Showing 93001 words to 96000 words out of 124668 words
Chapter 32 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
gaban Mama, da kayan sojiji a jikin shi amman nashi ba kalar na ragowan ba ne, yana zuwa ya nuna musu id card d’insa kafin yace “Muna neman Junaidu Usman Bashir!
Mun samu order daga sama!
Here” ( yayi maganan yana nuna musu wasu takardu )
Yace “We have a search warrant and arrest warrant!”
Umma ce ta matso kusa da Huda, a hankali tace
“Me kenan??”
Kallonta Hudan tayi sannan ta juya ta kalla mutumin tace
“Sir, for what please?”
Hannu mutumin ya mik’a baya
nan wani ya taho da gudu ya bashi wasu takardu sannan ya sara mishi ya k’ame!
Takardan ya hau bincikawa, sai da yazo kan wata ta tsakiya tukunna ya zarota ya mik’awa Hudan..
Da sauri ta sa hannu ta karb’i takardun ta shiga karantawa…
Sakina wadda ta matso suke karantawa tare ce ta rafka uban salati sannan tace
“Sir this cannot be true he h...”
Bindigar da d’ayan ya saita mata a kai ne ya sanyata yin shiru lokaci guda!
Jikinta na mugun karkarwa.
Umma kuwa fashewa tayi da kuka tana cewa
“Me yayi ake nemanshi har da bundugu?
Ku fad’a mana dan Allah!”
D’akunan gidan mutumin ya yiwa ragowan sojojin nuni sannan ya basu order!
Nan da na suka shishhiga suka hau bincike…
Su Umma duk suna tsakar gida banda k’arar fashewar abubuwa da fad’uwa ba abunda suke ji…
Har kitchen da band’aki sai da suka duba amman babu Junaidu ba labarinshi.. basu samu komai ba.
Mutumin ne ya kalli Sakina yace “how are you related to him!”
Nan ta fad’a mishi sannan yace mata
“Akwai siblings d’inshi ko Mamanshi a nan?” (Duk da turanci).
Direct ta juya ta nuna mishi Umma…
Nan kuwa Umma ta sake rud’ewa ganin mutumin ya nufota tana cewa
“Dan uban ki me nayi kike nunani?”
Da gurbatacciyar Hausar shi yace mata “Ina wayanki?”
“Tana d’aki” tace, sannan jiki na rawa ta cewa Jalila “ta shiga ta d’auko!”
Ana kawo wayar ya karb’a ya mik’a mata sannan yace
“Ki kira Yaron ki, kice duk abunda ya kayi ya baro yazo yanzun nan, and kar ki bari ya zargi komai!
If not, sai na fasa miki kai da bindigar nan”
Jiki na rawa Umma ta hau kiran Junaidu bayan ya umarceta data saka wayar a handsfree….
Sai da ta kusan katsewa tukunna ya d’auka!
Daga muryarshi zaka fahimci bacci yake yi..
“Kana Ina?”
tace mishi.
Shiruuu, yayi. Chaan! Yace
“I don’t really know!
Ina zuwa, zan kira ki”
Har zai kashe tace “dan Allah duk inda kake kazo yanzun nan kaji??”
“To” kawai yace sannan ya tsinke wayar.
Minti talatin mutumin ya bayar, dan haka yana cika yace “Umma ta sake kiran shi”…
Misscalls biyar tayi mishi bai d’auka ba, tana shirin yin na shidda suka ji k’arar parking d’in mota! Bai dad’e ba ya shigo cikin gidan…
Kayan jikinshi ne na jiya da yamma a jikinsa, amman kamar harda jini jini sannan duk ya yamushe kamar wanda yayi kokawa.
Gabanshi ne ya fad’i dan daman tun a waje yayi karo da wasu sojojin, a tunanin shi ba gidan suka zo ba amma yanzu kam ya tabbatar gidan nasu aka zo.
Dan haka ya k’araso da wuri!
Yana zuwa yana k’ok’arin yiwa su Umma magana sojojin suka rufar mishi suka hau k’ok’arin datsa mishi ankwa!
Ganin haka yasa gaba d’aya suka fashe da kuka har Mama….
Da kyar Sakina ta iya tambayarsu ‘ina zasu kaishi?’.
Ba b’ata lokaci mutumin yace mata “K’irik’iri maximum security prison!”
Babu irin kuka da burgimar da Umma bata yi ba har waje amman haka aka saka shi a mota aka tafi dashi!
Duk ta tara jama’a.
Shi kam Junaidu yama kasa magana dan gaba d’aya kanshi a d’aure yake…
Da kyar su Mama suka ja Umma suka maida gida sannan Mama ta kira Baba da su Kaka ta gaya musu halin da ake ciki.
BULAMA ✍️.
So da Buri
Free Book
29
Kafin minti ashirin Kaka, Madu, Shuwa, Baaba Talatu, Baaba Laraba da K’asimu sun k’araso cikin gidan!.
Baaba Laraba sai lallashin y’arta take yi itama tana nata kukan.
Baba ne ya shigo a k’arshe daman shi ake jira, dan haka yana zuwa su Kaka sukace “ba b’ata lokaci, bara a bi sahun su…”.
Sai a lokacin tukunna Sakina tayi magana, tace
“Sun tafi da shi Lagos fa!”.
Wani uban ashaar!! K’asimu ya buga sannan yace
“Wai wannan wanne irin rashin mutunci ne!
Haka kurum sun zo sun tafi da Yaro, kuma bama zasu barshi a nan ba sun kama sun kaishi har Lagos!! Sai kace wanda akace yayi kisan kai!
Sun fad’a muku laifin da yayi??”.
Cikin Kuka Hudan ta share hawayenta sannan tace
“A jikin takardan cewa aka yi wai ‘sun yi fashi su uku a gidan cheif justice jiya kuma sun kasheshi sun kashe y’ay’an shi hud’u!”.
Salati tsakar gidan ya d’auka, gaba d’aya. Baba kuwa dab’ass!! Haka ya zauna a k’asa…
Da sauri Umma tace “wallahi k’arya ne, sharri aka yi mishi, Junaidu tun yana Yaro ko cinnaka idan ya cije shi baya kashewa ballantana mutum, wallahi k’arya ne.”
Kaka ne yace “Sadiya ki yi shiru, kowa anan ya san k’arya ne, abun da ya kamacemu yanzu shine addua sai kuma mu nemo lawyer mu fara k’ok’arin fitar da shi ko?
Tunda kunga har an tafi dashi.”
…..
Nan suka hau shirye shirye aka ware masu tafiya Lagos d’in, sannan suka kira Ya Jamilu (Yayan Baba) shima.
Kuma suka nemo lawyer sannan aka yi shirin tafiya…..
Gidan Ummu za su fara zuwa su tambayi Mijinta akan ya barta a tafi da ita tunda lawyer ce itama mai zaman kanta..
Hakan kuwa aka yi a ranar zasu bishi.
Sai da suka raba sauk’ar Al Qurani da addu’o’i a wajaje daban daban, sannan suka d’au azumi kaff d’insu, har Jalila wadda rabonta da azumi har ta manta wai tana da ulcer Umma kuwa ko da yaushe cewa take yi “ai Allah ma ya ga zuciyarta kuma shine ya d’aura mata rashin lafiyar”.
Baba, Madu, Ummu, Kaka sai d’ayan lawyern da aka tafi da shi ne suka kama hanyar Lagos, sai washegarin ranar tukunna suka samu kansu bayan sunyi settling a hotel d’in da suka kama lokacin
Ya Jamilu shima ya k’araso dan haka ba tare da b’ata lokaci ba suka nufi inda aka kaishi!.
A nan ran Kaka ya sake b’aci da yaga wajen da aka kaishi d’in! Shi da ba a gama tabbatar da laifin shi ba saboda Allah meyasa zasu kawoshi prison?!
Haka nan yayita fad’a su Ummu suna bashi hak’uri… da kyar yayi shiru suka nufi gate d’in..
Kalar binciken da ake yi musu duk wanda ya gani zai yi tunanin ‘sun zo ganin wani hamshak’in d’an ta’adda ne’. Kuma dukda haka cewa akayi “sai dai mutum uku su shiga ba zai yiu su shiga su duka ba!”.
Baba, Ummu sai d’ayan lawyer d’in da aka tafi da shi ne suka shiga, shi kam Ya Jamilu ID card kawai ya nuna musu ya wuce…
Bayan y’an gwaje gwaje aka kaisu wajen zama (chan gaba da parking lot) aka ce “su jira shi a nan”
Anfi 30 minutes tukunna aka fito da shi.
Daga nesa da ya taho basu gane sa ba sai da aka matso dashi aka zaunar, tukunna.
Kuka kawai Baba yasa yayi saurin tashi a wajen.
Mai tsaron da ya kawo shi ne ya had’asu ya bashi iya lokutan da yake dasu sannan yad’an koma gefe kad’an ya tsaya.
Ganin basu da isheshshen lokaci yasa Ummu tace
“Junaidu, how are you?”
Ahankali muryar shi baya fita sosai yace
“Alhamdulillah”
Ba tare da b’ata lokaci ba tace
“ya aka yi? Mai
ya faru? Me
ka sani?”.
D’an gyara zama yayi tukunna ya fara magana…..
“…...shekaran jiya da daddare ina d’akin Abokina.
Ba a Kano yake ba, a nan Lagos yake, amma yana da apartment a Kano d’in.
Shekaran jiyan ya kira ni yace mini ‘zai shigo gari amman a jiya zai koma kuma akwai wani aiki da za muyi akwai samu a ciki sosai!
In da hali yana son ganina sharp sharp’.
Nan da nan nace mishi gani nan zuwa.
Ina zuwa ba tare da b’ata lokaci ba ya hau yi mini bayanin business d’in..
..’Wake ne zamu kawo daga Taraba, ko wanne a kan 9k zamu siya amman idan yazo Kano zamu iya siyarwa a kan 23k!
Kuma kud’in mota dududu bai fi mu biya dubu arba’in ba dan ya san wani me mota da suke irin wannan harkar, sannan za a kawo mana buhu sama da d’ari, a mota daya!’.
Nan da nan na amince…
Muna cikin maganar wata ta shigo har d’akin ta kawo mana Lemo..
Ban kawo komai a raina ba
dan irin gidan hayan nan yake kowa da dakinshi, da band’aki mai kyau sosai,
compound dinsu ne kawai d’aya, and tsarin d’akin har da d’an mini kitchen a ta chan gefe da d’an k’aramin dining kamar dai na turawa.
Na san shi, bashi da sakewa da mutum bashi da saurin yarda in ba wai ya san ka sosai ba!
Yadda suke wasa da barkwanci da wadda ta kawo lemon yasa na gane ya santa sosai shiyasa na aminta ba sha…
Amman wani abun mamaki
sip d’aya kawai nayi wa lemon ko ciki na bana jin ya k’arasa shiga na fara ganin uku uku!
Daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba.......
K’arar k’aramar wayata ce ta farkar dani daga wani irin bacci…
Mamakin d’akin da na tsinci kaina na dinga yi dan ban san inane ba!
Amman har da mukullin mota na a hannu na. Sai dai babu wallet d’ina kuma ba babbar wayata.
Yadda naji muryar Umma a waya ne ya sanya nayi saurin fitowa, ban ma san layin ba!
Gidane mai bene mai kyau sosai amman duk k’ofofin a bud’e da alama an bud’e mini ne dan in fita!.
Ina fitowa naga motata a parke, dan haka nayi gaggawar shiga na taho…
Sai da na fito titi tukunna na gane ashe a chan cikin Farawa nake.........
Tun lokacin da suka taho dani kwakwalwata take min flashin wasu abubuwa kamar mafarki
Amman na gane a shekaran jiya abun ya faru dan da kayan nan na jikina nake ganina!”.
Ajjiyar zuciya Ummu ta sauk’e sannan tace “suna interrogating d’inka ne?”
“Sosai ma!” yace, sannan yaci gaba “In fact sai sun dake ni ma idan na suma most in zan farfad’o ne memories d’in suke flashing…
Amman d’azu da safe around 8 sun kawo wasu takardu
har da flash!
Ina wajen suka ce a maidani ciki tou tun daga lokacin basu sake yi min komai ba.
D’ayan d’an sandan ne yake ce min wai ‘Allah ya taimakeni amman still in ci gaba da addu a’.”
Sauke ajiyar zuciya lawyer d’in da Ummu suka yi a tare bayan sun gama rubuce rubucen su!..
Tabbas this is a very serious case, kisan kai ga fashi, ko da ace bai yi komai ba in dai dashi aka je wajen to hukuncinshi d’aya ne da waenda suka yi aikin, wanda definitely ‘kisa’ ne!.
Maganar shi ce ta dawo da Ummu daga duniyar tunanin data tafi jin yana cewa
“Ummu na rantse da Allah gaskiya na fad’a miki duk maganar nan
Wallahi ban tab’a fashi ba, ballantana kisan kai, ko bayan rai na, ki fad’awa Hudan wannan maganar, wallahi ni ba d’an fashi bane ba!”
Yana gama fad’in haka ya fashe da kuka.
Tausayin shi ne ya sa Ummu itama ta fara hawaye..
Tabbas ta yarda da Junaidu to amman wannan k’atamurmurar Allah kad’ai ne zai fitar da shi!
Dan bama taga ta inda zasu fara neman evidence domin kare shi ba!.
Wani mutum sanye cikin suit da sojoji biyu a gefe da gefen shi ne ya tunkaro su.
Suna hangoshi Ummu tayi saurin goge hawayenta sannan suka mik’e tsaye.
Ba tare da b’ata lokaci ba ya cewa su Ummu su biyoshi sannan a mayar da Junaidu inda aka d’auko shi
..........
Bayan kamar 2 hours su Ummu suka fito suka tarar da su Madu a inda suka barsu.
Suna ganin su tun kafin su k’arasa wajen motar su suka iso garesu suka hau tambayarsu halin da ake ciki
D’ayar lawyer d’inne yace musu “su k’arasa mota za suyi musu bayani a chan..
Ganin basu fito tare da Junaidun ba gashi kuma sun k’i yi musu bayani ya sanya tun a nan jikin su Madu yayi sanyi.
Ko a motar ma Ummu da taa yunk’ura zata fara bayani sai kuma tayi shiru dan bama ta san ta ina zata fara ba!
Sai da suka k’arasa hotel d’in, bayan sun fiffito Kaka yace “su je garden, su tattauna a chan!”
Zama suka yi aka kawo musu d’an abun sha tukunna bayan sun huta Ummu tace
“Kaka Junaidu is innocent! duk da cewa na san duk mun san da hakan amma yanzu haka suma mutanen da kansu sun san cewa bashi da laifin komai.”
“Alhamdulillah”
Gaba d’ayansu suka furta
kafin Kaka yace “tou dan maiyasa suka kamashi saboda Allah? Sannan maiyasa baku taho da shi ba?”.
D’ayan lawyer d’in ne yace
“A jiya da suka zo suka tafi da shi basu san babu shi a laifin ba!
Asalima shine prime suspect saboda wayarshi da wallet d’inshi dake a wajen sannan bindigar da aka yi amfani da ita aka harbi mutumin da aka duba hannun Junaidu ne ya fito a jiki…
Babu kalar duka da horon da basuyi mishi ba amman shi dai magana d’aya yake maimaita musu, itace maganar daya fad’a mana d’azu ni da Ummu
‘He’s innocent!’
iya abunda ya faru da shi na gaskiya yake fada..
Shiyasa suka d’an saka kokwonta a lamarin.
Kuma tun jiya da daddare suka tsananta bincike a gidan mutumin…nan kuwa aka samu wata b’oyayyiyar camera a parlour wadda babu wanda ya isa ya ganta, dan su kansu sai da camera detector tukunna suka iya ganota a jikin chandelier!
Nan da nan kuwa suka d’auka suka turo nan.
D’azu muna tare da shi Junaidun, aka zo aka kira mu, a ofice d’in muka samu Ya Jamilu shima..
Ba tare da b’ata lokaci ba mutumin ya nuna mana video din......
…’Shi Junaidu a sume ma wasu mutane guda biyu da mask suka shiga da shi, bayan wasu k’arti biyar sun firfito da CJ d’in da Yaran shi sun d’add’aure,
ana shiga da shi d’ayan yayi mishi wata allura sannan ya hau yayyafa mishi ruwa yana marin gefen fuskarshi…
Da kyar ya farka sai dai kana ganinshi ka san baya hayyacinshi sannan suna mik’ar dashi tsaye ya koma ya sume…
Babu yadda ba suyi da shi ba amma yak’i farkawa.
Nan d’ayan wanda suka shigo dashi ya koma gefe ya fara waya, bama jin abunda suke fad’a kwata kwata saboda camerar babu voice.
Yana gama wayar ya d’auki video d’in Junaidu da parlourn ya turawa wanda muke tunanin ya gama waya dashi.
After some minutes aka sake kiranshi, yana gama wayar ya zo ya kama hannun Junaidu (bayan ya sakawa nashi hannun socks da leda) ya damk’e bindigar da hannun Junaidu wanda yake ta baccinshi..sai dai okaci zuwa lokaci ya kan d’an bud’e idanununshi sai kuma ya maidasu ya kulle…
Bayan sun damk’a mishi bindigar ba tare da b’ata lokaci ba suka saita kan CJ d’in suka harba daga nan ragowar suka harharbe Yaransa…
Da alama k’arar jiniya sukaji dan lokaci d’aya suka rikice!
Kan kujera d’ayan ya hau ya dan daddaki p.o.p d’in wajen kamar yana knocking
Daga nan yasa hannu ya d’an fara jaaaa!
Kamar akwai mai taimaka mishi a take suka janye ya d’aura a kan kujera.
Ladder, d’in da aka zuro mishi ne yasa muka gane akai wani a saman a cikin ceiling d’in.
Sai da d’ayan ya cire wallet da wayar Junaidu ya yar a tsakar falon da bindigar da aka kashe CJ d’in da ita sannan ya ciccib’eshi ya fara haurawa da shi saman..
Yana gama hawa ragowar ma suka ciccib’i maka makan akwatunan da suke a parlourn da alama kud’ad’e ne a ciki suka bi bayanshi suka haye.
Last one d’in ne ya d’auko dakin pop d’in da suka cire
suka taimaka mishi suka jaa wajen suka rufe tsaff yadda duk k’urillar mutum bai isa ya gane wajen a fashe yake ba....”
Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan yace
“Ba yadda bamu yi da shi akan ya barmu mu tafi da Junaidu ba amman yace mana “kasancewar wanda aka kashe babban mutum ne! Wallahi an basu kwakkwarar doka akan kar a sakeshi har sai an gama case d’in!
Kuma kafin ma a samu ayi settling a gama mourning rasuwar nan sai anyi wajen wata d’aya ko sama da haka.
Guda biyu masu mask d’in an rasa su, dan waenda akayi fashin da su ragowar mutane ukun d’ayan tun a jiya aka ga gawar shi ba a san wa ya kashesa ba!
Su kuma ragowar biyun awa biyu da suka wuce aka samesu da kyar a Bauchi
An harbi d’ayan dan yayi attempting guduwa ne
Shi kuma d’ayan yace ‘wallahi bai tab’a ganinsu ba bai san ya yanayin fuskarsu ta asali take
ba! Dan tun a
lokacin da suka zo musu da tayin aikin ma da mask a fuskokinsu….dan haka basu tab’a ganin fuskokinsu ba kuma basu damu da su gani d’in ba saboda su ta kud’in kawai suke kuma sunyi musu alk’awarin in dai aka yi fashin duk kud’in da aka samu nasu ne dan su ba zasu tab’a ko sisi a ciki ba, basa buk’ata......”
Kuka Baba ya saka kafin yace
“Yanzu kenan Junaidu a wannan waje zai yi ta zama kenan har sai an yankewa waenchan hukuncinshi?? Har zuwa yaushe kenan?”
Ummu ce ta share hawayenta kafin tace
“Wallahi Baba muma bamu sani ba.
Kawai dai mu ci gaba da addu’a, dan na tabbatar addu armu ce da taimakon Ubangiji ya sa aka ga wannan b’oyayyiyar camerar!
Kuma mutumin yayi min alk’awarin ba zai bari a bashi horo ba ko ta yaya.
Dan a office d’in wani Abokin Ya Jamilu ma suka nuna mana suka ce zai ci gaba da zama.
Sannan Ya Jamilu har yanzu yana chan yana dubawa in an samu rara anytime from now zasu iya tahowa, in kuma sun k’i yarda to sai dai mu yi hak’uri mutu ta addua. Dan mutumin yace zuwa gobe za‘a rufe ganin su sai ranar da za a fara zuwa kotu!
So in dai Ya Jamilu bai dace a yau ba, sai dai mu jira ranar.
Amman mutumin yayi mana alk’awari ya sake yi mana alkawari a kan ba zai bari a cutar da shi ko ya wahala ba..........”
Sun yi zaman jira kam har washegari, da safe ganin Ya Jamilu ya dawo shi kad’ai yasa duk jikinsu yayi sanyi.
Haka nan su Ummu suna ji suna gani washegari suka shirya suka tafi suka bar Junaidu a Lagos tare da addu’o’i