Showing 99001 words to 102000 words out of 180927 words
Chapter 34 - GARKUWA Book 1 Original Pdf By Garkuwar Fulani.txt
Baba Basiru Baba Nasiru dama duk sauran manyan masarautarsu.
Da sauri ya juyo ya kalli Lamiɗo da nufin yin tambaya sai kuma yayi shiru ganin Lamiɗo na mgna da Galadima da kuma wani amintaccen bafadanshi.
Tsaki ya ɗan ja tare da cewa.
"To wannan ƙus-ƙus du na menene, ku duk abinda babu kyau kuna jin daɗin yinshi."
Shiru yayi ganin motoci sama da talatin ne suka shigo Rugar.
Kana duk manyan mutanene kuma sun fito cikin motocin sun nufo inda suke zazzaune.
Wanda tuni Arɗo Bani yasa an kuma firfito da taburman cikin masallacin su.
Kana yasa an fito da sauran dardumai da kilisai anzo an shimfiɗa.
Suna isowa sarki Jalaluddin da Abba suka dafa kafaɗun Jabeer tare da sanya mushi al'barka kana suka zauna gefenshi ya zama sun sakashi a tsakiya.
Kusa dashi Abbanshi ya zauna,
Kana Jalaluddin ya zauna kusa da Abban.
Lamiɗo kuwa na kusa dashi shida Galadima.
Da sauri Haroon dasu Jamil kan sukabi bayan fadawan da suka nufi motocin da sukazo yanzu da ido.
Shi kuwa Sheykh Jabeer ido kawai ya zubawa wayarshi.
Yana wasu aiyukanshi a ciki.
A hankali ya ɗago kanshi ya kalli Haroon dake taɓashi.
Da yatsa Haroon ya nuna mishi gabanshi.
A hankali ya juya kanshi ya kalli inda Haroon ke nuna mishi.
Fadawane da hadimansu keta jido katon-katon ɗin sweet ga kuma fufun goro shima sunata jidowa suna ajiyewa a gabansu Arɗo Bani.
Cikin mamaki ya kalli Lamiɗo tare da cewa.
"Me za'ayi da wannan kuma? Kamar wanda suka zo ɗaurin aure!".
Da sauri Galadima yace.
"Eh ashe ka gane ai ɗaurkin auren ne".
Cikin mamaki Haroon yace.
"Aure kuma? To auren waye?".
Lamiɗo ne ya kalleshi cikin isa yace.
"Auren Muhammad Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa!".
Wani irin yunƙura Jabeer yayi zai miƙe, cikin tsananin haɗe fuskarnan tamkar zatayi aman jini ya kalli Lamiɗo tare da yunƙurin miƙewa yace.
"Zancen banza kenan a wurin banza, ai wlh baka isaba, wlh Lamiɗo kafa kiyayeni kanafa shigemin rayuwa, ka fita hanyata ka fice min a ido kar in rintsa da kai fa kadafa ka bari in juyo kanka".
Ya ƙarishe mgnar da miƙewa tsaye. Sai kuma ya juyo jin an kamo hannunshi an medashi zaune, a fusace ya kalli inda yaji anja hannun nashi ganin Sarki Jalaluddin ne ya riƙo hannunshi ya sashi kuma tsuke fuskarsa cikin faɗa yace.
"Jadda sakarmin hannu bana so! Bana son abinda kuke min da rayuwata, wlh gwarama kun tashi mun tafi, dan babu ruwana dan Ni bazanyi aure ba".
Da sauri ya juyo jin muryar Abbanshi yana cewa.
"...!
Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, sai in saki cikin Normal group wanda a kwana talatin za'a gama littafin. Ko kuma kiyi min TRANSFER ɗin dubu ɗaya ta asusuna na Jaiz 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276. Sai in saki a Special Group inda cikin mako biyu kacal za'a gama Part 1 da izinin ubangiji.
By
*GARKUWAR FULANI*
*GARKUWAR FULANI*"Muhammad!". Ya kira babban sunanshi tare da jawo hannunshi, ya zaunar dashi bisa kujerar da ya tashi a kai.
Cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoron abinda suke shirin aikatawa, ya kalli Mahaifin nashi, kana ya juyo ya kalli Lamiɗo da Galadima gefen damanshi ya juyo ya kalli Jadda cikin rauni ya kuma kalli mahaifin nashi tare dayin ƙasa da murya yace.
"Abba kada ka bari su ɗaura auren nan, dan Allah kace musu su bari, kada su ɗaura".
Ya ƙarishe mgnar cikin tashin hankali da ɓacin rai da tarin rauni a fuskarshi.
Cikin zuba mishi ido Abbanshi yace.
"Meyasa? Sabida me za'a bari!? Meyasa baka so!?."
Kanshi ya jujjuya tare da haɗe hannayenshi wuri ɗaya ya fuskanci mahaifin nashi cikin sanyi yace.
"Ni dai bana so. Abba dan Allah kada ka bari suyi.
Bana son garin nan bare mutanen cikinsa, kuma bawai haka banza naƙi auren nan ba, Abba inada matsala, Please Abba na tuba dan Allah kace su bari. In yaso a ɗaura da wani amman banda ni kam".
Lamiɗo ne ya kamo hannunshi cikin isa yace.
"Auren' nanfa, kamar ma an ɗaurashi an gama, domin babu wani abu ko wani mahaluƙin da ya isa ya hana wannan ɗaurin auren, gwarama ka kontar da hankalinka. Tunda ka iya jure bulalin aiko tabbas dole ka aureta, babu shakka dole sai ka aureta, bazai yiwu a dakeka a kantaba sannan ka barmusu itaba."
Cikin jin haushin wannan fitinenne tsohon ya kwace hannunshi daya riƙe tare da cewa.
"Haka kenan kullum zanyi ta wahala a bisa wasu dalilanka da bana addiniba, me ruwanka da dukan da akayi min, ba dai kai-kasa dole aka dakeni ba".
A hankali Galadima yace.
"Eh da kuma bakayi kukaba, baka guduba, yau kuma kasa yayi kuka ya gudu ai dole ka aure matar da a kanta aka haɗaku gasar, tunda mu dai ba sakarkaru bane, bare ace bamu san dokar gasar Shaɗi ba."
Wayyo Jabeer ji yakeyi tamkar ya mammake tsoffin nan dan tarin baƙin ciki. Rai a ɓace yace.
"Bakufa fini sanin kainaba, tunda nace muku bana son aure, bazan kuma yi aureba, to ku barni mana, rayuwata ce ko taku, ko dole ne duk wata matsalata da sirrin rayuwata sai kun sani! Nace muku bana son wannan garin na tsani garin bana son mutanen garin karankatab ɗinsu.
Bani babu su, in kuma kukayi gangancin cusa min wata muguwar yarsu, tabbas! lallai ilaihin! A kanta zan rama sauran bulali ashirin da wancan ƙaton gardin ya min, hamsin, ni a talatin ya gudu".
Kai Jadda ya girgiza tare da cewa.
"Ka rama mana kaida matarka, ka rama ka kuma jinyace ta".
Shiru sukayi sabida jin muryar Dr Aliyu da kuma Galadima da Arɗo Bani da Bappa suna tabbar wa juna lfyar yaransu, cikin Mamaki ya kalli Galadima dake cewa.
"Muma ɗanmu lfyarshi lau, Namiji ne".
Cikin sanyi Jabeer yace.
"Ji maƙaryacin tsoho, wai lafiyata lau, ko yaushe ya zama likita ya gwadani. Harda wani karkacewa yana zuba ƙarya ko farin gemunshi bai martaba-ba".
Jin Abbanshi ya daki gefen ƙafarshi ne yasashi yin shiru.
A nan a gabanshi a gaban mahaifinshi. A gaban dubban al'ummar fulani makiyaya daketa tsastsafo tako wani sashi na duniya, a kuma gaban Lamiɗo da tawagarsa hakama Jalaluddin da tawagarsa.
Aka ɗaura auren Muhammad Jabeer da Aysha. Bisa koyarwan addinin Musulunci.
Sosai su Jalal, Jamil, Hashim, Haroon, Sulaiman. Sukayi mamakin wannan aure na ba zata. Ba zato ba tsammani.
Bayan an gama dai-dai-ta komai an ɗaura auren ne, kuma.
Lamiɗo ya kalli Arɗo Bani, cikin girma da ƙasaita yace.
"Yanzu zai tafi da matarshi."
Cikin sanyi da al'hini Bappa yace.
"Allah rene yanzu kuma!?".
Galadima ne ya amshi zancen da cewa.
"Haƙƙun yanzu zamu tafi da ita!".
Arɗo Bani ne yayi murmushi mai cike da jin daɗin yace.
"To ba laifi ai, muje a fito muku da ita".
Shi kuwa Bappa ido ya zuba musu.
Dan shi a zatonshi ba yau zasu tafin mishi da Shatunsa ba.
Nan duk suka ɗunguzuma, suka shiga motocin. suka nufi ƙofar gidansu Shatu.
Ya Salmanu kuwa, tuni ya shiga cikin gidan su.
Ya shiga ɗakinshi yana ta kuka kamar yaro. Bai tsamci haka abin kan iya juyewa ba, Ba'ana ya rasa Shatu shima ya rasata.
Suna isa ƙofar gidansu, duk motocin suka tsaya.
A hankali Bappa da Arɗo Bani suka kutsa kansu cikin gidan.
A tsakar gidan suka samu.
Shatu na zaune dan dawowarta kenan, hannunta tasa ta tallabe haɓarta ta zubawa su Junainah ido, shigowarta gida kenan daga dawowarta.
Cikin Ɓadamaya su Binto suka shigo gidan a guje suna ce mata wai an ɗaura aurenta da ɗan sarkin da akayi gasar Shaɗi dashi.
Jin hakane yasata yin murmushi tare sauƙe dogon ajiyan zuciya na gajiyar tafiyar da tayi, ido ta lumshe tare da cewa.
"Auren kuma wasane, da zai zama an aura min wani wanda ba'a san halinshi ba, ko ƴar tsana ma ai ba'a aurar da ita a hakaba bare ni".
Ta faɗi mgnar cikin fargaban ganin yadda suketa rantse mata. Duk da bawai ta yarda da zancensu bane. Junainah kuwa dariya takeyi tare da ɗan tsalle-tsallenta tana cewa.
"Yeeh Auren Addana yazo, zanyi gayyan fati muyi gaɗa".
Cikin zuba musu ido, ta zauna gefen, Ummey dake ta Binta da ido, cikin sanyi tace.
"Ummey na dawo! Ya jikin naki!?."
Da sauri ta gyara zamanta tare da zubawa Ummey ido, cikin mamaki take kallonta ganin idanunta nata zubda hawaye ne, yasata cikin ruɗani da tashin hankali da fargabar abinda ke shirin faruwa da ita da rayuwarta.
A kiɗime tace.
"Ummey meya sameki? meya saki kuka? Jikin ne yake miki ciwo?."
Sam Ummey bata iya mgna ba, sai kukan da takeyi,
hakanne yasa zuciyar Shatu karaya, cikin rauni wasu hawaye masu ɗumi suka fara tsiyayo mata.
Hakan ya ƙara ingiza kukan Ummey hakama,
Junainah sai ta raɓa gefensu tayi, zurui a zatonta aure abun daɗi ne ba kukaba to gashi taga su kuma kuka sukeyi.
Sosai Shatu takeyin kuka mai tarin dalilai.
Suna isa Bappa yasa hannunshi ya kamo nata, cikin sanyi yace.
"Taso kizo".
Ido cike da hawaye ta mike tsaye bisa umarnin Bappa.
Shi kuwa Bappa cikin sanyi ya kalli Ummey da Junainah yace.
"Kada kuyi kuka, kuyi mata addu'o'in samun nasara a cikin wannan al'amari, muyi mata fatan aurenta ya zamo haske ne a rayuwarsa shi mijin da ahlinshin baki daya, fatanmu aurenta ya zamo ƙungiyar da zata jawo gskya cikin raminda aka binneta ya fito da ita kowa ya gani."
Shiru Ummey tayi sai hawayen da suke kwaranya.
Hakama Shatu hawayenta wani na korar wani.
Ita kuwa Junainah faɗawa jikin Ummey tayi sukaci gaba da zubda hawaye.
Bappa kuwa hannunta yaja suka juya suna nufi hanyar fita.
Da kayanta na ɗazu wanda taje Genaral Hospital Ɓadawaya dasu, hatta hand bag ɗinta na rataye a kafaɗarta wayarta na ciki.
Cikin mamaki take bin bayan Bappa, tare da yin taku a hankali tana bin bayanshi yadda yake jan hannunta.
Arɗo Bani kuma na biye dasu a baya.
Suna fitowa ƙofar gidan, Haroon da Jalal suka juyo suka kalli juna,
Cikin tarin mamakin ganin kamar yarinyar ɗazuce.
Shi kuwa Sheykh Jabeer yana zaune cikin motar, shi ɗaya dan duk sun fita.
Da sauri ya dafe saitin ƙahon zuciyarshi jin ta tsananta bugawar da yakeyi.
A hankali ya maida bayanshi ya jingina da sit ɗin tare da rufe idonshi.
Yana mai jin sanyin A/C na ratsa mishi jiki da jini da zuciya.
Amman duk da haka zuface ke tsastsafo mishi a jikinshi sabida bugun da Zuciyarshi keyi ya wuce misalin.
A hankali ya juya kanshi ya kalli gefen hagunshi inda yaga motar Jadda da kuma Dr Aliyu ne da Barrister Kamal ke jere a wurin.
Bappa kuwa a hankali yake taku, yana nufo inda Lamiɗo ke tsaye Dogari na riƙe masa da laima, Ɗanzagi da fadawa na zube a kasa.
Ita kuwa Shatu cikin rawan jikin jin idanun mutane na yawo a jikinta dan ma Allah yasa akwai niƙab a fuskarta.
Take bin bayanshi. Shi kuwa Sheykh Jabeer yadda suke ƙara matso inda yake haka bugun zuciyarshin keta tsananta.
Suna isa gaban Lamiɗo Bappa ya miƙawa Lamiɗo hannunta cikin sanyi da nitsuwa da taushin lafazi yace.
"Allah rene, ga Aishatu matar Muhammad Jabeer.
Gata amana bisa jagoranci ka, nasabarka da yardarka.
Da kamala da nitsuwa da na gani a fuskar yaron yasa naji ƙarfin guiwar baku aurenta.
Ba tare da fargaba ba, yanzu kaine kaka kuma jagora a gareta".
Sai ya kuma nuna Barrister Kamal da shima yana cikin wakilai, shi a zatonsa ma shine mahaifin Jabeer cikin sanyi yace.
"Kai kuma kaine matsayin mahaifi a gareta ku zame mata dangin ta data rasa, naso ace da mata a masu ɗaukanta, dan in danƙa amanarta a hannun macce yar uwarta.
Amman ba komai, na baku amanarta dan Allah kada a cutar da ita, domin nima ta kasance amanace a uwurina, domin ƴaƴan mu da muka haifama amanace Allah ya bamu kuma abun kiyayewa, bare kuma ɗiya irin Shatu ɗiyace da take da nasabobi masu yawa a gareni".
Cikin gamsuwa Lamiɗo yasa hannunshi ya amshi hannunta daketa karkarwa, tuni niƙab ɗin fuskarta ya jiƙe jilak da ruwan hawaye.
Cikin Dattaku Lamiɗo yace.
"In sha Allah zan kula da dukkan lamuranta tamkar yadda nake kula dashi Jabeer, kuma kada ka damu akwai masu meye mata gurbin uwa ƙanwa yaya dama duk danginta a cikin masarauta Joɗo, baƙoma baya kukan maraici bare kuma, matar sashin jinina".
Cikin sanyi da wasu hawaye Bappa yace.
"To Ngd matuƙa".
Arɗo Bani ne ya dafashi tare da cewa.
"Ka sanya mata al'barka a cikin aurenta ba zubda hawaye ba."
Sosai Haroon ya zuba mata ido.
Shi kuwa Sheykh Jabeer da mamaki yake kallon Bappa dake zubda hawaye.
A hankali su Bappa suka ɗan ja da baya.
Shi kuwa Lamiɗo ya juya ya nufi motar riƙe da hannunta.
Haroon ne yayi saurin buɗe musu marfin motar, suka nufoshi gadan-gadan.
Jalal kuwa ido ya zubawa yatsun hannunta da Lamiɗo ke riƙe dashi.
Shi kuwa Jabeer idonshi ya rufe da ƙarfi. Sai kuma ya buɗesu, dai-dai lokacin Lamiɗo ya kawota bakin ƙofar motar tare da cewa.
"Mamana kiyi bismillah ki shiga da ƙafar dama".
Cikin shessheƙan kuka ta gyaɗa kai tare da yin bisimilla kana ta ɗan sunkuyo, sai kuma kukan ya kubce mata.
Shi kuwa Jabeer da sauri ya buɗe marfin motar ta gefen hagunshi. Kamar gilmawar walƙiya ya fita cikin motar.
Dai-dai lokacin da Shatu tasa ƙafarta ciki.
da sauri yasa hannunshi ya buɗe motar Jadda tare da shigewa ciki yaja marfin ya rufe sabida ji yayi zuciyarshi zatayi bindiga, wani irin dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai ƙarfi.
Ita kuwa Shatu, a hankali ta shiga ta zauna, don batama lura da shi bane tabbas dai taga mutun ya fita cikin motar.
Tana shiga Haroon ya maida marfin ya rufe
Shida Lamiɗo suka koma sit ɗin bayan wannan sabida su a zatonsu Jabeer na ciki.
Ganin Lamiɗo ya shigane yasa duk kowa ya shiga motarshi.
Hakama Jadda ya shiga ya zauna hankalinshi na woje.
Sai da akaja motocin suka fara tafiya ne, ya juyo da sauri jin Jabeer na jan wani ja'irin tsaki mai tare da ajiyan zuciya.
Cikin mamaki Jadda yace.
"Haaahh kai kuma Meya kawoka nan? Yaushe ka shigo min mota!?".
Bai kula Jadda ba, asalima yi yayi tamkar bai jishiba.
Haroon kuwa cikin dariya ya ɗan bugi sit ɗin da yake zaton yana wurin cikin juya harcen Larabci yace.
"Masha ALLAH, gasar Shaɗi tayi mana rana mun rabaka da gwauranci".
Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Haroon yace.
"Saura kai". Murmushi yayi tare da cewa.
"Ni ai nan kusa za'ayi".
Jin shirune, yasa Haroon yayi shiru,
Azotonshi ya ƙin mgna da shariyar ne suka zowa Jabeer bare, yasan yanzu a cike yake.
Su Jalal kuwa kab da al'hini suke tafeyi.
Jadda kuwa yayi iya mgnarshi yayi shiru ganin bai kulashi ba.
A haka suka isa cikin Masarauta Joɗo.
Suna isa kuwa Jabeer ya fito ya nufi Side ɗinsa, fitowarsa cikin motar Jadda ne yayi matuƙar bawa Haroon da Lamiɗo mamaki.
Haroon kuwa bayanshi yabi da sauri.
Suna shiga Side ɗinsa kuwa suka samu babu kowa.
Suna gama tsayuwa Sallama ya nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu bisa umarni Lamiɗo.
Yana shiga a babban Falon ya samu. Umaymah, Ummi, Aunty Juwairiyya, Hibba, Adda Rumana wacce take yayarsu Jabeer yar farin Abba kenan, sai mai bin mata Rumaisa.
Kana sai Gimbiya Aminatu dake tsakiyarsu, sai hadimanta.
Koda ya sanar musu, sun iso.
Kusan duk a tare suka miƙe sai Gimbiya Aminatu ce bata tashiba da hadimanta.
Su kuwa da sauri suka nufi woje, Umaymah ce gaba sai Aunty Juwairiyya dake biye da ita a baya riƙe da wani tire wanda samanshi ke ɗauke da al'kyabbar irin tasu ta matan masarauta da kuma wasu sauran tarkace.
Suna fitowa motar na isowa har bakin wurin. Da sauri suka nufi jikin motar.
Ita kuwa Zuwa yanzu ta tsagaita da kukanta, sabida ababen da take gani a cikin masarautar ya shallake tunanin mai tunani,
gaba ɗaya jikinta tsuma yakeyi, sabida idonta na gane mata ababe na ban tsoro.
Cikin ranta take mgnar zuci.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, wannan wanne irin gidane? Me yake faruwa da mutanen masarautar? Sunko san gskyar junansu?".
Da sauri ta rumtse idanunta sabida wasu irin hayaƙi da take gani yana tashi tako ina na gidan yayiwa gidan rumfa gaba ɗayansa.
A da sauri ta buɗe idonta jin an kamo tafin hannunta,
Umaymah kuwa cikin tsantsar jin daɗin da farin ciki maras misaltuwa tace.
"Marhababiki ya binti". Wani irin azabebben tsinkewar zuciya da firgici da razanine ya daki zuciyar Shatu a lokaci ɗaya.
Da sauri ta ƙara ware idanunta, dan son kallon matar da take jawota tare da cewa.
"Kiyi bismillah ki fito da ƙafar dama, ki riƙe hannuna da kyau ɗiyata, ki kalleni nan nice jagorarki ki taka ƙafarki a inda zakiga na taka tawa".
Ido ta zuba mata, tare da fitowa a hankali.
Tana fitowa bakin ƙofar Umaymah tasa hannu ta amshi al'kyabbar da Aunty Juwairiyya take miƙa mata.
Kangeta tayi kana tasa mata al'kyabbar, sannan ta gyara mata rufuwarshi da kyau ta rufa mata hularshi. Yadda sam mutun bazai samu damar ganinta ba.
Ga niƙab ga kuma hular al'kyabbar da lu'ulu'u danke reto a fuskarta.
Da sauri Aunty Juwairiyya ta matso tare da cewa.
"Marhabin yar uwarta, Alhamdulillah yau kam na samu yar uwa".
Adda Rumana ce ta matso kusa da ita tare da yin mgna da fillanci tace.
"Sannu da zuwa Masarautar Joɗa ƙanwata".
Adda Rumaisa kuwa murmushi yaketayi tare da matsowa, haka suka sata a tsakiya.
Jakadiyarsu kuwa sai bin takun ƙafar Shatu takeyin da ido.
A haka suka zagayeta, kana hadimai suka mara musu baya.
A haka suka isa babban falon Gimbiya Aminatu.
Suna isa Umaymah ta kaita har gabanta ta ajiyeta,
Cikin tsantsar jin daɗi tace.
"Alhamdulillah Gimbiya yau dai ga sabuwar Gimbiya dan yanzu itace amarya ba keba".
Cikin dariyar jin daɗi Gimbiya Aminatu tasa hannu ta kamo hannun Shatu da Umaymah ke miƙa mata tare da cewa.
"Kishiya ban haushi, ta isa ta zama Gimbiya zakisa yanzu in korata woje".
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Yayinda tuni hadimai mata suketa jere ababen maƙulashe a gaban Shatu.
Danginsu, Zuma, Madarar shanu, Da ƴaƴan itatuwa masu sanyi.
Ita dai Shatu ƙasa tayi da kanta,
tana jin fargaba da kuma tsoron wannan bahagon gidan data shigo.
Su kuwa nan sukayi ta mata hidima da nuna mata so.
Ganin magriba ta ƙara to ne yasa,
Umaymah ta jawo hannunta ta kaita wani ɗaki dake nan kusa dana Gimbiya Aminatu.
Tare da cewa.
"Yauwa ɗiyata kiyi salla. Za'a kawo miki abinci, kada kici komai sai nazo".
Cikin sanyi ta gyaɗa mata kai.
Ita kuwa Umaymah hannu tasa ta fara zare mata al'kyabbar, koda ta cire mata shi, cikin kula tace.
"Cire niƙab ɗin, babu mai shigowa nan yanzu sai nida Gimbiya Aminatu da Juwairiyya sai Jakadiyarsu".
A