudu ta fita tana cewa “kinga Mammy Yaya har ya fara jera min misscalls, bara in je in na dawo zamu yi magana.”

Sarai Mammy ta fahimci dodging d’inta Aaima take yi saboda bata son tayi mata maganar.

Ta so tsayar da ita amman kafin ma ta lek’a tuni har an bud’e musu gate sun fice........


BULAMA ✍️




So da Buri
Free Book
26


Abun duniya duk ya bi ya taru ya ishi Mammy..
Hakan yasa ta mik’e, hijab d’inta kawai ta d’auka ta nufi gidan Mom.

Tana shiga kuwa kamar had’in baki ta tarar da Ummi itama a falon.
Sai da ta nemi waje ta zauna suka d’an gaisa tukunna tace
“Alhamdulillah! Da na sameki a nan.”

Murmushi Ummi tayi kafin tace
“Me kuma ya faru yanzu?”

Ajiyar zuciya Mammy ta sauk’e sannan tace “Aaima da Arshaad ne! Wai ace Yaran nan har sun san su had’e mini kai suna k’usk’us a tsakanin su?”
Sai a lokacin tukunna Mom tayi magana, tace “Haba Mammy, ai abin farin cikine ma ace y’ay’anka sun had’e kai, kinga bakida matsala kenan dan babu mai iya shiga tsakaninsu!”

Murmushin takaici Mammy tayi kafin tace “Na san da wannan Adama, amman abunda nake so ki gane shine ‘da ace abun kirki suke k’ullawa to da sai nafi kowa farin ciki !’.

Kin tab’a jin labarin wasu Yara da Aaima take gaya min Arshaad d’in ya kai ya had’ata da su?”

Shiruu, su Mom d’in suka yi kamar masu k’ok’arin tuna wani abun kafin chaan! Mom
tace “‘Sakina’ kamar naji tace ko? Waenda take cewa d’ayar Yarinyar tana kama da Aslam.”

“Allah yayi miki albarka Adama, su dai. To wai d’ayar fa yake so, shine suketa k’us k’us d’insu.
Jiya Arshaad d’in inaga har kuka yayi wai ko tak’i d’aukar wayarshi ko fad’a sukaa yi, Oho musu dai.”

Ummi ce tace “amman Yaron nan anyi ja’iri! Yanzu ya za muyi da maganar Khadija?? Kin san ko jiya sai da na had’u da Mahaifiyarta a wajen gyaran farce…
Tanata tambaya ta ya sirikinta
harma take gaya min next week khadijan zata dawo ta kammala masters d’inta.”

“Banda Arshaad ma dai da abinshi, da class d’insa da komai amma shine zai je ya d’auko mana wachchar?? Daman wallahi ni jikina sai da ya bani.
A yanayin labarin Aaima kamar fa har provision shi yake yi mata lokacin da suke makaranta.”
Cewar mom

Da sauri Mammy tace
“Kinji ko! D’azun nan kuma ya gama cemin ‘ai she’s very rich waye waye kawai dai iyayenta sunyi choosing ta tafi a scholarship ne waye waye’.”

Murmushi Mom tayi tace
“k’arya yake yi!
Aaima ai ta tab’a bawa Auwal Labari, tace Yaran ko ishashshen turanci basu iya ba, ita ta dinga yi musu lesson lokacin tana chan…da zata tafi ma sai da ta had’asu da wasu.
Waenna Yara da suka samu good foundation a makarantar kirki ne za a ce basu iya turanci ba saboda Allah??
Kawai dai k’ok’arin watsa mana k’asa a ido yake yi.”

Mammy kamar zata yi kuka tace “Ni ba wannan ne problem d’ina ba, dan bai auri Khadijah ba (ya watsamin k’asa a ido) shi ya sani!! Ni babban bak’in ciki na kar ya d’auko min Yarinyar da bata waye ba! Bana son had’a jini da su kwata kwata, zuciyata zata iya bugawa!
Kuma yadda yake son Yarinyar nan, in dai ya aure ta to shikenan ni da shi sai dai kallo daga nesa! Dan na san janyeshi zata yi gaba d’aya, gata kuma y’ar matsiyata na san ta dinga sakawa yana yiwa iyayenta abubuwa kenan, a gindinsu kud’insa zasu k’are!”.

Murmushi Ummi tayi sannan ta dafa kafad’arta kafin tace
“Ki kwantar da hankalinki, Granpa fa ba zai tab’a yarda da wannan had’in ba, kin san yadda yake.”

“Um um fa! Granpa d’innan ba a gane mishi alk’ibla, kar mu dogara dashi yaje ya watsa mana k’asa a ido, mu dai nemo wani solution d’in gaskiya, dan wallahi koni naji bana son Yarinyar tun kafin a je ko’ina, kuma daga gani yana sonta over ma kuwa! Kina ji fa wai jiya har da kuka , k’ato dashi.”
Cewar Mom.

Ummi ce tace “na san ba a ganewa Granpa alk’ibla amman dai kin san ya fiki k’in son had’a jini da talakawa ko? Ki tuna Aisha fa.”

Mom ce ta katseta ta hanyar cewa “Ai bamu gama confirming ya yanayin gidan su Yarinyar yake ba!
In aka yi rashin sa’a kuma ta fito daga middle class kinga ai an gama magana, dan Granpa ba lalle ya hana ba.
Kawai mu bama son Yarinyar ne, in ya aure ta akwai matsala
kar ya manta da mu da uwar shi, and ke kinfi kowa sanin ulterior motive d’inmu akan aurenshi da Khadija, ko?”

Shiru Ummi tayi sannnan tace “hakane kam gaskiya, to anjima ki sa Auwal ya bugi cikin Aaima mana, na san ba zata san lokacin da zata fad’a mishi komai ba.”

“Bama magana da shi, amman zuwa anjima d’in ke ki kirashi ki tamabayeshi maybe zai yi.”

“Me ya had’aku, har ba kwa magana?“
Ummi ta tambayeta da mamaki akan fuskarta.

Murmushi Mom tayi sannan tace “ba komai, ki manta kawai wani issue ne daban”
Tana maganar tana satan kallon Mammy…
Ita kam Mammy gaba d’aya hankalinta baya kansu, ta tsunduma duniyar tunani….kawai zooming take yi
‘gashi har anyi auren Hudan da Arshaad, Hudan tasa Arshaad ya daina kulata, ita kuma sai bauta yake yi mata daga ita sai iyayenta! Yana ta kula da ita ‘Hudan’ baya son ganin b’acin ranta
Ita kuma ‘Mammy’ an ajjiyeta a gefe.

Sai da Ummi ta d’an tab’a ta tukunna ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi.
Fahimtar yadda duk ta gigice da suka yi ne yasa sukaita k’ok’arin kwantar mata da hankali tare da alk’awarin zasu saka Auwal ya bugi cikin Aaima, daga nan sai su san abun yi.

Da kyar dai suka samu Mammyn ta d’an kwantar da hankalinta.


Da yamma kuwa, Auwal yana dawowa daman Ummi tayi mishi message ‘tana son ganinsa’, hakan yasa wanka kawai yayi ya nufi gidan…

Bayan sun gaisa ne take gaya masa dalilin kiran
“So suke yi ya bugi cikin Aaima..akwai wata Yarinya budurwar Arshaad da suka fahimci yana mugun so har Mammy yake yiwa jainja a kan Yarinyar, bayan already anyi maganarshi da Khadija!
Therefore, suna son sanin gidansu da yanayin Yarinyar, daga nan sai su san abunyi.”

Murmushi kawai Auwal yayi bayan ya gama ji, sannan ya mik’e tare da yi mata alk’awarin ‘in shaa Allah zai binciko musu!’.
Daga haka yayi mata sallama ya fita a gidan ranshi fess!!!

Yana komawa b’angaren su direct d’aki ya wuce ya d’au waya ya kira main driver na estate d’in na yanzu,
dayake daman shima duk bakin su d’aya
Micheal!
Cikin girmamawa, Micheal ya gaishe da Auwal, nan Auwal ya zayyano mishi abunda yake so yayi mishi sannan ya kashe wayar, yana wani killer smile.
A ranshi yake tunanin abunda zai yiwa Arshaad….tunda dai gashi an tabbatar mishi yana mugun son Yarinyar!
Su Ummi kuma ko sun sake yi mishi maganar kawai zai ce musu ya manta ne dan bayaso su shigo case d’in ba tare da ya gama abunda ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login