Showing 75001 words to 78000 words out of 87228 words

Chapter 26 - YARO DA KUDI Complete Hausa Novels by Binta Umar Abbale .txt

ba.








"Momy nagode sosai Allah yakara girma"
Yafada fuskarshi cike da murmushi




Tare suka shiga falo Momy na rike dashi tamkar wani zai kwace shi sai tsokanrshi takeyi ango babu babbar Riga








Ya zauna cikin kujera yana dafe kanshi yace"Momy in banda kin damu ni ina ruwana da wata babbar riga, ko dazu ma da nasa damuna tayi wallahi








Tace"Yanzu dole ka rika sanyawa sabida girma ya hau kanka"






"Momy wane irin girma kuma"






"Na aure gashi kana da mata biyu"






"Momy ko mata hudu gareni babu abinda zai hanani sanya kananun kaya"
Yafada yana tabe baki




"Nasan bazaka fasa halinka ba ai"
Momy tafada tana kokarin mikewa tsaye
Tace"a kawo maka abinci ko"?




"A'a Momy ruwan tea zan sha ya isa"
Yafada yana kallonta sabida yasan dole sai tayi magana






Hararashi tayi tace "baka isa ba kaji nafada mak....








Sallamar su Alhaji Alhasan ce ta katse Momy, fuska a sake ta amsa tana musu barka da zuwa






Momy ta nuna musu kujeru tace bisimillah Ku zazzauna






Cikin mutumci suka gaigaisa da juna, Alhaji Alhassan yayi gyaran Murya yana kallon Momy yace"tabbas Hajiya Aminatu kin haifu kuma kin haifi Dan halak, yafada yana nuna Nasir ya cigaba da cewa Wannan yaro ya rufa min asiri a lokacin da Dan Uwanshi Abdul latif ya so ya tona min a siri a cikin jama'a
[09/06, 00:18] +234 808 996 5176: [08/06/2019 7:23 PM] ®Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*112*
Alhaji Alhassan ya cigaba da cewa "Nasiru babu abinda zan ce dakai, ka rufa min asiri koma ka cika Umarnin da mahaifinka ya bari ubangiji Allah ya tayaka riko yayi maka jagora, Allah ya rufa maka asiri ya kareka daga sharrin masu sharri"




Fuska a sake Momy tace"wallahi babu komai Alhaji dama duk abinda kaga ya faru to dama haka Allah ya hukunta Allah ya rubuta Maryam ba matar Abdul bace shiyasa haka tafaru kuma dama mutum bai taba auran matar wani ba, ni dai abinda nakeso don Allah karkayiwa Abdul baki ka qaddara cewar dama Allah bai nufa Maryam zata zama matarshi ba"








"Duk abinda ya faru ya wuce agurina Hajiya shi kuma abinda yayi kanshi ya cuta ba wani ba gaba zaizo yana nadama, yayi nufin tozarta yarinyar mutane sai Allah ya rufa mata asiri dake batada hakkinsa"






"Momy ta sauke ajiyar zuciya sannan tace"wallahi Alhaji banji dadi wannan abu ba


"Allah yasa haka shi yafi alkairi"






"Alkairin kenan ma ki kwantar da hankalinki"
Alhaji Alhassan yafada yana kokarin mikewa tare da jama'arsa






Nasir ya mike ya biyo bayansu,


Da sauri Momy ta dauko masa babar rigarsa ta biyosu a baya ta mika masa wai lallai sai yasa




Dole tasa ya karba yasa tare da sa bakin Alhji Alhassan yace"a kwai sauran jama'ata dole zaka fito ku gaggaisa sosai domin dazu bansan lokacin daka gudo gida ba"








Momy tasa dariya gami da cewa"kamar ka manta halin Dan naka Alhaji kasan kwata-kwata baya son jama'a fa"








Shima dariyar yasa yace" dole yanzu yayi hulda da jama'a yadda nauyi ya hau kanshi yanzu yazama cikkaken mutum"


Momy tayi murmushi ita kadai tasan farin cikin da take ciki






Sai data ga ficewarsu sannan ta koma ciki








To ban garan su Maryam kuwa lokacin da labari iskesu, kasa katabus sukayi jikinsu yayi sanyi, Aunty tafi minti ashirin tana jajanta abun , Nasir ne ya auri diyarta Maryam anya wannan Abu ya hadu


Sai ta dinga tuhumar Nafi'u yadda a kaiyi haka tafaru, nan ya warware mata dukkanin abinda ya faru


Maryam kamar ta mutu Dan bakin ciki kuka takeyi wiwi, babu Abinda zata cewa Anwar sai dai tace "Allah yayi mata sakayya wannan tozarcin da yayi mata cikin jama'a
[08/06/2019 7:42 PM] ®Binta Umar Abbale: Shi kuma Abdul, ta barshi da Allah yadda yaci amanarta bazata taba yafe masa ba, in ta tuno wai ita matar aure ce kuma matar Nasir sai gabanta yayi ta mugun faduwa, Ya Rabi tayi tayi da ita tayi shiru abin ya gagara ,








Malam ya shigo yana sa6e babbar riga kana ganinshi kasan yana cikin tsantsan farin ciki






Kawai ya taddasu sunyi jingum jingum sai kace gidan makoki, ya bisu da kallo daya bayan daya kana ya mayar kan Maryam wacce ke rakube gefan kujera tana shirgar kuka kamar wacce a kai ma mutuwa






Ranshi ya baci ya daka mata tsawa gami da cewa"kukan mai kikeyi Maryamu"?








Ya Rabi tace"wallahi kuka take tun da taji labarin abinda ya faru, anyi anyi tayi shiru taki yi"






Zama yayi cikin kujera yana fuskantar ta yace" wani irin kuka zakiyi Maryamu ke da Allah ya rufawa Asiri lokacin da a kaso a tona miki, tabbas nasan a kwai abinda Allah ya boye a wannan al'amarin,
Abinda nakeso dake shine ki kwantar da hankalinki kina tare da albarkamu insha Allahu zakiga alkairi a rayuwarki mutukar kika yimana biyyaya, nine mahaifinki na kuma karbi sadakinki na kuma bawa Nasiru Auranki a madadin Abdul"
Malam ya karashe maganar gami da zira hannu cikin aljihun malin malin din dake jikinshi ya ciro kudi yace"ga kudin sadakin ki Maryamu Allah yayi miki albarka ya baki zuri'a tagari tare da "yar uwarki abokinyar zamanki"


Maryam tana kuka ta sanya hannu bibbiyu ta karbi kudin dake hannun mahaifinta
[09/06, 19:26] +234 808 996 5176: [09/06/2019 2:23 PM] ®Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*113*
Da kyar Ya Rabi ta rarrashi Maryam ta bar kukan da takeyi ta sanyata tayi Wanka ta fito mata da wani uban les blue colour yayi mugun yi mata kyau abinka da farar fata ta sata tayi kwalliya dai-dai misali dama Maryam bata da matsalar gashi kullum cikin gyarashi take, dan haka Ya Rabi ta kara gyara matashi sosai ta fito mata da mayafi pink colour hade da yari da sarka fashion munti colour set din Takalmi da jaka iri daya masu bala'in kyau da tsada,kan kace kwabo Maryam tafito Amarya sosai tayi kyau, haka "yan uwan mahaifiyarta suka sanya ta a gaba suna ta bata baki kan ta godewa Allah akan sauyin da yayi mata, dama haka shi yafi alkairi a rayuwarta








Lokacin da Mubina taji labarin abinda ya faru sai da takusa yin dan Karamin hauka, kamar ita ace zatayi kishi da wannan yarinyar tasan tafita komai na rayuwa ilimi kudi wayewa nasaba uwa uba kyau ita a ganinta tafi Maryam komai da komai sabida haka taci alwashin akan sai dai Nasir ya zaba ita ko Maryam din domin bazata taba yin kishi da wannan jahilar ba.








Kwayenta sai zugata sukeyi kan in taje kar ta saurarwa Maryam kuma kar ta sake ta yadda su zauna gida daya da ita domin babu aji.


Hanifa kuwa dariya take tana farin ciki a fili tafito tace"wallahi haukan bazan kike domin ko makawo ne ya sha fa ki ya shafa kishiyarki yasan tafiki kyau, nesa ba kusa ba sabida haka ki daina wani hura hanci"






Mubina ta rika zaginta kamar "yar maguzawa a kan me zatace Maryam tafita ita irin matan nan ne masu San kansu komai sun fi kowa iyawa






A waya ta kira Nasir din tace masa ita Sam bazata zauna gida daya da wata wallahi kuma sai dai ya zaba Ita ko Maryam








Lokacin yana tare da Momynsa kuma duk taji abinda Mubina tace hankalinta ya tashi, tun ba'aje ko ina ba Mubina tafara shigo da tsirfa dama kwata kwata ita tasan Maryam ba zata damu ba
Mubina ce abin ji




Ganin Nasir din bai bata amsa ba ya kashe wayarsa tace"My son wane mataki zaka dauka ne nifa banason rigima kuma ba nasan abinda zai daga maka hankali"
[09/06/2019 2:42 PM] ®Binta Umar Abbale: Tsaki yaja yace"Momy karki damu babu macan da ta isa tasa na sauka daga kan ra'ayina , mutukar Mubina tana San zama dani dole tabi umarnina, Momy bani da ra'ayin raba gida kuma bazan raba ba tare zasu zauna da juna shikkean nagama magana"






"Myson ina ganin ka raba musu gidan kawai zaifi alkairi"




"Momy ki kyaleni Dan Allah wallahi Momy Mubina bata isa tasa ni nayi abinda banyi niyya ba, kawai ki bar maganar,ke dai kawai ki cigaba da min addu'a"






"Toum shikkenan My son Allah ya taya riko ya baka ikon yin adalci a tsakaninsu"






"Ameen Momyna abinda nake so inji kenan"


"Yanzu cikin Estet din zaka zauna ko zaka fita"?








A jiyar zuciya ta sauke gami da cewa "gidan Dady dake Tarauni nan nasa a gyara dazu munyi waya da mai akin za'a mishi fanti ko wane part kowa zai dau daya tunda uku ne shikkenan naraba gaddama babu wacce zata ga "yar uwarta sai taso"








"Kayi dabara Myson"
Momy tafada ta cigaba da cewa "yanzu ni kadai zaka bari a gidan nan ko"




Dariya yayi yace"Momy ko kinaso in zauna nan din"?




Itama dariya tasa tace"A'a babu ruwana ni bana son zama da sirika, Myson ina nan ina maku fatan alkairi




Murmushi kawai yayi yana girgiza kai
Ya mike tsaye gami da cewa "zan shiga inyi Wanka in fito yanzu zan Dan fita a kwai wasu baki da za muyi daga Fatkwat abinda ya hana Abbas halarta daurin auran kenan, gashi na kashe wayoyina dole nasan zasu nemeni"








Momy tace" Yau dai daya su yi maka uziri yau ranar auranka ma sai ka fita My son"




Murmushi yayi yace"Momy kenan"
[11/06, 11:02] +234 808 996 5176: [10/06/2019 6:00 PM] Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*114*


Wanka yayi ya sanya wata shadda mai uban tsada wagambari fara kal ya sanya hula fara takalmi mai gidan dan tsaya baki sai a goganshi na silver mai mugun tsada sosai dressing din yayi mishi kyau kana ganinshi kasan ango ne hannushi rike da farin glass ya fito sai zabga kamshi yake
Momy na zaune tana waya da mutananta tana fada musu yadda al'amarin ya kasance, yace"Momy zan fita ni sai bayan isha'i zan dawo"






Momy ta mike ta biyo bayanshi tace"yanzu yaushe zasu tare iyalin naka"?




"Gobe insha Allahu
Za'ayi komai a gama"


"To Allah ya kaimu lafiya"
Momy tafada cikin farin ciki




Sai da ta ga fitarshi daga gidan sannan ta koma ciki




Ban garansu Mubina kuwa buki suke sosai da sosai babu yadda bata dayi da Nasir ba a kan ta shirya party tanaso ya hallata amma yace mata babu inda zashi dan bashi ya sata ba, haka dai tayi hidimar bikin ita da kawayenta






Wata kawar Ya Rabi ce tazo ta dauki Maryam ta kaita gidanta ta dauko mai mai kunshi gami da gyaran jiki, kunshi yayi kyau sosai baki da ja daki guda ta sata ta turara mata jiki gami da gyaran fata sai da fatar Maryam tayi mulmul sosai Hajiya Aisha ta shirya Maryam sosai sannan ta dauketa a motarta suka nufi wani hadaddan boutique ta dinga jidar mata kananun kaya masu kyau da tsada.






Hajiya Aisha tana dreving ta kalli Maryam dake kusa da ita tace"kinga wannan kananun kayan da na sai mai ki in kinje gidan mijinki su zaki riqa amfani dasu, kar ki tsaya kunya kinji ko tunda kinga kina da kishiya








Kiyi kokari ki kama mijinki a hannu tunda dai Allah ya qaddara wannan yaron Mijikin ne sai ki godewa Allah, yanzu sauran yaki yana gareki
[10/06/2019 8:00 PM] Binta Umar Abbale: Hajiya Aisha ta dage tana koyar da Maryam dabarun zama da miji da yadda a ke kula dashi tace "su mazan wannan zamani da kike ganinsu sai da rarrashi da siyasa, sabida haka sai in zage damtse gurin ganin kin kama mijinki a hannu"






Maryam kuwa sunkuyar da kanta tayi tana jin kunya Hajiya Aisha jin irin abinda take fada ita kam kunya take ji tana ganin bazata iya amfani da wadan nan kananun kayan ba








Sai daf da magariba suka shiga gida,


Ya Rabi taji dadin abinda kawarta kuma aminiyarta tayi mata ganin yadda Diyarta Maryam take walwali ga wani mugun kamshi tana zabgawa duk inda ta gifta










Bayan sallah magariba Ya Rabi tace ai ya kamata su shiga bangaran Momy domin su gaisheta kuma suyi mata godiya da fatan alkairi










Duk su ukun suka shiga gurin Momy ta karbe su cikin mutumci gami da kyautatawa




Ya Rabi tace" Hajiya sai mukaji wannan abin alkairi kuma"






Momy tayi dariya tace"ai haka Allah ya tsara dukkanin abinda Allah ya tsara babu mahalukin da ya isa ya hana, Allah yayi Maryam matar Nasir ce"








"Wannan abu haka yake hajiya, Ubangiji Allah ya sanya alkairi ya basu zaman lafiya Allah ya bashi ikon kyautata adalci a tsakaninsu"




"Ameen ya rabbi nagode sosai"
Momy tafada tana kallonsu cike da murmushi








Ta cigaba da cewa gobe insha Allahu zasu tare a gidanshi dake tarauni kar ku wahalar da kanku komai an tanada a gidan, Maryam kadai muke bukata,insha Allah kayan lefanta ma zataje ta tadda a can"










"Hajiya Allah ya saka da alkairi ubangiji Allah ya kara arzuqi da wata mukan babu Cabinda zamuce daku wallahi"
Aunty tafada tana sunkuyar da kanta








Momy tace "nasan dai Dota bata da matsala yarinyar tana da nutsuwa amma dai sai a kara ja mata kunne sabida ba ita kadai zasu zauna ba a kwai "yar uwarta duk abinda zata gani ta kauda kanta wataran sai labari












"Insha Allahu za'a yi mata fada Hajiya duk da cewar Maryam bata da kwarfinaya da yawa, amma yau da gobe ta wuce wasa
Hajiya Aisha tafada cikin nutsuwa da dattako




Hira suka cigaba da yi cikin fahimta gami da wayewa dake Hajiya Aisha wayayyiyar Mace ce kuma "yar boko shine dalilin da yasa Momy ta ji hankalinta ya kwanta da ita
[11/06, 13:58] +234 808 996 5176: [10/06/2019 10:17 PM] Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*115*
Nan sukayi sallahr isha'i Momy ta sanya mai aikinta Uwani ta hada musu abinci dole babu yadda suka iya suka zauna suna ci suna mamakin karamcin Momy










Karfe takwas na daran rabar Lahadi Maryam ce durkushe gaban mahaifinta tana kuka sosai shi kuma yana mata fada kan ta kula da auranta kuma tayiwa mijinta biyyaya da dukkanin abunda ya umarce ta.








Aunty ma tayi mata addu'a sosai sannan tayi mata nasiha irin tama ta mata yi nayi bari na bari




Yaya Rabi daman ita kullum Cokin yiwa Maryam din nasiha




Dake babu jama'a sosai sabida basu wuce su biyar ba sai Momy tacewa drevar ya dauki babbar mota kawai ta isa




Haka Ya Rabi ta sanya Maryam cikin mota tana gursheken kuka kamar ranta zai fita wai yau ita ce ta auri Wanda bataso Wanda yayi mata muguwar tsana a rayuwarshi
[11/06/2019 7:09 AM] Binta Umar Abbale: Momy ta rungume ta a jikinta tace "kiyi hakuri Dota ki zauna da mijinki lafiya da "yar uwarki nice mahaifiyar Nasir nafi kowa sanin halinshi duk wani abu da kike tunani zai faru babu shi sai alkairi, ni da kaina zan damka masa amanarki shine ki kwantar da hankalinki in kika iya zama da Nasir zaki ji dadinshi sabida yana da saukin kai duk ranar da kika ga ya tashi yana muskilanci to mybe da akwai abinda yake damunshi ke zaki dinga bibibyarshi tunda shi zurfin ciki gareshi, dan Allah Maryam ga amanar Nasir nan Na damkata a hannunki kamar yadda ba bashi taki amanar ki lura da cinsha da shansa domin Sam baya son cin abinci sai na tsaya a kanshi sannan"








Wani irin tausayin Momy ne ya kama Maryam babu abinda Momy zata nema ta Gaza yi mata shi a rayuwarta sabida haka tayi alkawarin ko da Nasiru zai yankata gunduwa gunduwa za ta tsaya ta rike amanar da ta karba






Wani irin gida ne mai bala'in kyau da tsari plate ne mai dauke da part uku sai katowar haraba gurin ajiye motaci ma na mussaman ne can gefe lambu ne an kewaye shi da wasu karafuna sun sha ado gurin gress kafet ne a ko ina na gurin yanayin gidan kamar irin gina ginen kasashan waje ko ina tsaf tsaf Ma'aikatan gidan sai kaiwa suke suna kawowa ko wanne da aikinshi








Nura tayi parking din mota Momy ta fito hannuta rike da Maryam Ya Rabi da sauran jama'a suka fito suna bin gidan da kallo cike da kauyanci sabida kalar faint gidan ma abin kallo ne Momy ta fito da waya tana neman Nasir ta kira ya kai sau uku ba'a daga ba, gashi tana ring sai ta kashe wayar tana tuna in wane part din ne na Maryam tana tsaka da tunani motoci suka fara shigowa gidan dauke da amarya Mubina da ta wagarta, motoci sun kai goma












Kan kace kwabo gurin ya cika da hayaniya dangin Mubina suka dinga fitowa daga mota kamar bazasu kare ba.








Wata yar Momynta ce ta hangi Momy tsaye jingene da mota ,abin ya bata mamaki yanzu yanzu sukaje can gidanta domin su mikamata Mubina a matsayinta uwar miji ba ta nan abin mamaki sai gata anan ko mai ya kawota oho








Har kusa da Momy ta karasa inda Momy take tace"Hajiya Aminatu ashe kina nan, yanzu yanzu mukaje domin mu mika miki amarya kamar yadda al'ada ta gadar ba mu same ki ba"










Cikin nutsuwa da sakin fuska Momy tace"wallahi kuwa ai sabani mukayi domin bamu Dade da fitowa daga gida ba nayi tunanin zan sameku anan, ai babu matsala ga "yar uwar tata ma yanzu zan hadasu in yi musu nasiha"
Momy tafada tana kara damqe hannun Maryam












Hajiya Abu wato yayar Momyn Mubina ta dago kanta cikin mamaki tana kallon Momy kana ta mayar da kallonta kan Maryam wacce sukayi kafada da kafada da Momy cikin zuciyarta tace wato ita ce ta dauko ta ma lallai yarinyar tana da fada a gurin Momy








Sai ta hau yaqen karya tana danne abinda yake zuciyarta kamar gaske tace"Masha Allahu haka yayi, bari mu bude part din Mubina sai mu shiga ciki tunda dai ita ce uwargida"








"To babu matsala"
Momy tafada cikin nutsuwa da dattako










Hajiya Abu ta kauce daga gurin cikin dinbun mamaki dole sai sun zage damtse kan Hajiya Aminatu in ba haka ba burinsu baxai cika ba a kan Nasiru dole ne su ci arzigi su bar arziqi a mazauninsa.
[11/06/2019 7:49 AM] Binta Umar Abbale: Momy taja tsaki abinda ba halinta ba tace"wallahi wasu mutanen suna bani mamaki wai sai mutum yazo ya tadda mutane a guri ya kasa gaidashi sabida girman kai Allah ya kyauta"








Ya Rabi tayi murmushi tace"Hajiya kenan aiko mutane kowa da irinshi sai hakuri"






"Allah ya sawaqe ameen"
Momy tafada tana kara kiran wayar Nasir din a karo na biyu
Gashi tana ring bai daga ba Momy jikinta ya bata babu lafiya amma ta barwa zuciyarta addu'a kawai take masa








Hajiya Abu ta dawo gurin a karo na biyu tace"Hajiya Bisimilah"
Dukkaninsu suka rufa mata baya








Farlo a cike sai hayaniya suke Momy ta nufi wani bedrom dake falon tace"a shigo mata da Mubina








Nan Hajiya Abu ta kamo Hannun Mubina wacce ke cikin kawayenta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login