Showing 117001 words to 120000 words out of 124668 words
Chapter 40 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
tana cewa “In na dawo zan yi miki bayani”…
Sai dai kuma
tana zuwa gidansu Aslam d’in ta tarar su Gwaggo Asabe sun yowa Mommyn rakiya
Flight d’inta nan da awa d’aya (9:00pm) zai tashi!!
Lokacin appointment d’inta da Neurologist d’in da Granpa yayi mata booking yayi…
Kamar Mom ta had’iye zuciya haka taji, ba yadda ta iya haka nan ta hau yi musu fatan alkhairi suka wuce ita da Aaima. Flight d’in Abuja za su bi, idan sun sauk’a a Abujan Aaima zata wuce makaranta ita kuma Mommy su wuce tare da Dad…
BAYAN WATA D’AYA!
(After a month!!).
Da gudu Jalila ta fito daga d’akin Umma..
Bata kai ga k’arasawa band’akin da ta fito na niyyar zuwa ba! Ta hau kwarara aman da ya taho mata babu shiri
a nan bakin rijiyarsu wajen wanke wanke!.
Da sauri Mama ta fito daga d’aki jin mutum yana amai
Dai dai nan itama Umma ta fito da waya kare a kunnenta tana cewa
“Haba Zainab! tafiyar taku ba sai gobe ba?
Kiyi sauri kizo muje mu kaita asibitin mu dawo a san abunyi.
Kinga yanzun ma fa tana sa ruwa a bakinta kinganta ta fito ta hau amai!
Gara a yita a gama dan ni wallahi jikina ya na bani c.....”
Ganin Mama ne ya sanya ta had’iye ragowar maganar tata.
Ita kam Mama ta Jalila ma takeyi, dan haka tayi saurin k’arasawa inda take ta hau shafa mata baya tana yi mata sannu….
Dama fa ita kwana biyu ta d’an ga wasu changes a tattare da Jalilan
Kuma tana lura da yadda Umman ta hanata zaman tsakar gida kwata kwata! Maybe ko dan ta lura da kallon kurillar da take yiwa Jalilan ne? Oho!
Da kyar Jalila ta samu ta amayar da d’an ragowar ruwan da yake a cikin ta sannnan ta d’ago tana mayar da numfashi
Dai dai nan Umma ta k’araso wajen nasu tana hararar Mama..
Da mamaki Maman take k’arewa Jalilan kallo!..Tayi wani haske na ban mamaki
Bakinta sun yi pink sosai!
Sannan k’irjinta yayi mugun cika!
A hankali Mama da taji k’irjinta ya buga da k’arfi ta lumshe idanuwanta tace
“Innalillahi wa innailaihirrajiun”
Kafin ta bud’e su ta zubasu a kan Jalilan wadda itama ta kafeta da nata idanun…
A hankali Maman tace mata
“Sannu, me yake damunki?”
Jalila ancikin wata d’ayan nan ba k’aramin sanyi tayi ba,
yanayinta ma gaba d’aya ya sauya kamar ba Jalila ba..
Ta bud’e baki za tayi magana kenan Umma tace
“Ina ruwan ki!?
Sannan da kike wani salati
shin aljana kika gani ko me?
Kinga! Maryam!! wallahi ki fita a harkaata ni da y’ay’ana..
Ina jin ku jiya ke da Bilkisu kuna munafurcin Ja’afar
Bayan ke Huda ta fi sati bata a gidannan Allah kad’ai ya san inda ta tafi wannan karon!!
Ki fita a idona tun muna sheda juna wallahi….”
Tana ga fad’in haka ta jaa hannun Jalilan fuuuu suka shige d’aki.
Mama kam kasa motsi tayi a wajen…duk kalar tarin rashin d’aa’ar da Jalila ke zuba mata hakan bai hanata jin tsananin tausayinta ba!
Tabbas idan idanuwanta sun gane mata daidai to d’anyen ciki ta hango a jikin Jalila!
Bayan yadda ilahirin jikinta ya nuna
Aman da ta gama yi yanzu mai mugun k’arni ya sake tabbatar mata….
Salati kawai take yi tana sake nanatawa a cikin zuciyarta…
Ta ma kasa d’aga k’afafuwanta ta bar wajen!
Da kyar ta samu ta d’an motsa ta jawo ruwa a rijiya ta d’auraye wajen
daga nan ta sake luluwa duniyar tunani…..
A haka su Ummu suka shigo suka sameta.
Sai da su Sakina suka yi hugging d’inta tukunna tayi firgigit ta dawo daga duniyar tunanin data lulu.
Ummun ce ta d’an k’ura mata ido sanann tace
“Tunanin me kike yi haka?”
Wata nannauyar Ajiyar zuciya ta sauk’e kafin tace
“Ba komai”
Daga nan suka d’unguma suka yi d’aki.
Ba kalar tambayar da Ummu bata yi mata ba amman tace mata “ba komai” kawai!
Saboda hasashen alkhairi ake so a yayata, na sharri kuwa ba a fad’i!
Harshe na da kaifi!.
Ganin tak’i fad’a ya sanya Ummu kawai ta kyaleta
dan ta san da tanaso ta sani to da tuni ta fad’a matan..
Shiyasa bata sake yi mata maganar ba ta sako wani zancen ta hanyar cewa
“Mama anata shiri..
Gobe da sassafe duk zamu wuce.
Dan Allah ki zo kema mu tafi mana
Kin san In babu ke ba zan ji dad’in bikin ba.”
Murmushi Maman tayi kafin tace
“Bilkisu ke kad’ai fa kike ta gayyatata!
Jiya ina ji Zainab da Sadiya suna yada min magana bayan kin wuce..
A haka kikeso In kwashi k’afa in tafi bikin y’arta har Kaduna?
Besides kin san ba ishashshiyar lafiya gare ni ba those days
kar inje su yi mini wani abun itama Hajiya ta d’aura da nata inje jinina ya hau!.
Dan Allah na rok’eki da girman Allah ku barmu a nan Ai naji Baaba Talatu ma tace
‘In an d’aukota daga Kaduna a nan gidan Kaka za a fara sauk’a saboda y’an tsofaffin da basu je su Kadunan ba!
Bayan an d’auke su sai a wuce gidanta’.
Nayi miki alk’awarin k’arfe takwas zan shirya ga anko na nan ma na wunin kai amarya an d’inko…duk inda takwas da rabi tayi ina gidan Kaka kuna zuwa sai mu wuce tare gaba d’aya.
Banda abinki ma, In dai ke da Sakina kunje ai kamar munje ne ko?”
Ta k’arashe maganar da d’an murmushi a kan fuskarta.
Murmushi Ummun itama tayi.
Ba dan ransu ya so ba
haka suka hak’ura akabi tsarin yadda Maman tace…
Sakina itama daa cewa tayi ba zata je ba
Sai da Mama ta lallab’a ta tukunna ta yarda zata je d’in.
Kamar minti talatin da yin wayar Umma da Anty Zainab sai gata nan!
Tana shiga d’akin Umma tace
“Yauwa Zainab!
Na gode da kika bani lokacinki,
mu je ko?”
Tayi maganar tana k’ok’arin tashin Jalila wadda tayi bacci.
Dakatar da ita
Anty Zainab d’in tayi ta hanyar cewa
“Tsaya tukunna
Yanzun nan Baban Khadija ya kira yanata faman masifa
wai danginshi suna chan sun fara mitar ya uwar amarya har yanzu bata k’arasoba!
Yanzu haka da nake yi miki maganar nan drivern da akayi shata zai kaini Kaduna yana bakin k’ofar gidan Kaka yana jira!.
Yace ba zai you ince sai gobe zan je ba!
Dole in tafi a yau…
So kiyi hak’uri ba zan iya rakaki asibiti ba gaskiya
Amman ga wannan”
Tayi maganar tana zaro pt a jakaar ta, sannan ta ci gaba
“Yanzun nan na tsaya na siya na taho dashi..
Scanning ne kawai ba zai nuna ba!
Amman ciki in dai akwai shi ko na kwana biyar ne to zamu gani.
Tashe ta yanzun nan ta gwada mu gani.”
A hankali Umma ta sauk’e ajiyar zuciya sanann ta k’araso ta tada Jalila.
Dalla dalla Anty Zainab ta yiwa Jalila bayanin yadda zata yi amfani da abun
sannan ta d’aura da cewa
“In babu za muga layi d’aya
In kuma akwai za muga layi biyu”
Karb’a tayi ta fita zuwa band’aki!
Kamar minti biyar haka sai gata ta dawo..
Anty Zainab ta mik’awa, cikin rawar jiki Umma ma ta taso tazo ta hau lek’awa…
A tare suka saka salati kafin Umma ta zauna dab’ass!!! A k’asa ta d’aura hannu a ka ta fashe da kuka!.
Da sauri Anty Zainab ta tsugunna ta shiga lallashinta…
Ita kam Jalila tunda ta shigo ta mik’a musu suka karb’a ta wuce kan gado ta zauna ta rafka uban tagumi!
So take tayi kuka amman ta kasa…
Wani irin tuk’uk’i ne yake taso mata daga k’asan zuciyarta!
Inda ace zata ga Auwal yanzu wallahi da sai ta kasheshi!
Ba abunda yake b’ata mata rai irin yadda ya dinga muamala da ita a wulakance! Kamar ma irin kyamarta d’innan yake yi sai kace an yi mishi dole!.
Da kuma yadda ya fito k’iri k’iri ya zazzage ta ya gurza mata rashin mutunci!!!
Taya zata haifi cikin nan??
Ta san ko sama da k’asa zasu hadu Auwal ba zai tab’a accepting cikin ba!
Ace ma ya karb’a yayi accepting….shikenan ta zama bazawarar k’arfi da yaji kenan??
Dan ita dai ba zata zubar da ciki ba!
‘Tana tuna wani lokaci…akwai wata a ajinsu…
Ta tab’a yin ciki!
Malamin da yayi mata ya kwasheta zuwa wani asibiti
dan basaso makarantar ta sani da kuma iyayen ita Yarinyar. Haka nan aka zo garin cire ciki Yarinyar ta mutu!.
Sannan Akwai wata ma a bayan layin su
Itama b’arin ciki kawai tayi ta mutu…..’
Wata zuciyarce tace mata “ba gara to kema ki mutun ba!
A haka ma tun baki haihu ba kina tunanin ta yaya Arshaad zai soki
Ballantana yanzu idan kika haihu ko kallon ki ba zai yi ba.“
Tunda Jalila take a rayuwarta bata tab’a jin tashin hankali irin na wanann rana ba!
Ji take inama ace ba a haliccetaba
Banda wani irin huci da ajiyar zuciya ba abunda take yi…
Chan!!!
Kamar an tsikareta, da mugun gudu suka ga ta mik’e tayi waje
dan haka suma suka tashi
suka rufa mata baya.
Da kyar bayan sun fita suka jiyo motsinta a kitchen dan kafin su fito har ta b’ace musu kamar wata aljana.
Da gudu kamar mahaukata haka suka nufi
kitchen d’in!
Tun kafin su k’arasa warin d’an kalanzir d’in da suke kunna icce da shi ya bakwanci hancinansu…
Suna shiga suka ganta tana k’ok’arin kunna ashana tana wani irin kuka zata had’iye zuciyarta!
Ga jikinta sharkaf!! Ta kwarara kalanzir ta koina.
Umma kasa k’arasawa wajen tayi…
Ba abunda take jin tsoro sai ‘Kar taje tana matsawa Jalilan kuma ta kunna ashanar taje
wutar ta tashi da ita!’.
Anty Zainab ce tayi k’ok’arin k’arasawa ta gudu ta kwace ashanar ta jefar sanann ta d’auketa da mari!!!
A take ta durk’ushe a wajen tana wani irin kuka abun tausayi.
Sai a lokacin Umma ta samu ta iya matsawa kusa dasu.
Tana zuwa tasa hannu ta d’ago ta ta rungumeta a jikinta tana shafa bayanta tana lallashinta.
Da kyar suka samu tayi shiru.
A hankali Umma ta d’ago fuskarta tana shafawa, tace
“Ki kwantar da hankalinki ki nutsu ki daina kuka ki bani hankalinki mu nemo mafita!
Sannan dan Allah kar ki sake yunk’urin kashe kanki Jalila
Ni Sadiya na yi miki alk’awarin ba zaki wulak’antata sanann zan bi miki hakkinki za kiyi dariya za kiyi farin ciki in shaa Allah
Amman fa sai kin nutsu, sannan sai kina raye tukunna za kici ribar bak’in cikin nan da kike ciki a yanzu!
Kin ji ko?”.
A hankali ta d’aga mata kai tana sauk’e wasu tagwayen ajiyar zuciya.
Nisawa Umma tayi kafin tace mata “Jalila ko da wasa bai tab’a gaya miki sunan unguwarsu ba?”
Shiruuu, ta d’anyi kamar tana tunani…fuskarta tayi mugun kumbura idanunwanta sun k’ank’ance sun yi jazir!
A hankali tace
“A jikin duk motocin da yake amfani da su Ina ganin ‘MT’ a sak’ale a jikin glass d’in gaban motar tashi
Amman turarene irin wanda ake sawa a d’aki ko band’aki ko office dan k’amshi yake fitarwa na tab’a tab’ata ma hannunna ya kwana yana k’amshi.
Sannan na tab’a ganin wasu takardu a motar tashi shima an yi rubutun ‘MT’
Babba sosai!
Sai kuma wasu bayanai a k’asa a cikin envelope mai kyau irin mai shara sharan nan.
Inaga ko yana da alak’a da company d’in ne…watak’ilan in mukaje ‘MT’ d’in mu sameshi a chan.”
Ajiyar zuciya Umma ta sauk’e kafin ta juya wajen Anty Zainab tace
“Kiyi tafiyarki kawai Zainab
Kar yayi ta jiran ki!
Zan dinga gaya miki halin da ake ciki ta waya..
Bara mu tafi MT ni da Jalilan.”
Ajiyar zuciya Anty Zainab ta sauk’e kafin tace
“Kar ki bari ya raina muku hankali!
Ku bud’e mishi wuta sosai!!
Jalila kar ki bari ya ga lagonki
ki daina wannan kukan.
Sannan kar ki k’ara attempting abunda kika so kiyi yanzu
Komai yayi safi maganinshi Allah kin ji ko?”
A hankali Jalilan ta d’aga mata kai.
Shafa kanta tayi tana d’an murmushi tukunna ta yi ma Umma sallama ta wuce.
Tana fita Umma ta kamo hannun Jalila suka fito a kitchen d’in.
Sai da ta dallawa k’ofar d’akin Mama harara a ranta tace
“Munafukai na san sarai kuna jin mu.”
Tukunna suka shige d’aki….
Babu abunda yafi bawa Jalila mamaki irin yadda taga Umma ta had’e mata kayanta kakaff!! Hatta inne wears!
Gashi Umman tace mata
“Kar ta kuskura tace komai
Kawo yanzu har zuwa suje wajen Auwal a gama magana kar tace komai!
Ta bar mata komai a hannunta.”
Sai da ta had’a Ghana most go uku manya!!
Tukunna ta fice taje tayi wanka ta dawo d’akin.
Tana gama shiryawa ana kiran azahar, dan haka ta cewa Jalila “ta taso su tafi!
Kar su makara ya tashi a office d’in.”
Umman ce tayi jigilar kayan ta fitar ta tsare musu adaidaita sahu suka kama hanyar Mai Turare & co.
A bakin tangamemen had’add’en company d’in mai adaidaitan ya sauk’e su.
“Hmm…yana aiki a nan ai dole yayi ta wasa da kud’i yana yiwa mutane rashin mutunci.”
Umma ta fad’i hakan a ranta
bayan ta gana k’arewa k’ererren ginin kallo.
Kayan su suka kwasa
sannan suka sallami mai adedeta sahun suka nufi bakin gate d’in shiga…
Suna zuwa wani soja a cikin masu gadin ya fito ya tsaresu
yana yi musu kallon tara saura kwata kafin yace
“Where to? Maam!”.
Sai da ya sake maimaita tambayar tukunna tace
“Muna son ganin Auwal.”
Da mamaki yake sake k’are musu kallo dasu da kayansu kafin yace
“Sir Auwal?
Mai Turare?”.
Da mamaki Umma ta d’an juya ya kalli Jalila da sauri sai kuma ta juyo gareshi tace
“Yes yes shi.”
Dariya sojan yayi
kafin cikin gurb’atacciyar Hausar shi yace
“Bar nan wajen!
Bana son raina.”
Yana gama fad’in haka ya juya
Sai a lokacin Jalila tace “sir”
Yana juyowa ta mik’a mishi wayarta.
Kallonta yayi kafin yasa hannu ya karb’i wayar
Da mamaki yake kallonta yake kallon hoton da suka d’auka ita da Auwal a cikin mota!
Yafi minti d’aya a tsaye yana kallonta da hoton
Daga k’arshe ya sauk’e ajiyar zuciya yace “ok”
ya mik’a mata wayarta ya juya yayi ciiki…
Kallon hoton take yi a hankali tana shafa fuskar wayar
tana tuna lokacin da ta d’auki hoton…
Lokacin zuwan sa na biyu ne,
tanata y’an hotunanta Ita d’aya shi kuma yana driving,
ba tare da ya sani ba ta d’an karkato ta d’auke su.
Gashi nan ya fito tarr! Amman iya gefen fuskarshi sai dai duk wanda ya sanshi yana gani zai san shin d’in ne….
“Jalila kar fa ki fara son Yaron nan!
Dan in dai kina sonshi to ba zaki iya abunda na shirya ba.
Ki daina kallonshi ki goge hotonnan tunda yanzu na san ya gama aiki.”
Muryar Umma ta katse mata tunani.
Murmushi kawai tayi ta maida wayar lock ta rik’e a hannunta.
A chan office kuwa!
Ana gayawa Auwal wata na nemanshi a waje yace “Ace musu aiki yake yi!”
Shi bai ma kawo Jalila bace ba yayi tunanin a cikin tarin y’an matanshine wata ta boyisa har office, dan sun saba,
sai dai kuma yayi mamakin yadda bata shigo har office d’in nashi ba
Instead
Ta tsaya a gate!….
Kamar bayan minti goma sai ga mai gadin ya sake dawowa.
Yana zuwa yace matar da take tare da Yarinyar tace ace mishi “Dangin Mamansa ne suka zo daga k’auye!”
“Dangin Adama?”
Suka ji muryar Granpa wanda ya shigo zagaye yanzu a bayansu!!!!
Sai da Auwal yaga wani duhu na y’an sakanni…
Tukunna ya mik’e tsaye
ya gaida Granpa cikin girmamawa.
Bai amsa ba sai tambayar d’azu da ya sake jeho mishi!!.
A hankali Auwal ya goge wata zufa da ta karyo mishi a goshi sannan yace
“Eh, I think so, amman bb ba bamu yi maganar wasu za suzo da ita ba!”.
Ajiyar zuciya Granpa ya sauk’e kafin yace
“I’m leaving, kazo muje gida sai ka kaisu wajenta!
Su yi abunda ya kawosu su wuce..
Make sure basu dad’e ba
ka san bana son kwashe kwashe!.”
Wani yawu mai mugun d’aci da tauri Auwal ya had’iye kafin yace “Ok Granpa.”
Sannan ya bi bayanshi suka fice tare a office d’in hankalinshi a masifar tashe!!
Tabbas ya san ba y’an uwan Mom bane suka zo!
Ummi ita kad’ai ce cousin d’inta tunda mata biyu kacal kakarsu ta haifa!
Da maaman Ummi da Maman Mom
Su kuma suka haifi mata d’aya d’aya
Ummi da Mom.
Sai dai In ko relatives d’in kakar tasu, amman ya san Mom ba huld’a take yi da su ba
dan tun tana y’ar k’ank’anuwarta ta kwaso kayanta ta dawo wajen Ummi Gramma ta had’asu ta renesu tare..
Sannan har gobe sai anyi da gaske tukunna take zuwa k’auye wajen Mahaifiyarta ta d’anyi kwana biyu ta dubota ta dawo sam bata son k’auye
Sannan Maman nata irin matan nan ne masu fad’in gaskiya da tsananin imani
acewarta kenan (mom d’in)
D’an mistake kad’an Idan tayi nan zata had’u da fushinta!
Hakan ya sanya da taga tafiyar su ba zata zo d’aya ba sannan ita kuma (Mahaifiyar tata) ta k’i zaman birni, ta ajjiye ta a k’auyen ta siya mata gida take tura mata kud’i duk wata,
waya ma suna yi amman ba sosai ba.
Zuwa kuwa sai tafi shekara bata lek’a ta ba……
Yana wannan tunanin suka k’arasa wajen da suka yi parking motocinsu!
Granpa ne ya juyo ya cewa mai gadin da yake tare dasu yana yi musu rakiya
“Ina bak’in??”
Sai da sojan ya d’an rissina tukunna yace
“Suna waje bara inje In shigo da su.”
“Okay hurry”
Shine abunda Granpa yace yana mai gyara tsayuwar shi a jikin motar.
Wasu zufa ne suke tsatsafowa Auwal ta kowacce b’ular gashin dake jikinshi…
Da ace Granpa zai lura dashi da kyau to da tabbas a tashi d’aya zai karanto tsananin tashin hankali tsoro da rashin gaskiyar da suke tattare da shi!.
Tabbas ya san kashin shi ya bushe yau!!
Saboda bashi da tantama
wata a cikin y’an matan shi ce ta zo!
Duba kuma da
irin yanayin halayyarshi tabbas!! Ya san ba alkhairi ne ya kawota ba….
Wata idea ce ta fad’o mishi dan haka da sauri yasa hannu a aljihu ya zaro wayarshi ya shiga message….
Yana gama sending message d’in dai dai su Umma suna k’arasowa wajen tare da wasu masu gadi da suka tayasu d’ibar kayansu.
Da mamaki yake kallonsu especially Jalila wadda yaga
ta chanza!
Itan ma shi take kallo
ido cikin ido
Tana mamakin yadda ya nutsu a gaban wannan tsohon,
kamar ba shin ba.
Umma ce ta gaida Granpa
wanda taga yana yi musu kallon k’urilla!.
Ba tare da ya amsa ba ya cewa Auwal
“Did you recognize them?”
Sai da ya d’an russunar da kai tukunna yace
“No Granpa.”
“Call Adama”
Granpa ya bashi umarni.
Wani sanyi Auwal yaji ya na ratsashi
a hankali yace
“Ok”
kafin ya danna kiran Mom.
Ya san ta d’auka amman bai saka wayar a handsfree ba
Sai kawai yayi shiru chaan kuma ya kashe!
Ya bada kamar minti d’aya dan ta samu ta karanta sak’on nashi sannan ya