Showing 84001 words to 87000 words out of 95576 words

Chapter 29 - YAR LESBIAN COMPLETE BY Nadiya Muhammad Ahmad.doc

Wani banxan kallo Kausar tama mufeeda kafin ta juya kan khady. Ke khady waye yace kirufa mishi Asiri Anan? Idan kinsan Xaki iya fadama wannan kece Silar jefani Cikin harkan lesbian tayaya Xaki kasa fadama mijin daya Aureni? duk katuwar macen da bata kira yusuf tafada mishi cewa ni YAR LESBIAN CE ba batacika Cikakkiyar yar'iska ba Wlh. Kallonta Mufeeda tayi ba take Nake ba dan ke Yusuf yariga ya Aura mara tarbiyya. Amma duk Shegiyar yarinyar dake Shirin Auren mun Saurayi Tama Shirya ma kanta cewa yariga yasan itadin YAR LESBIAN CE. tashi Leemah tayi ta dawo kusa da Mufeeda Ada Ina miki kallon yar'bariki Mara kamun kai yar tasha Ashe Abun yawuce gaban haka harda Hauka kika tarama kanki. Idan baki kira yazeed yazo kinfada mishi cewa duk yan lesbian ne muba bakicika Cikakkiyar tababba ba. Idan kin fada mishi ya Aureki ya Xauna dake ke kamilallaiya, juyawa tayi wajen khady Uban waye yace kikasa fadama Su yusuf gaskiyan Abinda ya kawoki? Kema kiyi gaggawan kiransu ki fada musu dalilin Xuwanku nan kunxone domin kusaka musu tsanarmu Cikin ransu, Kuga miye Xai faru. Kwafaaa kawai Mufeeda tayi tafita fuuuuu Wlh Xakusan koni wacece. da karfi Leemah ta bude murya Sanin koke wacece na Nawa Kuma birkitatta kawai. Kekuma tashi kifita wannan yaxama last daxakizo gidan Kausar,idan fadama mijinta Abun datayi Abaya Kikeson yi kitareshi kifadamishi a titi. Tashi khady tayi dan ita harcikin Ranta tana Shakkar Leemah bin bayanta Seemah tayi Suka fita Suka bar gidan. komawa Leemah tayi ta Xauna, kallon feenah tayi miye kuma Abun kuka Anan besty? Leemah kigafa Shiyasa kokadan ba'ason Sa'bon Allah kota Wani Hali. Yanxu Kinga khady ta fadama kawayenta Abinda mukai Abaya,Allah kadai yasan iya adadin mutanin daxasusan wannan maganar. dukda Nasan ba lallai Yusuf ya dau mataki kan Kausar ba,Amma muddun yasani Xaiji badadi Cikin Ranshi Xai kuma iya fishi da ita. dan Allah feenah kada kidamu kan wannan duk Shirme Suke Allah yasani munyi taubatan Nasuwa kuma Shine ke rufama bawa Asiri dan haka babu Abinda xasu iya Akanmu. Hakane kaman yanda leemah ta fada feenah Kada kidamu dasu komai idan kikaga yafaru da bawa da Sanin Ubangiji Dan haka babu Abinda xasu iya yi. Allah yakara mana gafara kawai. Amin duk Suka fada. Lokaci daya sukacire tunanin Su khady Cikin Ransu sukaciga da firarsu Suna Raha. Karfe8 na dare Yusuf da yazeed suka Shigo Sallama su leemah sukaida Kausar kan saisun Kara Xuwa duk da damuwar dasuka nuna gaba daya hakan besa Sun karya Alkawarin mamy nacewa baxasuyi kuka ba. Koda Suka koma Cike Suka samu parlon Mamyn Su mumy sunzo. muryar inno kawai kakeji tana kwararo bayani kan Abubuwan dasuka faru a bikin Kausar. Shiga su Feenah Sukai Akacigaba da firar dasu. Karfi goma su mumy suka tashi tafiya feenah itama gida tace yau Xata koma Dan haka duk Suka dunguma Nazeer ya kwashesu Xuwa gida.

Bayan wasu lokuta Rayuwa na tafiyama Su feenah yanda suke so. Lokaci Xuwa lokaci Suna xiyartan Kausar,itama takan jemusu. Sati daya Kenan dasuka dunguma garin yola Akasha bikin Kabeer dasu,bayan Cema feenah da'akai Sabida batasonshi yasa yanemi wata ya Aura. Hakan ba wani damunta yayi ba Dan Ita tama mance dawani kabeer in badan labarin aurenshi datajiba. bayan Sun dawo daga yola ne Abba yaba yazeed Wasu takaddu ya duba mishi. Saida ya natsu ya duba, daga bisani ya shedama Abba Cewa takaddun Sunyi kyau xa'aiya daukan masushi Aiki Akowani hospital. Dadin maganar Yazeed Abba yaji Shikenan yazeed wannan takaddun yara nane su3 Zaka daukesu Aiki A Asibitinka tunda Naji kana neman kara ma'aikata daman. Sai yanxu yazeed yagane Cewa paper's din su Leemah ne,ba yanda ya'iya da Abba dan haka yace toh Abba. Yawwa dan'albarka Xuwa yaushe Xasu fara xuwa? Ko Monday ma Xasu'iya Abba. Shikenan tashi kaje Allah yayi Albarka. Amin yazeed ya fada yatashi yabar parlon. Kiran yusuf Abba yayi Awaya,bayan sun gaisa yake cemai kashedama Matarka Xasu fara Xuwa aiki Ran Monday. Gdy Sosai Yusuf yama Abba dan bayanda beyi da yazeed kan ya daukesu aikiba yaki. lokacin da yusuf ya shedama Kausar ba karamin murna tayi ba, phone ta dauka tafadama leemah itama tayi murna Sosai. daga bisani feenah Kausar ta kira ta fada mawa. Ba yabo ba fallasa feenah ta Amsa domin ita haushima taji,Acewarta dama Xama tayi ba Aiki,Akan wannan Aikin a karkashin wanda tafi tsana fiye da kowa. Haka kuwa Akai Monday Nayi Suka Shirya dan Xuwa Hospital. Office din yaxeed suka wuce face Adaure yamusu tambayoyi Suna bashi Amsa. Ka'idoji nason ranshi ya kafa Musu Cewa idan Suna aiki bazasu hadu d juna ba har saisun tashi, duk Wanda ya kira babu bata lokaci da dai sauransu. Babbu wacce tabashi Amsa haka yakaraci surutunshi yace sutafi. Abinda baxai yuwuva Kenan feenah ta fada lokacin dasuka fita. Dariya duk Sukai Rabu dashi saikace besan suwaye mudinba Kausar ta fada. Haka Rayuwansu tacigava gwanin shaw'awa kullum Suna haduwa basuda wata matsala. Gashi yanxu Sun Saba da sauran ma'aikatan Asivinti, feenah mace daya ta kasa sakin jiki da ita Dr Zainab itama Sabida feenar yazeed datake cemata yasa takejin Haushi.

Xuwa yanxu khady ta kara daukan Shawaran Seemah Sosai. ta yanda Mufeeda tarinka kafa hanyoyi da dama daxataga ta mallake yazeed amma Abu ya gagara.bata san Abokan shawararta Sune suke kara ruguxa mata Al'amarin nata ba. Kowace Hanya ta bullu Abu baya yiwuwa,wajen bokaye taje amma ina. Kudin data kashe wannan karan har yafi na kwanakin baya yawa, yanxu kan yazeed gaba daya takoma Mahaukaciyar karfi da yaji. Yauma xaune Suke su'uku Suna firarsu ta yan'Duniya. Nifa wlh Seemah harga Allah yanxu tsakani da Allah Nakeson yazeed badan wani dukiyarshi ba kowani Abun, Xan'iya Ajiye duk Wani mugun Hali Nawa Sabida Nasamu na aureshi. Kallonta Seemah tayi kawata Nima na rasa wannan Al'amari duk inda kika bullo ya toshe. Ammafa inaganin kodan Xaki tuba badan Allah bane,kinsan Hausawa nacewa "kowa yatuba dan wuya ba lada" hade Rai Mufeeda tayi toh mekike nufi? Aa Ni bana nufin komai kawai kikara dagewa Akanshi. kwafa Mufeeda tayi nifa Naga tunda khady dinnan ta dawo Nan Kika kara wani shigemata. Toh miye kuma yashafe Khady da Abinki? Nothing Mufeeda ta fada lokacin data tashi. Ina Xaki kuma Seemah ke tambayar ta. Wajen yaxeed Zani! D Sauri khady dake kwance ta tashi.Alama Seemah tayimata data koma ta kwanta,hakan kuwa tayi. Amma mufeeda ai yazeed baya gida yanxu ko? baya gida Seemah hospital dinshi Zani. Ayya Allah yasa kidace. Ai yau xandace kuwa Sabida Abinda ban fadamishi va Xan fada. Oh Wai dama baki fada mishi kina Sonshi ba??? Mitsww wannan kuma Na nawa. Xan fadamishi Halin kanwarshi da wannan Shegiyar yarinyar ne. gaskiya kam gara yasani kidawo lfy. fita Mufeeda tayi Cikin Shigar Rashin Mutumci. tana fita khady ta tashi kinjifa inda tace Xata Seemah. Naji Khady tashi Zakiyi yanzu kishirya kibi bayant???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?a, kisan inda Xaki boye idan kinje data fito kisamu kishiga office din nashi kisan mai Xaki fadamishi tayanda Xai kalleki Amatsayin mai ilimi, kinga maybe ayauma kishiga Ranshi. Ok Khady ta fada lokaci daya tashirya Nayi kuwa Seemah? Wow kinganki kuwa Lallai hijaf ma shine mutumcin mace wlh Kamar bake ba.dariya Khady tayi kinji kuwa Yanda na takura. Ai Abu kike bukata maxa daure kije. fita khady tayi tana fadin byeee. Saida tafita Seemah tace wahalallun banxa,Allah yasa yaxeed dinma duk yahadaku ya xane.

=ؖ?=؋?=؋?=؋?=ؖ?=؋?=؋?=ؖ?
YAR LESBIAN CE
=ؖ?=؋?=؋?=ؖ?=؋?=؋?=؋?=ؖ?
By
Nadeeya mohd Ahmad
(=ؖ?Nadseer=؋?)

dedicated to
Xaynab Ummu mahbub

Page....57/58

daret Hospital din Yaxeed Mufeeda ta karasa. Ba wani bata lokaci tayi wajen Shiga Office dinshi ba. Yana ganinta ya Nuna mata kofa yana miye ya kawoki?? Xan fita yazeed Alkairi y kawoni. Ke ai ganinki babu wani Alkairi Acikinsa kifita kawai nafada miki. Hakadai Kace Honey Amma yau Sako Naxo isar maka. Shedan dai ya angizo ki bana bukatar bude ido naganki So get Out. Ok Mr yazeed kabani 10mns kadai. Kauda kai yayi gefe bekara magana ba,ganin haka yasa Mufeeda ta karasa ta Xauna. ina hini? Bashi Nakeson Ji ba. gira Mufeeda ta daga Sama Alright y Aiki? buga table din dake gabanshi yayi wlh Xan takaki Anan. Wai dan Allah miye yasa ka tsanine haka yazeed?? Sabida kedin Shedaniya ce. Amma Dan nayi kuskure karami Shine naxama Shedaniya yazeed? Kinma fi Shedan ke Ai. Shikenan indan Abinda namaka Shine yasa ka tsananeni kake kirana Shedaniya, Ashe kuwa kana tare da manyan Shedanu Cikin gidanku, wajen Aikinka. Wani irin kallo yaxeed yamata wanda Saida hanjin Cikinta ya kada. Amma dayake yar duniyace kashe mai ido daya tayi gsky Ai. Idan Har xaka kirani shedaniya dan inabin maza,me Zaka kira Sauran matan dake bin mata yan'uwansu??? Mufeeda tashi kifita Dan Wlh Xan'iya Shakeki. Idan kina bin maxa,kuma Kina nufin ke YAR LESBIAN CE duk ke yashafa ba niba,tunda sakamakon Abinda kike yanaga Allah. Eh Nasani yazeed Shiyasama Naxo Shidamaka Na dau Alwashin daina duk Wani Abinda nake matukar Zaka dawo mucigaba da Soyayya har muyi Aure. dafe kai yazeed yayi ya dago ya kalleta ke koda Qur'an naganki kina karantawa baxan yarda dake ba, Na tsaneki Mufeeda bana sonki. Kece mace ta farko dakika fara Ruguxa Rayuwata. Kalaman yaxeed Sun mata daci matuka daurewa kawai tayi, Naji yazeed yanxu Kenan maganar danaji nacewa feenah kakeso gaskene? "La haula wala kuwwata llah billah" yazeed ya fada wai bana miki kashedi da kada kikara Xuwa Nan ba? Kamun Amma ka Amsamun tambayata natashi nafita. Beshafeki ba Naga inason wata feenah ko bana sonta. Tashi mufeeda tayi ta rataye Jakarta Saida takai bakin kofa Idanma kana tunanin danni karuwace yasa baxaka aureni ba! Haka nan bada dadewa ba wani Xai kawo maka Complain kan kanwarka. Banma San miye yasa kake neman yar masu mutumci ka Aura ba bayan gidan naku basuda tarbiyya, idan bakasaniba kasani yau! kanwarka Halima Ahmad YAR LESBIAN CE! Matar dakake Son Aure kake wulakanta wasu wato Feenah Umar Faruk itama YAR LESBIAN CE So kaga har wajen ubangiji nafi kanwarka da budurwarka matsayi daga Haka mufeeda tafita tabar gaba daya Hospital din. yaxeed daya daskare Xaune har yanxu inda Mufeeda ta tsaya yake kallo. "banma San miye yasa kake neman yar mutumci ka Aura ba bayan gidan naku bashida tarbiyya" Abinda Xuciyar Yazeed ke nanata mishi kenan. " kanwarka haleema Ahmaad YAR LESBIAN CE! Budurwar dakake Son Aure YAR LESBIAN CE!" Innalillah Yazeed yashiga maimaitawa. Tabbas Abinda nadade Ina tunani yau ya tabbata, Kenan dama Surutan danaji Sunayi kwanaki Abinda Suke Aikatawa Kenan?? Table din gabanshi ya buga Noooo yafada lokacin dayake bargaxa gashin kanshi. Leemah Bazata Aikata haka ba. feenah?? No Itama duk da banasonta Nasan ba Halinta bane. Kausar fa? Aa itama Harda ita lokacin dasuna Wa'azee Akan masu Aikata halin nan. Amma miye yasa naji kwanaki Suna.....Turo kofar da'akai yasa yazeed dagowa gaba daya idonshi yayi jaaa. karasowa tayi taxauna kan daya daga kujerun dake kallon yaxeed. barka Dr yazeed. Kallonta kawai yake be'iya bata Amsa ba. Sunana khadija Nasan Xaka ganeni, Sannan nasan Wannan bacin ran Naka bewuce nasaba kan Abinda Aka fada maka yanxu ba. Amma inason kasani Mazon Allah S. A.W. yace kada kayi Shedar Zur Akan Abinda bakada masaniya Akai. Nasan kaji Abinda Nafadama Yusuf cewa Ni Kawar Su feenah ce, Kagani Kenan ni Sheda ce Akansu nacewa basa Aikata wani Abu makamancin Abinda Aka fadamaka yanxu. Idan wannan be gamsar da kaiba. Nasan baka taba ganin Sun'aikata Agabanka ba, kuma nasan ba'a taba kawo maka karar Leemah daga Skul kan Cewa Ta taba aikata wani Rashin ji ballantana Abinda ya yashafi wannan. Ko Kana nufin Xasu Aikata Abu sama da Shekara3 dasukai a Skul kuma Akasa ganewa?? Kenan duk wannan sun isheka Sheda. Sannan kasan irin tarbiyyan da Akabaku a gidanku bazesa Leemah ta Aikata haka ba,bare feenah da bata mu'amala da mutane kuma itama kasan tarbiyyan gidansu. Kausar kuma da'ace tanayi yasuf Xaifara Sanar dakai kafin wata Mufeeda. kacire Wannan Aranka bekamata kanama Amfani da irin maganganun karuwan matan Nan ba. Kafin ta fito daga gida Xuwa nan ta fadamun Cewa tunda yanxu ba ita kakesoba Xataxo tasaka maka kiyayyar wacce kake so.Sannan tasamaka Xargin kanwar ka.taso ace Yusuf yana Nan, dan yaji yasaki Kausar Ayau Amma dayake Sharri tayi niyar yi ka gani yakoma mata. Abinda yasa ka ganni Anan tace Nima Naxo nakara Xugaka ne. tamance dacewa Nima Dan narinka Musu Wa'axee naje gidansu. tunda khadija tafara magana yazeed ke saurarenta kuma tabbas Zafin Ran daya shiga ya Ragu Sosai.ganin yadan Sakko khady Cikin Ranta tace da wuri haka. Afili cewa tayi Ni Xantafi Dr yazeed inakara jan Hankalin ka daka xama Mai koyi da halaye irin na manzon Allah S.A.W. danshi baya daukan Ziga,kuma baya daukan Kace nace. Sannan ya koyar damu cewa idan kaga Abin kyama daga jikin dan'uwanka kacireshi da Halshenka,idan bazaiyuwaba kacireshi da Hanunka,idan bazai yuwuba kacireshi da xuciyarka. Kaga da'ace mufeeda mutuniyar Arziki ce koda da gaske Suna aikata lesbian ba tona musu Asiri yakamata tayi ba,wa'azi yakamata tamusu, idan bazata Iya ba taji kyamar Abun Nasu Cikin Ranta Sannan tamusu Addu'an Shiriya. Murmushi ne ya bayyana a face din yazeed Alamar ya gamsu. Ganin haka ba karamin dadi khadija taci ba Sai Anjuma tamishi tafita.Cikin Ranta tana murnan ko Yanzu kasuwa ta watse dan koli yaci Riva.Acewarta har tasamu Waje Cikin Xuciyar Yazeed. Lallai Shidin maison kamilar mace ne dole nadawo kamila ta kwarai Amma bayanxu ba Gaskiya. Uppp wannan hijaf ya isheni Sai xafin jaraba.haka ta tari Napep tana sambatu Cikin Ranta.

Leemah dake tsaye Ita da Dr Zainab Suna fira taga sanda Khady ta fito daga office din yazeed dan haka tunanin maiya kawota tarinka yi. Kallonta Dr Zainab tayi kokin Santa ne Leemah? am..Emma..inaxuwa nakira su Feenah Leemah ta fada cikin in'ina. Tare Suka karaso wajen Dr Zainab Suka Xauna. Wai menene limcy Kamar kina cikin rudu Kausar ke tambayar Leemah? Hmm kausar Khady Naga tafita daga hospital dinnan yanzu. Feenat batakawo komai Aranta ba tace maybe ko tazo neman aiki ne. girgixa Kai Kausar tayi da kamar wuya feenah, Ina ganin taxo ta fadama yazeed Halinmu ne Kamar yanda Suka Shirya Abaya. tabe baki Feenah tayi Sai yazo yabamu takardar Sallama Ai. Kai kenan duk in kariga ka'aikata Abu baya wucewa Sai anta barbadashi,kai Wlh nayi danasanin Xuwa Abuja karatu. Ina dalili kadaina Abu tsakaninka da Allah Amma Ace haryanxu tabon Abun baxai Rabu dakai ba. Dr Zainab dake kallon feenah tayi mamaki dataga feenah na magana haka Ayau. feenar yazeed Ayi hakuri dama haka Rayuwa take musamman idan kana hulda da mutane dole Akwai nagari da batattu kuma. Hakane Dr Zainab musamman Idan kana Tare da Hausawa Sunfi nacin Abu Kausar ta fada. Ni yauma nafara ganin yarinyar Anan hospiatal din Ashe kawarku ce. Nafi ganin wacce ta Shigo da farko. da Sauri leemah tace wace ta farkon. Bansanta ba amma Suna yawan fada da yazeed duk sanda tazo Har kashedi yamata da kada takara Xuwa,Amma kunga yau tazo. Kuma daga dukkan Alamu tare Suke da Kawar taku dan Naga Saida kawarku tafaki idon wacce tafara Shigowa tukun itama tashigo. Waya Kausar taciro tanemo pic din Mufeeda Dr Zainab wannan ce wacce tafara Shigowa din?? Kallon pic din Dr Zainab tayi kwarai itace Kenan kawarku ce itama? Lallai Abinda Suka fadama bro Yazeed kenan Leemah ta fada tana Xufaa. Da Sauri Kausar tace na lura itama khady dinnan son yaxeed din take shine ta Sako hijaf tazo kawo mishi gulma. Wai miyene hadinku dasu toh? Sirrine Kausar ta fada. da Sauri feenah dakejin Xuciyarta na tafasa tace wani Sirri kausar bayan Angama tallah damu? Ai bekamata mu boyema Dr Zainab komai ba tunda kadan ya Rage mujimu a gidan Radio tunda yazeed yaji halinmu. Dr Zainab Ada mun kasance dagani sai Leemah muke Rayuwarmu babu wani. Alokacin damuka Shiga Skul A Abuja Anan ne Rayuwarmu ta Chanza lokacin Damuka hadu da kausar da kawarta Khady. Kwashe kafff labarin Rayuwar dasukai Abaya da yanda Khady ta daura Kausar kan hanyar lesbian da yanda Suma Suka Shiga, da irin Rashin kulawar da iyayensu suke basu a farko, har Xuwa lokacin da iyayensu Suka lura da Abinda Suke Mamy tamusu Nasiha, da irin tuban dasukai na tsakani da Allah. Feenah na kuka takara dacewa Wlh Aunty Zainab tun lokacin damuka tuba bamu Kara Aikata lesbian daidai da Rana daya ba,dama Chan gaba daya ba halinmu bane son Xuciya ne da Sharrin shedan. Rungumesu Dr Zainab tayi gaba dayansu Suka rinka kuka Kamar yau Abun yafaru dasu. Babu mai lallashi Har ita Dr Zainab din tayasu take. Yazeed datun lokacin da khadija tafita Zuciyarshi tadanyi Sanyi,ya rage tunani amma haryanxu yanajin Xafin maganganun Mufeeda data mishi. Afili yace wai wannan ma ba'itace khadjar data rinka Rashin tarbiyya a Ranar walimansu ba? Itace meyasa taxama Malama? Maybe dama malamar ce wanchan lokacin dan "tamsiliyyace" yasa Akabata part din yan Rashin mutumci. Koma dai miye tunda kawar su Leemah ce Zatafi Sanin halinsu Lallai karya mufeeda tayi musu Saina koya mata hankali. Ahaka Yusuf yashigo yasameshi yana Surutai. Kaikuwa lafiyarka yazeed? Bakomai Yusuf. O.k. Yusuf yafada badan ya yarda ba.tashi Kazo kaga wani Abu danake. Aina Yusuf??? Office dina mana.tashi yaxeed yayi Sukafita tare da yusuf Xasu wuce Sukaji muryar feenah Na magana. Tohfa yau muryar feenah ce tafi ta kowa Yusuf ya fada.haka Kawai yazeed yaji yanason ganin mai Suke, jan Yusuf yayi suka nufi wajen su kausar.Anan ne kafin su karasa Sukaji bayanin da feenah kema Dr Zainab nagame da rayuwarsu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login