Showing 135001 words to 138000 words out of 180927 words

Chapter 46 - GARKUWA Book 1 Original Pdf By Garkuwar Fulani.txt

28 Aug 2025

1846

aikin sahur.
Cikin kula Ummi ta kalleta tare da cewa.
"Ɗauko kwanu kan nashi".
Kanta ta ɗan juyo ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ai bai dawo yaci ba ko?".
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Baya cin ƙosai, kuma kinga doyan ma jiya baiciba, ya gaji dasu ne, ki ɗauko a juyewa su Saratu shi ki ɗan haɗa mishi wani abu kafin ya dawo".
Cikin ɗan kauda kai tace.
"Ummi ai ƙoshi yake shiyasa bazai ciba, a barshi kawai in yaji yunwar yacima wani bai saniba, ai yunwa ba Umaymah bace ko ke bare zaku lallaɓashi".
Dariya Ummi tayi kana kuma ta haɗe fuska tare da cewa.
"Je kiyi abinda nace ko".
To tace ganin kamar ran Ummi ya ɓaci.

Bayan ta dawo da kwanukan ne,
Suka bawa Saratu ta juye, kana ta harhaɗa wonke-wonken ta fara.

Ita kuwa Shatu cikin yin miƙa tace.
"Ummi me zan dafa mishin?".
Juyawa tayi tana haura wurin da Fridge yake tare da ce mata.
"Duk abinda kika iya kika san ba mai nauyi bane".

Kanta ta gyaɗa tare da cewa.
"To".
Cikin ranta tace.
"Bari inyi Special Arish, in yaga dama yaci in yaso ya bari, mutun sai zaɓe-zaɓe kamar mai ciki.
Dankali ta ɗan ɗebo da Nama, kwai, tumatur, kabeji, Bama, maggi, tafarnuwa man gyaɗa, komai dai dai-dai misalin yadda zata buƙata duk ta ajiyesu kusa da ita.

Fere dankalin tayi ba tare da ta daddatsashi ba. Ta wonƙeshi fes kana tasa a ƴar tukunya tare da tarfa gishiri da ruwa dai-dai misali, sannan ta tafasashi.
Kwan ta ɗauka ta fasa ta kaɗashi da kyau tare dasa yankekken al'basa da Curry da maggi da tafarnuwa ɗan kaɗan.

Ganin dankalin yayine ta juyeshi a ɗan kondo ta tsaneshi.
Tare da ɗan barinshi yasha iska, kaɗan.
Kana ta ɗaura Naman da maggi da gishiri da Curry da tafarnuwa da al'basa. bisa wata a ɗan tukunta.
Sannan ɗaura man ta ɗauki dankalin ta tsomawa cikin kwan tana soyashi, saida ta gama ta ajiyeshi gefe.
kafin nan naman kuma yayi lugub yayi laushin.
saida ruwan ya kusa ƙarewa sai ta ƙara wata al'basar da tumatur suka nuna tare sannan ta kwashesu.
Kabejin ta yayyanka ƙanana sannan ta ɗauki dafaffan kwai ta yayyanka shi da ɗan girma.
Kana tasa Maggi da al'basa da Bama ta gauraya kana
Ummi ta miƙo mata ɗan ƙaramin Foodflaks alamun ta amsa ta saka.
Kanta ta jujjuya tare da cewa.
"Bari in sa mishi a plate kawai tunda ya dawo".
Da mamaki Ummi ta kalleta tare da cewa
"Yaushe ya dawo?"
Plate ta ɗauko tare da cewa.
"Tun ɗazu".
Da sauri ta sunkuyar da kanta ganin kamar Ummi na mata kallon Mamaki da tuhuma.
Ita kuwa Ummi cikin Binta da ido tace,
Ya akayi kika san ya dawo".
Kai ta rausayar tare daci gaba da aikin kamar bataji Ummi ba.
Plate ɗin ta ajiyeta, ta zuba Arish ɗin gefe kana tasa haɗin naman gefe, ta kuma zuba na Kabejin shima gefe.
Ta shiryashi yayi kyau sosai.
Ɗaya plate ɗin ta kife kanshi.
Kana tasa spoon da Fork a cikin tray'n data ajiye plate ɗin.
Ɗan madaidaicin flaks ɗin coffee ta ajiye gefe, kana tasa cup da tea spoon a ciki.
Sannan turashi gefe.
Zuwa lokacin kuma tuni Ummi da Saratu su gama aikin sahur ɗin har Saratu ta tafi.
Sauran ta sako a wani plate ɗin tare da cewa Ummu gashi.
Amsa Ummi tayi tare da cewa.
"Ɗauki ki kai mishi to".
To tace tare da ɗaukan tray'n ta fita.

A tsaye ta sameshi cikin wani tattausan jallabiya da alamun wonka ya fito,
Sai wani irin masifeffen ƙamshi yakeyi.

Cikin nitsuwa ta wuce ta bayanshi, inda yake tsaye yana kunna Tv.

Bisa santa table ɗin glass mai garai-garai dake tsakiyar falon ta ajiye mishi.
Kana ta juya a hankali ta fita.

Kai tsaye ɗakinta ta wuce, nan ta samu Hibba tuni tayi bacci.
Wonka tayi da ruwan ɗumi tare da shafa mai kana tasa wata tattausar rigar bacci gajera iya karta guiwa.
Hibaji ta zura a jikinta kana ta haura gado ta konta tare da jawo blanket ta duƙunƙune a ciki.
Sabida ita bata son sanyi, shiyasa takesa ƙaton hijabi kana ta shiga borgo.
Badon Hibba Bama dake masifar son sanyi da kashe AC'n zatayi.


Ƙarfe ɗaya dai-dai ta tashi bacci al'wala tayi kana tai ta nafila hakama Ummi.
Sheykh Jabeer kuwa tuni ya tashi shima.
Ya kira su Jalal ma a waya ya tashesu.

Ƙarfe huɗu da rabi dai-dai ta isa falonshi da tray'n abincin sahur ɗin shi.
Ta ajiye ta juyo kenan shi kuma yana fitowa falonshi.
Tazo tsakiyar falon kenan tana tafiyarta a hankali ba zato ba tsammani taji daram-dam ƙaran bindigar da kullum da asuba sai an saketa sau biyu, ta kuma kasa sabawa dashi bare ta daina tsoronshi.
Wani irin tsalle da zabura tayi tare da ficewa a guje tana cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Bayanta yabi da kallo tare da taɓe baki kana ya nufi Dinnin area.

Washe gari da safe yau Jumma'a kuma, yaune azumi na shida.

Bayan sun fitone, Ummi ta kalleta cikin dariya dan tuno yadda ta fito falon Sheykh Jabeer a guje da asuba, tana jan Allah ya isanmata ana tsinka mata zuciya,
Cikin murmushin tace.
"Ummi dariyar me kikeyi ne?".
Cikin gimtse dariyar tace.
"A babu, yauwa tashi muje ɗazu Gimbiya Aminatu ta aiko, wai tayi kewarki kwana biyu azumi ya ɓoyeki bakije ba".
Cikin murmushin tace to muje Ummi".
Ta ƙarishe mgnar tanayin gaba Hibba na biye da ita a baya.
Cikin sauri Ummi tace.
"A haka zaki fita ba al'kyabba".
Kai ta ɗan dafe tare da cewa.
"Wayyo Allah na, Allah kuwa ni nauyi sukemin wannan tsarabe-tsaraben wuya gareshi".
Murmushi Ummi tai tare da miƙewa ta ɗauko al'kyabbar.
Tazo tasa kana suka fita.

Da Side ɗin Hajia Mama suka fara,
A falo suka samesu.
Cikin fuskar ba yabo ba fallasa Hajia Mama ta amsa gaisuwar Shatu.
Batool kuwa sai auna mata harara takeyi.
Hira suka ɗan taɓa kana suka fito.
Har sun fito Shatu ta ɗan kalli Ummi cikin sanyi tace.
"Ummi jirani anan bari inje in isar da saƙon gaisuwar Ummey na wurin Hajia Mama".
Da Mamaki Ummi tace to kana ta juya ta nufi ciki, ganin Hibba za biyota ne tace.
"A a jirani ina zuwa".
Haka suka tsaya suna jiranta.

A hankali ta turo ƙafar falon.
Da sauri Hajia Mama ta zuba mata ido fuska cike da tsana.
Batool kuwa binta da ido takeyi ganin wani irin takun isa da ƙasaitar da takeyi.
Kujerar dake fuskantar wacce Hajia Mama ke zaune a kai ta zauna.
Ƙafarta ɗaya ta ɗaura kan ɗaya.
Kana ta jingina da kujerar, cikin tsare Hajia Mama da ido tace.
"Uhummmm kin sanni sarai, kar tasan karne, duk motsinki a tsakiyar tafin hannuna kike, dan haka gwara kiyiwa kanki gada ki fita harka da rayuwar mijina! Da ƙannenshi da wanshi. In kuwa kikaƙi zakisha mamakin Shatu."
Tana faɗin haka ta miƙe, tana kallon Batool da tun randa akace Shatu tazo ta bawa Hajia Mama haƙuri da ta shigo tayi wasu kalaman ya ɗaurewa Batool kai ta kasa tantance tsakanin aya da tsakuwa, shiyasa batayi gigin yin mgn ba, sabida tuno abinda Shatu tace mata a ranar cewa.
"Mijina kike so ko, to kizo in ya amince ya kalli inda kike na daƙiƙi biyu rak zan sashi ya aureki".
Da sauri Batool ta dawo daga duniyar tunanin da take jin ƙaran rufe ƙofar da Shatu tayi.

Ido ta maida kan Hajia Mama dake gurnani kamar macijiya.


Jim kaɗan ta fito.
Cike da son gano wani abu Ummi ke binta da ido, amman ta kasa gano komai domin Shatu ta iye takunta, ta fito kamar ba itaba gaba tayi.

Kana suka nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu.
Suna shiga ta miƙowa Shatu da Hibba hannu kusa da ita ta ajiyesu.
Bayan sun gaisane ta kallesu tare da cewa.
"Azumi ya boyeku da yake ku ragwagene".
Murmushi sukayi tare da cewa.
"Kai Gimbiya jiya nefa kawai bamu zoba".
Cikin kula Lamiɗo dake shigowa yanzu zai sabunta al'wala zai wuce masallaci yace.
"Shatu matar malam bauɗeɗɗe".
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kai.
Hibba ce tace.
"Sai na gaya mishi".
Dariya sukayi kana suka sallamesu suka tafi ganin lokacin sallan yayi.
Har sunje bakin ƙofa Gimbiya Aminatu tace.
"Yauwa Jakadiya kayan miyanku da saura ko ya ƙare?".
Cikin rusunawa tace.
"A'a da saura sosaima".
Kai ta gyaɗa kana suka tafi.
A hanyarsu ba komawane Shatu tace.
"Ummi wanne kayan miyan ne?".
Cikin sanyi tace.
"To ba kince bakya son na Hajia Mama ba, shine ita kuma Gimbiya Aminatu ta haɗo miki komai yanzu dasu muke amfani ai".
Cikin gamsuwa tace.
"To wancan ɗinfa ya akayi dashi?".
"Umaymah ta tafi dashi duka".
Hibba ta faɗa mata.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Ba matsala".

Nan suka tafi suna salla suka shiga kitchen yau harda Hibba.


Sannu-sannu dai bata hana zuwa sai dai a daɗe ba'a jeba.

Yau an cika azumi goma. Gobe za'a shiga goma na wuya, an gama na marmari.


Yau kuma makara Shatu tayi.
Ganin har su Jalal sun zone yasa Ummi ta nufi ɗakinsu.
Ai kuwa kan gado ta hangosu.
Tadasu tayi kana ta fito.
Tana cewa.
"Shatu kiyi sauri kizo ki kaiwa Sheykh nashi".
Kusan a tare suka diro ƙasa.
Brush kawai sukayi suka fito.
Da ƙaton hijabin ta fito.
Tana zuwa Dinning area Ummi ta miƙa mata tray'n abincin nasa.

Amsa tayi ya juya ta nufi falonshi.

Tsaye ta sameshi gaban show glass ɗin dake gefen Fridge ɗinsa dake Dinning area,
Cup ne a hannunshi cike da madarar gongoni da molt a haɗe.
A hankali ta wuceshi kaɗan ta ajiye tray'n.
Kana ta juyo da nufin sauƙowa, taku ɗaya tayi a na biyu ta iso gabanshi kenan.
Aka saki bindigar shaidar huɗu da rabi tayi.
Wani irin zabura tayi tare da af....!



Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, domin shiga Normal group wanda a wata ɗaya za'a, gama Part one. Ko kima kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank, domin samun shiga Special Group wanda a sati biyu cakal za'a gama Part two da izinin ubangiji, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853297.

Ke mai haushi kin turo ɗarinki uku, kinzo kinata haushi, nace ki turo ac no ɗinki in maida miki kuɗinki kin tsaya yimin tumasanci shiyasa nayi Black ɗinki, a rashin Sa'a na haɗa da number ki na goge. Kuma baki Turo ac na na meda miki shi ba. To Alhamdulillah a take a lokacin nayi miki sadaka da ɗarinki uku, ubangijina shine shaidata, banci kuɗinki ba, nasan zakiga PAGE ɗin sabida akwai waɗanda basu san darajar Allah da Manzonsa da iyayensuba, zasu fitar, to kiji ni Shatu na sauƙe nauyin ɗarinki uku.



By
*GARKUWAR FULANI*Cikin tsananin firgita, da tsinkewar zuciya da tsoro, tare da kerman jiki, ta juyo ta fuskanci inda yake tsaye tare da abkawa jikinshi.

Cikin abinda bai gaza one second ba tamkar gilmawar walƙiya ya janye jikinshi ya kauce gefe.
Hakan yasa ta faɗa jikin show glass ta ruggumeshi gam-gam cikin tsuma da karkarwa tare da sa hannunta duka biyu ta riƙe kanta, tana mai cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil, Auzubikalimatillahi ta'ammati minsherri makalaƙa."

Tanayi cikin ɗan ɗaga murya mai baiyana firgicin da take ciki.

Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin masifeffen dariya ne ya taso masa tun daga ƙasan zuciyarshi har zuwa kan lips ɗinshi dole ya taune lip ɗin shi na ƙasa.
Kana sai ya gimtse ya murtuƙe fuska cikin tsare gida yace.
"Karki fasamin abuna!".
Sai lokacin hankalinta ya dawo jikinta.
Janye jikinta tayi daga jikin show glass ɗin da abkawar da tayi kanshi marfinshi ya ɗan tsage.
Nannauyan ajiyan zuciya ta sauƙe da ƙarfi.
Kana ta tura baki sannan ta juya ta fara tafiya tana ƙunƙunin.
"Allah ya isana banzan al'ada a rinƙa razana mutun anasa hanjin cikina na hautsunewa".
Baki ya taɓe kana ya zauna bisa kujerar ya jawo tray'n ya ɗibi abincin tuƙeƙen tuwo ne da miyar kase.

Tana fitowa sukayi sahur ɗin a gaggauce sabida lokacin ya ɗan ƙara to.



Washe garin da rana bayan anyi sallan azahar.
Ya shigo kamar ko yaushe.
A falo ya samu Ummi da Hibba ita kuwa Shatu tana ɗakinta tana karatu so take ta samu izu uku a wunin yau ɗin.
Gefen su ya ratsa kana ya zauna bisa kujerar zamanshi.
Bayan sun mishi sannu da zuwa ne, ya kalli Hibba cikin kula yace.
"Muhibbat ya azumin".
Cikin langwaɓe kai tace.
"Da wuya".
Kanshi ya jinjina kana yace.
"Jeki kira Aunty Juwairiyya".
To tace tare da miƙewa da sauri ta fita.
Shi kuwa wayarshi ya ciro ya kira Jalal dasu Imaran yace suzo su sameshi a falo.

Jim kaɗan duk suka shigo.
Key ya zaro daga al'jihun tattausan jallabiyar dake ƙasan al'kyabbar jikinshi ya miƙa wa Jamil tare da cewa.
"Ɗauko min briefcase a kan Bedside drower'n."
To yace kana ya juya ya tafi.
Shi kuwa Ummi ya kalla tare da cewa.
"Ummi me dame kuke buƙata ne?".
Cikin kulawa tace.
"Akwai komai, sai zam-zam ɗin kane ya ƙare saura baifi gora biyarba".

Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"Ba matsala zai isa".
Lokacin Jamil ya iso. Miƙa mishi jakar yayi, tare da zaunawa gefenshi.
Shi kuwa buɗe jakar yayi.
Murmushi Jamil yayi ganin tana ciƙe maƙil da rafan dubu-dubu sabbi dal-dal.
Rafa huɗu ya miƙawa Jamil hakama Jalal da Imran da Sulaiman.
Sannan ya kallesu tare da cewa.
"Kuje KMC plaza ku zabi kayan sallan.
Sai ya kuma kalli Aunty Juwairiyya yace.
"Aunty Juwairiyya, kuje tare dasu, da Ya Jafar ayi yadda aka saba.
Sannan ku zaɓi abin buƙatar ku."
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"To mu gode, kuma za'ayi yadda kace."
Sai kuma ya kalli Ummi yace.
"Ummi kada ki manta da su Saratu".
Murmushi tayi tare da cewa.
"In Sha Allah babu abinda za'a mance".
Kai ya jinjina kana ya zaro rafan guda biyar ya miƙa mata, sannan ya miƙa wa Aunty Juwairiyya wasu rafofin kana ya bawa Hibba biyu.
Daga nan sukaci gaba da tattaunawarsu.


Washe gari kuwa da safe, suka shirya tsab zasu fita.
Aunty Juwairiyya ta Ummi cikin yin ƙasa da murya tace.
"Ko zan kirawo Shatu mu tafi tare da ita ne?".
Da sauri Ummi tace.
"A a mijinta baice muje da itaba mujata mu tafi. Muje dai mu zaɓo mata duk abinda takeso".
Cikin gamsuwa da hakan tace to.

Hibba kuwa cikin sanyi tace.
"Ayyah Ummi muje da ita".
Fitowar Shatu ne ta samesu a tsaye cikin shirin tafi yasa ta kalli Ummi cikin sauri tace.
"Ummi ina zakuje?".
"KMC plaza".
Ta Bata amsa a taƙaice cikin sanyi tace.
"Nima inzo muje, in samu in fita insha iskan woje".
Jalal ne ya ɗan kalleta tare da cewa.
"Boss ya hana". Ido ta zuba mishi kana ta juya ta kalli Ummi cikin sanyi tace.
"Shike nan Ummi kuje, Allah kiyaye hanya."
Amin Amin sukace har sun juya zasu tafi sai kuma tace.
"Ayyah Ummi dan Allah karku daɗe".
To sukace kana suka fita.


Shiru ta zauna a falon ba kowa hakane yasa ta kunna TV tashar Zee world.
Wani film mai daɗi ta samu sukeyi, sai dai bata san forkonshiba, bisa alamu duk sabone.
Konciya tayi bisa 3 str tana kallo wayarta na hannunta.
Tana mgna da Rafi'a.

A haka bacci yayi awon gaba da ita.

Can Cikin bacci take jin alamun kamar mutun na tsaye a kanta, cikin magagin baccin ta buɗe idonta.
Gabann Tv ta ganshi ya kashe TV kana ya juyo ya kalleta a fizge yace.
"Ba salla sai kallo da bacci".
Jin haka yasa ta miƙe zaune tana gyara mayafin kanta.
Shi kuwa tuni ya wuce Side ɗinsa.

Tana idar da salla ta fito. Nan ta samu Saratu tazo, kitchen Suka shiga suka fara aikin yamman.


Sai gab da la'asar su. Ummi suka dawo da kaya niƙi-niƙi. Nan suka ajiye sukayi salla kana suka shiga kitchen ɗin.

Hibba kuwa yashuwa tayi a ƙasa tana birgima kamar bazata kai magriba.

Sai bayan sallan isha'i sun gama aikin sahur ɗin ne.
Suka dawo falo, nan Ummi ta nuna mata ɗinkunanta da aka bada tun Umaymah bata tafiba.
Sosai taji daɗin kayan da ɗinkunan, lallai tana son dogayen riguna Amman tana son surkawa da Shadda, atampa, leshi, musamman Waɗan nan ɗinkunan sunyi masifar kyau. Ko wanne dai-dai jikinta kamar an gwada ta.
Daga nan kuma suka nuna mata gellulluka da hibai da takalma da saraƙunan da suka zaɓo mata bayan sun zaɓawa kansu.
Sun nuna mata nasun ma.
Ummi ta ƙara da cewa.
"Duk zannuwan da abun ɗinkawan kuma an bawa Kabir telen suma duk cikin KMC suke.
Nanda salla dai komai zaizo dai-dai.
Cikin jin daɗi tace.
"Ngd matuƙa Ummi Allah ya saka da al'khairi".
Amin Amin tace. Kana tace.
"Sheykh zakiyiwa godiya".
Shiru tayi kamar bataji ba.
Hibba kuwa cikin jin daɗi tace.
Aunty Shatu na zaɓa mana wani Shadda lace mai masifar kyau iri ɗaya na ɗauka mana Royal blue and white Golding color. Nace a tsantsara mana dogayen riguna".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Kai kinko kyauta mana".
Daga nan suka tattara tarkacen suka nufi makoncin baccin su.

Zaune take gefen Ummi tana riƙe da waya cikin murmushi tace.
"Allah ko Umaymah munyi kewarki".
Cikin jin daɗi Umaymah tace.
"To ko zaku zomin Barka da sallane".
Da sauri tace.
"Eh Umaymah Allah in ya yarda zamuzo ki tambayan mana shi".
Cikin dariya Umaymah tace.
"Yoh mace da mijinta sai wani ne zai tambayar miki".
Cikin sanyi tace.
"Uhummm".
Ita kuwa Umaymah cewa tayi.
"Ina Umminku?".
Da sauri tace.
"Gata ta ƙarishe mgnar da miƙawa Ummi wayar.
Cikin fara'a suka gaisa kana Umaymah ta tambayeta ya yaran nata, tace duk suna lfy.
Nan take ce musu ta cewa Shatu ai a saudia zasuyi salla.
Sosai Shatu ta tayasu Murna.

Suna cikin hirar Hadimai guda uku suka shigo da jakukkunan guda uku.
Rusunawa sukayi bayan sun gaidasu ne,
suka ajiye jakukkunan tare da cewa.
"Gashi biyun inji Lamiɗo ɗaya kuma Gimbiya Aminatu ce tace mu kawo miki".
Sukarishe mgnar suna kallon Shatu.
Godiya tayi musu kana ta kalli Hibba data miƙo mata kuɗi sun kai dubu biyar.
Ta gane manufar Hibba shiyasa ta amsa ta basu.
Godiya sukayi kana suka tafi.


Jim kaɗan Hadiman Hajia Mama sukazo da saƙon Hajia Maman.
Sosai Shatu tayi godiya ta mashi kuɗi a hannun Hibba ta basu.

Nan Hibba ta tattara kayan ta shigar dasu, zata shigar dana HAJIA MAMA tace
"A Hibba barsu zan shiga dasu."
Gefe ta nuna mata tace ajiyesu anan.


Bayan sunyi sallan azahar sun fito zasu Fara aiki ne ta kalli Ummi tace.
"Ummi bari inje inyi godiya wurin Hajia Mama".
Cikin tsareta da ido tace.
"Ki bari mana sai ansha ruwa sai in rakaki daga nan kiyiwa Lamiɗo ma godiya.
Duk dai wannan kyauta da yakeyiwa duk ahlin masarautar Joɗa in lokacin salla ya gabato amman muje kiyi godiyar."
Da sauri tace.
"No Ummi ba sai an rakani ba, zanje ni ɗaya ma, kinga nasa al'kyabba".
Daga nan ta fice, cike da mamaki suka bita da ido.

Bayan kamar 37 minute ta dawo cike da fara'a sukaci gaba da aikinsu.

Can da suka fito dan yin sallan la'asar,
Ba kayan ba dalilinshi. Da sauri Hibba tace.
"Aunty Shatu kin shigar da kayan ne?".
Ci gaba da tafiya tayi tare da cewa.
"Maisu ta aiko an kwashe mata abunta dai".
cikin mamaki sukabi bayanta.


Yau azumi goma sha huɗu gobe 15 in Allah ya kaimu.

Bayan yaci abinci ne ya kira Umaymah nan yake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login