Showing 99001 words to 102000 words out of 124668 words
Chapter 34 - So Da Buri Book 1 Hausa Novels by Humaira Bulama.txt
zai iya ba domin kuwa tak’i chin abinci kuma daga ya matso kusa da ita sai ihu! K’arshe ma suma ta fara yi…
Gaba d’aya duk ta firgice.
Ganin haka yasa ya d’auki waya ya kira Dad wanda shima d’in jin da yayi tanata suma yasa yace “bara ya zo ya gani.”
Sannan ya kira Doctor,
shima Doctor d’in yace gashi nan zuwa.
Dad d’in yana zuwa yayi knocking k’ofa Aslam ya bud’e, basu ankara ba kafin ya shigo ta taho da gudu ta hankad’o Aslam d’in waje ashe ta kunce hannayenta ba tare da ta bari ya lura ba!
A take ta saka key…
Ba suyi wata wata ba Aslam ya fara k’ok’arin b’alla k’ofar Dad kuma ya tafi ya d’auko spare key!…Amman ko da ya zo ya saka k’ofar k’in bud’uwa tayi sakamokon barin key d’in da tayi a jiki ta ciki..
Suna cikin kiciniyar bud’ewa suka ji k’arar fad’uwar abu kamar kujera, a rikice Aslam yayi kan 3 seater d’in da take a parlourn ya cewa Dad “ya zo ya kama mishi”.
Haka suka kinkimi kujerar da kyar, suka yi kan k’ofar da gudu da k’arfi suka buga!
Allah ya taimake su kuwa ta bud’u….
Aslam kasa motsi yayi sakamokon ganin k’afafuwanta a sama suna lilo kanta kuma tayi hanging a jikin chandelier d’in d’akin, sai dai k’afafuwan nata still suna d’an motsi!!.
Dad ne yayi k’arfin halin shiga da gudu ya d’auki kujerar data taka ta sak’ale kan nata ta yar! Ya saita mata ya d’aura kafafun nata a kai sannan ya hau ya kunto ta, sai dai zuwa wannan lokacin bata motsi!.
Shi dai Aslam duhu kawai ya fara gani daga nan bai sake sanin inda kanshi yake ba.
Sai da ya farfad’o tukunna ya fahimci ashe suma yayi…
Yana farfad’owa Dad da Arshaad suka yo kanshi suna tambayar shi jiki…
Cikin tsananin tashin hankali , muryarshi tana rawa yace
“Dad ta mutu ko?
Shikenan nayi silar mutuwar mahaifiyata!!”
Da sauri Dad yace mishi
“Bata mutu ba Aslam, suma kawai tayi.”
A tunanin Aslam kwantar mishi da hankali kawai Dad yake k’ok’arin yi, shiyasa yak’i yarda da zancenshi har sai da Dad d’in ya kaishi ya ganta ta window tana zaune Gwaggo Asabe tana bata abinci a baki hannunta kuma ana mata k’arin ruwa!.
Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan yace
“Alhamdulillah”
Ba a dad’e bai aka yi discharging d’inshi..
Auna komawa gida ko gama dedeta parking d’in mota bai bari Dad yayi ba, ya fito cikin hanzari ya nufi cikin gidan..
A d’akinsa Dad ya sameshi…yanata kiciniyar had’a kayayyakinsa, gaba d’aya ya sauk’o da akwatina ya hargitsa d’akin da alamun komai da komai yake son tattarawa dan hatta games d’insa suka har yayi parking nasu a daban.!
Da sauri Dad yaje ya rik’e mishi hannu..
Yana juyowa yace “Dad please! Don’t stop me i’ve to do this..”
“Shh” d’in da Dad yace mishi ne ya sanya shi yin shiru.
Ji yayi Dad d’in ya rungume shi ya fashe da kuka…..
Sai da Abba da Daddy suka shigo tukunna suka iya lallashin Dad! Dan Aslam shi kam ya ma kasa cigaba da magana in banda ajiyar zuciya babu abinda yake ta faman sauk’ewa!.
Bayan sun yi shiru ne Abba yayi suggesting “Aslam d’in ya je side d’inshi ya zauna, ba lalle su dinga had’uwa da ita ba in yana chan.”
Ajiyar zuciya Dad ya sauk’e kafin yace
“Abun nata kamar har da aljanu fa, dan indai suna a waje d’aya tou bata sakewa koda kuwa basu yi ido biyu ba!
Daman wajen da yafi dacewa yaje idan irin haka ta faru shine gidan Gwaggo Asabe tou itama yanzu mijin nata ya rasu a gidan itama take!
Sannan y’ay’anta(Gwaggo Asabe)duk ba wani girman
Aslam d’in suka yi ba ballantana a ce yaje gidansu ya zauna!
Babbar 3 years ta bashi, k’aramar kuma 2 months.
So kawai ni a nawa tunannin gara in tafi dashi Abuja…”
Aslam d’in ne yace musu “Dan Allah kawai yanason barin k’asar gaba d’aya! In komai ya lafa sai ya dawo…”
Haka nan ba yadda suka iya, ganin halin da yake ciki yasa suka amince ya tafi...............’.
…….
Kiran sallar farko ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi!
A hankali ya sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya,
idanuwan nan nasa sun kad’a sun yi jazir! Sannan jijiyoyin goshinsa duk sun yi rud’u rud’u!
A hankali yace
“Mommy, please this time around don’t push me away!
Ko menene kike ji ki yi k’ok’ari ki danne ki yi fighting…..i don’t want to run anymore! All my life tun Ina js 1 nake boarding school, hutu kuma sai dai inje inyi a wani waje!
I don’t want this life anymore, it sucks it hurts, i need you…”
A hankali yace
“I’m all alone, please get well.”
Motsi yaga ta fara alamun zata farka hakan yasa ya d’an matso da hannunta (wanda tun d’azun yake a cikin nashi) saitin lips d’inshi, a hankali yayi kissing hannun nata sannan ya mayar mata shi kan cikinta ya mik’e da sauri ya fita dan yaga motsin nata ya tsananta…..
Sai da yayi sallah yayi azkar..
Ya dad’e yana karatu tukunna bacci mai dad’i ya kwasheshi around 8:40 am.
Jin ana tab’a shi ne yasa ya fara k’ok’arin bud’e idanunsa,
dishi dishi yake ganin Arshaad kafin ya fara ganinshi sosai yana yi masa murmushi.
Mik’a yayi yai salati sannan ya d’an Mike ya gishingid’a a jikin gadon kafin yace “Morning,
You look energetic! Amman ni kam to me yau d’in lazy Sunday ne..so good bye, baccin bai ishe ni ba.”
Yana shirin sake komawa ya kwanta Arshaad ya rik’esa, sannan yana dariya ya zaro wayarshi ya nuna mishi screen d’in.
Kalla Aslam yayi sai kuma ya zaro idanu yana kallon shi kafin yace “you serious!! 2:00 as in 2:00 na pm?”
Dariya Arshaad yayi, cikin gatse yace “a’a,na am.”
Da sauri Aslam ya sauk’o akan gadon yana cewa “subhanallah ya akai time ya tafi haka!
Ban yi sallah ba fa!”
Sannan ya fad’a toilet cikin sauri, bai fito ba sai da yayi wanka..
D’aure da bathrobe bak’a ya fito kanshi na digar ruwa, a gurguje ya zura jallabiya sannan ya tada sallah.
Sai da yayi addu’o’i bayan ya idar, tukunna, ya mik’e ya nufi akwatinshi........
Arshaad wanda yake chattn da Huda, yanayi sama sama yana kallonshi yana mamaki
yadda Aslam d’in yake shiryawa, dan duk k‘ak’ale k’ak’alenshi Aslam kam ya fi sa…
Ya shafa wannan ya fesa wanchan ya goga wannan duk shi kad’ai! Sai da ya gama tsaf tukunnan ya zaro wasu riga da wanda masu masifar kyau, wandon black rigar kuma grey.
Sai da ya fara saka wandon tukunna ya zare jallabiyar ya saka singlet da rigar ya sake fesa turare sannan ya zo inda Arshaad yake ya zaune tukunna ya sa hannu ya warce wayar!.
Kallon screen d’in yayi sai kuma da sauri ya mik’awa Arshaad d’in wayar sakamokon heart heart d’in da ya fara gani tun kafin ma ya kai ga karanta chat d’in.
Dariya Arshaad d’in yayi kafin yace “saikace kaga dodo?Shine surprise d’in da nake ce maka zan nuna maka, yau za muje ma ku gaisa, i’ve told her already.”
Shiruuu, Aslam yayi for some minutes, chaaan! Ya nisa kafin yace
“Arshaad a brotherly advise..
Ka tabbata Yarinyar da kake so is suitable for Granpa, kar kaje ka d’auko wadda kai da ita duka zaku sha wahala!
Idan har ka san she’s not fit to be in this family to kar ma ka fara, kar ka wahalar da kan ka itama ka wahalar da ita…
Saboda i’ve seen a lot!
A duk lokacin da na zauna nayi tunani sai inga duk matar da aka auro cikin family d’innan ba tare da yarda Granpa d’ari bisa d’ari ba to sai tayi ending somehow! Take my Mom for example, ita da Anty Maryam
Those two ladies, zan iya ce maka they are the nicest of all amman ka duba ka gani halin da suka tsinci kansu a ciki,
har gara ma Anty Maryam dan na san yanzu kam ita maybe tama yi wani auren kuma definately sun shirya da iyayenta, Mommy fa?
She‘s still in hell!! Both me and her!
I’m not saying wai Granpa ne ya d’aura mata rashin lafiya or something like that, tunda God knows waye ya jefota a bene that very day!
But case d’in Anty Maryam da Abba kam laifinsa ne
Dan ranar ina nan a gaba na yace “ko Abba ya saketa ko kuma ya d’aureta a jail! Kuma bama a Nigeria ba, daga ita har iyayenta zai d’aure sannan kuma ya tsine mishi!
Wai ai daman ya gayawa ita Anty d’in cewa ‘babu ita ba gidanshi da family d’inshi kwata kwata!’ Amman shine relatives d’inta suka kwaso k’afa suka zo mishi estate, dan haka she has to pay a price, for not listening to him...”
Gramma tana kuka tana bashi hak’uri Abba ma haka amman tsohon nan haka ya tursasa su.
The only person da nake jiyewa ni a wannan time d’in is Anty Maryam, saboda idan kaga kalar korar Karen da Mahaifinta yayi mata time d’in data koma gida zaka yi mamaki!”
Shiruu, Aslam yayi, chaan kuma ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace “idan nace zan tsaya baka labari to ban san ranar barin mu d’akin nan ba.
All I’m saying is kar ka zab’o wadda zaka sha wahala itama ta sha wahala, kuma azo ayi ta case!
Shiyasa nake jiranshi nake kuma addu’a, saboda ni kam idan nayi mixing up issue na love da wanda nake ciki a yanzu! I don’t think i can make it out…”
Ahankali Arshaad ya sauk’e ajiyar zuciya sannan yace
“Thanks”
Kafin ya mik’e yace mishi “muje ka fara gaida su Granpa se sai wuce ko?”
“Not now, ai muna da aiki a gabanmu, although lawyer d’inka yace min za ayi postponding case d’in wai an kashe C J ko?”
“Eh fa”
Cewar Arshaad.
Ajiyar zuciya Aslam ya sauk’e kafin yace “Ina son zuwa gaisuwa ma fa!”
Kallonshi Arshaad yayi kafin yace “Ka san shi ne?”
“Eh.
Yayan wani classmate d’ina ne
Immediate i think!
He’s not that old..
Da kyar ma aka bashi
Saboda age d’inshi, bai ma
dad’e da yin aure ba.”
Da mamaki Arshaad ya d’an kalleshi kafin yace
“Naji ance har da yaranshi biyar…”
Cikin katseshi Aslam yace “yeah, yana da triplets!”
Cikin son kawo k’arshen maganar yace
“Allah yaji k’anshi.
Let’s talk, na san ba za a d’u lokaci ana mourning d’inba.
Mu san abun yi tun lokaci bai k’ure ba.”
A hankali Arshaad ya koma ya zauna ya fad’a mishi dalla dalla yadda Auwal yayi tricking d’inshi yayi signing pappers d’in da komai da komai…
Ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace “to kayi mishi zancen zaka mayar da kud’in??”
K’asa Arshaad yayi da kai sannan yace “shiyasa yanzu nake so idan mun je ka tayani bashi hak’uri ya yarda ‘ya karb’i kud’in ayi withdrawing case d’in’.
Kuma ai kasan Granpa yanzu abun ma fitar mishi a kai zai yi, tunda ka san yadda yake baya son jira kwata kwata…inaga idan aka d’aga k’arar ba lalle yayi ta jira yana jira ba maybe ya hak’ura.
“Understood”
Shine abinda Aslam yace sannan suka d’an sake tattaunawa kafin yace “muje in fara gaida Mammy tukunna kafin muje mu sameshi.”
Suna fita a babban parlour suka tarar da Gwaggo Asabe.
Tana ganinshi ta mik’e kafin tace
“Yau kam an sha baccin gajiya gaskiya ga d’an wake shima ya gaji da jira..”
Murmushi yayi sannan ya gaidata bayan ta amsa suka nufi dining ya zauna.
Babu yadda bai yi da Arshaad akan yaci d’an waken ba amman yak’i, yace
“shi yana reacting to kuka.”
Haka nan Aslam ya cinye abinshi daga nan suka mik’e suka nufi gidan Mammy….
Basu sameta a k’asa ba sai da suka haura sama a parlourn sama suka sameta a gaban makeken show glass d’inta tana zuba turaren wuta a burner!
Arshaad ne gaba sai Aslam a bayanshi, shiyasa da Mammyn ta juyo bata lura dashi sosai ba.
Kallon Arshaad d’in tayi tace “kai da waye? har ka dawo? Ya naga baka dad’e ba?”
Murmushi yayi sannan yace
“Eh, bak’o na kawo miki ne, shiyasa.”
Da fara’arta take k’ok’arin lek’a bayan Arshaad d’in tana cewa “waye? to matsa mana in gan shi....”
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun!!!!”
Shine abunda ta furta a mugun tsorace!!
Bata san lokacin da burner d’in turaren wutan nata ya fadi daga hannunta ba a lokacin da Arshaad ya matsa Aslam ya baiyyana a gabanta!
Duk tsayawa suka yi suna kallonta….
Da sauri ta juya ta kaiwa Arshaad d’in duka kafin tace
“Uban ka!!! wannan ai sai kasa zuciyata ta buga!
Shekara bakwai ban ganshi ba kawai yanzu In ganshi a gabana ya kake tunanin zan ji?”
Dariya dukkan su suka sa kafin Mammy ta share kwallarta ta jawo Aslam d’in jikinta ta rungumee tace
“Welcome home son, we really miss u.”
A hankali ya zare jikinshi yana d’an murmushi kafin ya sa hannu ya share mata hawayen daya sake zubo mata
Yace “Miss u too, Mammyn mu.”
Yana d’an murmushi…..
Kafin minti biyar tuni Mammy ta cika gaban Aslam da kayan chiye chiye sai tambayarshi takeyi “me za a dafa mishi?”
Arshaad kam ya koma gefe sai faman kumbura yake yana mitar “shi an share shi daman ai ya san tafi son Aslam a kan shi!”.
Suna cikin haka Aaima ta shigo..
Ihun da tayi sai da suka tsorata duk suka d’ago suna kallonta
Ai kuwa da gudu ta taho ta fad’a kanshi tana murna itama har da hawaye, duk ta kanainaye shi…
Sai da yayi mata fad’an ‘bata san ta girma ba?’ tukunna ta d’aga shi tana d’an jin kunya ta koma gefe ta zauna…
Nan suka hau gasar bashi abinci a baki, sunk’i ma su bari yaci da hannun shi!
Sai da Aslam ya cewa Mammy “zai yi amai!!” tukunna ta kyaleshi.
Ranshi fess!! Haka suka baro b’angaren Mammy a ranshi yana yaba so da k’aunar da familynshi suke yi mishi
babu wani maganar y’an ubanci a tsakaninsu!.
Suna fitowa daga gidan da shirin shiga gidan Granpa suka ji ana kiran sallar la’asar!
Hakan yasa suka nufi masallaci kawai, suna zuwa suka yi alwalla aka tada sallah.
Sun idar kenan Aslam ya juya yana y’an kalle kallen yadda aka tsara Masallacin aka sake gyarawa karaff! Ya had’a ido da Granpa wanda ya tsareshi da idanu, murmushi yayi sannan ya cewa Arshaad “taso mu je”
Suna mik’ewa suka ga shima ya mik’e ya fice waje, da sauri suka fito Arshaad yana cewa “da alama yau za kuyi fad’an farko kai da mutumin naka!”.
A bakin wata bishiya suka sameshi, suna zuwa Arshaad ne ya fara cewa
“Good afternoon Granpa”
Banza Granpa yayi dashi bai ko juyo ba shiyasa ya koma gefe ya tsaya
Aslam ma ya matsa yace mishi
“Good afternoon Granpa.”
Shima yayi banza da shi.
Murmushi Aslam d’in yayi sannan ya k’arasa inda yake yayi hugging d’inshi ta baya…
Sai a lokacin ne na tab’a ganin murmushin Granpa!, ashe har dimple gareshi….
A hankali yasa hannu ya d’anyi tapping hannun Aslam sannan ya d’an juyo lokacin da Aslam d’in ya cika shi..
Still da k’ayataccen murmushi kwance a kan kyakkyawar tsohuwar fuskar shi.
Yana juyowa yace
“yanzu ka dawo?”.
“A’a jiya around 2:00 am”.
“A time d’in da muka yi chat ma ka taho kenan?”.
“Eh, ai its a surprise.”
Murmushi Granpa d’in ya sake yi sannan yace
“I’m amazed!
Welcome home.
How have you been?”
“Alhamdulillah” Aslam yace.
A hankali Granpa d’in ya juya sannan yace mishi
“walk with me..”
A tare suka d’an fara tafiya…..
Haka nan sai da suka kusan zagaye estate d’in, suna tafe suna hira, Granpa yana tambayarshi yanayin aiki da kuma zamanshi a chan shi kuma yana bashi amsa…
Duk wanda ya ga Granpa a wannan rana to ya san yana cikin farin ciki.
Zagayowa suka yi ta wajen gate d’in shi dan haka ya cewa Aslam d’in “bara ya shiga ciki akwai wasu y’an takardu da zai duba.”
Har ya juya yaji Aslam d’in yace
“Granpa pls i need a favour”
Juyowa Granpa d’in yayi kafin yace “If it is about Arshaad don’t even go there, i won’t change my decision he must pay for wat he did!!”
Da sauri Aslam yace
“Wallahi Granpa framing d’inshi aka yi, kuma zai dawo da duk kud’in suna accnt d’inshi bai tab’a komai ba tunda daman ba sata yayi ba ballantana ya tab’a.”
Shiruuu, Granpa yayi, na d’an lokaci, chaan! Kuma yace
“Framing?”
With full confidence Aslam yace mishi “Yes, zamu iya maka presenting evidence!
Please Granpa, give us a chance.”
“Aslam, today I’m in a very good mood saboda na ganka…so zan iya yi mishi sassauchi.
Sassauchi na shine ‘ya kawomin evidence d’in cewa framing d’inshi aka yi, ni kuma daga nan zan janye case d’in, for your sake!”
Durk’usawa Aslam d’in yayi cike da farin ciki yace
“Thanks a lot Granpa, za a kawo evidence d’in in sha Allah.”
A hankali Granpa ya shafa lallausan gashin kanshi sannan yace
“Allah yayi maka albarka.”
“Ameen”
yace sannan ya mik’e
yace zai shigo zuwa anjima su gaida gramma in sha Allah.”
Daga haka ya juya ya tafi, shima Granpa ya shige.
A bakin masallaci inda ya bar Arshaad a nan ya sameshi
“Sorry.
Na barka kana ta jira ko?”
Murmushi kawai Arshaad yayi sannan yace
“Um um!
Someone kept me busy.”
Yayi maganar yana nuna mishi chat d’in da yake yi da Hudan.
Murmushi Aslam yayi kafin yace “muje dai inga Yarinyar da ta haukatamin kai haka.”
Dariya Arshaad yayi
Da sauri Aslam yace
“Um good news!
Granpa yace muyi presenting evidence to him daga nan case ya mutu!.”
Cikin murna Arshaad yayi hugging Aslam sannan yace
“Thanks a lot na gode!”
A hankali Aslam yayi murmushi yace “NVM”.
Sannan suka fara tattauna akan yadda zasu nemo evidence d’in…suna maganar suna tafiya…..
A hanyar shiga gidansu Aslam Arshaad ya hango motar Auwal da gudu ta taho…
Har Auwal d’in ya wucesu sai kuma yayi reverse ya dawo ya fito a motar ya zagayo ya zo inda suke.
Yana zuwa ya kalli Aslam sannan yayi murmushi yace
“Ashe ka dawo! Shine ba ko irin
‘Hi’ d’innan?”.
Murmushi Aslam yayi kafin yace “Hi, Auwal.
Ya gida?”.
“I’m gud, gida kuma ai tunda kana tare da little brother d’inka i’m pretty sure ya fad’a maka everything da cases d’in da suke faruwa da komai, right?”
Auwal yayi maganan yana kallon Arshaad yana murmushi!
Kafin ya d’an juyo da sauri to Aslam d’in yace
“Oh I almost forgot, na san ba zai tab’a fad’a maka wannan ba or maybe shi kanshi bai sani ba”
A hankali ya matso kusa dasu yad’an kare gefen bakin shi da tafin hannunshi kamar bayaso a ji kafin a hankali yace
“Because nima, i eavesdrop”
Sannan ya matsa yana d’an murmushi kafin ya fara magana
“last 3 months an fitar da Mommy India and her psychiatrist yayi conforming ‘she’ll