Showing 102001 words to 105000 words out of 109746 words
ma kasa cewa komai.
A hankali Arshaad ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace
“Auwal do me a favour..
Ka kira Sakina, inaso kayi mata bayanin komai
amman kace kar ta fad’awa kowa kawai a san yanda zaai a gudanar da event d’in ba tare da an jira ni ba!
Yanzu na san Mammy idonta a kaina yake dan tun d’azu nake lura tanata turo Aaima tana mata patrol so ba zan iya fita ba.
Sakina is smart she’ll know what to do yanzun
In shaa Allah ni kuma anjima da daddare za mu je
Ina son ganin Hudan
na san abunda zan yi.
For now amman kawai ka lallab’a mun Sakina tayi handling komai, kafin nan da anjima.”
Cike da gamsuwa Auwal d’in ya d’aga kai alamar to
sannan ya zaro waya ya fara kiran Sakina.
Tun lokacin da aka fara rangad’a gud’a taji
dan haka ta mik’e ta lek’a ta windown d’akin Shuwa..
Ji tayi kamar ta zuba ruwa a k’asa ta sha sakamokon hango su su biyu a zaune da ta yi!
Bata ganin fuskar su especially Huda da har yanzu tata fuskar a lullub’e take sannan windown a rufe ne kuma sun yi mata nesa..
Bata san lokacin da hawayen farin ciki suka zubo mata ba!
Tana gani yanda mata suke zuwa suna d’an d’aga mayafin kad’an suna shafa mata da hannuwanta shi kuma a tafukan hannunshi da goshinsa ake shafawa
sannan su ajjiye musu gift a cikin d’an kwanon da aka ajjiye wasu kuma kud’i.
Ba k’aramin burgeta suka yi ba, banda kalmar ‘Alhamdulillah’ ba abunda taketa nanata
a ranta tana mamakin dalilin da ya sanya Aaima karkacewa ta gilla mata wannan uwar k’aryar haka
Wata zuciyar kuma tace maybe an gyara abunne Mammyn ta sauk’o
cikin kawar da tunanin a ranta tace
“Chan ta matse musu”
Sannan ta hau raya yanda zata yiwa Arshaad in sun had’u na k’in d’aukar wayarta da yayi.
K’arar wayarta dake kan gado ce ta katse mata tunani
dan haka ta isa ta d’auki wayar..
Kamar ba zata d’auka ba
ganin sunan Auwal ne sai
kuma ta d’anyi murmushi a ranta tace
‘Kar In zama kaza mana’
dan haka ta d’auka ta kara a kunnenta kafin yace komai tace
“Gashi chan Ya Arshaad d’in yazo suna zaune ana saka su a lalle.
Thanks for your time”
Tana gama fad’in haka ta katse kiran.
Da mamaki suka kalli juna shi da Arshaad dan a hands free wayar take
Shiruu, d’akin ya d’auka chan kuma Auwal yace
“Bara inje wajen maybe ko fushi suka yi shiyasa tayi min gatse”
Cikin katseshi Arshaad yace
“Kaje wajen Mom mana.
Kace bama ka san ta dawo ba
bayan a gida d’aya kuka kwana.
Kaje wajenta daga nan
ka d’an lallab’ata
may be in tasa baki Mammy ta hak’ura.”
Har ya d’anyi gaba sai kuma ya juyo yace
“Su kuma fa?”
“Kar ka damu na gama tsara komai, zuwa anjima da daddare za muje in shaa Allah.
Zan sameka a gida.”
Cewar Arshaad yana mai maida kanshi da lumshe ido dan kanshi ba k’aramin ciwo yake yi ba amma kuma har ga Allah y’ar maganar da ya samu suka yi da Auwal ya d’an ji sassauci a ranshi.
“Allah ya kaimu”
Shine kawai abunda Auwal yace yana me fita daga d’akin
da waya kare a kunnen shi still yana sake kiran Sakina
sai dai har ya tsinke bata d’auka ba.
A tsakiyar main parlourn suka kusa yin karo da Aaima,
kasancewar hankalinshi naga wayarshi yana turawa Sakina message.
D’agowa yayi yana kallonta
itam ma shi take kallo kafin da kyar ta iya cewa
“Ya Auwal Ina wuni”
“Fine”
kawai yace yana me wuce ta.
Da sauri ta sha gabanshi kafin tace
“Am dan Allah gida zaka je?”
Maida hankalinshi yayi a wayar kafin yace
“Eh”
A hankali tace “Owk, d’an jirani plss
Mammy ta bani sak’o wajen Mom ina so zan kai mata.
Bara in d’auko vail d’ina”.
Ba tare da ya kalletaba ya k’arasa kan d’ayan daga cikin kujerun parlourn ya zauna still yana danna wayarshi.
Ta fahimci yaren kuramen nashi dan haka ta wuce sama da d’an sauri …
Bayan 5 minutes ta sauk’o!
Ta chanza kaya daga atamfar ankon dake jikinta
ta d’aura bak’ar abaya tayi rolling, ta sanya lipstick da powder. Ta yi kyau kuwa ba laifi.
Gabanshi tazo ta tsaya sannan tace “muje”
Tun kafin sauk’owarta daman ya san ta taho sakamokon k’amshin turarenta da ya karad’e parlorn! Tana sauk’owa kuwa ya lura da ita amman sai ya kawar da kai…
Wai me Aaima take nufi ne?
Ya kasa gane kanta kwana biyun nan! Har magana take mishi ta WhatsApp yanzu.
Yana tunawa lokacin da suke tare yasha gaya mata yana matuk’ar son yaga mace da black abaya tayi rolling abun yana burgeshi shiyasa
kusan duk lokacin da zasu fita tare takan yi irin wannan shigar kuma ta san baya son native cloth kwata kwata
Inba riga da wando ba to abaya…..
“Mu tafi, na shirya”
Muryarta ta katse shi.
Kallonta yake yi tun daga sama har k’asa! Hakan kuwa ba k’aramin dad’i yayi mata ba.
A hankali taji yace
“Ina sak’on??”
Diriricewa tayi kafin da kyar tace
“Yana cikin purse d’innan”
Tayi maganar tana nuna mishi purse d’inta wadda ta saka iya wayarta da lipstick a ciki.
Ajiyar zuciya ya sauk’e
kafin ya mik’e yayi gaba….
Shi fa har ga Allah kunyar ta yake ji a halin yanzu..idan
ya tuna irin yanda ya fito mata k’iri k’iri ya fad’a mata abunda yake buk’ata daga gareta da kuma yanda ya furta mata kalmar ‘ba ya k’aunarta’
Wasu abubuwan da yawa da ya yiyyi idan yana tunasu a yanzu sai ya dinga ji kamar k’asa ta tsage ya shiga!
Tabbas Daddy yayi gaskiya daman ya tab’a gaya mishi
‘’’Akwai ranar dana sani!Ranar da zaka ji inama ana yin reverse ayi maka domin ka samu ka aikata alkhairi ka kuma goge duk wani abun da kayi marar kyau.
Ranar tana nan zuwa, ko bayan raina za kace na fad’a maka‘’.
Tabbas kuwa tun kafin aje ko Ina gashi ranar ta zo
Ya san dalilin da ya sanya Sakina take gudunshi ta kuma k’i sa! Bai wuce akan tunanin da take yi na alak’ar shi da cikin jikin Jalila ba ne…..bai san
wanne kalar kallo zata yi masa ba idan taji tabbas cikin nasa ne!
Ballantana kuma azo kan maganar halayyarshi
da baya fatan Allah yasa Sakina ta sani!
So yake ya gyara komai
ya zama mutumin da ta ambata tana son kasancewa tare da! Gashi already yana da competition, yanzu ahaka ma ta riga ta nuna mishi ta zab’i Ashraff a kansa
ina kuma ga idan taji wata magana akanshi!
Ya kenan?….,
“Innalillahi wa innailaihirrajiun”
Itace kalmar da ya ambata yana mai dafa motar shi
dan har sun iso bakin motar.
Da sauri Aaima tace
“Subahanallah Ya Auwal mai ya faru?”
Tana mai matsowa inda yake.
Sai da ya d’an runtse idanunsa kafin ya dawo dai dai tukunna ya samu yace mata
“Ba komai, shiga mu tafi”
Yana mai zagayawa ya bud’e mazaunin driver ya zauna.
Tana shigowa ya tada motar yaja suka fita.
Har suka isa mansion d’in nasu babu wanda ya samu damar furta kalmar ‘a’ a cikin su.
Shi ya fara fita daga nan itama ta fito suka nufi ciki.
Suna shiga parlourn suka tarar da Jalila ta d’aura k’afa d’aya kan d’aya ga remote a hannunta tana ta chanja channel…
Lumshe idanuwanshi yayi a hankali ya shak’i iska ya furzar sannan ya bud’e idanuwan nashi
a hankali a fili yace
“My worst regret!!”
Ya kasa gaba ya kasa baya.
Aaima ce tayi k’arfin halin k’arasawa tsakiyar parlourn inda Jalilan take
tana kallon ta da d’an mamaki dan kamar bata tab’a ganinta ba.
Fitowar Mom daga kitchen ne ya katse mata tunani har shi Auwal d’in
Uwa mai dad’i suna had’a ido yaji wani sanyi a ranshi…
Takawa yayi har inda take yana zuwa ya sa hannu yayi hugging d’inta.....
Tun a cell Mom take aiyyana kalar abubuwan da zata yiwa Auwal kala kala
In Allah ya maidota gida lafiya dukda kuwa tana shakkarshi,
babu yadda bata yi mishi shi da Arshaad akan su basu kud’i su samu su fito ba
amman suka hana su
saboda suna shakkar Granpa sannan basu san darajar su uba and sun rainasu!
Sannan ta dawo amman tun jiya take zuba ido but bataga k’eyarsa ba.
A hankali yace “welcome home“
Ta manta rabon da Auwal ya nuna wani affection a kanta irin haka, ba ta san lokacin da wata kwalla ta zubo mata ba,
a hankali tasa hannu ta share
tana jin duk wata wutar masifar da ta shirya juye mishi tana sauk’a daga k’irjinta.
Muryar Jalila ce ta katsesu jin da d’an k’arfi tace
“Adama ina shayin nawa??”
Da mamaki Aaiima take kallonta sai kuma ta juya tana kallon su Mom.
Da sauri Auwal ya cika Mom ya yunk’ura zai yi wajen
yaji ta rik’e mishi hannu
yana juyowa ta girgiza mishi kai daga nan ta koma kitchen ta d’auko tea d’in daman ta gama had’awa waya take so tayi shiyasa ta manta ta fito d’aukar wayar.
Zata nufi wajen Jalilan amma ga mamakinta sai taga Auwal ya tare, yace
“Ba zata kaiwa Jalilan ba wallahi!.
Idan tana son sha to tazo ta d’auka anan d’in!”
Ya fad’a hakan yana mai karb’ar tea d’in ya d’aura akan dining sannan yaja hannun Mom d’in za suyi sama.
Da kyar mamakin Auwal ya barta ta iya ce mishi
“Ban ci abinci ba,
Bara in na gama sai muyi saman dukkanmu ko?”
Ajiyar zuciya ya sauk’e ya watsawa Jalilan wata uwar hararar da sai da y’an hanjin cikinta suka kad’a!
Daga nan ya cika hannun Mom d’in ya wuce sama.
Tabbas Jalila ta d’an sha jinin jikinta kuma it’s like kamar akwai abunda yake damunshi
sannan tanada buk’atar kud’i daga hannunshi da kuma alfarmar ya barta ta je wajen Umma
dan she can’t afford to loose Arshaad, duk da kuwa Umman tace mata akwai nasara amman tana son zuwa yau ta bita ta je da k’afafuwanta, shiyasa ta barshi kuma bata sake yiwa Mom wani yunk’uri ba ta hak’ura kawai ta barshi akan idan ya d’an huce kamar nan da 20 minutes haka zata kirashi ta zayyane mishi buk’atun ta.
Hira sosai Mom da Aaima suke yi, Jalila kuwa tana gefe tanata hura hanci.
Chan Mom ta cewa Aaiman tazo suje suci abinci.
Haka suka mik’e suka isa dining d’in sukai lunch d’insu cikin kwanciyar hankali.
Sai a sannan Aaima take tambayar Mom wacece jalila?
Murmushi kawai Mom d’in tayi sannan tace mata
“no one”
kawai, daga nan tace
“Ta mik’e ta je ta jirata a parlourn sama.
Hakan kuwa akayi,
Mom na ganin wucewar Aaima ta mik’e itama tayi kitchen…..
Dama tun d’azu ta sallami cooks da masu goge gogen gidan! Tace musu “su tafi part d’insu In akwai wani abun zata neme su!”
Har ta shiga ta d’auko abunda zata d’auka ta fito
hankalin Jalila yana kan kallo.
A dai dai stairs na bakwai ta tsaya ta zuba abunda zata zuba tayi sama abunta da cup d’in cikin sand’a.
Kamar minti biyu ta dawo bayan ta ajjiye abun hannunta a d’an gefe kad’an a nan saman ta tsaya a saman bata sauk’o ba kafin ta d’an fara sauk’owa sai kuma ta tsaya tana lek’en parlourn k’asan kafin tace
“Jalila ga Ummanki tayi miki message, ungo wayarki, tunda na hau nake ta jin k’arar wayar shine na duba d’akin naga misscalls da messages
Za ki zo ki karb’a?
Ko kuma ma kawai bara in karanto miki kina daga zaune dan na san mik’ewa yanzu aiki ce a gareki saboda yanayin da kike ciki.”
Ba tare da b’ata lokaci ba Mom ta fara karantowa
“Aslm Jalila ya gidan, yau banjki....”
A zabure Jalila ta mik’e tayi hanyar stairs tana masifa
“Adama bana son rashin mutunci!
Yanzu ke inda ace uwarki ce
tayi miki message zaki yarda a karanto miki….?”
A fusace take maganar tana tahowa da d’an cikinta wanda ya d’an fara tasowa!
K’arfen stairs d’in ta kama cikin sassarfa ta fara taka stairs d’in har da d’an gudunta,
tana zuwa kan na bakwai kuwa ta zulme santsi ya d’ebeta a take ta hantsila ta gangara ta koma k’asa ta fad’a ruf da ciki a kan cikinta!
Wata azababbiyar k’ara ta saki daga nan ta saki jiki
bata sake motsi ba!.
Da sauri Mom wadda daman da tsummanta har biyu
ta ajjiye
a gefe farkon stairs d’in
dan haka ta d’an juya ta d’auka ta sauk’o, dai dai wajen na bakwai d’in ta saka wet one d’in da ta jik’a a ruwan omo ta goge wajen tass kafin
ta saka dry one d’in ta goge wajen sosai shima.
Dai dai nan Auwal da Aaima waenda k’arar Jalilan ya janyowa hankali suka taho a tare…
Da sauri Mom ta d’ago ta kalleshi a rikice kafin tace
“Yauwa Auwal zo ka duba inaga jiri ne ya kwasheta kaga ta fad’i kamar ma ta suma bara in d’ebo ruwa.”
Ta fad’i hakan tana mai sake duk’unk’une tsummokaran a hannunta Yayinda su kuma gaba d’aya hankalinsu ke a kan Jalila…
Idan idanuwansu ba gizo suke musu ba kamar jini ne yake fitowa ta k’asan ta!
Shiyasa ma kwata kwata basu lura da Mom d’in ba
suka fara sauk’owa har suna y’ar rige rige, ita kuma ta wuce wuff!! Tayi kitchen tana mai cewa “bara in kawo ruwan”
Hankalin Aaima ba k’aramin tashi yayi ba ganin kamar ma ta mutu ne! Ga kuma jinin da taga yanata kara b’ulb’ulowa,
shi kanshi Auwal duk da cewa babban burinshi a halin yanzu yayi getting rid of Jalilan ne
amman sai da ya firgita ba kad’an ba.
Suna a haka Mom ta fito,
ruwan da ta zo da shi a jug gaba d’aya sai da ta juye mata shi amman ko gezau Jalilan bata yi ba!
Ganin haka yasa Auwal yin sama da gudu ya je ya d’auko makullin motarshi ya dawo ya zo ya kinkimeta yayi waje su Mom suna binshi a baya….
Yana gama sakata a bayan mota motocin su Dad na shigowa
ganinshi a d’an firgice yasa suka tsaidashi suka hau tambayarshi..
Da kyar ya iya ce musu Jalila ce ta fad’o a bene ta suma
ya shige ya tada motar ya fice a 70 ya bar su Mom suna sake yi musu bayani
“Allah ya sauwwak’e” suka ce.
Shi kam Dad bai ma san wacece suke magana akai ba
daga haka suka nufi side d’in Abba
dan Dad yad’an yiwa Daddy bayani a mota
So ya kamata su sameshi ya maida Ummi first kafin granpa ya tsine mishi, sannan kuma ayi maganar ta yanda za a b’ullo wa haukar Mammy
dan sun yi alk’awarin in dai sune mazan mt masu fad’a aji
to tabbas gobe sai an d’aura aure bi izinillahi!
Babu fashi…..
GANDUN ALBASA
“Ku bata iska mana ya duk kuka lullub’eta haka ne??!!”
Cewar Baaba Talatu wadda take k’arasowa wajen da kyar.
Da sauri duk aka fara matsawa gefe.
Hansai da Anty Zainab da wasu mata
Baaba Talatu ta umarta da su d’auketa a kaita parlourn
da ga nan ta cewa Maryam “ta kirawo Likitan da take zuwa tana dubasu.”
Hakan kuwa aka yi
Nan tace mata “gata nan zuwa tana ma kusa dama, su bata nan da minti goma.”
Ko da Likitan ta zo da kyar ta samu Umma ta farfad’o
amman ta bada shawarar a kaita emergency a take dan jininta ba k’aramin hawa yayi ba!
A motar Abba k’arami wanda suka iso yanzun nan shi da iyalinshi da Mahaifiyarsa da Baban sa aka kaita asibitin.
Duk da halin da take ciki da suka had’u da Ya Jamilu a waje bakin motar sai da ta tambayeshi “ina Baba?”
“Yana nan”
kawai ya iya ce mata daga nan ta shige ita da Anty Zainab wadda ta zauna a gaba suka wuce asibitin.
Da kyar Mama ta iya tsayawa aka gama kallon lefen da ita
daga nan ta wuce ta shige tayi sama…
Tun a corridor d’in d’akin Shuwa ta saki kukan da take ta k’ok’arin dannewa. Da sauri ta tura k’ofar ta shige tana wani matsanancin kuka a tunaninta ba kowa amman tana shiga suka yi ido biyu da Sakina. K’ok’ari take yi ta danne kukan ta wayance amman ta kasa dan haka kawai sai ta durk’usa ta sake sakin shi a wajen da dukkan k’arfinta tanayi kamar ranta zai fita.........
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
54
Da sauri Sakina ta k’arasa wajenta ta hau tambayarta “mai ya faru?”
Bata iya bata amsa ba, sai da ta d’an dedeta kanta da kyar
tukunna ta d’ago jajayen idanunta tana kallon Sakina tace
“Kina da number Abba?
Baban Huda.”
A hankali Sakina ta hau girgiza mata kai..kamar wadda ta tuna wani abun kuma sai
ta mik’e ta isa gado inda ta ajjiye purse d’inta,
tana cewa
“Amman ga wayar Hudan, bara in kira miki shi ta nan”
Da sauri Mama ta mik’e ta isa inda take dai dai
Sakina ta fara dialing number Abban, Mama ta sa hannu ta karb’a wayar ta kara a kunnenta.
Sai da kiran ya kusan tsinkewa tukunna ya d’auka! A hankali taji yace
“Princess, how was your day?”
Sai da Mama ta lumshe idanunta na sakanni wasu zafafan hawaye suna zubo mata tukunna tace
“Horrible, Abba!
Her day was horrible!”.
Da sauri ya gyara zamanshi
kafin yace
“Maryam”
Cikin son sake tabbatarwa.
Cikin kuka tace
“Lalata mini rayuwa da farin cikin da kayi bai isheka ba sai da ka had’a da Huda ko?
A haka sai faman ik’irari da pretending d’in kana k’aunarta kake yi!..
Abba in dai har kana son ta mai yasa ka jefa ta a irin wannan relationship d’in???
Da ka san mahaukaciyar matar yayanka ba zata so auren Arshaad da Hudan ba mai yasa tun farko kuka had’a?
Saboda ku maidamu abun kwatance ko me??
An tara mutane
k’iiri k’iri Ango yak’i zuwa! A Ina aka tab’a yin haka?
To bara kaji in gaya maka
Tunda har Mahaifiyar Arshaad da kanta ta furta cewar bata son y’ata a matsayin suruka
To
Wallahi ko ta dawo tace tana so, Ina so ka san cewa
‘maganar aure babu ita!!’
Sak’o ne wannan na baka, ka gaya mata ka gayawa Arshaad da wakilin shi!
Dan ba zan tab’a yarda in kai Huda gidan da ba’a k’aunarta ba wallahi.
Saboda na san zafin k’iyayyar surukai”
Ta fad’i haka tana fashewa da wani matsanancin kuka.
Da sauri Abba wanda yakejin zuciyarshi tana wani mahaukacin racing yace
“Maryam listen to me dan Allah ki bar wannan kukan”
Cikin tsananin b’acin rai tace “Abba kuka yanzu na fara!
Na san zan yi kuka especially idan Allah ya kaimu gobe aka yi calling off auren y’ata na ganta a