Showing 102001 words to 105000 words out of 124668 words
Chapter 35 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
never get better, domin kuwa duk wani therapy medication treatment duk sunyi amman duk a banza!’.
I don’t know why you choose to come back now, saboda home is not a fit place for you anymore!
Anyways,
it’s gonna be fun dan zan dawo ma gidanku ne da zama saboda in dinga watching dram.....”
Naushi kawai yaji Arshaad ya d’auke shi da shi yana huci!!!
Ya daga hannu zai k’ara mishi wani Aslam wanda idanuwanshi suka koma kamar garwashin wuta yayi saurin ruk’o shi..
K’ok’arin fisgewa Arshaad d’in ya fara yi, da k’arfi Aslam ya daka mishi tsawa yace
“Mu shige ciki’”
Juyowa Arshaad d’in yayi zai yi mishi magana amman sai
ganin yanayin da yake ciki yasa kawai ya juya zai shiga yaji an ruk’o shi, ya riga ya san Auwal ne shiyasa ya juyo a fusace amman bai gama juyowan ba ya rama naushin da yayi mishi sannan yace
“This should be the last time da zaka yi punching nawa, if not kaga ta wanchan gidan!?”yayi magana yana nuna gidan su Arshaad d’in kafin yace
“Wallahi a kanta zan rama, ko ban rama da hannu na ba zan saka ayi mata and it might not end well!
So be very careful.”
Yana gama fad’in haka, ya juya ya shiga motar shi ya ja
Aslam kuma ya ja hannun Arshaad suka shige cikin gidan.
Direct side d’inshi suka wuce ba wanda yace ‘k’ala’ asalima Arshaad d’in d’aki ya shige ya bar Aslam a nan kwance a parlour kan 3 seater, dan ko had’a ido da shi baya son yayi sakamokon tausayinshi da kuma haushi da suka hadu mishi guri guda! Abun Auwal kullum k’ara gaba yake yi ya rasa dalili…
Shi kuwa Auwal
Sai da ya koma gida ya chanja kaya dan waennan duk sun yi squeezing!
Tukunna ya saka turare ya zira wayoyinshi a aljihu ya fito ya fice daga estate d’in.
Kamar yadda suka tsara..motar mike tana gaba tashi tana baya, suna zuwa unguwar gandun albasa layin su Huda, mik’e din ya fito daga tashi motar ya nuna mishi gidan daga d’an nesa…
Sallamar sa Auwal yayi sannan yace mishi “zai iya tafiya”
Shi kuma ya tada motarshi ya k’arasa k’ofar gidan.
Da mamaki yake ta kallon gidan!
A take kuma sai yayi murmushi yana rayawa a ranshi ‘winning d’in Yarinyar da entire family d’inta will be an easy job ta hanyar kud’i tunda ya lura basu da shi!’.
Yaron da yazo wucewa ya d’an yafito alamar ‘yazo’.
Yaron yana zuwa ya d’auko 1k a wallet d’inshi ya bashi kafin yace “ya shiga gidannan yace wai Jalila ta zo inji Arshaad.”
Da gudu Yaron yayi cikin gidan bayan ya karb’i kud’in.
Yana shiga ya tarar da Umma tana wanke wanke!
K’arasawa yayi inda take ya gaisheta sannan yace
“wai ana kiran Jalila a waje inji Arshaad!”
Umma da kamar bata ji ba tace “me kace?”
Sake maimaita mata yayi, aikuwa da sauri tasa hannu ta toshe bakinshi gudun kar Mama ta jiyo.
Kallan k’ofar d’akin Maman tayi sai kuma ta juyo…k’asa k’asa tace
“kaje kace gata nan zxuwa yanzu.”
Sannan ta mik’e har tana tuntub’e ta nufi d’akinta har da d’an gudun ta!.
Tana isa ta tarar da Jalila ta bararraje akan gado tanata uban bacci!
Duka ta tak’ark’are ta maka mata..
Aikuwa da ihu Jalilan ta tashi.
Da sauri ta sa hannun ta toshe mata baki kafin ta jijjagata tace “Watstsake dan uban ki!!
Ki tashi ki je ki wanke fuskar ki yanzun nan! Ga Arshaad chan a waje yana jiranki.”
Jin an anbaci sunan ‘Arshaad’ yasa ta bud’e idanuwa da sauri sai kuma ta mik’e tayi waje.
A bakin rijiya ta wanke idanunta da bakinta, kafin ta dawo cikin d’akin, tuni har Umma ta fitar mata da kayan da zata saka da powder da jan baki da turarurruka kala kala da takalmi, duk a cikin kayan da su Huda suka kawo mata.
Tana zuwa ko minti biyar ba tayi ba ta shirya. Har zata fita Umma ta sake janyota ta mik’a mata janbakin tace “ta k’ara bai yi ba, sannan ta sake fesheta da turarurruka har suna tari!
Tukunna tace “ta je!” Har da binta har tsakar gida
ta karantto ta tofa mata alhamdu k’afa d’aya!
Daga nan ta dawo d’akin ta hau tattare inda suka zuzzubar da kayan da ta cire tana cewa
“Yau gashi da kanshi yace Jalila yake son gani! Maryam sai naga ta inda zaki nunamin d’agawa yanzu ai!!
Shima Arshaad d’in shegen Yaro! Wato ya gama da Huda shine yanzu ya dawo kan Jalila! Ai kuwa baai san inda ya zo ba, dan nan kam idan mutum ya shigo to baya fita!.
Na san yau kam har kakan had’a ido sai kun yi! Magana ta k’are! Kuka na ya zo k’arshe daga yau in sha Allah.”
Ranta fes! haka ta tattare d’akin ta fito domin k’arasa wanke wanken ta.
Jalila tana fita ta hango wata dandatsetsiyar mota a parke! Murmushi tayi sannan ta k’arasa inda motar take ta kwankwasa marfin…
Sai da ya d’an jima yana k’are mata kallo ta cikin tinted glass d’in…a ranshi yace “not bad tana da kyau! Amman bata yi yellow d’in da mike yake ta faman zuzutawa ba!”.
A hankali ya d’an zuge glass d’in iya idanuwanshi suka fito sannan yace “zagayo ki shigo mana.”
Jalila ba wani sanin Arshaad tayi sosai ba tunda duk ganin ta dashi ta lek’e ne
amman dukda haka taso ta gane ba shi bane ba daga yanayin muryar da idanun!
Jin hucin sanyi da yake tab’ota da wani azababben k’amshin turaren da yake fesowa ta cikin motar da kuma kwad’ayi shiga taga ya yanayin motar take ta ciki yasa kawai ta zagaya ta bud’e ta shiga ta zauna.
Tana juyowa kuwa suka yi ido biyu wanda ko da ace bata san shi sosai ba ta san wannan ba Arshaad bane ba, hakan yasa a d’an tsorace tace
“Waye kai?
Kace sunan ka Arshaad!”.
Murmushi yayi, sannan yace,
“Relax ni k’anin shi ne.”
Ajiyar zuciya ta d’an sauk’e sannan tace
“Aiko ka yayi?”
Girgiza kai yayi sannan yace “ni na aiko kaina.”
Bai jira jin me zata ce ba
dan yadda take kallon motar da yanayinta tun farkon fitowarta ya gano zata yi saurin shiga hannu! Musamman idan an yi amfani da kud’i.
A hankali yace
“Listen Jalila, ni mutum ne mai magana d’aya kuma idan zan yi abu kai tsaye zan yishi babu b’oye b’oye!
Farko farkon zuwan Arshaad ya tab’a zuwa dani sau d’aya amman ban fito ba a mota na tsaya thats when i saw u and since that day i have feelings for you!
Kawai daurewa nake yi saboda babu yadda zan yi..
Har satar wayar Arshaad nake yi in yi sending pics ba tare da ya sani ba
So something happened last week i don’t know if you are aware, ko kuma ya b’oye miki..
An zab’a mishi matar da zai aura a gida har an kai kud’i
Na san maybe baki sani ba dan naji yana cewa Mammy “he is going to hide it from you till after d wedding, honestly i don’t know wat he is planning on doing with you.
Ni dai aurene ya kawo ni wajenki, kuma mu a family d’inmu idan Namiji yayi aure sai yayi 20 years ya zama stable sosai tukunna za a barshi ya sake yin wani auren
Are u ready to wait for him for 20 years??”
Yayi mata tambayar yana kafeta da idanuwa…
Matsowa yayi kusa da ita, ya kama hannayenta sannan yace “Ba zan taba yaudarar ki ba nikam, just trust me, zan so ki tsakani na da Allah and a shekarar nan in sha Allah za muyi aure!”
Ahankali yaji tace
“Tam.” Sannan ta sunkuyar da kanta k’asa.
Murmushi yayi amman chan k’asan zuciyarsa yana mamakin saurin amincewarta haka..
Cikin son k’ara gasgatar da wani abu taji yace
“But promise me, ba zaki gayawa Arshaad muna tare ba, saboda abun zai iya zama case, and na san definately sai ya rabamu, bayan shi yana chan da tashi amaryar!
Nafi so sai ranar da aka d’aura aurenshi, da kamar 1 week tukunna ya sani, muma kinga kafin nan an fara maganar namu auren ko?”
A hankali ta d’aga mishi kai, alamun amincewa.
D’an murmushi yayi kawai ya sake rik’e hannunta…..a haka ya d’an dinga janta da hira yana nan rike da hannunta gam yana d’an matsawa lokaci zuwa lokaci.
Sama sama take amsa mishi iya wanda ta fahimta dan rabi da turanci yake magana kuma slanz,
Gaba d’aya ta k’agu yace zai tafi dan yadda ya matso gab da ita da yadda ya rik’e mata hannu kwata kwata she‘s not comfortable!
Sun yi kusan 1 hour a motar tukunna ya mik’o mata wayarshi yace “ta saka mishi numberta!”
Shiruu, tayi chaan! Tace “zan kiraka idan na saka layin a wayar Umma anjima, kai ka bani numberka.”
Shiru yayi yana d’an kallonta kafin yace
“Baki da waya?”
A hankali ta d’aga mishi kai.
Da mamaki ya d’an kalle ta yace “Taya kuke waya to? Ko bakwa yi kwata kwata?”
Girgiza kai tayi alamar ‘a’a’ kafin tace
“Ai ina saka layi na a wayar Umma lokaci zuwa lokaci.”
D’aya daga cikin wayoyinshi ya zaro….wadda bai dad’e da fara anfani da ita ba!
Gf d’inshi ce ta bashi ranar birthday d’inshi.
Bincika wayar yayi
sai da ya tabbatar bashi da wani abu important a ciki kafin ya cire sim d’in shi ya mik’a mata wayar sannan yace
“Idan kin shiga sai ki saka layin naki a nan.”
Kallonshi tayi sai kuma ta kalli wayar kafin ta sa hannu ta karb’a…
D’an zuba mata ido yayi alamun jiran godiyarta yake yi
amman sai yaga ita murmurshima take ta yi tanata dudduba wayar tana juyawa
Ganin dayayi batama da shirin yi mishi godiya ne yasa kawai ya share
ya zaro card d’inshi ya bata yace “ta kirashi ga number shi”
Kafin ya sake zaro y’an bandir d’in 5hndred ya mik’a mata yace gashi “ta saka kati!”
This time around ko d’an jinkirin da tayi first time na karb’ar waya ma bata yi ba
da saurinta ta sa hannu ta karb’a tana murmushi.
Shi kam kasa daurewa yayi hakan yasa ya ce mata
“Ba ko y’ar godiyar nan?”
Kunya ta d’an ji sai kuma ta sunkuyar da kanta k’asa kafin tace
“Na gode.”
Murmushi yayi ya d’an kalli agogon hannunshi kafin yace
“Bara in wuce sai naji kiranki ko?”.
D’aga kai tayi ta juyo ta kalleshi tana murmushi.
Shima murmushin ya mayar mata sannan ya d’an yi waving nata yace “bye” kafin yad’an matso ya bud’e mata marfin motar..
Sai taji kamar kuma kar ta fita
saboda bata son barin sanyi.
A hankali tasa k’afarta ta fita sannan ta d’an juyo tace mishi “sai anjima.”
Har zata fara tafiya taji yace
“Remember, don’t talk to him about me yet!”
“To” kawai tace kafin ta juya ta wuce cikin gida.
Binta yayi da kallo yana mamakin ‘me Arshaad yake planning akan Yarinyar nan?
Da farko da yaga gidan ya d’auka maybe ko saboda kyau ne!
Da kuma ya ganta, thou se is beautiful but not to the extend da zaace a guy like Arshaad yayi laying down level d’inshi yazo nan ba
Sai ya fara tunanin may be nutsuwa da hankalinta da tarbiyya ne ya jawo hankalinshi gareta!
But in less than 1 hour ya fahimci kwata kwata Yarinyar bata da nutsuwa da kalan tarbiyyan da ya kamata ace Arshaad ya sota!.
So wat is he up to?
Saboda ya san ko giyar wake yasha ba zai tab’a tuntub’ar Granpa a kan auren Yarinyar nan ba!
Sai dai idan ko yayi secret marriage ko ya siya musu gida b4 the wedding
Ko kuma ma kwata kwata ba aure ne ya kawoshi wajenta ba!
Dan ya lura Yarinyar in dai za a bata kud’i to da alama zata yi komai ma!
A ranshi kuma sai ya ce
“But ai Arshaad is not a humanizer”
Wata zuciyar ce tace mishi
“Kai dai kawai kaga mutum ka kyaleshi, baka san
me yake aikatawa behind closed doors ba!”.’
Murmushi yayi kafin yace
“Koma dai menene, na san cewa its important to Arshaad!
Ni kuma nayi alk’awarin sai na lalata komai in sha Allah.
But Yarinyar nan anya kuwa zan iya tolerating d’inta ko dai kawai mu dinga waya ina turo mata kud’i dan gaskiya she is not my type!
Amman kuma anya zata yarda da ni yadda nake buk’ata?
Ba tare da ina zuwa muna had’uwa ba kuwa?......”
Da waennan tunane tunanen ya ja motarshi yayi gaba....
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
31
Cike da farin ciki Jalila wadda take ji kamar an tsundumata a Aljannah ta shiga cikin gida!
A tsakar gidan ta tadda Umma da alama ita take jira..
Ko k’arasowa Jalilan bata yi ba Umma ta hango wayar hannunta da kud’in!
Tana zuwa ta bud’e baki zata yi magana kenan Umman ta rufe bakin, ta jata d’aki.
Har da rufe k’ofa bayan sun shiga wai duk dan kar a jiyo su!
Abunda bata sani ba ‘su Sakinan su kam ba ma sa cikin gidan’ dan tun safe Khadija ta kira su tace “dan Allah su zo ita da Huda su taya ta zab’ar kayan da zata yi amfani dasu da bikin nata.”
Suna shiga d’akin k’asa k’asa
Umma tace “Ya kuka yi da shi?baki yayi??”
Tayi maganar tana kallon hannun Jalilan kafin ta sa hannu ta karb’i wayar ta hau jujjuyawa.
Ajiyar zuciya Jalila ta sauk’e sannan ta jefar da mayafinta a kan gado ta nemi guri kan kujera ta zauna kafin tace
“Ba Arshaad bane ba! Wai k’aninsa ne, sunanshi Auwal!”.
Da mamaki Umma take kallonta kafin tace
“Ikon Allah, me ya ce miki tou? Me ya kawoshi? Arshaad d’inne ya turo shi?”.
“A’a, wai ce mini yayi wai Arshaad d’in aure zai yi, wai an zab’a mishi wata a gida…Shi kuma Auwal d’in wai yana sona ne zai aure ni! Sannan wai in yi shiru kar inyi magana da Arshaad d’in de komenene dai ni dai ban gane ba gaskiya.”
“Ikon Allah!”
Shine abunda Umman tace
kafin ta sake cewa
“Tou ai Alhamdulillah.”
Nufar wardrobe d’insu tayi mai b’allalliyar k’ofa.
Wajen kayanta ta hau bincikawa da alamun akwai abunda take nema…
Cike da son jin k’arin bayani
Umma ta matso kusa da ita tace “Jalila ki juyo ki yi mini bayanin da zan gane dan ni sam ban fahimci zancen ki ba.”
A d’an razane kuma sai ta tab’ata sannan tace
“Ince dai ba Hudan zai auraba ko? Shi Arshaad d’in!”.
“A’A”
Jalilan tace, kafin ta sake cewa
“Kina jina fa nace miki ‘a cikin danginsu aka zab’ar mishi mata!
A yadda na fahimta kamar ma fa bai gayawa ita Hudan ba har yanzu.”
Wata kalar dariyar mugunta Umma tayi sannan tace
“Allah shi k’ara!
Sai wani faman hura hanci suke yi su a dole y’arsu zata auri mai kud’i!
Ai ga irinta nan.”
Sai da ta d’an yi shiru kamar mai tunani kafin ta sake cewa
“Ikon Allah, wani hanin ga Allah baiwa ne…Kiga fa babu yadda ban yi dake akan ki fita ku had’u da Yaron nan ba amma Allah bai yi ba!
Yanzu fa da tuni ke zai yaudara ya gudu yaje ya auri wata kinaji kina gani.
Daman nifa an dad’e ana gaya min cewa
‘In kwantar da hankalina, ba Mijinta bane ba!’.
To Amman shi wannan d’in in ce dai mai kud’i ne sosai shima, ko Arshaad d’in ya fishi?”.
Juyawa Jalila wadda ta nemo layin ta da kyar a k’ark’ashin hargitsatstsun kayanta, tayi,
tana murmushin tambayar!
Sai da ta amshi wayar daga hannun Umma ta k’arasa ta zauna a kan yagalgalalliyar kujerar d’akin ta fara neman inda zata saka layin a wayar
tukunna ta fara magana
“Ai Umma, ba wai Arshaad d’in ne mai kud’in ba
Inaga kamar Babansu ne mai kud’in!
Domin kuwa shima wannan Auwal d’in yadda kikaga Arshaad tou haka yake..
Da had’add’iyar motar da gayun da yanayin turancin
duk! Kina gani kin san ya tsumu a naira!
Kinga fatar jikinshi kuwa?
Tafin hannunshi laushi kamar.....”
Shiruuu, Jalila tayi ta daina k’ok’arin neman inda zata saka layin a wayar, kamar tana tunani….
Mik’ewa ta yi taje inda Umma
take tsaye kafin tace
“Amma Umma gani nake yi kamar d’an iska ne wannan d’in, ina shiga motar fa ya hau rik’e min hannu!
Gaba d’aya ma ni kasa sakewa nayi da shi sosai.
Kuma ni Umma har ga Allah Arshaad nake so!
Inaga gara kawai ki san yadda zakiyi kawai a fasa auren nashi! Dan ni ya fi kwantamin a rai, shi wannan Auwal d’in gaskiya jinina bai wani d’auke shi ba!
Watak’ila mafa kinga d’an iska ne!.
Idan ya zo kar In sake fita ko?
Harda fa matsa mini hannun ya dinga yi!.”
Kallonta Umman tayi na y’an dak’ik’u, kafin tayi k’asa k’asa da murya tace
“Jalila anya kin san ciwon kan ki kuwa?
Idan kika kuskura kika yi wasa da damar ki
Wallahi ki kuka da kanki!
Tayaya aka samu kika yi saurayin ma?.
Kiga fa Yaron nan wannan shine zuwansa na farko amma kalli abun arzik’i!”
Tayi maganar tana nuna waya da kud’in da Auwal ya bayar
sannan taci gaba da cewa
“Su su Hudan kika san me suke yi?.
Ni dai a ganina dan dai rik’e hannu a wagga Yaro mai arzik’i ba laifi bane ba.
Yanzu fa rayuwar ta sauya ne gaba d’aya….
A matsayina na uwarki!
Ina mai baki shawara ki samu a lallab’a ko ta halin k’ak’a ne a samu ayi auren nan! Muma
mu samu muji dad’in rayuwa
a dama damu..
Kina gani dai ga yayanki chan a kulle wanda na tabbatar inda ace mu wasu hamshak’an masu arzik’i ne wallahi da tuni sun sake shi.
Ki tashi ki tsayawa kanki Jalila,
Junaidu yanzu sai ta Allah
wanda kin san shi ne yake taimaka mana da kud’i,
kuma na san kin san ba don
kud’in da yake bani ba da tuni yanzu bana cikin gidan nan!
Jiya banyi ishashshen bacci ba
tunani kawai nake yi ta yadda zan biya malan Yusuf kud’in aikin da yake bina dan har ya fara yi mini tuni!
Sai gashi Allah ya dubamu ya kawo mai bamu amma shine kike k’ok’arin yi mana bak’in ciki ko?
Ni dai ban ce kije kiyi abunda bai dace ba amma a iya tunani na da wayo ‘Rik’e hannu ba matsala bace ba’.”
Tana gama fad’in haka ta hau dudduba d’akin…
Chaan! Ta rarumo mayafinta tana cewa “Bari ma kiga in tashi inje gida!
Akwai maganar da ya kamata muyi da Baabaa Laraba.
Kin san ance da zafi zafi a kan daki k’arfe.”
Shiruu, taga Jalilan tayi kamar mai tunanin wani abu
hakan ya sanya ta