Showing 105001 words to 108000 words out of 124668 words

Chapter 36 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt

25 Sep 2025

2338

koma ta zauna a kusa da ita ta dafa ta tace “Ki kwantar da hankalinki,
komai zai tafi dai dai.
Ki cire wani Arshaad a ranki
Allah na tuba me za kiyi da mayaudari?
Abu na biyu kuma
Kin ga masu kud’in nan sun fimu iya shige shige
Idan muka ce zamu raba aurenshi da wachchar y’ar uwar tashi tsaf sai y’an kud’ad’enmu sun kare tass!!
Dan haka kawai kiyi abunda yake mai sauk’i,
kin ji ko?”.
Har zata mik’e sai kuma tace
“Yanzu shi wannan d’in a ina yace ya ganki?
Sannan shi Arshaad d’in ya aka yi yayi mishi maganar ki?
Ni fa ban gane komai ba gaskiya ki fahimtar dani ta yadda zan iya yiwa Baabaa Laraba bayani dalla dalla.”

Tsaki Jalilan taja sanann tace
“Wallahi Umma yadda baki fahimta ba nima hakan take.
Sam sam ban gane me yake nufi ba!.”

Da d’an fad’a Umman tace
“Kuma baki damu da ki tambaya ba!?
Kan ki yanata rawa…”

“Umma wai so kike yi in disga kaina ne?
Na fad’a miki da turanci yayi ta bayaninshi kuma irin mai saurin nan!
Kina ji kin san irin na turawa ne,
shiyasa nace miki shima akwai arzik’i dan daga ji ba a k’asar nan yayi karatu ba…
Yanayin nasa kalar turancin ba irin nasu Ya Junaidu bane ba.
Gashi shima kyakkyawa fari tass kalar hutu.”

“Tam shikenan, bara inje mu gani.”
Umma tayi maganar tana gyara mayafinta sannan ta d’auki wayarta tana cewa
“Alhamdulillah wayata zata huta!
Shegen malamin maths mai son bati, saura kuma inji kin kirashi da wannan wayar,
ke! Ni kima fita a harkar shi
dan yanzu kam kin fi k’arfin shi.”

Dariya Jalila tayi itama ta mik’e
tana cewa “Wallahi kuwa Ummata..
Bari nima ki ga yanzu inje
gidan su Jidda sune masu manyan wayoyi in basu su sakamin sim d’innan dan na kasa.
Sannan In d’an saka charji
inaga ya manta bai had’a min da charger ba, anjima ina kiranshi zan ce ya taho min da ita idan zai zo, kar in manta.”

Haka nan suka fice a gidan,
Umma tayi gidansu
Ita kuma Jalila ta nufi layin gidansu wachche ta kira da Jidda.


Umma tana zuwa gidansu ta tarar ana fad’a da Baaba Laraba da K’asimu da Anty amarya…
Ganin kalar zagi da cin mutuncin da K’asimu yake yi wa Baaba Laraba a tsakar gida gaban Yara da ita kanta Anty amaryar ne
ya sanya Umma ta jaa
Baaba Laraban suka shige d’aki suka bar su sunata rashin mutuncinsu!.

Umma ji take kamar tayi super ta dira kan Anty amarya taci ubanta, amma kuma gudu da tsoron karta janyowa uwarta saki yasa kawai ta ja bakinta tayi shiru…..ta san duk bala’in ta K’asimu ya dama ta ya shanye!
Yanzun nan zai yi musu abunda basu tab’a tsammaniba.

Suna shiga Baaba Laraba ta sa kuka, cikin kukan take cewa
“Sadiya wallahi uban ki ba d’an halak bane ba!.
Saboda Allah dan yaga yanzu amarya ke bashi kud’in kashewa shike nan ni sai in zama bola?
Wanne irin gata ne ban yi mishi ba?
Shifa ya karyani a sana’ar tawa saboda yadda nake bashi kud’ad’ena kyauta da bashi!
Amman yanzu dan yaga bani da shi shikenan na zama banza kenan??
Da gangan fa Yarinyar nan zata takalo ni da fad’a ina tankawa shikenan zai shigar mata su tisa ni gaba da cin mutunci tsofai tsofai da ni.”

Ajiyar zuciya Umma ta sauk’e kafin ta matso ta share mata hawaye sannan tace
“Kiyi hak’uri, ki kyalesu, ki daina shiga harkar ta, komai zata yi miki ki kar ki kulata.
Ki kwantar da hankalinki in dai na haifu y’ar halak to wallahi sai ta bar gidan nan!!
Dama ai babu ce tasa muka barta muka zuba mata ido ko?
To yanzu Allah ya kawo mana mafita .......”
Nan ta zayyano mata zancen Auwal da Jalila, da kuma maganar auren da Auwal d’in ya zo dashi, da maganar auren Arshaad!!
Duk bata bar komai ba.

Murmushi Baaba Laraba ta hau yi sannan tasa hannu ta goge ragowar hawayen fuskarta kafin tace
“Yanzu ba gwara hakan ba?
Ai sai sun fi jin ciwon hakan yanzu akan ace an rabasu tun farko!
Abunda nake ta gaya miki kenan tun lokacin da aka ce mana ‘ba Mijinta bane ba’
Wannan ranar nake kwad’ayi gani!
Ke kuma duk kika bi kika d’aga hankalinki kika gaza nutsuwa ki fahimceni…akan yana kawo mata abubuwa kuma ita tana fita Jalila tana zaune..
Yanzu tou ba gashi itama Jalilan Allah ya kawo ba?”.

Murmushi Umma tayi kafin tace “Ai dama Baabaa kin san ance duk abunda Babba ya hango Yaro ko kan dala ya hau ba zai ganiba.
Yanzu menene abun yi?
Dan idan mukayi sagegeluwar da su Maryam suka yi to fa muma hakan na iya faruwa da mu.”

“Kud’in hannunta da aka bata kin taho da su?”
Cewar Baaba Laraba.

Baki Umma ta kama kafin tace
“Niiiii? Kin dai san halin Jalila da shegen son abunta!
Yanzun ma ina lure da ita sai
wani kaffa kaffa take yi dan kar ince ta bani.
Shiyasa na kyaleta sai
munje kwanciya tukunna zan yi mata wayo In karb’a..
Kinga a ciki ma sai ki samu na jari.”

“Ya kamata kam”.
Shine abunda Baabaa Laraban tace.
Daga nan suka hau k’ulla yadda za suyi da
Auwal, K’asimu da Anty amarya........


BULAMA ✍️





So da Buri
Free Book
32


Tun azahar! Sai bayan sallar magrib tukunna
Hudan da Sakina suka baro gidan Baaba Talatu suka nufi gida.
…Tun azahar d’in suna
tare da su Anty Zainab wadda suka zo ita da y’arta Khadijah (amarya) ana ta shirye shiryen biki…
Yarinyar tana son Hudan sosai
sai faman sakota take yi acikin lamuran bikin
Anty Zainab ita kuma tana ta gwasalewa har sai da Baaba Talatu ta d’an tsawatar mata…..

Ganin Hakan ne ya sanya Hudan ta mik’e ta shige d’akin Baaba Talatu ta barsu nan.
Tana shiga ta hau video call da Arshaad, sai da aka kira Magrib tukunna suka yi sallama..



Suna shiga d’akin suka k’arasa da sauri wajen Mama sakamokon hangota da suka yi
kwance a duk’unk’une cikin bargo!
Dama sun fita sun bar ta tana d’an zazzab’i da ciwon kai!.

Sakina tana zuwa tasa hannu ta tab’a goshinta!
Aikuwa a rikice ta hau salati…
kafin ta shiga cewa Hudan “ta zo maza maza, su fita su nemo adaidaita a kai Maman asibiti!
Ko kuma su kira Ummu.”
Dan jikinta ba k’aramin zafi ya d’auka ba wanda hakan ya sanya gaba d’aya suka rikice lokaci guda.!


Da kyar Maman ta lallab’a su suka hak’ura suka bari akan ‘sai gobe da safe za a kaita asibitin’
A cewarta “ciwon nata, it not that serious.”

Tsumman d’ankwali suka jik’o suka hau d’ad’d’aura mata a jiki…
A hankali ta fara jin zazzab’in yana sauk’a, dan haka ta mik’e ta nufi bayi domin yin alwala..

Bayan ta idar da sallar ne
ta juyo ta kallesu, kafin tace
“Kika ce d’azu Arshaad zai zo kuma naga baku dawo ba.”

Sakina ce ta karb’e ta hanyar cewa “Eh! Ya kira waya…
wai Yayan nashi da zasu zo taren ne bashi da lafiya.
So sai gobe za su zo, in sha Allah.”

Kamar Maman ba zata ce komai ba, sai kuma tace
“D’azu naji kamar Yaro ya shigo yana cewa ‘wai Jalila taje inji Arshaad!’.”


“Around what time?”
Hudan ta tambaya tana d’an kallon Mama.”

“Wajajen biyar dai haka, zuwa, kafin Magrib naji ta shigo.”

Murmushi Sakina tayi kafin tace “Iskancin su ne kawai!
Maybe wani abun nasu suke son k’ullawa..
Amman ya Arshaad bai ma tab’a ganin Jalila ba!
I don’t even think ya san ma tana existing.
Ko kin tab’a gaya mishi akwai Jalila a gidan nan?”
Ta k’arashe maganar tana kallon Huda.”

“A’a” shine abinda Hudan tace
Sannan ta d’aura da cewa
“Tun wajajen hud’u da rabi ma muke video call da shi, sai da aka kira Magrib tukunna muka kashe.”

Jinjina kai Mama tayi alamun cikakkiyar gamsuwa da zancen nasu! Daganan ta mik’e ta gabatar da sallar isha dan har an fara kira…
Da kyar ta d’an tab’a abinci (‘ta zarcen’ da suka yi tun rana)
shima kuma dan su Hudan sun takura mata ne daga nan tabi gado, su Hudan kuwa basu kwanta da wuri ba!
Dan bayan sun yi sallah sun ci abinci sai da suka d’an tattauna akan bikin Khadija wanda da farko Hudan tace “ba zata je ba!”
Sai da Sakina tayi mata nuni da yadda amaryar take k’aunarta tukunna ta yarda suka bari akan zata je d’in amma ba zata je har Kaduna ba (dayake a chan za ayi bikin)
Ta yarda dai zata je wunin da Baaba Talatu ta had’a anan (Kano) Saboda jama’arta bayan an kawota an dawo Kano, za kuma taje bud’ar Kai gidanta amma gaskiya ba zata je har Kaduna ba!
Ta san Mama ma ba lalle taje chan d’in ba..
Dan haka za suyi zaman su idan an dawo Kano suje events d’in Kano….

Haka nan Sakina ta hak’ura,
dan taga Huda ta riga ta kafe a kan bakarta.


Kamar yadda Umma tayi zato!
Bayan ta koma gida…
Sai da suka kai ruwa rana
tukunna Jalila ta yarda ta bata rabin kud’in shima kuma dan
taji Umman tace ‘akan Auwal d’in yayi ta kawowa sannan ya turo da wuri za ayi aikin!!’
Ba dan hakan ba to da ba zata bayarba….
Daga nan ba suyi barci ba sai da Umma ta kokkoyawa Jalila d’abi’u da dabarun karb’ar kud’i a hannunshi.


Arshaad yana gama waya da Huda, ya mik’e yayi alwalar Magrib ya fito da zummar zuwa masallaci.
Ga mamakinshi a position d’in da ya bar Aslam a haka ya fito ya sameshi!
K’arasawa inda yake yayi
da sauri ya zauna a kusa da shi…
Yana kallon yadda jijiyoyin kanshi suka firfito waje
Idanuwanshi suka yi wani irin jaaa! Har abun tsoro.

A hankali Arshaad ya shiga lallashinshi..yana kwantar masa da hankali yana bashi baki.

Aslam, bai iya ce masa komai ba dan ya kasa magana ma!
Ji yake kamar ya b’intike zuciyarshi da kan shi ya jefar
sakamokon azababben ciwon da suke yi mishi..
Da kyar ya samu ya iya had’a sentence, yace “Jirani inyi alwala mu tafi mosque”.
Yana gama fad’in haka ya mik’e yayi ciki.
Bai d’ad’e ba ya fito.
Daga nan suka fita a side d’in.
Sai da sukayi sallar isha tukunna suka dawo.
A parlourn k’asa suka samu Mammy
Da kyar Aslam ya iya tsayawa ya gaida ita daganan ya hau jero mata tambayoyi
“Tun yaushe??
Mai yasa basu gaya mishi ba??”

Shiruuu, Mammyn tayi dan bata da amsar da zata bashi.
Ganin haka yasa yace
“Bari kawai ya je ya samu Granpa! Dan dole a nemo wani option din saboda ba zai yiu ace dashi da Mahaifiyarshi su d’auwwama a haka ba!
Ba zai yiu ba!!”
Duk ya bi ya hargitse!
In ka ganshi muddin kana da saurin kuka to sai ka koka.

Da kyar Mammy ta samu ta lallab’a shi ta hanyar ce mishi
“Shima Granpa d’in bai gamsu ba!
Yana nan yana ta shirin ganin best neorologiat na kaff duniya a dalilin case d’inta!
Sannan Granpa yayi warning d’insu ne akan kar su kuskura su bari Aslam d’in yaji maganar
Yanzu Idan ya san yaji ba zai yi duba da ‘Ai Auwal ne ya fad’a ba!’
Ta san had’a su zai yi gabad’ayansu yaci k’aniyarsu
Tunda shi dai ya san iyakar parents d’inne suka san zancen so one of them ne ya fad’awa Auwal d’in kenan!.
Yayi hak’uri ya kwantar da hankalinshi dan Allah
Ko ya samu Granpa ko bai sameshiba dole ta san sai inda k’arfin shi ya k’are wajen nemawa Mommy lafiya
Samun nashi kuma da yake shirin yi kawai matsala zai jawowa su Abba Dad Daddy da ita da su Mom.
Ya yi ta addu’a a samu a dace adduar ce ta kamata ba wai tado da case a kan case d’in rashin lafiyarta ba, mara lafiya baya buk’atar hakan.”
Da kyar da mugun kyar Aslam ya hak’ura da taimokon kalaman Mammy masu k’arfafa guiwa sannan bata barshiba sai da ta bashi full hope akan samun sauk’in Mommy
Bi’ixnillah

Duk da hakan dai, bai wani sake sosai ba!
Haka nan shi kad’ai sai ya zauna yayi ta tunani throughout abun tausayi…
Wasan b’uya kuwa
gadan gadan ya d’aura d’amarar yi da Mommy
dan kayansa ma Arshaad ya sanya yaje ya d’auko ya kawo
mishi gidansu side d’inshi (Arshaad)
Saboda jikin nata ya motsa wannan karon sosai!
Kamar ta san yazo wanda hakan ne yasa da Mammy tayi mishi tayin ya koma chan d’in kawai ya tattara ya koma za suke zama da Arshaad a side d’inshi.
Gwaggo Asabe kwata kwata bata so hakan ba
amman gudun kar ta sake d’aura mishi wata damuwar a kan wadda yake kai
ya sanya kawai ta amince ta bishi da addu’o’i
Bilaadadin.


Yau da safe suna tashi ya shirya yaje ya gaida su Mom da Ummi da Granmma.
Sai wajen 3:00 pm tukunna ya samu ganin su Daddy da Abba
A hakan ma wai yau sun dawo da wuri kenan…
Daddy aiki yayi mishi yawa
har Sundays sai yaje office.
Abba kuma akwai company d’insu shi da Aslam d’in da suke son bud’ewa wanda
shine abunda ya fitar da shi,
ya kuma sanya ya zama busy those days.

Sun ji surprise d’in kuwa
dan kawai ganinshi kawai suka yi.

Sun yi matuk’ar jin dad’in hakan ba kad’an ba Daddy har da y’ar kwallar shi….
Bayan sun gaggaisa ne aka hau hirar yaushe gamo
daganan kuma
Abba da Aslam d’in suka hau tattaunawa akan company d’in nasu wanda za su bud’e nan da y’an kwanaki k’alilan.
Su Daddy kuma suna taya su
da wasu shawarwarin…
Sai yamma suka rabu bayan sun yi sallar laasar tare.

Da kyar da sid’in goshi Aslam ya yarda zai raka Arshaad wajen hudan bayan Mammy ta saka baki.

Babu yadda Aaima bata yi akan aje da ita ba amman suka k’i. Haka ta haye sama tanata kumbure kumbure Mammy nayi mata dariya, tana ganin fitarsu tayi murmushi a ranta tace “Bara ku dawo, lokacin da zan bugi cikin Aslam ma ya fad’amin komai akan Yarinyar ba zaka sani ba
Tunda naga Auwal ya kasa.”


Arshaad ne yake tuk’in
Aslam na gefe yana sanye da
Top mai gajeran hannu maroon color da d’an ratsi ratsin blue black a jiki sai jeans, blue black .
Yayi kyau sosai dukda kuwa simple dressing ne yayi.

Arshaad kuma shadda ce a jikinshi yanayin d’inkin zamani mai mugun kyau!
Kalar ruwan zuma,
ya murza zanna bukar, wadda ta sake fito da ainahin kyawun fuskarshi…
Da bak’in agogo da takalmin fata kalar shaddarshi.

Kad’an kad’an yake jan Aslam da hira har sai da yaga yad’an saki fuska, dan idan akwai abunda baya son ganin shine
Yaga Aslam a irin wannan mood d’in.


A k’ofar gidan yayi parking kafin ya zaro waya ya nemo layin ta a recent ya kira yace
“Suna waje”

Da mamaki Aslam yake kallonshi, kafin yace
“Arshaad kana da ishashshen hankali kuwa?
Ba kaji shawarar dana baka ba ko?
Karka cuci Yarinyar mutane
ka b’ata mata lokaci!
Kasan ko bayan ran Granpa
ba lalle auren nan ya yiu ba dan na san Mammy ma won’t allow it
I know her too well!!”.

Murmushi kawai Arshaad yayi kafin yace don’t worry, I already have a plan..
Ka bari kawai lokacin yayi.”

Da d’an fad’a Aslam yace
“What plan?
Who are you planning on deceiving?
Parents d’inmu?
Ko su Yarinyar!
Dan dole sai an yi deceiving 1of 2 d’innan
tukunnan auren nan zai yiu.”

Ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace
“I love her!
Sosai!!
Ba zan iya hak’ura ba Aslam.
Kar ka damu, nothing will go wrong!
In shaa Allah.”

Wanann karon a harzuk’e Aslam yace
“How will....”
Ganin ma ba shi yake kallo ba ya sanya shima ya juya yana kallon inda yaga yana kalla…
Ko ba a fad’a mishi ba, ya san itace Hudan!
Ya jima yana kallonta!! Kafin da kyar ya samu ya iya janye idanunsa daga kanta.

Tun kafin ta k’araso Arshaad ya bud’e k’ofar ya fita.
Sai bayan kamar 20 minutes haka tukunna Arshaad d’in ya bud’e motar ya lek’o…… a zaune ya ganshi ya kwantar da kanshi a jikin seat!
Ya lumshe idanuwanshi kamar mai bacci.
Murmushi yayi kafin yace
“Ka fito mana, ku gaisa.”

Jinjina kai kawai Aslam yayi alamar ‘to’ ba tare da ya juyo
ko ya bud’e idanunshi ba.

Ganin haka yasa Arshaad d’in komawa tare da maida murfin motar ya rufe.


….Sam ya fidda ran Aslam d’in zai fito dan kusan 30 minutes
kenan da yayi mishi maganar!
Gashi ya san suna sauri ne saboda sunada appointment da Khadija GF d’in Auwal ta company wadda ta yarda da kyar zata gansu a yau, around 6pm ba tare da Auwal d’in ya sani ba.

Haka yasanya kawai ya fara yiwa Hudan sallama bayan ya kalli agogon hannunshi yaga time.
Kamar zata tambayeshi ina bak’on saboda d’azu yace mata ba shi kad’ai baneba
kuma har cewa yayi bara ya lek’a yace ya fito su gaisa..
Amma kuma ganin bai sake yi mata maganar ba yasanya kawai tace “ya gaida Aaima”
Tana shirin tafiya suka ji k’arar bud’e motar…
Ya kusan minti d’aya tukunna
kawai yayi tsaki ya mik’e ya fito ya zagayo inda suke tsaye.

Murmushi Arshaad yayi ya kalli Huda wadda take kallon k’asa tana mamakin yadda k’amshin turarenshi ya karad’e wajen, daga fitowarshi dan gashi har ma yana shirin k’orar na Ya Arshaad daga gurin gaba d’aya..
Muryar Arshaad taji yace
“Dan milki kenan!
Don’t mind him.”
Sai kuma yace
“Hudan ga yayana ‘Aslam’.”

D’agowa tayi tana kallon wanda ya kira da Aslam…wanda shi kuma sam kwata kwata yak’i yarda ya kalli inda take, chan wani waje ma taga ya juya yana kallo….
A ranta ta hau rayawa
….kwata kwata basa kama da Arshaad, Arshaad ya fishi hasken fata, amma fa tunda take a rayuwarta bata tab’a ganin skin colour d’in da yayi mata kyau!! Kamar na Aslam d’innan ba.
Yafi Arshaad tsayi, dukda kuwa shima Arshaad a sahun dogaye sosai za a sakashi.

Yanayin fad’in k’ashinsu shima kusan d’aya ne amman Arshaad ya d’an fishi k’iba……

Gyaran muryar da Arshaad yayi ne, ya dawo da hankalinta gareshi..
Ganin yadda ya kafeta da idanu ne ya sanya ta yi saurin sunkuyar da kanta k’asa
A hankali tace
“Ina wuni Ya Aslam”
Jin bai ce komai ba ne ya sanya ta d’ago kanta ta kalleshi sannan ta sake maimaita abinda ta fad’a da farko tare da d’an d’aga murya..

Sai da ya sake had’e rai
tukunna yace “lafiya”
Ba tare da ya kalleta ba!.

Arshaad, sam bai ji dad’in yadda Aslam d’in yayi mata ba!
Ganin kamar itama jikinta yayi sanyi ne kawai ya sanya yace
“Baby, bara mu tafi.
We have somewhere else to go.
Sai mun yi waya, ko?”.

“To”
Kawai tace, sannan ta d’an d’ago tana kallon Aslam tana mamakin kalar miskilanci da mugun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login