Showing 123001 words to 124668 words out of 124668 words

Chapter 42 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt

25 Sep 2025

2320

sauri..
Mammy ma tabi bayanta.
Mom kuma ta mik’e tayi sama.
Jalila kuma ta nufi dining tana tunani a ranta “menene haka sirrin da su Ummi basa so ya tonuu?”.

BAYAN KWANA HUD’U!!
(After four days!)

Kamar yadda Mama tayi alk’awari haka nan yau ta shirya tsaf! Tun k’arfe takwas ta sanya atamfar ankon Khadijah da niyyar zuwa gidan Baaba Talatu.
Tun bakwai suka yi waya da Ummu tace mata “sun fito tun tuni”
So ta san duk inda tara tayi sun k’araso in shaa Allah.

A kitchen ta fito ta samu Hudan tana d’an had’a musu abun kari da su da Ya Ja’afar dan shi ba a tafi da shi ba.
Ganin da tayi Huda bata k’arasa nata shirin bane ba ya sanya tace mata “ta wuce taje ta shirya ita zata k’arasa aikin”
Already ma Huda ta ida, zuzzubawa ne ya rage da had’a shayi….
“To” kawai Hudan tace daganan ta wuce d’aki.

Mama na shirin zama taji kamar kira ya shigo ya yanke dan haka ta zaro wayar daga purse d’inta..
Tana dubawa taga Ummu ce!
Ajjiye purse d’in tayi a gefe sannan ta gyara tsayuwarta ta hau kiran Ummun…
Tayi mata misscalls sama da bakwai amman bata d’auka ba!
Hankalinta ba k’aramin tashi yayi ba dan haka kawai ta yanke shawarar ta kira Shuwa
tunda d’azu Ummun tace mata ‘a mota d’aya suke ita da Shuwa da Sumayya
da Abba Madu da Ya Jamilu
da suka je d’aurin aure a jiyan.

Su Baba kuma suna tare da su Baaba Talatu.’

Bugu uku a na hud’un ta d’auka!
Bata ce komai ba ta dai d’auka ta kuma kara a kunnenta!!
A hankali Mama tace
“Ina kwana Hajiya,
Bilkisu tana kusa?
Inata kiranta bata d’auka.”

“Inaga wayar tana a silent ne”
Shine abunda Hajiya Shuwa tace, daganan tayi shiru.

A Ahankali Mama tace
“Tam shikenan”
Har zata kashe sai ta sake cewa “sai kun k’araso..
Muma gamu mun shirya yanzu zamu tafi gidan Baaba Talatu mu jira ku a chan.”

Cikin yaren shuwa Hajiya Shuwa tace
“Ku yi zaman ku kawai ba sai kun zo ba!
Maryam Ina cikin farin ciki kar ki ja a b’ata mini rai kokuma a gaya min magana a yau d’innan!!
Na gaya miki kar kuzo mana cikin taro da ke da y’arki amman kin k’i yarda ko??
Taurin kan naki da kika saba shi zaki gwada mini ko?”
Cikin fad’a sosai taci gaba da cewa
“Wallahi idan naga k’afar ki a inda nake ranki in yayi dubu sai ya baci!”
Tana gama fad’in haka ta yanke kiran…

Wayar Mama tana da volume sosai…dukda Huda ba wani yaren Shuwa take ji sosai ba
amma tabbas ta fahimci abunda Hajiya take nufi…

A hankali Mama wadda take jin kanta na masifar juyawa da sarawa ta sa hannu ta share hawayen da ya zubo mata!

Juyowa tayi da niyyar d’auko kwano a kwando suka had’a ido da Huda wadda take kallon ta tana zubar da hawaye…

Wani tausayinta ne ya lullub’e Mama lokaci guda!
A b’angaren Hudan ma hakan take.

Da sauri Mama ta zo ta giftata ta wuce ta fice daga kitchen d’in
Dan kallon fuskar Yarinyar sake narkar mata da zuciya yake yi..
Tana fita itama Hudan ta juya ta bi bayanta.

Duhun! Da ta fara gani ne ya sanya ta d’an tsaya ta dafe kanta…
A hankali ta fara jin wani irin jiri yana kwasarta kafin daga haka taji jinta da ganinta da k’arfin jikinta sun d’auke lokaci guda ta tafi ta sulale a tsakar gidan ta fadi!! Kamar matacciya!.

Da k’arfi Huda tace “Maamaa!!!”
Sai kuma ta yi kanta da gudu tana kuka......






Kuka take yi tun k’arfinta tana kiran sunanta amman ko motsi bata yi ba.
Ganin hakan yasa ta sake gigicewa ta rikice ta rasa ma ta Ina zata fara!
Tana shirin mik’ewa sai ga Ya Ja’afar ya shigo…
Da gudu ta k’arasa inda yake tace “Ya Ja’afar napep dan Allah ka nemo napep mu d’auki Mama a kaita asibiti dan Allah Ya Ja’afar..”
ta hau rirrik’esa tana mishi magana duk ta gigice..

Kallonta yayi ya kalli inda Maman take.
Kamar wanda zai yi abun arzik’i haka ya k’arasa inda Maman take kwance…
Dai dai setin fuskarta ya d’an yayyarfa hannunshi (kamar wanda zai kore mata sauro)
A hankali ya d’ago ya kalli Huda wadda take kuka kamar ranta zai fita yace
“Wannan ai napep ba zata yi aikin komai ba!
Sai dai a d’auko makara!! ayi mak’abarta da ita.
Kallifa ko uffan bata ce mini ba!
Bafa ta motsi.”

Cikin kuka Hudan tace Ya Jaafar asibitin dai!
Ka nemo mai napep ka taya ni d’aukar ta
Zata farfad’o in shaa Allah suma tayi.”

Banza yayi da ita ya juya ya nufi kan baranda sannan yace “bara in d’an rintsa In farka sai munje in yi mata sallah a mik’ata!.”

Sai a lokacin Huda ta lura da yadda yake tafe yana tangad’i!!!

“Na shiga uku yau!”
Tace tana wani irin kuka…

Ko myafinta bata tsaya d’auka ba ta fita da gudu gidan da yake a jikin nasu dake suna da mota su wai ko zata samu a tayata a taimaka mata su mik’a Maman asibiti.
Sai dai kuma tun kafin ta k’arasa ta hango k’atoton padlock mak’ale a k’ofar gate d’in gidan wanda hakan
yake nuni da ba kowa ma a gidan kenan!.

A rikice ta juya ta koma cikin gidan tana shiga ta tarar Ya Ja’afar har yayi bacci..

K’arar wayarta ta jiyo a d’aki sai a lokacin tunaninta ya bata kawai ta kira Arshaad.
Tana shiga ko bi ta kan misscall d’in bata yi ba ta hau kiranshi babu k’akk’autawa…..


MT & co.
A lokacin
Aslam ya je office d’inshi kenan
Granpa kuma
ya saka shi wani aiki
na gaggawa….
Duk ya rikice hakan yasa ko wayarshi bai tsaya d’auta ba ya wuce wajen da ake sarrafa turarurrukan wanda yake nan a gefen building d’in da yake d’auke da offices bayan ya cewa Aslam d’in ya jira shi a office d’in nasa nan da kamar 20 minutes zai dawo…

Yana fita ko 1 minutes bai yi da fitar ba wayarshi ta fara k’ara!

Aslam, kamar zai bishi da wayar sai kuma yayi tunanin ‘bara kawai ya jira har ya dawo sai ya bi kiran kawai’

Ganin yadda aka jera mishi kusan 20 misscalls a jere ba hutu ne ya sanya ya yanke shawarar kai mishi wayar kawai, dan ya san dole its important!!
Yana d’aukar wayar wani kiran yana sake shigowa tare da wani message da alamun yanzu aka turo!
“Life support ❤️”
Haka yaga sunan b’aro b’ari ya fito a akan screen d’in.
Ko ba a gaya mishi ba
Ya san Huda ce!
A hankali ya lumshe kyawawan idanuwanshi ya bud’e su kafin ya maida wayar kawai ya ajjiye ya koma ya zauna yayi shiruuu….
Ganin tanata kira still babu k’akk’autawa ne ya sanya ya mik’a hannu ya d’auki wayar a karo na biyu
Yana d’auka kiran yana tsinkewa dan haka ya samu damar ganin sak’on data turo ta notification bar!
“Ya arshaad Mama ta suma ba kowa agidan sai mu biyu ka taimakamin Dan Allah kazo mu kaita asibiti!”

Da mugun k’arfi yaji k’irjin shi ya buga!

Tsintar kanshi kawai yayi da mik’ewa tsaya ya fice daga office d’in gaba d’aya bayan ya ajjiye wayar a kan tebur.

Ko takan wayar Arshaad d’in bai sake bi ba!
Ya isa inda motar shi take ya shiga ya bata wuta ya fice daga companyn da gudu…

Babu nisa tsakanin company d’in da gandun albasa hakan ya sanya ya samu damar k’arasawa acikin mintuna k’alilan!

Yanayin parking ya fito da d’an gudu ya shiga gidan kanshi tsaye…
A tsakar gidan ya hango su
Hudan tanata k’ok’arin d’aura Mama a bayanta tana kuka
amman ta gagara!

Tanajin shigowar mutum ta d’ago idanuwanta tana kallonshi…
Shima itan yake kallo!
Wani sabon kuka ne ta ji ya kufce mata mai k’arfi ba tare da ta shirya ba!

Da sauri ya k’arasa inda suke yana kallon ta yana jin yadda k’irjin shi yake bugawa…

Da kyar ya iya ce mata
“Muje”
Sannan ya durk’usa da niyyar d’aukar Mama.

Zabura!! Yayi bai san lokacin da yace
“Anty Maryam!!!”
da d’an k’arfi, ba…
Sai kuma ya sago yana kallon Huda wadda take yi mishi kallon mamaki..
Mayar da dubanshi yayi a fuskar Mama yana yi mata kallon kurilla
Kana ganinshi ka san a firgice yake!! Cike kuma da mamaki
sannan kanshi a d’aure yake.
D’agowa ya sake yi ya kalli Huda!
Sai
kuma ya sake maida idanunsa akan fuskar Mama…..

Cikin kuka Hudan tace
“Ya Aslam dan Allah mu je
kar wani abun ya sake samunta…

Wani yawu mai d’aci ya had’iye kafin a hankali still idanuwanshi suna a kan fuskar Maman ya sanya hannu ya d’auketa yayi waje da ita….


Ita ma Hudan kanta a d’an d’aure yake….sakamokon jin yadda ya kira sunan Mama lokaci d’aya kuma har da
‘anty’ wanda ko lokacin da su Jalila suna Yara ta san ba anty suke ce mata ba!
Sanann bata tunanin ko Ya Arshaad ta tab’a gayawa sunan Mama balle tayi tunanin ko shine ya fad’awa Aslam d’in!.
Bata wannan take ba yanzu ta
Lafiyar Mama take dan itace abun dubawa!
Dan haka ta kawar da tunanin gefe…
Tana ganin sun fita itama
da gudu ta koma ta d’au mayafinta ta d’auko y’an kud’ad’en da suke dashi ta zuba a jakar Maman ta d’auko mata purse d’inta data bari a kitchen tasa a cikin jakar ta fito daga gidan
Lokacin Aslam har ya saka Maaman a Bayan mota yana gyara mata ruffin mayafinta daya d’an zame kad’an.

Ganin ya juya ya shiga mazaunin driver ne ya sanya itama ta bud’e motar ta shiga baya ta zauna ta d’aura kan Mama akan laps d’inta tana shafawa tana kuka....

Basu kaiga k’arasawa asibitin ba taji yace
“Assalam alaikom,
Abba Ina wuni!
Dan Allah duk abunda kake yi ka bari kazo emergency yanzu akth…
Ba zan iya bayani a waya ba
Dan Allah Abba ka zo
Dan Allah.”

Shiru taji ya d’an yi kafin ya sake cewa
“Ok tam
Nagode.”

Ita dai Huda mamakin Aslam take yi yadda duk ya rikice
Da kuma yadda ya kira sunan Mama!
Sannan yanzu taji ya kira wani ‘ABBA’ yace ya samesu a akth!
A hankali a chan k’asan zuciyarta tace
“Waye ABBA???”.

BULAMA ✍️

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login