Showing 63001 words to 66000 words out of 95576 words

Chapter 22 - YAR LESBIAN COMPLETE BY Nadiya Muhammad Ahmad.doc

lissafa. Babu wani Nan kedai fadi gaskiya. Uwarka ke karya, dogon banxa dama nabarka da kafurar yarinyar Nan itace daidai da kai Wlh.tsaki yazeed yaja yatashi yabar parlon. kinganshi fa yanda yake tafiya kamar wani doki. Mamah Wannan Kaya haka Halan innah Nafisa ta hadaki dasu. Eh Wlh Fatima ai Sirikan Hafsat badai mutumci ba, Allah yakara Arziki. Amn mamy tace tashiga daukan kayan tana Aje kowanne inda yadace.

Akwana Atashi babu wuya yau yarage Saura kawana biyu Su feenah Su kammala Karatu. Xaune Suke Su Uku Suna fira. Wai dan Allah ku kalli kaman yau muka fara karatun nan gashi haryazo karshe Kausar ke magana. Leemah ce tace kedai bari Shiyasa Akeson Mutum ya fifita Lahirarsa Akan duniya lokacinmu muketa cinyewa bamu Sani ba watarana Saidai ace Anwayi gari bamu Acikin duniyar da muka dauketa da fadi. Allah yasa muyi kyakykyawan karshe feenah ta fada.Atare Suka Amsa da Amin. besty kindai Haddace Abinda Zaki fadi gobe ko? My Leemah Allah dai yakaimu Wannan walima,Naga kinfi Kowa Xumudi. dariya Leemah tayi wayace miki Nafi kowa Zumudi ga gwana Agefe Kausar itafa tace Xata fara bude taro da addu'a. dariya Sukayi gaba daya wainikam Malan yasamu mace dayan dayace Xatayi tare damu? Wama yasani tunda kikaga be kara magana ba yasamu. Hakane kausar ta fada,Nifa duk ma nakosa Muyi mubar makarantar nan. Me kikeci ta baka Nazuba Leemah ta fada! tarewa ne dai baza'ayiba saimunsha Shagalin biki. Dariya Kausar tayi toh wacece ni daxance Xan tare banga Yanda Halimcy na Xata Chashe Ranar Aurena ba? Kimace mana kinsan baze yuwubane. Kudai Kamar Tom and jerry kuke wlh Feenah ta fada irin Sun isheta din Nan. Murmushi Leemat tayi Ni Wlh besty harkin tunamun wasu tom nd Jerry munkusa komawa Naga yanda game din Zaizo karshe, Ai kema kinsansu ko kausar? Ahhhh Sosai ma Ai ina mamkin yanda Akai feenah bata sansu ba.tashi feenah tayi kanku Akeji,idan kunga dama kushirya ma Gobe idan baku ga dama ba kuyita Xama kada ku kwanta. dariya Sukai Suka cigaba da firarsu inda Suka tsaya. yazeed ne ya Shigo parlon nasu yana Kiran Mamy. Ohni yazeed wannan kira haka kamar kabani Ajiya. Inno dake kusa tace Kamar dai dan Mafarauta,ni nakasa gane maka tsaka Kwana biyun Nan duk sai wani farin Ciki kake. Hararta Yazeed yayi babu Ruwanki da matsalata malama. Umm Nasan matsalarka yaro kaidai Acigaba Ahaka.Cikin Rashin fahimta yazeed yace eh naji Sa ido kawai. Mamy Saudiyya nakeson Xuwa Cikin Satin Nan. Ah haba my Son wlh daka kyauta. da gaske mamy Xanje nayi Addu'a namuku Kuma. Allah yabaka iko Dan Albarka.Amn yazeed yafada yana maijin dadi.tabe baki inno tayi kariga kasamu Abinda kakeso yaro yanxu Kawai kaje kayi addu'a Allah ya rabaka da bakin Halinka.kallonta yazeed yayi tsofa na dawainiya dake Wlh. Kuma hakan besa nakasa gane matsalar kaba Shegen yaro. Mamy ce tamai Alama dayayi Shiru, Kasan gobe Zaka kaimu Abuja gaba dayan Mu ko? Mamy Abuja wajen wa kuma? Su Leemah Xasuyi walima gobe. Mamy bayan Celebrity dasukai na gama Skul Satin daya wuce? Nifa dadina dakai kenan, tunda nafada maka Zaka kaimu kacemun Toh. Gudun kada inno ta Samu nayi yace Allah yakaimu badan yaso ba Xaije Abuja wai wata walima. Su mumy ma gaba dayansu Shirin Xuwa Walima Suke Su Twins sai doke Suke musamman dasukaji yaya Nazir yace musu wajen Aunty feenah Xasu. Haka gidan Su Yusuf suma Sun shirya Shirin walimar kasancewa yanzu Akwai kara sabida Kausar. Itamadai Hajiyar Kausar Shiri take ba'abarta Abaya ba.

=ؖ?=؋?=؋?=؋?=ؖ?=؋?=؋?=ؖ?
YAR LESBIAN CE
=ؖ?=؋?=؋?=ؖ?=؋?=؋?=؋?=ؖ?
By
Nadeeya muhd Ahmad
(=ؖ?Nadseer=؋?)

dedicated to
Xaynab Ummu mahbub

*Nadiya kina burgeni,Nadiya Insonki da Kawa,Nadiya Allah yamiki Albarka yakara basira,Nadiya....Nadiya.... Ina matukar Jin dadin Sakoninku Na Alkairi my Lovers.Nima kuna Burgeni insonku Addu'an Alkairin Allah ya Amsa Thanks Alot Sisters and brothers*d'd'

Page....42/43

duk girma da fadi irin na makarantar tasu feenah be Hana dandazon Matan Arewa Cikata ba. Matane Kota Ina daker kake Samun wajen dazaka Ratsa ka Shiga,Kasancewar taron gaba daya na matane,Inda daluban Xasu Shirya TAMSILIYYA(Drama) domin Su fadakar Akan Zaman takewar Matan Aure Agidan mazanjensu da irin kishin dasuke nunawa na Hauka kan kishiya. Kutsawa narinka yi domin Nasamu wajen daya dace na dauko muku yanda taron Zai kasance, Kai da dama ma live video Naso nai muku join Amma yawan mutane Inaaaa. Gaba gaba Nayi ganin tawarga Su mamy yasa Naja burki Anan kusa da inno na raba na Zauna,juyowa tayi tamun wani irin kallo ganin haka nai Saurin cewa Inno banida Alaka da Mufeeda fa. Murmushi tamun tace yanzu naji batu matso kusa domin kitayini fira Kafin Afara gudanar da jawabi. Matsawa Nayi kusa nace Inno banga yazeed ba ko lafiya.Tabe baki Tayi Yazo kin ganshi chan. daga kai nayi na hangoshi tsakiyar Nazir da yusuf fuskar nan a daure daga gani Hayaniyar da Ake ita ta takura Shi. Bangare guda kuma manyan malamai ne Na Sunnah wanda Ake jidasu afadin najeria, irinsu "Shek fantami, kabir gombe, Asadussunah da Sauran Su. Ayya inno yanzu kenan....Kafin nakasara ta dagamun Hannu Alamar ya isheta, Nima Shan kamshi Xan fara irin Nasu tsaka da feenah,Kafin Sudawo Nagama koya domin Abun da Sukemun ya isheni.ganin haka Nayi gum da ba kina Ina jiran Naga yanda Xa'a fara Abun. daga Kai nayi jin Ana kabbara Su feenah na hango jere kusan Su8 farin material dinkin doguwar Riga ne Ajikinsu, yayin da Suka daura dogon farin hijaf har kasa Masha Allah. Sun hasku kuwa. Tun kafin Su Xauna Naga feenah ta dafe kanta,Leemah ta tambaya besty lfy ko kanki ke ciwo? Wlh Leemah mutanen nan Sunmin yawa Anya Xan'iya tashi jifa mutane ga Hayaniya. Sorry besty Ki daure nan da 1h mun gama Insha Allah. Kada Kai feenah tayi Alamar toh. Cikin kan kanin lokaci wani malami yazo yafara bude taron da Addu'a. ya yaba kwarai da Hazakar Su feenah bangarin Boko,da islam Acewarshi be taba ganin babbar makaranta da'aka ware bangaren islam ba Sai wannan, Nan dai yagama Sanar da Abin da zeyi daga bisani ya Ambaci Leemah Amatsayin wacce Xata fara fadakarwa. fitowa Leemah tayi Anatse ta karasa tsakiyar wajen ta karbi Speaker. Nazeer na hango Sai wani Murmushi yake Ko mai yake fadi Aranshi Oho. da Sallam ta fara bayan Jama'ar wajen Sun Amsa tacigaba. (UMIRNA AN NAKIFA AMAMAKUM) " An umarceni dan na tsaya Agabanku, domin Nayi muku wani Dan jan hankali/wata yar Nasiha da Abunda naga matan Aure Sun fara mancewa ko kuma Sunakin Aikata Maganar Allah S W A da Abinda ya Aiko mazonsa Annabi Muhammad S A W dashi. Ayanzu mafi Akasirin matan Aure Sune masu Aikata babban laifi,Toh bari nafada miki yake yar'uwata kada Ki bari Azugaki kirinka dagawa ki tsaya Amatsayin da Allah ya Ajiyeki,ki Zauna dakin ki kada kifiye yawan yawo Kamar yadda Allah S.W.A. Yake Cewa (wakarna fi biyuti kunnah wala tabarrajina tabarrijal jahiliyatal Ula) MA'ANA kuzauna Adakinku kada kufiye yawan yawo irin Na Matan jahiliyya na farko. Ai wannan Abunda Allah yai mana gata yayi mana Kuma darajarmu Allah ya daukaka.domin Alokacin Jahiliyya mata ke biyan Sadaki,matan da da muke yawo tsirara wanda da birnesu Ake da Ransu,Alokacin Jahiliyya Mata Su Suke nemoma mijinsu Abinci,Alokacin Na miji yanada ikon ya Auri mace dari ko dubu,Alokacin jahiliyya mace Saita Sadu dana miji20 ko30 koma fiye da haka, har saita haihu Sannan Asamo wacce tasan kama da Sifa Sannan Atara Samarin nata Sannan adauko jaririn yana Hannu Anatafe Ana kallon Fuskar Samarin nata duk wanda yayi kama da Wannan yaron toh Shine uban Dan dashi Za'a durama Uwar yaron Aure! (MA'AZALLAH) "wannan kazanta har ina" Amma da Zuwan musulumci ya Ruguza yin hakan,yace mace yar'gata ce Kai Namiji kai Zaka nemo mata Abinci,Sutura,ilimi,lafiya da makamantansu.kuma Akace Shi Namijin Shine Zai bata Sadaki kuma Akace ta lullube jikinta ba'ayarda ta nuna tsiraicinta ba. Toh Mata kuna nufin Allah bai iyaba,Mazon Allah bai iyaba kuma musulunci bai iyaba??? Sai Ayanzu ne Wasu tsinanu, Fasikai, fajirai Zasu fitoh da mata suce Wai A inganta Rayuwarsu,Ai wannan Raini ne da wulakanci,Sai Ayanzu wasu Zasuce wai Asama ma mace kaykykyawar Rayuwa, wai duk Namiji ya Auri mace daya Kawai ta isa!=?!? Toh Akwai Rayuwar data fi ta Allah da manzon Sa ne??? ko kuwa Akwai Rayuwar datafi ta musulumci? Abun bakin ciki Mu mata Shagalar tamu tayi yawa muda Akace kada mu bayyanar da adonmu ga mazajen daba namuba,Amma yanzu mata dazarar Zasuje unguwa,Zaka ga Sun dauki jan baki,jagira,hoda,eyeshadow, da dinki na Rashin mutumci mai matse jiki, Waishi Show me! ko follow me da mayafinta Akafada. ( wannan Sai a Instagram Zakaga mata da Shigar Nan kaya ya matsesu Ana juyi Ana daukar Video domin mutane Sugani Asan Ita mai kyauce) Toh Mazon Allah S A W yace( Nau'i biyu daga yan huta banga kamarsu ba! Wasu mutane ne Atare dasu Akwai bulalai kamar kunnuwan Shanu Suna dukan mutane da ita.da kuma wadansu mata da tufafinsu Amma matsairaita ne karkatattu idan Suna tafiya masu karkatar da hankulan mutane izuwa garesu,kawunansu kamar tozon Rakumi bazasu Shiga Aljannah ba,bama Zasuji kamshinta ba kuma kamshinta Ansamu ne daga tafiyar kaza Zuwa kaza.) Bama Wannan ne yafi bani haushi ba kamar yanda mata yanzu Suke illata mazajen Su,wasu Su kashe su,wasu Su konasu wai duk Dan Sabida basa Son kishiya! Toh wallahi tallahi idan muka yarda da Wannan Muna Aikata Son Ranmu muna Cikin bala'i da Musiba Mai girma. Dan haka manzon Allah S A W yace ma Sahabbanshi (kaifa bikum iza daga'imatikum Wa fasaka Shababikum) "yaya Zaku kasance idan matanku Suka rinka dagawa da Shishshigi, Samarinku Suka Zama fasikai?" Sai Sahabbai Sukace (Aya kuna Zalika ya Rasulullah?) "Shin haka Zai kasance ya Ma'Aikin Allah?" (Sai manzo yace musu fiye da haka ma Zai kasance)
Yau gashi muna gani maganar Mazon Allah S A W ta tabbata. domin gashi muna gani matanmu Na yanzu Saidai muce INNALILLAH WAINNAH ILAIHIR RAJI'UN! domin mace ce Zaka ganta ta tawo mayafi Akafada tasaka Chewingom Abaki tana tafiya tanaci Har Wani karairaya Zakaga tanayi tum barin Idan tazo majilisar maza har wani fari da ido Zakaga tanayi Wa'iyazubillah=?-? kuma matar Aurece Zakaga taje gidan biki tacire dan kwali tana tikar Rawa Ita da yarta Ai wannan babbar musibace. Uwa'Uba yanzu mafi yawan Akasirin mata dabi'ar lesbian ita Suka maida Kamar Ruwan Sha! Leemah na kaiwa Nan kuka ya kwace mata, Saida tadanyi mai isarta tacigaba, da Matan kasashen waje Su Akasani da Wannan dabi'ar Amma yanz matanmu Na Hausawa Su Suke Aikata hakan musamman idan kahau Twitter Anan Suke Xuba video's dinsu idan Ka gani kai ka Rantse kace ba yaran Hausawa bane Innalillah Saidai kawai muce Allah ya gyara ya Shiryar da Xukatanmu. Daga Haka ta Ajiye Speaker ta bar wajen da dan Hawayenta. Malamar dake gabatarwa ta taso Masha Allah tubarakallah Malama Halimatu Ahmad mungode Allah yasaka da Alkairi. mata iyayenmu da yayyenmu da fatam kun gane Cewa Zafin kishi Hauka ne,domin ada mata bamuda Wani yanci Saida musulunci ya kawo mana, toh Kuma Dan Allah ya hallata ma maza Auren mace fiye da daya,muce bamu yarda ba Anya Munma kanmu adalci Anan???? Allah ya kyauta. Malamarmu ta gaba itace Kausar Hafiz malama bisimillah... domin nasan Kema bazaki Rasa Abin fadi ba.

Tasowa Kausar tayi daga inda take da'alama itama kukan tayi game da jawabin Leemah.Sallama tayi irinta addinin musulunci, gaba daya jama'ar wajen Suka Amsa. Tafara dacewa Abinda Malama Halimat Ahmad ta fada tafadi gaskiya,kuma ta kara Zaburar damu.dama ba wani Abu bane yake Rudarmu Mu Mata illah Rashin hakuri da dangana, da kwadayi dakuma Son kyalekyale na duniya. Shi yake Shagalatar damu harmu manta Xamu koma ga Ubangijimu. Wlh malama dazaki fita kiga Yanda mata Suke A hanya ke kya Rantse kice ko babu Sauran mace Acikin gida. Ayanzu Saiki Kasa gane wacece matar Auren wacece Mara Auren,domin Zaka gansu Sunci ado kuma babu lullubi Atare dasu.Toh mai tsira da Aminci Allah Su kara tabbata Agareshi yace!( mace tanada Sutura guda biyu.mijinta dakuma kabarinta) Amma Saika ga Uwa A zamanin nan tasaka yarta Agaba tana mata huduba wai don mijinta ya hanata Xuwa biki, Suna, ko Zuwa gida wankan jego=?$?toh wannan Hadisin Saiya tunamun da Wani babban Sahabin Manzon Allah S.A.W. yakasance Shi dakanshi yake ma yarshi Aure ya kaita gidanta,yayi Sallama da mijin nata yace ga yata Nan nakawo Maka Amana,kekuma idan kika fitoh kabarinki Za'a kaiki.Kuma tashiga ba zaka taba ganin tafito ba. Amma wannan Matan namu na Xamani dazaran Ka gansu Ahanya,kai Amarya Zasu,ko party,Ko Hinin Suna, ko kamun Ango.Wlh most especially batare da izinin mazajensu Suke fitowa ba.Toh yar'uwa mai tsira da Amincin Allah yace(duk mancen data Saba ma mijinta tsinuwar Allah da Mala'iku data mutane gaba daya ta tabbata Agareta) yar'uwa kodan wannan Abinda Allah ya fada ai kya Rage Wani Abu daga Cikin Halinki. MANZO YACE KUMA (Duk matar data mutu mijinta yana Mai yarda da ita Allah S.W.A Zai sakata Agidan Aljannah) Sannan manzo yana maiyimana gargadi Akan Kada mufita batare da izinin mazajenmu ba. ga dai Abinda yace (dukkan matar data fita daga gidan Mijinta batare da izininsa ba ta kasance tana Cikin fishin Allah S.W.A. har saita dawo ta nemi daya yafe Mata kuma ya yafe matan) Wlh wani Abu dayake Kara cimun tuwo A kwarya Shine,Saikaga maza Sun fita da dadi ba dadi Suna nema ma iyalansu Abinda Xasu ci,Kosu daura,ko suba yaransu,Amma su Rasa wanda Xasu ha'inta Sai mijin nasu,idan basu ha'inceshi ta wajen cefane ba Xasu ha'inceshi ta Wajen fita Un'guwa. Abin bakin Ciki Ayanzu Uwa Ita ke kashema yarta Aure,toh Dan Allah menene Rivar,Saikiga Andawo gida Anzauna Anajiran bazawari yazo mata,daga Anji Shiri na lokaci Saikiji anfara Xuwa Wajen boka, Wlh Malan yatace tunda Aurenta ya mutu har yanzu bata Samu Wani Mijin ba, inaganin tsohon mijinta Shi yayimata Asiri. Shikuma boka Dan iska makiyin Allah saikiga ya karkace yasata Ahanyar karyace karyace Kawai dan ya karbi Abin hanunta. Wai yaushe mata Zamuyi Hankali ne?kiduba mazanjenmu Xasu kawo mana kayan Abinci Kamar su Shinkafa,masara,wake da dai Sauran Su, Amma Saikiga mace ta iba tana boyewa wai dan kada mamarta tazo tarasa Abinda daxata bata wannan ai Sata ne Wlh.domin laifi kikaima Allah Sa'anan shi mijin Naki. Allah ya sawwake yasa mufi karfin Zukatanmu. daga haka kausar takoma ta Xauna. Wata daga Cikin daluban ta taso tayi gdy daga bisani tace Malama Khadija bisimillah.

Kallon feenah Kausar tayi Ashe Malan khady yasamu dayar? toh nimadai sai yanzu nagani Kausar.tafff bari Naji me yabata ta fada. Sallama itama khady tayima jama'ar wajen kamar Yanda taga Saura Sunyi.gaba daya taron wajen Aka Amsa.ta daura da Cewa Ni bansanma Mai Xanfada ba domin duk wa'inan malaman sunriga Sungama kwance mana Xani Akasuwa. Kallom Kausar Leemah tayi sukayi dariya,Lallai Malan Abinda yabata ta yayi daidai da yanayinta ne. Cigaba tayi Ku'inaganin bakusan Halin mazan Nan bane bawasu wanda Xa'a dauka Ayita tarairayarsu bane, da Zarar kinama Namiji ladabi da biyayya Abinda ma Xaifara Shiga tsakaninku Raini ne da wulakanci Harma yayi nufin yayi miki kishiya.kuma dakuke ta Wani fadin kar mufita kar mufita mu Zauna Adakin mazajenmu,Sukuma Mazan dasuke yawonsu Cikin gari fa? Har kuke kawo Hadisi da Aya wannan hadisan da Ayayoyin Ai bada matan wannan Xamanin Ake ba da matan Sahabbai ko Annabawa Ake. Kuma idan mace bata fita ta Neme yancinta ba yaushe Xata nema? Kullum tana daka Akulle kamar wata wardrobe waye Xai Santa? Kuduba Matan Sauran kasashe wa'inda kansu ya waye,inda Zakiga mace a Shugaban kasa ko Governor,kuma kuduba matanmu na wannan kasar Suma nan Zakiga mace a minister ko C M N,Ko Kuma Shugabar wata ma"aikatar. Amma kwa hada matan nan daku Wanda kanku yake Aduhu haryanzu baku waye ba?Ku bakusan duniya ta chanza ba kuna yawo cikin lullubi kamar wasu Munafukai=?$?wlh nidin nan dakuke gani n.a. tsakanina da namiji babu wata Amana domin shi ba dan goyo bane ba,ke matukar ma Naga Zaimun wata gargada sainace Ya Sakeni nikuma na bidi Wasu ga mazan Nan suna Yawo Kamar janfer a jos. Ni iya Abinda zan fada Kenan. Mai gabatarwan ce ta Amsa toh Allah ya kyauta Zan'Iya cewa kawai Anan. Malama Feenah Umar Faruk bisimillah. Yazeed da kanshi ke durkushe besan Sanda ya dago yana kallon yanayin yanda take tafiya Kamar batason taka Kasa.Subhanallah 1yr danayi kadai banga yarinyar Nan ba kalli yanda takara girma da Kyau dan tsaki yaja inama Ruwana da ita. Cikin natsuwa ta karasa Wajen..Sallama tayi Cikin Xaxxakar Muryarta Wanda ta dira Cikin kunnan yazeed! " She is So Cute nd She have a Nice Voice" Cikin Ranshi yayi maganar Amma Sai yaji Yusuf yace Allah ko? Kenan Afili Nayi maganar. Kallon Yusuf yayi yace yes kallitafa nadade inason wakokinta wayarshi ya Nuna mai Wata mace.dariya Abun yaba Yusuf Sosai yace Kawai ka Aureta. Tsaki Yazeed yaja yabar maganar. Magana feenah tafara. Haba malama Khadija Koda yake bakibani mamaki ba domin Kowa yasan Halinki da tarbiyarki. Wainan Abun da yan'uwana suka fada aiba kwance Xani a kasuwa bane, Gyara kayanka Ai baya Xama Sauke mu Raba.dakike cewa bamu San halin mazan nan ba toh kinsan duk Namijin dayake sonka baxai wulakantaka ba.domin Manzo S.A. W. Yace (duk Wanda baya kishin matarsa bazai Shiga Aljannah ba) kuma dakike maganar kishiya ai Allah bai Hana mutum ya Auri mace fiye da daya ba. Saurara kiji Abinda Allah S.W.A. ya fada Cikin Al'Qur'an *FAMKIHU MAZADA LAKUM MINAN NISA'I

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login