Showing 111001 words to 114000 words out of 124668 words
Chapter 38 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
a duk yadda yace!
Ki barni da shi, ni na san me zan yi.”
A hankali Jalilan tace
“Umma to ba yadda wai za ayi In auri Ya Arshaad? dole sai wannan?
Nifa shi nake so!”.
Cikin fad’e Umma tace
“Jalila wallahi zan ci buhun uban ki daga ke har Arshaad d’in!
Nace miki ki hak’ura da shi ko?
Ga hanya nan mafi sauk’i amman kin gagara fahimta?
Da me Arshaad d’in yafi wanann??.
Cikin katseta Jalila tace
“Umma shine a zuciyata da haka kawai ya fishi...”
Buge mata baki Umman tayi
kafin tace “Bara kiji in fito miki a mutum!!
Wallahi ba zan iya kokawar bin Malamai da masu kud’i ba!
Ba zai yiu inje in bada dubu talatin mai kud’i ya zo ya ajjiye dubu d’ari ko d’ari biyu sannan kiyi tunanin za ai mana aiki iri d’aya ba!
A nawa tunanin fa kenan, bansan ya naki yake a k’aramar kwakwalwarki ba.
Ki cire wata soyayya a ranki…
A zamanin mu ne muka bi soyayya, kuma gashi muna cin ubanmu!
Gata nake yi miki Jalila ki bari
mu nutsu waje d’aya mu yi abinda zai yiu, kar ki je kiyi saki reshe kama ganye!
Na dai fad’a miki.”
Tana gama fad’in haka ta mik’e tace mata
“Asubah ta gari
Bara in je
ki saki net dan yau akwai sauro .”
Daganan ta fice ta nufi d’akin Baba.
Jalila ta dad’e tana tufka da warwara daga k’arshe ta yankee shawarar tabi zab’in Umma!
Haka nan ta hak’ura da Arshaad ba dan zuciyarta tana so ba.
Ta zo kwanciya kenan kiran Auwal ya shigo wayarta!
Tana gani har ta tsinke bata d’auka ba!
Tabbas duk tsaurin idonta da rashin kunyarta yau ta had’u da kakanta!
Kuma kalli ba kunya ba tsoron Allah kiranta ma yake yi
Ita kam kafin ta samu ta sake iya had’a ido da shi ma
ai sai nan da kwana biyu ko uku ma..
Miss call d’aya ta samu daga gareshi daga nan bai sake kira ba!
Dan ba zai tsaya kuchaka kamar ta tana ja mishi aji ba!
Although ya san a d’an rikice take har yanzu wanda hakan ne ma ya sake tabbatar mishi da ‘Yarinyar sabon hannu ce!’
Ko banza ya san zai tsinci dami akala!
Amman dukda haka
zai yi sauri ne kawai yayi abunda zai yi ya gama ya kuma gano dalilin alak’arta da Arshaad daga nan ya had’a mishi bomb d’in da yaga ya dace dashi! Ita kuma ya wurga ta a dustbin! Tun kafin wani a cikin Abokanayen sa ya gano yana kula mace irinta…
Although, she’s beautiful,
tabbas tanada kyau, ta fanni daban daban wanda hakan ne
ma ya sanya ya d’an sake janta a jiki amman dai still ba zai bari Abokanayensa su ga yana kula a girl like her, ba!.
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
34
A meeting point d’in da suka yi zasu had’u…
A nan suka tarar da Khadijahn tana jiransu.
Ba tare da b’ata lokaci ba
Aslam ya zaro blank check ya mik’a mata yace
“Ta rubuta ko nawa take so
muddin ta san zata fad’i gaskiyar abunda ta sani game da case d’in Arshaad.”
“Mai yasa kake so ka sani”
Ta yi musu tambayar tana mai kallonsu.
Fahimtar da Aslam yayi za ta yi taurin kai ne ya sanya
kawai yace mata
“Ko ta fad’a ko kuma ya d’auke check d’in ya hanata kud’in kuma dole in za a shigo court sai anje da ita dan sunanta ya fito! Dan Auwal ya ambato sunanta a cikin case d’in.”
Cikin tsanannin tashin hankali da b’acin rai tace
“Auwal d’inne ya ambato sunana?
Sannan abun naku har da court daman?”.
Arshaad ne,
yayi mata bayanin komai
sannan ya d’aura da cewa “ina da recording d’in wayar da muka yi da Auwal lokacin da ya ambato sunanki a ciiki”
Saboda haka ki taimaki kanki ki taimaki Auwal ta hanyar fad’in gaskiyar iyaka abunda kika sani.
If not zata rufta da ke da Auwal d’in, duk ranar da aka zauna a kotu….
Domin kuwa shi Auwal yana tunanin yayi mini sharri!
Sai dai kuma bai san iyaka wannan evidence d’in na voice call ya isa ya d’auresa tamau!!
Kuma dole abun ya shafe ki.
Jikinta har rawa yake yi
tace “Dan Allah….zan gaya muku komai amman kar ku gayawa Auwal ni ce na fad’a!”
….Nan ta hau zayyano duk abunda suke da buk’atar ji da zai taimaka wajen wanke Arshaad!
Daga k’arshe tace “gobe da sassafe su had’u a nan, zata kawo wasu takardun duk akan bayanan da zasu taimaka wajen wanke Arshaad d’in ne..”
Sannan ta sake rok’ar su akan dan Allah dan Annabi kar su bari Auwal ya san itace ta fad’a musu, dan in dai ya sani to sai ya koreta a aiki bayan wulak’ancin da Allah kad’ai ya san kalar wanda zai yi mata…
Sanann su yi k’ok’ari kar a shiga court kar sunanta ya fito
dan ta san nan ma zata samu matsala da CEO!
Bayan an yanke mata hukunci kuma kora ta biyo baya..
Da wannan aikin ta dogara
su uku ne a family d’inta
Ita , mamanta, sai k’anwarta
Babanta ya dad’e da rasuwa
ita take providing a family d’in
su taimaketa! Dan Allah.
Ta k’arashe maganar cikin had’e hannunwanta alamun rok’o!.
“Thankyou Khadijah!.” shine kawai abunda Aslam yace mata daga nan ya mik’e tsaye yana cewa “Nayi miki alk’awarin ‘sunanki ba zai fito ba’.” Kafin yace
“Rubuta kud’in da kike buk’ata
za mu wuce.
Da farko cewa tayi su barshi kawai. Sai da Arshaad yace “Ai alk’awari suka yi mata tun farko kuma ta fad’i abunda sukeson ji don haka dole su cika mata alk’awarin da suka d’auka.”
Tukunna ta d’auki blank check d’in ta rubuta 300k!
Sukayi signing mata suka wuce…
Suna yin gaba Aslam ya zaro wayarshi a gaban aljihun rigarshi ya katse video d’in da ya saita tun kafin su fito daga mota.
Basu samu sun je wajen Auwal a ranar ba!
Saboda busy d’in da Aslam da Abba suka shiga har ma da Arshaad dan so suke su yi su gama shirye shirye su samu su bud’e company d’in nasu soon.
Around 9:00 pm washegarin ranar bayan kowa ya dawo a office an yi dinner da isha suka nufi gidansu Auwal..
Da Mom suka fara cin karo a k’asa tana waya.
Faram faram ta karb’esu
bayan y’an gaishe gaishe Arshaad yace “Auwal yana nan?”.
“Eh, yana sama har ya
kwanta ma.
Wai ya gaji yau sosai.”Ta basu amsa, a tunaninta za su bari ne amman sai taga Aslam ya mik’e yana cewa “yana nan a side d’inshi na daa har yanzu ko?”
“Eh” ta sake basu amsa.
“Muje”
Aslam ya cewa Arshaad, daga haka suka nufi saman.
Mom ji take yi kamar ta bisu ta lab’e taji meyene ya kawo su dan
tabbas ta san ba lafiya ba!
Tunda dai Auwal ba shiri yake yi da either of them ba.
Tana shirin mik’ewa Daddy ya shigo! Kamar ta kurma ihu haka taji, haka nan tana ji tana gani ba yadda ta iya…ba dan ta so ba ta hak’ura da lab’en data shirya yi.
Kamar yadda Mom ta fad’a musu, Auwal d’in har ya kwanta!
Har cikin bedroom d’inshi suka shiga Arshaad ya lalubo switch ya kunna!.
Baccin nasa bai yi wani nisa ba
shiyasa yayi saurin farkawa
yana mitsi mitsi da idanuwa.
Da mamaki yake kallonsu
kafin ya mik’e ya zauna a kan gadon yace “Lafiya!
Zaku tashi mutum yana bacci?
Infact
baku san babu kyau invading privacy ba?”.
Murmushi Arshaad yayi ya k’arasa inda yake ya zauna a gefenshi kafin yace
“Ai baka taki zaman lafiya da kwanciyar hankali ba!
So ka cire bacci a agenda d’inka for now and start worrying about yourself.”
Tsaki kawai yayi ya
fara k’ok’arin komawa ya kwanta. Dai dai nan Aslam ya k’araso yayi masa playing video d’in da suka yiwa Khadijah jiya ba tare da ta sani ba.
Jin muryar Khadijah ya sanya ya d’ago yasa hannu ya karb’a
dan da farko k’in kallon wayar ma yayi.
Sai da video d’in ya k’are tukunna Aslam ya jawo stool ya zauna a kai yana facing Auwal d’in!
A hankali ya fara magana
“Auwal da kai da Arshaad ba ku da bambanci a wajena amma i have to sopport wanda yake da gaskiya!
Ka taimaki kanka
ka taimaka mana mu kashe case d’innan if not kai kanka ka san ba zatayi maka kyau ba!
In ka yarda kayi sopporting d’in mu
Ni na san ya yadda zan yi
in rufa maka asiri In rufawa ita Khadijah asiri Case d’in ya mutu ba tare da sunan either of you ya fito ba!
Amman if you try to act stubborn and rude to
bani da wani choice d’in daya wuce In saki video d’innan!
And the first person da zan turawa shine ‘Granpa’
Followed by su Dad
Daga nan su Mom
After them kuma har a MT estate da company sai kowa yaji kuma ya gani!
Wallahi.
Shiruuu, Auwal yayi yana lissafi…
Duk ta inda ya duba ya zagaya ya zagayo bashi da mafita!
Dan haka kawai ya yanke shawarar hak’ura. Amman fa sai ya gasawa Aslam aya a hannu wallahi!
Zai san ya tab’o shi..
But first zai bari komai ya lafa
zuwan nan da kamar 2 ko 3 months haka
A lokacin zai san wayene Auwal!
And he will make sure yayi takunshi da kyau ta yadda ba za su samu damar kamashi ta ko wacce hanya ba….
“Kai muke jira!”
Ya ji muryar Arshaad.
Ajiyar xuciya ya sauk’e sannan yayi murmushi ya d’ago ya kalli Aslam kafin yace
“Selfish bitch!!
Kar in sake jin kace ‘da ni da Arshaad d’aya muke a wajenka!’
Bana son munafurci gara kawai ka fito a mutum ka bi bayan brother d’inka ka bar yin wasu kwana kwana..”
Mik’ewa kawai Aslam yayi ya cewa Arshaad “muje!
He’s not ready to negotiate.”
Sai da Auwal ya runtse idanunsa da k’arfi! Yana mai jin takaicin abunda zai fad’a, tukunna a hankali yace
“Truce accepted!”
Murmushi Aslam yayi ya juyo yace “Good boy!
First of all..
Zaka kawo takardun da kace ka had’a na wasu laifuffukan da zaka sake d’aurawa Arshaad idan an je court.
Sannan Akwai papers d’in da nake buk’ata ka yimin zuwa nan da 24 hours..
( nan ya zayyano mishi abunda takardun za su k’unsa)
“Zan had’a tare da na Khadijah In kaiwa Granpa
Once yayi accepting, shikenan
case ya mutu!
Daga nan sai ka sameni ni kuma zan goge video d’innan a gabanka har wanda na tura a laptop duk zan goge.”
“Sounds fare”
Shine abunda Auwal yace
daga nan ya juya ya kwanta
yace “Ku kashe min bulb in kun tashi fita.”
Har zasu wuce Aslam ya juyo yace “Ina so kayi promising d’ina ‘ba zaka yiwa Khadijah komai ba’
Saboda na riga nayi mata alk’awarin kareta ta ko wacce hanya.”
Sai da Aslam ya kira sunanshi tukunna yace
“To!!”
Ba tare da ya juyo ya kalle su ba.
Arshaad ne ya fara ficewa
sannan Aslam bayan ya kashe mishi bulb d’in ya jawo k’ofar d’akin, suka wuce.
Suna fitowa a d’akin Arshaad yace “Thankyou!
Case zai mutu ba tare da sunan kowa ya b’aci ba.”
Murmushi Aslam yayi sannan yace “ka fahimceni kenan..
Gara hakan ai dan ni a ganina idan muka had’ashi da Granpa rigima ce babba da Allah kad’ai ya san k’arshenta.
Ni da in da ace za a bi ta tawa
To
da an bar maganar bada company d’innan a mutum d’aya da Granpa yake son yi!
Rivalry kawai hakan zai janyo
da bitterness d’in da Allah kad’ai ya san k’arshen shi.......”
Da safe kamar yadda Khadijah ta fad’a, haka ta kai takardu.
Auwal ma 24 hours suna cika ya cika alk’awari….. Da mamaki a kan fuskokinsu suka dinga kallon sharrin da Auwal ya k’ukk’ulawa Arshaad kala kala! Wanda tabbas idan takardun suka fita to da wuya in Granpa ba zai saka Arshaad ya k’are rayuwarsa a jail ba!
A take suka yaga takardun
sannan Aslam ya had’a da na wajen Khadijah da ragowar takardun daya had’a yake kuma buk’ata
Ya nufi wajen Granpa da su.
Sai da Aslam ya tabbatar Granpa ya yarda kuma ya hak’ura sannan case ya mutu!
Tukunna ya dawo ya goge videos d’in Khadija a gaban auwal kamar yadda yayi alk’awari..
Sai dai kuma Auwal d’in bai kai ga barin wajen ba ma
Message d’in Granpa ya shigo wayarshi../
“He’s not serious, ba shi da lura he’s reckless!!
Shiyasa aka samu har kud’i masu yawa haka suka shiga account d’in Arshaad instead of account d’in turawan da ya kamata ace an tura..
Gashi yanzu sun yi loosing contract d’in!
Saboda haka gobe yana zuwa office ya kwashe kayanshi daga office d’in md ya maida ground floor.....”.
Da kyar Auwal ya iya jan k’afafuwan shi yana ganin dishi dishi ya fice daga side d’in nasu ba tare da ya cewa d’aya daga cikin su uffan ba!
Ikon Allah ne kawai ya maidashi gidansu.
Yana fita ba da dad’ewa ba
Message ya shigo wayar Arshaad shima..
‘An maidashi aiki
But ya samu demotion kamar Auwal
A ground floor zai koma aikinshi.’
Murmushi yayi bayan ya gama karantawa, ya turawa Granpa d’in “Thankyou Granpa
A lot.”
Sannan ya mik’awa Aslam wayar yana mai cewa
“Da babu gara ba dad’i.”
Kwata Kwata Aslam bai ji dad’in hakan ba!
Ganin haka yasa Arshaad d’in yayi ta mishi nuni da
‘daman ya san sai an hukuntashi ko da ace an yafe mishi, so shi a ganinshi babu wata damuwa..
Dama shi burin shi case ya mutu kuma ya mutu!
Dan haka Alhamdulillah
Ya san k’ark’ari a rage mishi salary wanda shi salary d’in da ake biyan shin ma kamar bonus ne saboda company d’in shine ja baya a harkoki daban daban d’in da yake yi wajen kawo mishi kud’i!
Kuma yanzu ya san tunda a ground floor yake to duk inda 3 tayi ya tashi! Hakan zai bashi dama wajen focusing a kan ragowar businesses d’in da yake yi…’.
Sai da yaga Aslam d’in ya fahimceshi tukunna ya kyaleshi haka
suka fad’a wata hirar.
Tun a Daren ranar Granpa ya gama deciding sannan ya rubuta
‘Kujerar md ta koma hannun Aslam!’
Daga nan ya kira Baban Auwal yace “ya ci gaba da managing branch d’in ‘Mai Turare’ na Uk ko wata wata ne ya dinga lek’awa saboda ya san a anan ma akawai wani company d’in su daban da yake kula dashi.
Tunda yanzu Aslam ya dawo nan to shi zai zama MD na nan, saboda Arshaad da Auwal wawaye ne basu san aiikin ba!
Sannan baya buk’atar Aslam d’in ya sake komawa UK!
Ya isa haka..
Maganar Mahaifiyarshi kuma in shaa Allah yana sa ran dacewa dan yayi booking appointment da ‘best neorologist in the world’ za a kaita ta ganshi, in shaa Allah akwai alaman nasara..
So ayi arranging papers na change of position d’in da aka samu da office
In shaa Allah gobe shi da kanshi zai yi introducing Aslam as their new MD na wannan branch d’in!
Next week kuma sai suje UK d’in nan ma a yi y’an tsare tsare………”
Yana gama fad’an haka suka yi sallam bayan Baban Auwal d’in ya nuna mishi fahimta da amincewar hakan 100%.
Yana ajjiye wayar ya kasa juyowa ya kalla inda Mom take
dan tun lokacin da ya fara wayar yaji ta mik’e ta zauna a kan gadon.
Sarai ya san ko bata ji komai ba to ta fahimci wani abun!
Bai san ta ina zai fara yi mata bayani ba, dan in dai a kan Auwal ne to gaba d’aya yanzu notikan kanta za su kwance! Shi kuma har ga Allah bai shiryawa hakan ba cikin daren nan, kanshi ciwo yake yi besides kuma yana tunanin rik’e manyan company’s har biyu! Dan bayan ‘Mai Turare’ company na oils d’in da yake rik’e dashi is the second largest a family d’in….
Yana cikin wannan tunanin ya ji lallausan tafin hannunta a kan kafad’ar shi.
Shiruuu, yayi bai kulata ba, hakan ya bata daman fara magana..
“Ka san dai na fahimci akwai matsala, ko?
Rashin sanar dani da yin shirun ka sake saka zuciyata cikin zullumi zai yi! Dan Allah ko menene komai d’acinsa ka fad’amin, please Mijina.”
Tayi maganar tana amfani da tafin hannunta wajen shafashi.
Juyowa yayi gareta ya kamo hannun ya rik’e sannan ba tare da b’oye b’oye ba, ya hau fad’a mata yadda suka yi game da ‘zai koma MD na branch d’in Uk, tunda Aslam ya dawo..shi kuma Aslam d’in an bashi MD na nan!’
Tun kafin ya k’arasa rufe bakinshi tace “Auwal fa?”
Ajiyar zuciya ya sake sauk’ewa kafin yace
“Ya samu demotion! Da shi da Arshaad Granpa yace ‘they are not capable’…..
Mom wadda ranta ya b’aci hankalinta ya tashi bata san lokacin da ta manta da duk wani karatun kissar ta ba tace
“Zancen banza kenan!!! Daga bakin mutanen banza, wallahi ba zai yiu....”
Tsawar da Daddy ya daka mata ce ta sanya ta d’an seseta hankalinta ya d’an dawo
“Bana son raini fa Adama!!!! Ni ne mutumin banzan ko mahaifina??
Hukuncine ya riga ya yanke kuma dole uban kowa ya bi! Idan kuma kina da ja na tabbatar kin san inda zaki iya samunshi.
Ai tun Auwal bai kawo haka ba!
Tun bai gagaremu ba nake gargad’arki…
Yanzu gashi anzo gab’ar da bamu da wani choice d’in da ya wuce muna ji muna gani mu dinga take laifukanshi muna b’oyewa saboda rufun asirin mu baki d’aya! Ko kin san irin kalar b’arnar da yake tafkawa a office kuwa??
Baki da abinda kika d’orasa a kai tun tasowarshi kawo yanzu sai ‘ya bi duk wata hanya da zai bi don a Mallakaa mishi Mai Turare!’ Ko kina tunanin ban san me kike yi ba? Baki damu da kare mutumcinshi ba! Baki damu da d’orashi a kan addini ba! Baki damu..baki damu…baki damu ba da yawa, Adama!!!.
Tarbiyyar ma ba bashi kika yi ba instead ina yi kina warware min!
Gashi yanzu ya addabeni ya addabeki kuma kwad’ayin Mai Turaren da kike yi…due to yadda kika maidashi ya sanya yana abu kamar psyco psyco gashi yanzu instead of daga MD ya wuce CEO gashi an maidashi ground floor!!!
Wa gari ya waya kenan??
Daga 10th maimaikon ya k’are yin sama amma instead ya dawo ground flour! Kinga garin neman gira an rasa ido……”
Hakanan Daddy yayi mata tatass! Kamar ya ari baki..
Mom kam kasa danne bak’in cikin ta tayi haka nan ta dinga kuka wiwi har da majina kamar wata k’aramar Yarinya..
Ganin haka ya sa Daddy ya d’an sassauta muryarshi yace
“Kiyi hak’uri Adama, da Auwal da Arshaad da Aslam duk abu d’aya ne!