Showing 63001 words to 66000 words out of 124668 words
Chapter 22 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
ba.
Bilkisu a lokacin Yaranta biyu
Itama ta kammala karatunta na law tana aikin ta!
Kowa dai da y’ar sana’ar shi ko wani means of samun kud’i dan hatta Sadiya business d’in kaya take yi, amma ita Maryam a duk lokacin da tace tana son yin karatu ko sana’a tashi d’aya Ya Usman zai ce “a’a!!
Salon tayi kud’i ta gujesa!.”
Ranar da abun ya isheta daman ko kayan sallah baya yi musu ita da Huda idan ka gansu kullum cikin tsumma, Baba Bashir da Baba Talatu ne suke dan k’ok’artawa suyi musu sai ko Bilkisu,
hakan yasa ta d’auki waya ta kira Baba Talatu tana kuka tana gaya mata.
Ashe Shuwa na gefen ta a lokacin suna tare
Baba Talatu batayi auni ba taji Shuwa ta karb’e wayar!
Maryam zata iya cewa ta manta rabon da taji muryar Shuwa amma maimakon magana mai dad’i sai kawai Shuwan ta rufeta da fad’a ko gaisuwarta bata tsaya amsawaba, tace hau fad’a tana cewa
“Ai ta riga tabar gini tun ran zane! Lokacin da su Zainab da Bilkisu suka yi nasu karatun a lokacin daya dace ai ita saurayi tabi, sai yanzu god’ai god’ai da itane zata wani ce tanaso zata koma makaranta??!.
Kawai ta zauna idan Usman d’in yaga dama yaayi mata to, idan kuma bai yi mata ba ta hak’ura, sannan tama daina k’ok’arin had’a kanta ‘jahila! mara aikin yi! Da su Bilkisu masu ilimi masu aikin yi dan indai tace haka zata yi to kuwa wahala zata sha!.”…
Tana gama fad’in haka ta kashe wayar.
Haka rayuwa taci gaba su Shuwa ko k’ofar gidansu har yau har gobe sun hana Maryam zuwa ballantana Huda, ko Bilkisu ta je gani idan emergency ya taso sai dai su had’u a waje ko a gidan Baba Bashir..
Sunce ‘ai tun ranar data saka k’afa tabi Abba suka cireta a matsayin y’arsu, su bama su da ita ba.…..
Ana haka rana d’aya kawai Usman Ya mayar da Sadiya aka d’aura aure.
Da farko su Baba Bashir sun so hanawa amman yadda ya nuna kamar idan bai auri Sadiya a ranar ba to tabbas zai iya mutuwa! Ne ya sanya kawai aka d’aura musu aure ta tare…
Tun daga wannan lokacin kuma Ya Usman d’in sai ya zamana kamar irin tsoron Sadiyar ma yake yi
,baya son ganin b’acin ranta baya iya hanata abu.
Tana dawowa gidan ta janye y’ay’anta duk wahalar su da Maryam taci ba ayi shekara uku ba gaba d’aya hankali Jalila ya koma kan Mahaifiyarta, tun bata kulata har ta fara kulata daga baya data gane uwar ta kuma sai ta fara yiwa Maryam rashin kunya da rashin mutunci kala kala tun bama data lura da Maryam d’in bata so a tab’a Huda ba, nan ta samu abunyi…
Saboda ita aka cire Huda daga makarantar islamiyyar
da suke yi aka chanjamata
boko kuwa sai da suka san yadda suka yi k’iri k’iri aka hanata zuwa..
Junaidu tun yana dukan Jalila har Sadiya ta bud’e mishi ido ya daina.
Haka kurum sai su rufe Huda da duka babu laifin tsaye babu na zaune..
Maryam bata samun sauk’i a kaf fad’in duniyar nan sai in tana karatun Alqurani ko kuma idan Bilkisu da Yaranta sun zo
Sakina itace Babba watanni uku Hudan ta bata amman irin Yaran nanne masu garin jiki
shiyasa ta zama kamar ma ta girmi Hudan, sai k’anwarta
Sumayya.
Sakina irin Yaran nan ne da basa barin takwana, takan zo wasu lokutan tayi weekend a gidan itama Hudan takan je musu,
ammanfa duk ranar da Sakina tazo sai an kwashi y’an kallo ita da Jalila duk da kuwa Jalilan mugun duka take yi mata amman takanci nasara itama akanta itama wasu lokutan.
Akwai ranar da suka yi wani dambe! Jalila tayi mata duka ita kuma da taji zafi ta rarumi dutse ta bugawa Jalilan a kai wanda har saida ya kaita ga suma.
Ya Usman da Sadiya kuwa suka d’aukowa Sakina y’an sanda, su kuma y’an sanda da son banza suka zo zasu tafi da ita.
Suna shirin sakata a mota kenan daman Babansu ya taho d’aukarsu kuma Mama ta kirasa dan haka ya k’araso a rikice.
Ya ji haushin abun sosai dan haka fad’an ya koma na manya akai baram baram da shi da Ya Usman.
Tun daga nan suka hana Yaran su zuwa gidajensu.
Shiyasa ko lokacin da Bilkisu tace zata d’auki Huda Shuwa ta hanata a cewarta ba zata bari matsalar Maryam ta shafi aurenta ba.................
………………………………
Mama bataji shigowar Sakina da Ummu ba, dafa ta d’in da
Ummu tayi ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin data lulaaa..
A hankali ta juyo gareta tana kallonta fuskarta sharkaf da hawaye.
Numfashi Ummu ta fesar kafin ta tsugunna a gabanta sannan ta shiga share mata hawayen har sai da taga tayi shiru tana sauk’e ajiyar zuciya…
Motsa hannun da Huda tayi ne ya katsewa Ummu maganar da take shirin farawa.
..A hankali take bud’e idanuwanta da suka chanza kala suka k’ank’ance.
Tana gama bud’ewa hawaye suka shiga zubo mata.
Rad’ad’i take ji har yanzu a wajen da Ya Ja’afar ya daketa da katako ga ciwon kan da take ji kamar zata mutu!.
Sakina ce ta hau kan gadon ta zauna ta wajen kanta kafin ta kamo hannunta ta kuma shiga share mata hawaye tana cewa “ta yi hak’uri tayi shiru karta k’arawa kanta ciwon.”
Da kyar dai itama Hudan tayi shiru.
Bayan Likita ta shigone ta chanja mata d’aurin ruwa sannan tayi mata wasu allurai tace “ba zai yiu a sallamesu yau ba sai dai gobe”
Kasancewar dare yayi sosai hakan ya sanya Mama ta lallab’a su Ummu suka wuce gida.
Ya junaidu kam sai da ya tabbatar sun kintsa ya nemo musu duk abun buk’ata tukunna ya wuce
shima.
Washegari da sassafe su Ummu suka zo musu da breakfast, bayan sun biya gidan Hajiya sun ajjiye Sumayya dan itama jikin nata sai a hankali.
Kamar jiya yau ma har dare Ummu tana wajensu, saboda zazzab’in da ya sake lullub’e Hudan ya sanya Likitocin suka fasa sallamarsu aka kuma k’ara mata allurai masu nauyi da magunguna ta wuni tana barci. Sakina Ummu ta sake aikawa taje gida tayo musu girki ta dawo.
Suna zaune wajajen 8 daman kamar Mama ta sani tana ta cewa Ummu ta tashi su tafi sa dawo gobe amman tak’i!
Kawai sai ga kiran Hajiya Shuwa, Ummu na d’auka ko gaisuwarta bata amsaba ta hau zazzaga mata bala’i
tana cewa “taya zata tafi ta bar mara lafiya haka!?
Tabi duk ta wani d’aga hankalinta akan wata Huda, koma meye ya sameta ai sune suka jawa kansu!
Tayi maza ta dawo yanzun nan idan ba hakaba ranta sai ya b’aci!”.
Sarai Mama taji abinda Hajiya tace saboda wayar Ummu irin mai volume d’in nan ce
amman sai ta nuna kamar bata ji ba.
Ummu kam jikinta duk yayi sanyi ko tambayar jikin Huda Hajiya bata tsaya yiba tace a taho a barsu su suka sani.
Haka nan dai jiki duk ba kwari, ta d’auki jakarta bayan ta tabbatar ta biya komai kuma tabar musu isheshshen kud’i a hannu da alk’awarin gobe da sassafe za su dawo In sha Allah.
Suna shirin fita Junaidu kuma yana shirin shigowa da ledoji a hannunshi. Gaisawa suka yi da Ummu sannan yayi mata sai da safe ya shigo.
A gefen gadon wajen k’afafunta ya nemi waje ya zauna bayan ya gaida Mama.
A hankali yake kallonta yana jin wani zafi a ranshi kafin yace mata “ya jikin?”.
Sai da ta gaisheshi bata damu da rashin amsawar shi ba tace masa “da sauk’i”
Shiru d’akin yayi babu mai cewa komai kafin a hankali Hudan tace “Mama zan yi sallah.”
“To”
Maman tace sannan ta mik’e ta fara k’ok’arin d’aga Hudan wadda azaba tasa ta fara yin wani kuka mara sauti abin tausayi.
Runtse ido Junaidu yayi kafin yace “Mama idan ba zata iya ba gara kawai a nemo kwano da ruwa, tayi alwala anan tunda daman yanzu jikin nata zai yi tsami sosai.”
Hakan kuwan akayi da kyar ta iya zama sannan ta samu tayi alwala tayi sallar.
Bayan ta idar ne ya janyo ledojin da ya shigo dasu ya fara bubbud’ewa….
D’ayan fresh milk ne da su maltina, sau d’ayan kuma gasassun kaji ne mai yawa, da zafin su sai maik’o da kamshi suke yi.
Mik’ewa yayi ya d’auko plate da cup, kazan ya fara zuba mata kamar rabi, har ya d’auko
fresh milk zai zuba mata sai kuma ya d’ago manyan idanuwanshi ya kalleta yace
“Me zaki sha??”
Cike da jin kunya, dan ya kamata tana kallon kazar daya zuba mata
ta nuna mishi Maltina.
Murmushi yayi sannan ya ajjiye fresh milk d’in ya d’auki Maltina ya zuba mata kafin ya sake mik’ewa ya dawo kusa da ita ya ajjiye plate d’in akan cinyarta, cup d’in kuma a kan drawer gefen gadon, shi kuma ya tsaya a kanta kafin yace “Bismillah”
Har ga Allah so yake yad’an zauna kusa da ita amman kuma yana jin kunyar Mama.
Da kyar ta iya cin rabi, daga nan tace masa “ta k’oshi” dan ji tayi cikinta har ya cika taf!
Amma da farko lokacin da yana zubawa kamar tace masa ya juye duka.
Gyara tsayuwar shi yayi sannan yace “ko ta cinye ko ya d’ura mata!”
Ba yadda ta iya haka ta dinga turawa saida yaga tana k’ok’arin yin amai tukunna ya kyaleta.
Gaba d’aya Mama itama a takure take, kayana kunya da nauyi duk ya kanainaiyeta.
Har ga Allah idan aka tsareta ba zata iya nuna makusa guda d’aya a tare da Junaidu ba.
Yaron yana da hankali, gashi yayi karatun shi yanzu haka ma masters yake yi, part time.
Yana kuma sana’a dan yana da zuciyar nema, sanna ta san yana son Hudan tsakaninsa da Allah,sosai.
To amman matsalar d’aya itace iyayen shi, da ace Junaidu ba d’an Sadiya da Usman baneba da ita da kanta zata tsaya tsayin daka ya auri Huda.
Tsakanin d’aa da uwa sai Allah dan ta d’auki lesson akan Jalila, duk runtsi wata rana dole yabi maganar Mahaifiyar shi kuma itama Hudan dole ta yiwa Sadiya biyayya tunda uwar Mijinta ce……ta san Huda ba k’aramin wahala zata sha a hannun Sadiyar ba…
Ita kuwa tana ganin wahalar da Huda ta sha daga yarintarta kawo yanzu yaci ace ta samu kwanciyar hankali a gidan aurenta!
Apart from all this ma, ta san Sadiya da Usman ba zasu tab’a yadda da auren ba sai dai wani tsananin rabo..
Sallamar Baba Bashir da Baaba Talatu ce ta katse mata tunaninta..ta yi saurin d’agowa
tana kallon k’ofa.........
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
21
Murmushi Mama tayi kafin ta mik’e ta shiga yi musu ‘sannu da zuwa’.
Baba Bashir ta jawa kujera ya zauna, Baaba Talatu da d’an gidan Ya Jamilu mai sunan Madu su kuma ta shimfid’a musu darduma.
Bayan sun gaggaisa ne Kaka (Baba Bashir) ya ke tambayar Mama “mai ya faru?,d’azu Bilkisu ta kira take ce musu Hudan na asibiti.”
Shiru Maama tayi dan ita harga Allah bata san ta ina zata fara ba, gashi tanajin kunyar su.
Junaidu ne yayi gyaran murya, ya hau zayyano musu duk abunda ya faru.
Ai kuwa nan Kaka ya hau fad’a! Ta inda yake shiga bata nan yake fita ba
A take ya sa aka kira mishi Baba yace masa “yazo yanzun nan yana son ganinshi a asibitin da aka kwantar da Huda.”
Bayan kamar minti biyu Baba ya kira Junaidu ya tambayeshi “ko ya san sunan asibitin?” nan ya fad’a mishi harda number d’akin.
Suna zaune Baaba Talatu itama tanata bawa Mama baki
Baba ya turo k’ofa da sallama a bakinsa ya shigo.
Tun kafin ya zauna Kaka yace
“Wato Usman ban isa da kai ba ko?
Wato na hana su Sadiya zaluntar Yarinyar nan shine ka b’ullo ta hannun Ja’afar ko!?
Tayaya ma zaka bari shi da ba ishashshiyar nutsuwa garesa ba ya bugi Yarinya haka?!
Haba Usman, katako fa mai k’usoshi a jiki ya maka mata, a ciki!!!.
Yaro gaba daya duk ya bi ya haukace? Yo hauka mana, idan ba hauka ba wa zai yi wannan ta’asar saboda Allah?
Sannan ku kuma kai da uwar sa sam baku son kuji laifinshi.
Lokacin da yake hannun Maryam ai tun farkon fara lalacewar shi sai da ta nutsar da shi amma tun dawowar Sadiya gaba d’aya ya sake tab’arb’arewa!
Daga ya saci akuya sai ya saci kaza!
Shekaran jiya sai da aka kawo mana k’arar sa akan ya saci zakara!. Kuma abun haushi naira ashirin ko talatin yake saidawa k’arshen tsadar d’ari ko d’ari da hamsin.
Mai unguwa da kanshi yace mini ‘dan kawai ya ga jikanmu ne shiyasa yake d’aga mishi k’afa.
Usman kai ka san a irin unguwar da muke Abu kad’an suke jira a fara gustiri tsoma!
Dan haka tunda kun kasa tsawatar masa ni zan dauk’i mataki! Tun kafin yaje ya janyo mana maganar da tafi wannan in dai baku tashi tsaye a kanshi ya shiryu ba to wallahi kaji na rantse ‘Ni da kaina nan zan kaishi gidan mahaukata!!’.”
Da sauri Baba ya d’ago ya kalleshi..
“Kwarai kuwa!”
Shine abinda Kaka ya fad’a kafin Baaba Talatu itama ta d’aura da cewa
“Yo ai Usman dole a kai sa gidan mahaukata, domin kuwa kwata kwata Jaafar baya yin abun masu hankali, kuma
gashi kun barshi a gida yana shirin yin kisan kai!!
Idan k’ungiyar masu kare lafiyar d’an Adam taji maganar nan Ina mai tabbatar maka da ‘su zasu fara kaishi kafin mu mu kaishi’!
Shekaran jiya fa da Jamilu da iyalinshi suka zo…
ga Abba k’arami anan ka tambayeshi kaji
‘a bakin kwata suka sami Jaafar ya tsugunna yana ta shak’a!’ Babbar kwatar layi mai uban d’oyi.
Yau Huda ya yiwa zamu iya rufa asiri, gobe ka san wa zai yiwa??
Gaskiya ce muke gaya maka tun wuri kusan abunyi kai da uwarsa da bakwasan jin laifin shi….”
Shiru d’akin ya d’auka, a hankali Kaka ya mik’e ya isa inda Hudan take…..shafa kanta yayi yai mata sannu sannan ya cewa Abba k’arami ”su taso su tafi.”
Baba talatu ce itama ta mik’e tana mai cewa “Yanzu inda ace Jaafar mai hankali ne ai da tuni shima ya tara iyali
Kalli Abba shekara d’aya aka haifesu amma shi y’ay’ansa biyu….
Idan kuka bari so ya rufe muku ido zaku yi dana sani a gaba, dan gaba d’aya rayuwarshi kuke neman lalatawa ba tare da kun sani ba.”
Tana gama fad’in haka itama ta yiwa Mama sai da safe sannan tayi hanyar fita tana cewa “ita kuma Hudan idan ta warke ki turo min ita inji waye wannan Yaron da suka ce ya sakota a napep d’in.”
“To in sha Allah”
Shine abinda Maama tace
tana mai sake yi mata “sai da safe”
Har zata fita sai kuma ta juyo tace mata “Sadiyar sun zo??”
Shiruuu Mama tayi nanma ta kasa magana.
Girgiza kai kawai Baaba Talatun tayi tace “Hmmm”
Daga haka ta sa kai ta fita.
Jikin Mama har rawa yake yi, dan a tunanin ta Baba zai sauk’e mata buhun masifa ne
amman sai taga kawai ya juya shima yabi bayansu ya fita.
Junaidu ne yace
“Ai da idan ina magana akan Ya Ja’afar gani suke yi abin kamar wasa ne..
Gashi yanzu daga anyi zancen ‘gidan mahaukata’ hankalinsa duk ya tashi! Tun ba a je ko’ina ba.”
“Allah ya kyauta” shine abinda Mama tace sannan
suka d’an shiga tab’a hira ita da Junaidun dan already Hudan tayi bacci.
Sai wajen 10:30 tukunna da kyar Mama ta lallab’a shi ya tafi dan daa cewa yayi “a wajen zai kwana”
Ita Mama da farko ma dariya ya bata sai da taga dagaske yake tukunna ta nuna mishi ba zai yiu ba….
Washegari da safe wajen k’arfe sha d’aya aka sallameta
bayan su Ummu sunzo da Sakina harda Sumayya wadda ta ji sauk’i. Ya Junaidu shima ya zo tare suka zo da matar Ya Jamilu da safe, su suka kawo musu abun kari, bata dad’e ba tace “ya mayar da ita saboda su fara shiri anjima zasu koma.” Ya tafi maidata dake motar mijinta sukai using, bai kai ga dawowa ba aka sallamesu.
A motar Mijin Ummu aka mayar da Huda gida, bayan
sun siya mata duk magungunanta.
Suna zuwa a bakin k’ofa suka tarar da Jalila tana zance da malamin maths d’insu, ko kallonsu bata yi ba haka ma ta nuna kamar bata san dasu a wajenba..da Ummu da Mama ne suka kamo Hudan tana tafiya da kyar, sai da suka zo
daff da su kawai Jalilan da doka tsaki ta tofar da yawu a daidai inda zasu taka su wuce su shiga cikin gidan!
Sakina ce ta yunk’ura zata tanka mata amman Ummu ta daka mata tsawa tace “ta wuce tayi ciki!”
Ba yadda ta iya dolenta tayi shiru, kamar zata fashe ta shige ciki tana gunguni…
Haka nan suka wuce ciki ko bi ta kan Jalilan basu yi ba.
Tun safe su Ummu basu tafi ba sai daff da Magriba..haka wuni sunata hira ana wasa da dariya a tsakaninsu, d’an uwa mai dad’i! Gaba d’aya sai Mama da Huda suka nemi damuwar su suka rasa……
Haka rayuwa taci gaba da tafiya….
Har Hudan ta warke a tsakanin
Sadiya ko Jalila ba wadda tace mata ci kanki!
Gidan kuwa haka nan ya koma kacha kacha dan Jalila ba gyarawa take yiba tace waec take yi itama bata da lokaci.
Ranar asabar da yamma Hudan ta dawo daga islamiyya kenan, Yaro yayi sallama yace “wai ana son ganin Hudan a waje”
Da k’arfi Jalila wadda take m cin abinci ta kware, sai da tayi kusan minti d’aya tana tari idanunta harda hawaye da kyar ta dawo dai dai.
Maganar da Yaron ya sake yi ne ya sanya Mama fitiwa tacewa Yaron “kaje kace inji wa?”
Fita yayi cikin k’ank’anin lokaci ya dawo yace “Yace wai ace mata Arshaad ne”
“To” kawai Mama tace sannan ta koma ciki ta shiga tambayar Huda wadda take chanja uniform d’inta “Waye Arshaad?”
Shiruuu! Hudan tayi kamar tana so ta tuna wani abun
chan ta d’ago ta cewa Maama “wannan mutumin da ya bani handkerchief d’inshi ne, ranar da su Ya Jalila suka aikeni siyo zob’o.”
Ajiyar xuciya Mama ta sauk’e sannan tace “ki maida mishi handkerchief d’insa sannan kice mishi baki fara zance ba!”
Zaro ido Huda tayi tace
“Mama bafa zance muka yi ba ranar ba ma, kuma yau ma ba zance yazo ba, ba saurayina bane ba.”
Kallonta Maman tayi sannan tace “kije ki gaya mishi haka ki dawo da wuri!.”
Tana gama fad’in hakan ta juya ta fita zuwa kitchen ba tare data tsaya sauraron amsar da Hudan taketa nanatawa