Showing 45001 words to 48000 words out of 87228 words
Chapter 16 - YARO DA KUDI Complete Hausa Novels by Binta Umar Abbale .txt
ya yini ya kwana bai kula kowa ba har Momyn sa tare da "yan uwanta da suke kara kaina a gidan tun safe yake shiryawa ya fice ,kwata kwata yanzu ya dai na saka kananun kaya kullum cikin doguwar Riga yake"yar saudia kanshi da hula irin ta Larabawa sai ya dawo tamkar wani balarabe,kullum zaka Ganshi a masalaci ,nan yake zama yayiwa dadynshi addu'o yana zubar da hawaye, yau tsawon kwanaki goma shabiyar da rasuwar dady din Momy bata ga ko da murmushin sa ba ko magana zai mata ,bata wuce kalma biyar ko kasa da haka ,kwata-kwata baya yin doguwar magana kullum fuskarshi a murtuke abokanshi sunzo mai ta'aziyya mussaman Abbas da Anwar sunji mutuwar dady sosai kadai Anwar in ya tuno rashin kunyar da yayiwa dady din sai jikinshi yayi sanyi,to ko su kansu in sun zo Nasir din baya sakar musu fuska haka zasu karaci shirmensu su tafi,
Bayan sadakar arba'in yafara aiki a asibitinshi domin shine burin dadynshi,yanzu duk abinda yasan dady yana so kafin rasuwarshi shi yakeyi ta mai da gidan fursuna da gidan marayu gurin zuwa bayayin sati daya batare da yaje ba tsakaninshi da Malam Ya'u kuwa gaisuwa ce itama sama sama baya taba yadda wata doguwar hira ta shiga tsakaninsu shi kuwa Malam Ya'u yayi ta janshi da magana wani sa'in yana jinsa yake shareshi Allah sarki Malam baya gajiya da hidima dashi
[17/05/2019 5:14 PM] Binta U Abble: Tun ranar da dady ya mutu rabon da ya sanya Maryam a idonsa, kwata-kwata baya son su hada hanya sabida yadda ya tsane ta tsanar da yake mata ta yanzu taci uwar ta da, shiyasa yake gudun haduwarsu domin yana ganin zai iya kasheta a yadda yake jin zafinta a zuciyarsa,shi gani yakeyi itace silar mutawar dadynshi
Allah sarki Momy duk tayi sanyi itama zuwa yanzu ta fawwala wa Allah komai su Nafi'u da miftahu kullum suna gurin ta suna de mata kewa duk ranar da basu shiga bangaran nata sai ta aika Uwani mai aikinta ko lafiya, wani lokacin kuma suna makaranta,
Auntt ta dauki zafi da Maryam sosai lokacin da mijinta ya warware mata dukkanin abinda ya faru kafin rasuwar dady ,ta dinga yi mata fada sosai da sosai tunda ga ranar Maryam ta dai na ganin dariyarta
Maryam duk jin ta takeyi a takure kullum tana dakinta tayi kuka har ta gode Allah kullum cikin bawa auntt ta hakuri takeyi,aunty tace indai kika ga na hakura to sai kinje kin bawa uncle dinki hakuri,sannan nima zan yafe miki,
Maryam taci alwashin baza ta taba zuwa tabawa uncle hakuri ba sabida ai bai fita jin radadin mutuwar dady ba ,yadda takejin dady a ranta ,gani takeyi tafishi son sa da kaunarsa ,sabida haka ita a ganinta ita ce ya cancanci a bawa hakuri bashi ba
[06/06, 00:45] +234 808 996 5176: [18/05/2019 10:31 AM] Bint U Abbale 💜: *YARO DA KUDI*
*77*
Yanzu duk wasu abubuwa da yakeyi a da marasa kyau ya rage yi ,sallah cikin jam'i bata wuce shi , duk abinda yakeyi lokaci nayi zai nufi masjid ya rage saka kananun kaya, sosai yana saka kayanmu na hausawa, askin da yake kanshi yasa an gyara masa Sosai yanzu ya dawo cikkaken mutum amma duk da haka akidarshi tananan ,ta turawa yana yawan sauraron wakokinsu ,zuwa club ma ya rage ba sosai yake zuwa ba, duk dai wani abinda yasan dady dinshi yanaso kafin rasuwarshi yana kokari ya yi abin , Son matanshi kuma wannan ma tun daga mutuwar dady din bai kara kwanciya da wata yarinya ba,sabida yanzu duk "yan matan nashi tsoro yake basu yadda kullum suka tunkareshi zasu ga fuskarshi babu Rahama ko ta kwabo ,baby ce kamar mayya kullum sai ta bishi asibiti taje ta isheshi da iyayi ,baya ko sauraronta
Yau ta kasance ranar Sunday ce , yana part dinshi a kwance bacci yakeyi Momy ta shiga tana tashinshi , tashi yayi yana dan ya mutse fuska Momy ta karaso ta zauna bakin gadon tana kallon Dan nata tace"My son wannan baccin naka fa yayi yawa dubi time yanzu daya shaura ,ina ta zuba ido shiru baka shigo ba"
Mika yayi yana kallon agogo yace "Wallahi Mom gajiya ce a jikin nan nawa ,kin san tunda nafara aiki bani da lokacin kai na wallahi , yau din ma dole zan fita a kwai wasu mata da nayiwa aiki zan je na dubasu duk da cewar Dr Sofia na kula min dasu amma zuwan nawa yana da muhimanci"
"Hakane Son ai ladanka na gurin Allah, duk Wanda yazo ka taimakama sa ko da kudi ko babu ,kasan wannan shine burin dadynka dama"
Taci gaba da cewa yanzu ma aikin lada zakayi ,Baban gida ne gashi can ciwonshi ya tashi ,muje ka dubashi
Kallon Momy yayi yana murtuke fuska yace"waye baban gida"?
Cikin Mamaki Mom din tace "banason rainin hankalin ka fa my son Baban gidan kake tambayar wanene"
Ya bata Fuska yana kokarin mikewa tsaye yace"Mom kije ki dubashi ke mana ,nifa duk abinda zai hadani da wa"yancan mutanen bana so"
"A'a kai yafi can can ta kadubashi kaji ko"
"Momy nifa likitan mata ne kawai bazan gane mai ke damunshi ba"
Hararsa Momy tayi tace"kasa ba fada ina fada ko My son"
Tafada ran ta abace
Ganin ranta ya baci yasa yace"Momy kije ganin zanzo Wanka zanyi shikkenan"
Momy ta mike gami da cewa "ok kafito yanzu Dan Allah yana jin jiki"
"Ok Momy"
Yafada yana kokarin shaga toleit
A nitse yayi shirinsa ya fito cikin Wani uban yadi piltex yayi mishi uban kyau sosai, bai sanya hula ba ,sai sumarshi da ya gyara sai daukar ido takeyi ,fatarshi kamar ka taba jini ya fito fara tas ,sai kwantaccan gashi baki sidiq da yabi lafiyar fatartashi,
Kunneshi makale da eirpix ya fito harabar gidan,ganinsu yayi ,sunyi cirko cirko a tsaye
[18/05/2019 10:44 AM] Bint U Abbale 💜: Ranshi ya baci ganin yadda suka zuba masa ido ,harda wancan banzan yarinyar ,a fili ya ja tsaki ya karasa gurin ,gami da mikawa Malam Ya'u hannu suka gaisa, Sama-Sama ya gaida auntt da sauran jama'ar gurin ,Nafi'u ya mika masa hannu su gaisa kamar yadda ya saba yi musu,nan ma bai wani sakarwa yaran fuska,kai tsaye ya kalli Malam Ya'u yace "ina Baban gida yake?"
Can gurin Baban gidan ya nuna masa yace"yana ciki a kwance"wallahi jiya ba muyi bacci ba ,ciwonshi ne ya tashi"
Tabe baki yayi bai ce komai ba ya nufi motarshi ,yana tafiya yace"ku dauko shi ku kawo min asibiti"
Ya bude motarshi kawai ya shiga Malam ya tafi da sauri yaje ya bude masa get din ya fice daga gidan ko kallonsa bai yi ba
Maryam kamar ta saka hannu a gurin tai ta kurma ihu haka takeji cikin zuciyarta wani irin zafi take mata lallai talauci bai yi ba, gata a tsaye ana wulakanta mata iyaye tun lokacin da uncle din ya fito take satar kallonshi ,tana lure da yadda yake wani ya mutse fuska yanawa iyayenta wani banzan kallo, gaskiya baza ta iya jure wannan bakin cikinba, dole zata nemi aiki domin ta sharewa iyayenta hawaye,wata zuciyar tace mata kin manta alkawarin dady akanki ,na auran Abdul gabanta ya fadi ,girgiza kai tayi tace dole muyi yarjejeniya da Abdul domin bazan bari iyayena su kaskanta ba
[06/06, 00:45] +234 808 996 5176: [19/05/2019 11:04 AM] Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*68*
Momy tafito daga part din ta ta gansu tsaye har yanzu tace"A'a Nasir din bai fito bane"?
Aunt tace"ya fito yanzu ya fita yace a kai masa shi can asibitinsa"
Girgiza kai Mom tayi kawai tana mamakin halin danta, yuyawa tayi ta koma ciki ta sanyo hijab gami da daukar key din motarta ta fito ta sanya sucurutiy dake waje su saka mata Baban gida a mota,sannan su Malam Ya'u suka shiga tare da auntt da wata yayarta sai Maryam da su Nafi'u Momy taja motar suka fita daga gidan.
Lokacin da suka isa asibitin Nasir yana teater room ,yana duba mara sa lafiya , kwata -kwata ya manta da wani Baban gida ,tare suka fito da Dr Sofia tana cikin kayan aiki cinyoyinta duk a waje kasancewar siket din dake jikinta karami ne iya cinya (mini) gashi antsaga shi ta baya, kanta yasha karin gashi sosai kafarta sanye da wani takalmi mai mugun tsayi fuskarta manne da tubarau ,kwata kwata bata jin hausa ko daya ,duk abinda sukeyi da turanchi sukeyi Dr Sofia ta Dade tana kaunar Nasir tun lokacin suna karatu , shi a lokacin baya ta tata shiyasa yanzu da yayi mata maganar yanaso tazo tayi aiki a sabitin sa yasa ta'amince da sauri tana burin Allah yasa yafara sonta,shima
Duk da cewar tasamu aiki mai tsoka amma tana ganin aiki da Nasir wani ci gaba ne a rayuwarta
[19/05/2019 2:49 PM] Binta Umar Abbale: Fuskarshi a sake yake zagaya feshen din sa , yana tambayar su yadda suke jin jikinsu,alhmdullhi kowa lafiya ,tare suka fito Dr Sofia sai shisshige masa takeyi shima fuskarsa a sake yake amsa mata
Momy ta kalleshi tace"ka kyauta Nasir tuntuni muna zaune muna jiranka ko kana ciki kayi banza da mutane"
Murumshi yayi kadan ya karaso gurin yace"Mom kiyi hakuri kinji bana son kurafi kince lallai sai ni ne zan dubashi bayan kema likita ce"
Hararsa tayi kawai ta dauke kan ta
Dr Sofia taje ta durkusa tana gaida Momy cikin turanchi Momy ta rungume ta tana amsawa cikin sakin fuska,
Dr Sofia ko kallon su Maryam bata yi balle ta gaida su Malam.
Maryam zuciyarta sai zafi take mata
Nan take Nasir yasa a ka dora Baban gida a wani gado yace a kaishi wani daki gashinan zuwa
Malam Ya'u ya mike da sauri zai bisu Nasir ya buga masa tsawa cikin izgili yace"bama bukatarka a gurin ,ka tsaya a matsayin ka"
[06/06, 00:47] +234 808 996 5176: [20/05/2019 10:45 AM] Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*79*
Maryam ta yi masa wani banza kallo a nutse ta ce"in kun shiga ku to ku hana Allah ikonshi ,domin duk abinda kake takama kana dashi na ilimi ko kudi ko wani abin daban Allah ne ya baka ,kuma zai iya bawa kowa ,sabida haka duk inda mutum yake yana da daraja da baiwarsa , ba muce lallai sai ka duba Baban gida ba ancle a kwai lokitoci a duniya masu tsoran Allah gami da yin abu dominshi, ka sani ta lauci ba hauka ba ne da zaga rika zagar min iyaye a gabana ,in kai bakasan darajar naka ba ni Maryam nasan darajar iyayena domin sune kashin bayan samar dani"
Ta karashe maganar tana wani huci! Dagani kasan a cikin mugun bacin rai take.
[20/05/2019 1:37 PM] Binta Umar Abbale: Aunt ta tsinka mata mari ,rai a bace tace "yaushe kika zama haka, uncle din kikewa rashin kunya, Na lura dama ko gai dashi bakiyi ba , to maza ki bashi hakuri ko yanzu in miki dukan tsiya a gurin,
Momy taji dadin abinda Maryam tayiwa Nasir din domin ita ma ta gaji da rashin mutumcin da yake yi wallahi,dan haka aunt take wa fada a kan me zata mari Maryam din ai gaskiya tafada.
Maryam kuwa kuka takeyi wurjanjan kuma taki cewa komai ballantana tabawa taje ta bawa uncle din hakuri,Wanda tuni ya wuce cikin dakin da Baban gida yake kwance,yana mamaki wai yau shi yarinyar take mayarwa da magana sabida wuyanta ya isa yanka tabbas taci darajar dady din shi ,amma duk da haka sai ya kaskantar da ita,
A yanzu dai bashi da lokacin kulata balle ya mayar mata da martani
To ba wani abin ne yake damun Baban gida ba illah ciwon suga ga Jininsa ya hau sosai,nan yayi masa taimakon gaggawa Dr Sofia na gefanshi tana saka masa ruwa , kan kace kwabo bacci ya dauki Baban gida , Nasir ya kunna masa Ac dai-dai misali ,sannan suka fito tare da Dr Sofia tana binshi sai kace jela.
Duk suna zaune a inda ya barsu ,ya kalli aunt yana ya mutse fuska kamar bayaso yace"ya samu bacci yanzu alhmdullhi jiki yayi sauki sai dai zai kwanta anan tsowan sati domin samun kulawa ,amma a rika kiyayewa da cimarsa zan dorashi kan magani"
"Alhmdullahi Uncle Allah ya saka da alkairi kaji"
Aunt tafada tana kokarin mayar da hawayen da yakeso ya zubo mata
Ta cigaba da cewa "kayi hakuri kaji Nasir Wacan shashashar tana yi maka rashin kunya"
Bai ce komai ba ya kalli Momy tace "ni zan wuce Momy zan je in fidda kudi kin san mun fara business da aboki na Abbas ko zamu bude shakatawa a can bayan gari ,bayan haka kuma zan fitar da kudi za'ayo min odar motoci zan fara gwada wa in gani"
Cikin farin ciki Momy tace"Allah ya taimaka my son Allah yayi jagora"
Malam Ya'u dake tsaye hannunshi nannade a kirjinshi ,tun lokacin da Nasir yayi mishi tsawa jikinshi yayi sanyi sosai kwata-kwata bai ga laifin "yarshi ba sabida yasan kokarinta gurin ganin ta kare musu mutuchi cikin zuciyarsa yake nai mawarwa kanshi mafita dole ta fita ya nemi na kanshi ,domin ya tsaya da kakafunshi tunda a kwai sauran karfi a tare dashi ba zai yuhu ace ya zubawa Yaro kamar Nasir shi zai dinga da wainiya dashi da iyalinshi, in Alh Hussen yayi wannan daban da Nasir,yasan a kwai kudi masu yawa da har su kare rayuwarsu a gidan ,Wanda za'a iya dawainiya dasu ,to ma lokaci yayi da zai yi amfani da damarshi domin tsira da mutumci
Ya kalli Nasir din yana danne ,damuwar da take damunshi duk a kokarinshi na kula da amanar da akabar mishi,yace"Nasiru Allah yayi maka jagora Allah yayi riqo da hannuwanka yasa kafara wannan Sana'a a'sa"
Ciki ciki Nasir ya amsa ya Sakai ya fice daga Ofis din batare da ya amsa wa aunt maganar da take masa ba
Momy tace"sai hakuri nima in halin nashi ya motsa haka yake yimin in ta yi mishi magana yana share ni"
[06/06, 00:48] +234 808 996 5176: [20/05/2019 8:57 PM] Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*80*
Wata yayar aunty mai suna Rabi tace"ai babu komai Hajiya wallahi ,ai yaron ma yana kokari mu dai babu abinda zamuce sai dai muce Allah ya saka muku da alkairi ubangiji Allah ya jikan Alhji Huseen domin yayi mana abinda bazamu taba matan tawa dashi ba"
Momy tayi murmushi tace "babu komai Rabi ai duk yiwa kai ne , zamu cigaba daga inda dady ya tsaya ,domin mu cika masa burinsa,ni dai fatana daku dan Allah ku riqa hakuri kan dukkanin abinda zai biyo baya ta gefan Nasir ,wallahi ni kai na narasa in da ya sa gaba,kullum cikin bacin rai yake, duk ya canja hali"
Tausayin ta ne ya kama Ya'u yace"Hajiya ki kwantar da hankalin ki in sha Allahu komai zai warware ai mun gode Allah ma , yanzu Nasir ta samu ba kamar da ba yana sallah cikin jam'i wannan shine mataki na farkon shiriya ,duk wasu abubuwa da yakeyi zai dai nayi in sha Allahu"
"To masha Allah Malam Godiya nake da wannan addu'a taka"
Momy tafada Tana jin dadin yadda Malam Ya'u yake kula da Nasir din kuma baya ,yadda ya sa bacin ran abinda Nasir din yake masa
Nasir yana fita ,suka ci karo da Abdul latif yana parking din motarsa a gurin da'aka tanada domin ajiye ta
Nasir ya dakata har Abdul din ya fito bayan ya kulle motar ya karaso gurin Nasir din Fuskarshi babu yabo babu fallasa ,ya bashi hannu kamar yadda suka saba,Nasir tace"ya akayi ne, ina ka shiga kwana biyu"
Abdul yace"ka manta nace da kai zanje Legos ko kasan na sami aiki acan wani babban kamfani ne suka dauke ni aiki wallahi, naje munyi intervio dasu kwanana biyar a can "
"Ok na manta wallahi amma na taya ka murna , sosai yaushe zaka tafi"
"Sai Monday ta sama amma ranar Sunday zan tafi da safe"
Tabe baki Nasir yayi kadan yace"yaya salary din ka ,yana da kyau in ce ko"
Abdul yace " alhamdullhi babu laifi , dubu Dari da sittin ne"
Dariya Nasir yayi yana nuna Abdul da hannu cikin tsabar iskanci da ya saba yi masa yace" ok kana nufin da wannan zaka iya rike mace ,ka tsaya sai wata za'a biya ka kudin da basu kai sun kawo ba ,ai da wannan aiki da ka hakura ,ka nema a nan kawai ,domin zai fi maka"
Abdul ya hade fuska yace"banason wulakanci da rainin hankali Malam ni rayuwata ban takura ta ba ina yin komai a tsari da sannu sannu komai mai zuwa ne
[20/05/2019 9:16 PM] Binta Umar Abbale: Nasir ya zakuda kafada alamun bai damu ba yace"ok tunda haka kake ganin zai fi maka shikkenan ai"
Kokarin bude motarsa yakeyi Abdul yace "ina zaka yanzu ,daga can gidanku nake naje gurin mutuniyar , sai naji mummunan labari wai Baban gida babu lafiya"
"Eh Hakane"
Nasir yafada bayan ya shiga motarshi yana kokarin kunna motar ya kalli Abdul latif fuskarshi ta rikide tamkar zaki a cikin dawa yana Neman abinci yace" wai kai har yanzu kana kan bakanka na auran waccan yarinyar"?
"Yes of course" Abdul din yafada babu alamun wasa a tattare dashi
Nasir ya girgiza kai yana cije lebansa na kasa minti biyu ,sai ya dago kai yana sakin wani murmushi daga ni kasan na mugunta ne , yace "banaso in fada maka abinda zai tayar maka da hankali ,a kan yarinyar wallahi tun wuri ina baka shawarar ka janye maganar auranta shine zai fi maka alkairi"
Cikin namaki Abdul ya zubawa Nasir ido ya gyara tsayuwarsa sosai yace"wai kai don Allah yau dai ka fada min dalilin da yasa kake a dawa da wannan Abu,kar ka manta da cewar dady kafin ya rasu ya bar wasiyyar tabbatuwar auran"
Nasir ya girgiza kai yana jin wani mugun bakin ciki ,a zuciyarsa har yanzu ,yana ganin Hoton Anwar da Yarinyar cikin Mota
Abdul yace"kai nake sauraro kayi shiru ,yarinyar nan dai na tabbata baza tayi zina ba shine dai karshen wanda zai sa inji kyamar auranta,bayan haka kuwa duk abinda tayi mai sauki ne"
Nasir bakinshi na daci kwata-kwata ba yaji tes din komai sabida bacin rai ya tashi motarshi batare da ya kara cewa Abdul komai ba ,ya fige mota tamkar zai banke Abdul din
Cikin zafin nama Abdul ya kauce , yana kallonsa cikin mamaki abinda yayi sai kace wani mahaukaci ,sai da yaga ficeawarsa sannan ya sauke ajiyar zuciya shi ma ya bar gurin
[06/06, 01:42] +234 808 996 5176: [21/05/2019 9:20 AM] Binta Umar Abbale: [21/05/2019 8:43 AM] Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*81*
Abdul sun jima da