Showing 159001 words to 162000 words out of 180927 words
Chapter 54 - GARKUWA Book 1 Original Pdf By Garkuwar Fulani.txt
komai.
A haka taci gaba da tono tana kuma faɗaɗa ramin ta ƙasa.
Wani irin zabura Jamil da Ummi sukayi lokacin da suka ga wani baƙin hayaƙi yana fitowa cikin ramin.
Ita kuwa Shatu da sauri tasa hannun damanta taci gaba da tonon.
Tare da yin mgna da sauri tace.
"Jamilu buɗe windows da sauri hayaƙin nan ya fita".
Cikin rawan jiki yace to.
Kana ya fara buɗe wa da sauri sabida, hayaƙin ya fara cika ɗakin.
Yana buɗe windows ɗin kuwa hayaƙin ya fara fita.
Tonon taci gaba dayi tare da cewa.
"Inama da akwai wani yardajjen mu a kusa, bayan ku biyun nan da yabi hayaƙin nan zaigane mana ina zai shiga cikin sashukan mutanen gidannan shaidar aiki ya koma kan wanda ya yishi."
Da sauri Jamil yace.
"To ko in fitane inbi hayaƙin".
Cikin sauri tace.
"A a kada ka fita ku tsaya kaida Ummi."
Numfashi suka fara sauƙewa, a hankali lokacin da sukaga duk hayaƙin ya gama fita.
Sai kuma suka fara takowa suna zuwa inda take ganin yadda hannunta dake cikin ramin yake karkarwa.
Ga wata zufa dake keto mata kamar da bakin kwarya.
Wani marfin tukunyar ƙasa ta ɗago.
Kana a hankali ta ɗago tukunyar.
Ta ajiyeta gefe kana ta koma ta jingina tana mai jan numfashin.
Cikin sauri Ummi taje ta kunna sauran wutan ɗakin duka, ya zama kamar farin wata.
Jamil ne ya fara leƙa cikin tukunyar.
Da sauri yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ummi zo ki gani".
Ya ƙarishe mgnar yana sunkuyowa da kai hannunshi zai kama tukunyar ƙasan cikin sauri da ƙarfi Shatu ta buge hannunshi da hannunta na hagu tare da cewa.
"Jininka ɗaya da Yah Sheykh in ka taɓa duk abun zai iya dawowa jikinka."
Ta ƙarishe mgnar da ɗago hannun ta na dama tasa a ciki.
Tukunyar da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen tsikara da taji an mata a hannunta.
A can ƙasar Cameroon kuwa cikin Rugar Duno dake, kusa da Rugar Malam Babayo.
Ba'ana ne zaune bisa buzun aikinshi.
Da kasko a gabanshi yana kallon cikin kaskon gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi cikin tashin hankali da fargaba yace.
"A'a A a Mata kada ki taɓa, baki amince na baki mgnin kariyar tonar sihiriba, iya ganin idan a zuba sihiri a abinci yake na shayar dake shi nanma a bisa dole baki saniba.
Kada ki taɓa zai cutar dake".
Ya ƙarishe mgnar hawaye na zubo mishi, Allah ya sani baya son abinda zai cutar da Shatu ko kaɗan.
Ita kuwa Shatu a hankali ta fara fito da wasu irin tabka-tabkan layu wanda aka liƙesu da yadin al'kyabba daga gani kasan na Sheykh ne sabida shi ɗaya kesa irinsu a masarautar Joɗa tun yana ɗan yaro matashinsa.
Wani dogon ajiyan zuciya taja tare da fizgo wani dogon maciji a cikin tukunyar ƙasar.
Da sauri Ummi taja da baya, shi kuwa Jamil sai leƙowa yakeyi.
A dai-dai lokacin kuma Sheykh dake cikin Office dinshi na cikin Genaral Hospital Ɓadawaya shi ɗaya, dan yau ba mutane sosai dudu mutun biyar ne kuma ya gama dubasu ya musu komai, yana zaune ko za'a turo wasu.
Wani irin zabura yayi ya miƙe tsaye da ƙarfi tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Sai kuma ya sunkuyo yana kallon yadda babbar yatsarshi ta ƙafar dama wacce zanen maci ke kanta take rawa kar-kar.
Da sauri ya juya ya nufi bathroom ɗin cikin Office dinshi.
Cikin sauri ya zare malum-malum ɗin jikinshi juyowa yayi ya ajiyeta saman kujerarshi.
Kana da sauri ya nufi Bathroom sabida yadda yakejin ana fizgo wani abu kamar jijiya a jikinshi tun daga saman cikinsa kusa da ƙirjinsa, har zuwa kan ɗan yatsarshi.
Da sauri ya cire rigarshi da snglet ɗin, da ido yabi zanen dake jikinshi wanda samanshi zanen kan macijine.
Gaba ɗaya jikinshi rawa ya farayi tamkar mazari.
Duk wata jijiya dake jikinsa saida ta tashi tsaye.
Cikin tashin hankali yake ambaton sunayen Allah da duk addu'o'in da sukazo bakinsa.
Hannunshi yasa ya damƙi bnnarshi data miƙe tayi wani irin harbawa da masifar ƙarfi, riƙeta yayi da kyau jin yadda take tashi tana kumbura da cika tana tsawo tamkar zata faso boxes ɗin shi ta fito woje.
Wannan shine babban tashin hankalinshi dan tsawon shekaru kusan ashirin bai sake ji ko ganin bnnarshi ta miƙe kamar hakaba sai yau.
Karkarwa duk jikinshi keyi, hatta jijiyoyin kanshi dana damatsan hannunshi tasowa sukayi ruɗu-ruɗu jijiyar goshinsa har harbawa takeyi".
Innalillahi wa innailaihi rajiun yaketa maimaitawa, yanajin kamar ana jan jijiyoyin jikinsa.
A haka ya maida kayanshi kana ya fito.
Sai dai bai samu damar maida gariyar ba, zama kawai yayi bisa kujerar yana rawan sanyi.
A haka abokinshi Dr Arabi ya shigo ya sameshi cikin mamakin ganin yadda yake karkarwa yace.
"Dakta Jabeer lfy kuwa meya sameka".
Cikin muryar alamun zazzaɓi yace.
"Zazzaɓi ne Arabi. Sanyi nakeji".
Da sauri ya iso inda yake taimaka mishi yayi ya saka mishi gariyar.
Kana ya kamoshi ya kawoshi bisa tattausan kujerar 3 str dadake cikin Office ɗin ya kwantar dashi.
Aunashi yayi tare da kiran wata Nurse ya gaya mata magungunan da zata amsa musu a Pharmacyn nasu, cewa Dr Jabeer ba lfy.
Ai lokacin ɗaya sai gata da manyan likitoci har uku.
Cikin tarin kulawa, suka fara dubashi ganin yana gab da fita haiyacinsa ne, yasa suka mishi allurar bacci.
Da sauri Dr Arabi kuma ya kira, Jalal ya sanar mishi.
Jalal kuwa dake falon Hajia Mama ba tare da ya gaya mata ba ya miƙe da sauri ya fita.
Tana tambayarshi lfy.
Yace lfy sabida baison tayar mata da hankali.
A bakin ƙofar fita ya haɗu da Ya Affan da sauri ya kamo hanunshi suka juya yana cewa.
"Ya Affan Hamma Jabeer ba lfy, yana Genaral Hospital Ɓadawaya, yanzu Yayan abokina Umar Dr Arabi abokinshi ya kirani ya gaya min yace baida lfy sosai fa".
Ai da sauri Affan ya fara lalubo car key dake cikin al'jihunsa cikin kiɗima da tashin hankali yace.
"Muje, muje da sauri mu tafi a maidashi Valli Hospital yafi kwararrun likitoci".
Kusan a tare suka shiga motar Affan suka tafi.
Kafin suje kuwa tuni bacci ya ɗauke shi, an ɗaura mishi ruwa da allurai.
Sauran Doctors ɗin sun fita.
Sai Dr Arabi da yake zaune gabanshi.
Da sauri Affan yasa hannun shi ya taɓa jikinshi tamkar wuta.
Jalal kuma yatsarshi daketa karkarwa yake kallo tare da rauni a fuskarshi yace.
"Yah Arabi meya sameshi ne?".
Cikin sanyi Dr Arabi yace.
"To wlh nima shigowa kawai nayi na sameshi yanata karkarwa, yace min zazzaɓi yakeji sanyi na damunshi.
Na kira Nurse ta kawo min injections and drip kafin muyi mishi allurar ma tuni ya kusa suma, abun yafa bani tsoro.
Amman Alhamdulillah kunga yanzu kuma da sauƙi".
Ajiyan zuciya sukayi kana suka zauna a nan, ba tare da sun gayawa kowa ba.
A can masarautar Joɗa kuwa.
Cikin tarin firgici da al'ajabi Jamil da Ummi ke kallon Shatu.
Data fizgo macijin da ƙarfi cikin tukunyar.
wurgar dashi tayi a ƙasa sai gashi yayi wutsul-wutsul sau biyu, shike nan ya mutu."
Mazargin mondo ta fitar da kuma hula wanda duk na Sheykh ne.
Cikin murya mai rauni tace.
"Yanzu Jamil zaka iya taɓasu.
Haɗasu kaje in akwai inda zaka wurgar dasu ka wurgar dasu, ka fasa tulun.
Kada ka binne macijin ya bushe akeso.
Ummi ɗauki Hular Yah Sheykh da zariyarshi a wonkesu.
Da sauri Jamil yace.
"Eh akwai inda zan wurgar dasu".
Nan ya tattare macijin da da layun ya saka cikin tulun ya fita.
Key ɗin ƙofar baya ya ɗauka ya buɗe ya tafi cikin Garden ɗin.
Tafiya yayi sosai saida yaje can cikin dajin ya fasa tulun macijin da layun suka watse kana ya juyo ya dawo ba tare da ko waiwaya ba sabida tsoro.
Ita kuwa Ummi bathroom ɗin shi ta shiga a take ta wonkesu kana ta fito dasu.
Cikin sanyi Shatu tace.
"Wai hannuna Ummi yi sauri ki wonko gero ki kawo min ruwan tsarin."
Da sauri Ummi ta fita.
Murmushi tayi ganin Ɗalha mai gyaran tayis yaci yayi haniƙan yana kallon tv.
Cikin sauri tace.
"Yi haƙuri dan Allah Ɗalha muna tattare ɗakin ne da yake tayis ɗin ƙasan gadone ya fashe".
Cikin shan iskar yace.
"Ba komai Ummi".
To tace kana taje ta wonke gero, sannan ta fito da ruwan tsarin tazo.
Tana zuwa ta bawa Shatu cikin ramin ta watsa ruwan.
Kana ta fara tura ƙasar da kuma fashesshe-fashesshen tayis da fulo ɗin tanayi tana yayyafa ruwan.
Dai-dai lokacin Jamil kuma ya shigo.
Ganin yadda hannunta yaketa karkarwane yasa ya tayata tura ƙasar saida suka gyara komai fes kamar ba fasawan ganganci akayiba.
Kana ta miƙe tare dasa hannun hagunta ta riƙo na damanta tana cewa.
"Shima Yah Sheykh dole zaiji wani abu a jikinshi duk inada yake".
Sai kuma tayi shiru tare da rumtse idanunta tace.
"Wash hannuna".
Cikin sauri Ummi tace.
"Sannu hannun ya gaji ko".
Kai kawai ta gyaɗa mata.
A haka suka fito falon. Kai tsaye bedroom ɗin ta ta nufa.
Shi kuwa Jamil yayiwa Ɗalha jagoro,
Suka shiga suka gyara wurin da aka fasa ɗin fes.
Kana Ummi ta share wurin ta goge, sannan suka tura gadon suka maidashi.
Nanma ta ƙara gyara ɗakin Jamil kuwa ya ɗauki Ɗalha ya maidashi wurin aikinshi.
Ummi na gamawa taja ƙofar ta rufe tana al'ajabin wannan abu da ta gani da idonta.
Kitchen ta wuce ta ɗaura musu Lunch tana kiran Umaymah ta gaya mata duk abinda ya faru.
"Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Kaɗan daga cikin mafarkan da nakeyi kan Sheykh ya auro ba fulatar daji sun fara tabbata.
Ya Allah kasa abinda zai faru a sanadin shigowar Shatu masarautar Joɗa ne kake nunamin a mafarkaina".
Umaymah ta faɗi lokacin da Ummi ta mata bayanin abinda ya faru.
"Amin Amin, Ummi tace kana ta katse kiran jin muryar Aunty Juwairiyya da Hibba."
Umaymah kuwa da sauri ta kira Lamiɗo ta gaya mishi abinda ya faru.
Murmushi yayi irin nasu na manyan sarakuna yace.
"Alhamdulillah warakafa nan shigowa masarautar Joɗa baki ɗayanmu zamu rabu da mugun iri a cikinmu, kada ki gayawa kowa Khadijatu kinji ko".
Cikin jin daɗi Umaymah tace.
"In sha Allah kuwa ko Jadda bazan gaya mishi ba".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Masha Allah, Allah ya miki al'barka Khadijatu da ace duk ƴan uwa haka suke riƙe ƴaƴan yar uwarsu da zumunci ya ƙara ƙarfi kin musu abinda mahaifiyarsu bazata iya musuba".
Amin Amin tace kana ya katse kiran.
A cikin ɗakin Shatu kuwa.
Wani irin...!
Wani irin zufane ke tsastsafo mata.
Tako wani hudan gashin jikinta.
Gaba ɗaya ji takeyi hannunta na dama wanda dashi ta buɗe tukunyar ƙasan yana wani irin suka kamar ana tsikarinta da allurai masu dafi.
Jiki na rawa ta konta bisa gadon.
Wani zazzafan zazzaɓi ne ya rufeta a take.
Cikin rawan jiki tasa hannun hagunta ta jawo tattausan blanket ɗin ta rufe jikinta.
Rumtse idanunta tayi da ƙarfi tanajin zafin na ratsa mata jiki a hankali take addu'o'in cikin ranta. Jikinta na ci gaba da ɓari.
Ita kuwa Ummi a kitchen ita da Hibba da Aunty Juwairiyya sukayi girki suka gama.
Saratu ta share ko ina.
Ganin azahar tayi ne, sukaje sukayi salla kana suka dawo falon.
Shiru-shiru Shatu bata fitoba, hakane yasa Ummi tace Hibba take ta kirata.
Hibba na tafiya Jamil ya shigo.
Nan suka zauna.
Juyowa Ummi tayi tana kallon Hibba dake cewa.
"Ummi! Ummi!! Aunty Shatun kamar bata da lfy, naga sai rawan sanyi takeyi."
Da sauri Ummi ta miƙe ta nufi cikin ɗakin bisa sallaya ta sameta alamun tayi sallan azahar kenan.
Da sauri ta nufi inda take tare da cewa.
"Shatu meyake damunki".
Cikin sanyi murya tace.
"Zazzaɓi ne Ummi".
Cikin tausayawa tace.
"Subahanallahi sannu ko! Barin in Sheykh ya dawo sai ya dubaki, yanzu muje ki samu kici wani abu".
Cikin rawan murya tace.
"Na ƙoshi Ummi".
Hannunta takai ta taɓa jikinta kamar wuta cikin kula tace.
"To me kikaci da zakice kin ƙoshi?".
Danne kukan dake son kubce mata tayi, wanda halittartace dama in ɓata da lfy dai to kuka kuma zata shashi.
Cikin rawan murya tace.
"Na ƙoshi bazan ciba".
Cikin jin ba daɗi Ummi tace.
"To tashi in taimaka miki ki koma kan gado.
Sai anjima kici abincin".
Ta ƙarishe mgnar dasa hannu ta kamo hannun daman Shatu.
Da sauri ta miƙe tare da saƙin ƙara a hankali tace.
"Wayyo Ummi hannun zafi, kamanin wannan in tashi".
Ta ƙarishe mgnar hawaye na zuba.
Cikin tsoro Ummi tace.
"Ayyah sannu. To amman kin bige hannune ko kin yankene?".
Cikin karkarwan zazzaɓin tace.
"A a".
Konciya tayi a kan gadon.
Borgo Ummi taja ta rufeta dashi.
Kana ta fita tana cewa.
"Allah ya sauwaƙa".
A falon ta samesu zaune, cikin sanyin jiki tace.
"Jamil ina Jalal naga kai kaɗai".
kanshi ya ɗago ya kalli Ummi tare da cewa.
"Yau tun da mukayi breakfast ban ganshi ba.
Bari in kirashi".
To tace kana ta zauna. Shi kuma wayarshi ya zaro ya kira layin Jalal.
Bugu biyu ana uku ya ɗaga sabida baya son sautin kiran wayarshi ya tashi Hamma Jabeer ɗin nasu daga baccin da yakeyi.
"Hello Jalal ina kake ne, yau tunda safe ban gankaba".
Cikin sanyi yace.
"Jamil Hamma Jabeer baida lfy, yanzu haka muna asibiti dashi nida Yah Affan".
Cikin ruɗani Jamil ya kalli Ummi kana ya kalli wayar tare da cewa.
"Meya sameshi? Wanne asibiti kuke?".
Affan ne ya amshi wayar Jalal tare da cewa.
"Jamil kadafa ka gayawa Mama hankalinta zai tashi.
Jikinshi da sauƙi sosai zazzaɓi ne kawai yanzu kam ma bacci yakeyi, yana farkawa dai zamu dawo gida".
Cikin ɗan samun nitsuwa yace.
"Ka tabbatar Ya Affan?".
"Zan maka ƙarya ne?".
Affan ya amsa mishi tambaya da tabaya.
Kana yace.
"Bawa Ummi wayar".
To yace kana ya miƙa mata wayar.
Nan yace mata. Sheykh ba lfy, amman jikinsa da sauƙi.
Su kontar da hankalinsu in ya farka zasu dawo.
To Ummi tace tare da mishi addu'a kana sukayi sallama.
Shiru sukayi a falon suna nazarin to meke faruwa.
Musamman shi Jamil da yaji Ummi na cewa Aunty Juwairiyya cewa Shatu ba lfy.
A haka dai sukaci abinci.
Sheykh Jabeer kuwa, sai ƙarfe Shida na yamma gab da magriba ya farka.
Da sauri Affan ya matso kusa dashi.
Tare da kama hannunshi yace.
"Sannu Hamma Jabeer, ya jikin naka? Da sauƙi ko? Me yake maka ciwo?".
Shiru yayi yana kallonsu yana tuna lokacin da yayi baccin.
Jalal ne ya ɗan kalleshi cike da rauni yace.
"Hamma Jabeer ya jikin naka.
Me zakaci in kawo maka?".
A hankali yace.
"Meyasa baku tadani ba nayi sallan azahar, la'asar, gashi har magriba ta kusa."
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa zaune da alamun ɓacin ran rashin tada shi da basuyi ba.
A hankali Affan ya miƙe tare da kamo hannunshi alamun zai tallafa mishi ya tashi.
"Janye hannunshi yayi tare da kallonshi cikin alamun faɗa yace.
"Lokacin Sallah yayi kuna ganina ku barni ina baccin asara baccin yammaci sabida baku ɗauki salla da mahimmanci ba, ai ko bana gani bana mgn zaku tasheni kuyi min alamun lokacin salla yayi inyi niya kuyi min al'wala inyi salla.
Bare ina cikin hayyacina, ku jinyarku sai kace jinyar kafurai babu tada majinyaci batun salla".
Ya ƙareshe mgnar yana nufar hanyar bathroom.
Da ido suka bishi suna cewa.
"Kayi haƙuri".
A hankali yake taku sabida har yanzu yanajin kamar ana zare mishi jijiya a jikinshi dai-dai inda zanen tafiyar macijin nan yake.
Al'wala yayi kana ya fito, yayi salla.
Sannan yace.
"To mu tafi ko".
Cikin sauri sukace to sukabi bayanshi.
Suna sauƙa ana kiran sallan magriba a masallacin cikin asibitin.
Nan suka tsaya a masalacin asibitin sukayi sallan magriba.
Kana suka nufi gida.
Ana kiran salla. Isha'i suna shiga masarautar Joɗa shiyasa kai tsaye suka wuce masallacin.
A cikin masarautar kuwa, sosai jikin Aysha yayi zafi da zazzaɓin.
Da kyar Ummi ta taimaka mata tayi al'wala kana tayi salla.
ana ta zauna saida tayi sallan isha'i kana itama tayi.
Sannan ta kalli Hibba tare da cewa.
"Hibba haɗo min koda tea ne ki kawo in bata tasha".
Cikin rauni ta girgiza kai alamun bazata shaba, murya na rawa tace.
"Ummi zan kwanta".
Cike da mamaki tace.
"To Aysha jinya ba abinci kuma ai shike tsananta jinyar.
Ki ɗan sha koda tea ɗin ne in Sheykh ya dawo ya dubaki.
Shiyama ɗin baida lfy yau wuni yayi kwance a asibiti".
Cikin rumtse idanunta tace.
"Ba matsala zaiji sauƙi, dama dole zaiji a jikinshi alamun a kunce abubuwa da yawa a jikinshi".
Sai kuma ta miƙowa Ummi hannu tare da cewa.
"Ummi zan kwanta, kaina ciwo kamar zai rabe gida biyu hannu ciwo kamar zai tsinke".
Cikin tausayawa tace.
"Aysha ko dai taɓa abun nanne da kikayi ya jawo wannan abun".
A hankali tace.
"Wata ƙil".
Amsar kofin da Hibba ta miƙo mata tayi tare da cewa.
"Yauwa amshi kisha kinji ko Aysha".
Cikin sauri ta girgiza kai sabida bazata iya ci ko shan wani abun a yauba irin zafin da takeji".
Ganin haka ne yasa Ummi ta taimaka mata ta miƙe tsaye kana ta koma kan gado.
Sannan ta rufe mata jiki tace.
"Bari inje in sanarwa Gimbiya Aminatu kafin Sheykh ya dawo".
Cikin sanyi tace.
"To amma Ummi kada kice mata na cire wani abu".
To tace kana ta juya ta fita.
Tuni dama Hibba ta fita.
A falon ta samesu harda Jalal Affan da kuma Sheykh yana zaune da alamun jinya a jikinshi.
Jamil kuwa tamkar likita haka ya tsareshi da tambayoyin meke damunshi meke mishi ciwo.
Ummi kuwa babbar yatsarshi da har yanzu take motsine ta kalla tare da cewa.
"Sheykh sannu ko! Ya jikin naka? Da sauƙi ko?
Me zan kawo maka kaci?".
Cikin lumshe ido yace.
"Alhamdulillah da sauƙi".
Aunty Juwairiyya da Ya Jafar da yanzu suka shigone,
Ya Jafar ne ya zauna a gabanshi.
Yana kallon yatsarshi. Murmushin yayi wanda ya bawa su Jalal Jamil Affan mamaki yayi kana ya kalli Sheykh sai ya kuma miƙa ya zauna gefenshi ya ruggumeshi.
Ummi ce ta kuma kallonshi tace.
"Sheykh me kakeso in dafa maka".
A hankali yace.
"Ummi bani nono mai sanyi da zuma, insha ya isa".
Da sauri ta juya ta nufi kitchen, Jim kaɗan kuwa ta fito da cup a cike da haɗin mai sanyi.
Amsa yayi tare da riƙewa.
Yana kallon Hibba da ke cewa.
"Hamma Jabeer Aunty Aysha ma bata da lfy, yau babu abinda taci tun safe".
Uhum yace tare da kai kofin burgeggen kinɗirmo da zuma a madadin sugar bakinshi.
Zuƙa ya ɗan yi, a hankali ya lumshe idonshi jin sanyin nonon ya ratsashi.
yaji zafin da yakeji cikin jikinsa yana raguwa.
Hakane yasa yaci gaba da sha, idonshi ya ɗan ɗago ya kalli Ummi jin tana cewa.
"Sheykh Aysha fa babu lfy sosai.
Dama kai nake jira, ka dawo ka dubata".
Maida idonshi yayi bisa kofin
Yayi kamar baijiba, saida ya shanye madarar ne, ya ɗan miƙe tsaye cikin sanyi yace.
"Affan je ka ɗauko Dr Kubra tazo ta dubata".
Da sauri Affan yace.
To kana ya miƙe ya fita.
Shi kuwa Sheykh a hankali jiki a mace ya wuce Side ɗinsa.
Cikin jan ƙafa ya ƙarasa bedroom ɗinsa.
Kai tsaye kan gado ya faɗa sabida har yanzu allurar baccin tana ɗan fizgarshi ko dan haka ya haɗu da rashin lafiyar ne.
Ko gariyarsa bai cireba ya kwanta.
Yana konciya kuma ya fara tasbihi kamar koda yaushe.
Lokaci ɗaya daddaɗan bacci ya kwasheshi.
A falon kuwa bayan ya shiga ne.
Aunty Juwairiyya ta miƙe ta tare da cewa.
"Ummi bari in koma na bar yara su kaɗai".
Ta miƙewa Ya Jafar yabi bayanta.
Jalal kuwa da Jamil Dinning area suka nufa dan cin abincin dare.
Ba jimawa Affan ya dawo.
Da wata Kekkyawar mata yar duma-duma mai sakin fuska.
Bayan sun gaisa da Ummi ne Hibba ta gaidata kana suka wuce ɗakin Aysha.
Bisa jagorancin Ummi.
Da sauri ta ɗan yaye borgon