Showing 66001 words to 69000 words out of 124668 words
Chapter 23 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
ba akan
“itafa ba zance aka zo wajenta ba.”
Yaron ne ya sake dawowa da same sak’o!
Hakan yasa Hudan ta zira hijabinta ta fito.
A soro ta hango Jalila, ta kasa tsaye ta kasa zaune, da alama lek’en sa take yi amman tana ganin Hudan sai ta baasar kawai tayi cikin gida.
Arshaad, yana cikin mota a zaune, Abokinshi wanda ya rakosa yanata tsokanarshi,
yana cewa “Yanzu Dude!! Saboda Allah a nan kayo matar da kabi ka isheni da ‘kayi mata’ take?
may be ma ba right kwatance bane gaskiya, tunda kaga fa har yanzu bata fitoba!
Kaga kawai mu juya, kai kanka kace Yarinya ce, maybe ma ba zance take yi ba! Kar ka sa yayanta ya biyo mu da sanda.”
Murmushi Arshaad yayi sannan ya juyo ya kalli Jamil wanda shima shi d’in yake kallo! Nuna kanshi yayi da yatsa sannan yace
“Ni, In juya??
Hmm tab!! Ai ba wannan zancen! Ka shirya kwana a nan
dan yau za aga naci!!.”
Dariya Jamil ya kwashe dashi kafin yace “So makaho!
Yau ga wanda y’ay’an senators da governors suke hauka akai ya mato akan y’ar gidan Malan shehu!.”
Duka Arshaad ya kai mishi sannan yace “Bana son rainin wayo…you beta learn on how to talk about my in-laws dude! And you b……”
maganar tasa ce ta sark’e sakamokon hango Hudan da yayi ta fito tana d’an duddubawa da alamun neman wanda aka ce yana neman nata take yi.
Motar ta kalla sannan ta d’auke kai tana kallon d’ayan gefen dan ba da motar da suka had’u da shi waccchar ranar yazo ba.
Sai da ya duba fuskarsa a mirror d’in gaban motar tukunna ya sa hannu zai bud’e marfin motar ya fita yaji Jamil ya rik’e mishi hannu. Cikin dariyar mugunta Jamil d’in yace “haba Man! Ka d’an ja aji mana..”
Fisge hannunshi Arshaad yayi sannan yace “na bar maka ajin yau, ka had’a da naka idan kaje wajen taka sai kayi.”
Daga haka ya murd’a hannun murfin motar ya fita.
Fitarsa tayi dai dai da sake juyowar Huda, aikuwa suka had’a ido.
Tana ganinsa ta gane shi….
Yana sanye da blue jeans mai kyau da wata bak’ar riga mai k’aramin hannu data d’an kama jikinsa, ga wani takalmi sau ciki kamar canvas da bak’in agogo a hannunshi
Yayi kyau sosai.!
“Me kuma ya kawo shi? oho!”
Shine abunda ta fad’a a ranta
sannan ta ci gaba da tunanin
“Lalle, da ace Mama taga wannan da ba zata ce zance ya zo wajena ba! Wannan ko a mai aiki ba lalle ya yarda ya d’auke niba.”
Tunawa tayi da handkerchief d’inshi mai kyau, da Mama tace ta kawo mishi abinshi,
wata k’ilan shi ya biyo dan haka ta fara tunanin kalar hak’urin da zata bashi dan ita bata san inda yake ba……
Sallamar da yayi mata ce ta katse mata zancen zucin da take yi.
A hankali ta sannan tace masa “ina wuni” tana mai shak’ar wani nutsatsen k’amshin turare da yake tashi daga jikinshi.
Murmushi yayi kafin yace “Lafiya Huda, ya gida?”
A hankali ta sake cewa “lafiya” dan ji take kamar k’amshin turarensh za sanyata bacci.
Ganin tayi shiru yasa yace
“Tun last two weeks naso zuwa, amman sai nayi tafiya. Jiya na dawo inata Allah Allah in zo, but sai naga kamar I’m not welcome..”
Kamar an fisgi maganar a bakinta tace “Kayi hak’uri ya b’ata ne”.
Da mamaki yake kallonta kafin yace “Me??”
“Handkerchief” ta bashi amsa.
Dariya ma ta bashi….tabbas ya san ya bata handkercheif amman shi yama manta dashi,
dan haka kanshi tsaye yace “bashi na biyo ba ai, wajenki na zo.”
Still yanzun ma kamar an fizgi maganar a bakinta, tace”Mama tace ince maka bana zance”
Sai kuma taji kamar ta nutse a k’asa, taya zata ce mishi haka? bayan ta tabbatar ba wannan ne ma ya kawo sa wajenta ba.
Jin shiru yasa ta d’ago kanta cike da jin kunya.
Tana d’agowa kuwa suka had’a ido dan shima itan yake kallo yana murmushi….
kafin ya sauk’e ajiyar zuciya yace “To sai yaushe zaki fara zancen??”
“Nima ban san lokacin ba”
Ta bashi amsa.
“To yanzu ya za ayi kenan?”
Ya sake tambayarta.
Shiruuu, tayi dan ta rasa bakin magana yanzu kam.
A hankali yace “ko sai kin tambayi Mama?”
Da sauri ta d’aga kai alamar ‘eh’.
Murmushi yayi yace
“Yaushe zan dawo to inji me tace??”
Da sauri tace “a’a bara in shiga In tambayo ta.”
This time around sai da yayi dariya kafin yace “No, ki bari jibi zan dawo sai inji me tace, ko?”
“To”kawai tace.
Ganin yak’i tafiya yasa tace mishi “sai anjima”.
Murmushi yayi kafin yace mata “bye” sannan ya fara tafiya da baya yana waving d’inta, har ya kusan motarsa tukunna ya juya ya isa ya bud’e ya shiga.
Ita ma ta juya tayi cikin gida…
A soro suka kuma cin karo da Jalila, ita dai Huda bata ce mata k’ala ba tayi wucewarta.
D’aki ta wuce direct dan bata hango Mama a kitchen ba.
Tana zuwa ta fad’a mata yadda suka yi dashi..
Sai da Mama ta d’anyi jim!! Tunkunna tace mata “ta tashi taje da d’aura ruwan miya” dan already Maman ta tuk’a tuwon tun kafin ta dawo a makaranta.
Tana fita Mama ta janyo waya
ta hau kiran Ummu…..
Bayan sun gaisa ne,
Cikin d’an rage murya dan taji kamar akwai mutum a k’ofar d’akinta!
Ta fad’a mata halin da ake ciki sannan ta k’ara da cewa
“Na san cewa Hudan tayi Yarinta yanzu, amma akwai abubuwan da na hango nakeso in taka musu burki tun kafin su zo su fi k’arfin mu.
Kinga na farko..
Furucin Baba da yayi na ‘zai aura mata mallan iro mai kayan miya’ nake jin tsoro.
Ga su Sadiya su kuma kinga kar su k’ulla mata wani sharrin da zai sanya hatta su Kaka suma su zuciya su bada goyon baya a aura mata mallan iro. Mutumin nan matanshi uku kin sani, kullum ana bala’i a gidan sa ga asirce asirce a tsakaninsu, sannan uwar gidanshi kin san k’awar su Laraba da dillaliya ce, abun ba zai zo da dadi ba! Ni ba wai arzik’in shi na raina ba wannan shine dalilina.
Sannan yayi mata girma har ga Allah.
Na san su Kaka ba lalle su yarda su bata malan iro ba amman fa munafuki ko d’akin mahaifiyarka ya riga ka shiga to sai ya had’a ku, su Sadiya sunga ta d’an fara tasawa kinga ai har sun fara k’ulla mata sharri, Allah kad’ai ya san me zasu ce a gaba, Ina tsoro kar a b’ata mata suna a zo hatta su Kaka su daina goyon bayanmu!
Mai gata ma idan sunan shi ya b’aci ya yake k’arewa? ballantana ita da Mahaifin nata ma cewa yayi kar a fad’a mata ko da sunan shi ne.
Abu na biyu kuma shine Junaidu!
inaso tun kafin yaje ya samu su Kaka da maganar son auran Hudan, ya zaman ace tanada tsayayye already..
Dan naga take takenshi kenan kwana biyun nan.
Harga Allah ba zance miki ga laifin Junaidu ko makusarshiba amman idan Hudan ta auri Junaidu ban san wacce kalar rayuwa zata yi a hannun Sadiya ba, yes na san Junaidu shine Mijin amman ina gudun sharrin Sadiya kina gani fa yanzu yadda ta mayar da Ya Usman sai fa abinda tace tukunna shi akeyi a cikin gidan nan ko b’acin ranta baya so ya gani.
Sannan shi kanshi Ya Usman d’in ba son Hudan yake yi ba!
Ba zan so ta zauna da irin waennan surakan ba na san zafin k’iyayyar suruki sam babu dad’i kwata kwata!
Bana so Huda tayi irin rayuwar da nayi a baya, a wahalar rayuwa da Hudan tasha tun daga tasowarta inaso ace taji dad’i a gidan Mijinta.
Sannan abu na uku..
Hudan fa tana zaune ne kawai
Ita ba makaranta take zuwa ba
ballantana ace tayi facing karatunta, duk wata hanya da suka san zata samu ci gaba k’ok’ari kawai sukeyi su datse.
Kaka yana iya bakin k’ok’arin shi amman shima wani lokacin baya iya tankawa saboda halin sharrin mata, akan batun karatun Hudan yadda kika san an datse bakinsu shi da Baaba Talatu.
In Allah ya taimaka ta samu mai kishin karatun sai ya barta tayi a d’akin ta, bana so Hudan ta k’are kamar ni kwata kwata…
Waennan dalilan ne suka sanya da akace yana son ganin ta kawai na bata sak’on da amsarshi zata sanya in fahimci manufarsa a kantaZ
Ni dai a ganina kawai a samu a bincika ko shi waye idan aka dace sai kiga komai ya zo da sauk’i.”
100% Ummu ta yarda da duk bayanan da Mama tayi, dan ji tayi ma kamar Maman ta shiga zuciyarta ne.
Dan haka tace mata
“Yanzu ya kike ganin za ayi??
Kina ganin idan yaje wajen su Kaka maganar ba zata jewa shi Junaidun ba?”
Ajiyar zuciya Maman ta sauk’e kafin tace “Baban Sakina zaki yiwa magana.
Yaron zai zo ya gaidashi..
In maganar tayi k’arfi muka ji manufarshi aka sanshi sai ya zo wajen Kaka, Tunda yanzu hasashe ne muke yi.”
Furzar da numfashi Ummu tayi sannan tace “to shikenan ba damuwa, amma sai dai abun nan fa ya zama sirri, dan kin san In Shuwa taji mun shallake su Kaka to kashin mu ya bushe!!”
‘Na’am’ Mama tayi da hakan.
Sannan suka d’an tab’a hira kafin ta kashe wayar.
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
22
Kamar yadda Arshaad d’in ya fad’a, ranar litinin da yamma sai gashi ya zo. Wannan karon bai zo da Jamil ba shi kad’ai ya zo dan bayan tafiyar su ranar asabar Jamil d’in yayita yaba kyawun Hudan yana cewa “ai yaga dalilin da yasa Arshaad d’in yazo ya mak’ale a irin wannan arean” har da cewa “In tanada k’anwa mai kama da ita ya had’a su, yanaso.”
Shiyasa yau ya k’i zuwa dashi, dan in yana yaba Hudan ji yake kishi na neman kumbura mishi zuciya.
Kamar ranar farko, yau ma Yaro ya kira ya aika yace ace “Hudan tazo inji Arshaad”
Yau d’in Jalila tana makaranta suna tsakiyar jarabawa Umma kuma ta tafi yawonta ita da wata bazawara y’ar k’anwar dillaliya da take zaune a gaban dillaliyar shiyasa abun ya zo da sauk’i.
Yauma Hudan bata dad’e da dawowa daga makarantar ba,
suna tsakar gida ita da Mama suna d’an tab’a hira, tana cin d’umamen tuwon masararta da miyar kuka Yaron ya shigo ya fad’i sak’on ya juya ya fita…
Rau rau Hudan tayi da ido sannan tace “Mama na ce mishi kin ce bana zance shine ranar yace ‘yau zai dawo’ ai na fad’a miki ko?”
Murmushi Maman tayi ganin yadda duk Hudan ta bi ta rud’e.
A hankali Mama ta mik’e ta shiga d’aki ta d’auko wayarta da pencil da y’ar k’aramar takarda sannan ta fito.
Har lokacin Hudan tana zaune tana cin tuwon ta.
Umartata Mama tayi da ta tashi taje ta wanke hannunta ta kai masa sak’o.
Yadda Maman tace haka akayi
Bayan tayi copying number Baban Sakina ta rubuta da sunanshi a jikin takardar ta bawa Hudan tace mata “gashi ta kai masa.”
D’aki Hudan ta shiga ta d’auko hijabinta sannan ta fita zuwa wajenshi.
Motar ta fara ganewa dan da ita suka fara had’uwa, yana tsaye ya jingina a jikin motar yana daddana waya…
wata dakakakkiyar sky blue d’in shadda ce a jikinsa, d’inkin Boda mai d’an k’aramin hannu da hularshi zanna bukar itama sky blue mai d’an ratsi ratsin black a jiki, sai takalminsa na fata black wanda kana gani ka san mai mugun tsada ne dan sai wani kalar shek’i yake yi yayi wa fararen sawunshi mugun kyau.
Bai san ta k’araso ba dan gaba d’aya hankalinshi yana kan chatting d’in da yake yi da Yayansa.
Sallamarta ce ta dawo da hankalinshi wajen…
A hankali ya d’ago ya zuba mata kyawawan idanuwanshi kafin ya sakar mata wani tsadadden murmushi sannan
a hankali ya amsa.
K’asa tayi da kanta ta gaidashi,
Yanzun ma a hankali ya kuma amsawa yana mai tambayarta “ya gida”
“Lafiya” kawai ta iya ce mishi sannan ta mik’a mishi takardar hannunta tace gashi inji Mama, dan ita Allah Allah take ta koma gida saboda yadda yake ta faman kallonta….
Babu wani datti ko squeezing a jikin kayanta dukda iya hijabin yake iya gani baya ganin rigar dan hijabinnata ma ya kusan rufe zanin jikinta gaba d’aya
amman yadda kayan suka kod’e tashi d’aya zaka tabbatar da sun ji jiki kuma sun gaji da ruwa!
Tausayinta ne yaji ya lullub’e shi, ahankali ya fara tunanin ta yadda zai yi ya taimaka mata dan gaskiya suna buk’atar taimako.
Ga gidan nasu ma kanshi yana buk’atar a d’an gyara shi
Gabansa ne yaji yayi mugun fad’uwa da ya tuno da Granpa domin kuwa ya san ko a verge of death yake wallahi Granpa ba zai tab’a yarda ya barsa ya auri Yarinyar data fito daga irin wannan gidan ba!
Ajiyar zuciya ya sauk’e a ranshi yana cewa “tabbas he has to do a lot kafin ma yaje ya fara nunata…..dan he don’t think he can keep on living idan aka yi tunanin rabashi da Hudan!
Shi fa har mamaki yake yi ta yadda kawai lokaci guda yaji yana mugun mugun sonta!
Dan ko lokacin da yayi tafiya ji yake kamar yayi hauka, a gaggauce ya gama aikin da aka turashi ya dawo dan kawai ya samu yazo ya ganta…….
“Zan tafi, sai anjima.”
Shine abinda tace masa wanda yayi sanadiyyar dawo da hankalinshi wajen.
Murmushi yayi sannan ya ware takardar ya duba…
Number waya ne a ciki an rubuta Alhaji Muhammad a saman.
Kallon ta yayi kafin yace
“Your Dad??”
Yayi mata tambayar yana mai nuna mata number.
Kallon sunan tayi, sai da
ta had’a gumi tukunnan kwakwalwarta ta iya karanta mata ‘Muhammad’ d’in amman abun farkon kam sam ta gagara karantawa ita dai taga ‘A’ da su ‘L’.
Kalmar Muhammad d’in ta furta mishi.
Kallonta yake yana mamaki yadda karatun yake bata wahala dan tun farko ya lura da hakan dama shiyasa yana sane ya bar mata ta karanta dan yana son ganin iyakar ilimin nata.
“Eh, Alhaji Muhammad.”
Yace da ita sannan ya janye takardar kafin ya sake cewa
“Your Dads number, right?”
A hankali tayi k’asa da kanta ta shiga girgiza mishi kai, kafin tace “Ba na Baba na bane ba, shi bamu da number shi
wannan number Baban su Sakina ne mijin Anty na.”
Da mamaki yake kallonta ‘taya zata ce bata da number Babanta?’
Ya so ya tambayeta ‘a ina baban nata yake?’ Amma kuma fahimtar da yayi tun lokacin da yayi mata maganar Baban nata gaba d’aya kamar ranta ya dagule dan har idanunta ma sun kawo kwalla ne yasanya kawai ya kyaleta ya zaro wallet d’inshi ya saka takardar a ciki with care sannan yace mata
“I’m going to call him Ina barin nan, in shaa Allah.
And pls ki cewa Mama na gode sosai sosai, Ina so In shiga In gaidata amman maybe sai dai next time tunda ta bani number, bara in fara zuwa inda ta turani inji komai tukunna ko?”.
A hankali ta d’aga mishi kai alamar ‘to’ sannan tace “sai anjima” tana mai k’ok’arin juyawa.
Yunk’urawa yayi da sauri daga jinginar da yayi a jikin motar kafin yace “Saurin me kike yi ne? Ko irin y’ar hirar nan babu?
Ko har kin gaji da ganina ne?”
Ya jero mata tambayoyin yana kallonta.
A hankali ta girgiza kai sannan tace “Mama zata ga na dad’e”
Murmushi yayi yace “ba za tayi fad’a ba.
Bani labari ko guda d’aya ne tukunna sai ki tafi.”
Shiru tayi dan ita bata san ta Ina zata fara ba.
“D’aya kawai, sai ki tafi”
Ta sake jin muryarshi a shagwab’e.
Ita dai bata da labari shiyasa tace mishi “Wanne iri tou!”
Cikin son fahimtar wani abu yace mata “School, wanne subject kika fi ganewa wanne ne kuma yake baki wahala?”
Ta gane me yake nufi amman sanin bata da amsar wanchan yasa kawai tace masa “nafi son hadisi”
Murmushi yayi kafin yace
“A boko fa?”
Sai da tayi k’asa da fuskarta sosai sannan tace
“An cire ni tun tuni, bana zuwa.”
As he was suspecting!
Dan haka da sauri ya d’an matso yace “mai yasa bakya zuwa? Tun yaushe aka cire ki?”
Cikin wata kalar angry voice sukaji ance “Saboda baka saka ta ba, shiyasa bata zuwa!”.
Da sauri ta d’ago ta kalli Ya Junaidu wanda yake kallon Arshaad kamar zai rufeshi da duka!! Tunda take bata tab’a ganin wannan kalar b’acin ran a kan fuskar Ya Junaidun ba.
Juyowa yayi ya daka mata tsawa “Bar nan kafin In b’abb’allaki!!!”
Ai kuwa a take tayi cikin gida da sauri har tana tuntub’e.
Bata san ya suka k’are da Arshaad d’in ba.
Sai bayan kusan minti uku ya shigo cikin gidan..
Har d’akin Mama ya biyota!
Yana shiga Hudan tai saurin b’uya a bayan Mama dan har ga Allah ta mugun tsorata da lamarin sa na yau d’in.
Sai da ya d’an daidaita kanshi kafin yace “Mama kin san a waje naga Huda da wani a tsaye?”
Kai tsaye Mama tace mishi
“Eh, na sani.”
Da mamaki yake kallonta kafin yace “Waye?”
Mama bata b’oye masa ba nan ta sake cewa
“Wanda kuke tunanin wajenshi taje kwanakin baya.”
Zuciyarshi na wani irin mugun tafarfasa cikin b’acin rai, yace
“Kenan wajen nashi taje da gaske tunda gashi yau ma ya biyota!”.
A d’an fad’ace Mama tace
“Junaidu fitar min a d’aki tunda rashin kunya kaima zaka yi min!”
Runtse idanunsa yayi da k’arfi! Ya kusan minti biyu bai fita ba bai kuma bud’e idanun nasa ba. Tukunna a hankali ya bud’e idanunsa ya zuba su akan Hudan, da sauri ta sake shigewa bayan Maama,
takowa yayi ya k’araso ya zo gaban Mama kafin yace
“Kiyi hak’uri Mama ba rashin kunya zan yi miki ba, a tunani na bai kamata ta fita ta kula waani ba! She’s still young and na san kin san inason Hudan ko da ace ban kai ga furtawa ba, shiyasa sai naga kamar hakan cin fuska ne aka yi mini.
Ban fad’awa su Kaka ba saboda a tunanina Hudan tayi k’ank’anta, amman Mama da k’arancin shekarunta kin barta tana kula wanchan mutumin!
Kin ganshi kuwa?
Irin waennan yaudarar ta kawai zai yi, a zamanin yanzu fa kwarya tabi kwarya ake yi.
A tunani na ya kamata ace kin fara sanin waye shi kafin ma ayi tunanin barin ta fita wajensa…”
Ji yayi muryarshi ta fara sark’ewa, tsabar b’acin rai! Gashi sai k’ok’ari yake ya danne! Ganin haka yasa ba tare da ya sake cewa komai ba kawai ya juya ya fita.
Shiru d’akin yayi sai k’arar sheshshek’ar kukan Huda.
Chan Mama ta juyo ta zaro ta daga bayanta