Showing 150001 words to 153000 words out of 180927 words

Chapter 51 - GARKUWA Book 1 Original Pdf By Garkuwar Fulani.txt

28 Aug 2025

1882

nan na zamani mai ɗan karen kai duk inda sirin yanken fisis ɗin yake an bishi da jerin duwasun shuwa riski masu sheƙin Daimond, cib-cib rigar tayi a jikinta.
Murza ɗauri ɗan kwali tayi irin mai stpes ɗin nan
Kana ta tura ɗan kwalin kaɗan wannan tattausan saje da suman dake konce a goshinta ya fito ras.
Sai ta baya kuma ta tsakiyar ɗan kwalin ta bar rami ta fito da jelan gashinta ya konto har kafaɗanta ba tare da ta kitseshi ba.
Wasu ƴan kunne da sarka na azurfa ta saka a wuyanta,
sai wani kekyawan agogon fata rea ƙirar Gucci ta manna a tsintsiyar farin hannunta da yake, ɗanɗase da zanen jan lalle mai kyau.
Gyale rea color mai masifar kyau ta ɗan yafa a kafaɗunta.
Wasu turaruka kala biyu ta fesa, kana ta kalli muskarta da jikinta a madubin.
Wayarta ta ɗauka ta ɗan kaikaice ta ɗauki kanta hoto ta cikin madubin tayi kyau sosai.
Wasu takalma marasa tudu tasa suma rea color ne.
Tana riƙe da wayarta ta fito falon.

Da sauri Hibba ta miƙe tare da cewa.
"Wow! Wow!! Wow!!! masha Allah Aunty Shatu kin ganki kuwa masha Allah."
Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa.
"Kai gsky amaryar Sheykh ta fito da madarar kyau masha ALLAH".
Ita dai sai murmushi takeyi dace musu.
"Ngd".
Cikin jin kunya.
Hibba kuwa duk takun da motsin da zatayi sai ta ɗauke ta hoto.
Daga ƙarshe ta rinƙa yi musu selfi su duka huɗu.
Saida suka gajine kana suka zauna suna hira.


Nan suka kira Umaymah suka sha hira.

Suna cikin hira Ummi ta juyo da sauri jin muryar Affan yana sallama tare da cewa.
"Assalamu alaikum. Ina Umminmu ina amaryar Hamma tuzuru".
Miƙewa da sauri Ummi da Aunty Juwairiyya sukayi tare da cewa.
"La Affan yaushe ka dawo".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Jiya da tsakiyar dare, ina Auntyn nawa".
Ya ƙarishe mgnar yana shigowa cikin tsakiyar falon.
Tafa hannu Ummi tayi tare da cewa.
"Suwa nake gani kamar Yusuf da Aryan".
Cikin dariya sukace.
"Muɗin ne dai Ummi".

Cike da jin daɗi Ummi da Aunty Juwairiyya ke cewa.
"Kai maraba lale lallai yau munada manyan baƙi , oh duniya Yusuf da Aryan kamar ba kuba".
Dariya sukayi tare da zama a kujeru.
Hibba kuwa tuni ta isa gaban Affan lakace hancinta yayi tare da cewa.
"Sakaliyar Umaymah ashe kina nan bana zakiga shagalin sallan Masarautar Joɗa".
Cikin sauri ya kalli Shatu dake ce musu.
"Sannunku da zuwa".
Da sauri ya juyo ya kalli Ummi kana ya kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa.
"Wannan ce Auntyn nawa amaryar Sheykh Ustaz Malam Dr Jabeer akarmakallu".
Murmushi Ummi tai tare da cewa.
"Eh itace".
Cikin dariya ya kalli Yusuf da Aryan da suke gaisawa da ita yace.
"Kan bala'i ashe dama Sheykh Hamma Jabeer yana kallon mata kalli yadda ya zaƙulo zankaɗediyar sarauniya".
Yusuf ne ya daki kafaɗarshi tare da cewa.
"Kaifa Affan ɗan iskane baka da mutunci, baiyi aureba kace mishi. Shugaban tuzuran Afirka.
Yanzu yayi auren kuma zakace yana kallon to dama ce maka akayi shi makaho ne?".
Dariya sukayi baki ɗayansu,
Aryan ne yace.
"Bar Affan da shegiyar surutu".
Dariya suka kumayi kana duk suka zauna.

Suka gaisa cikin tsokana Affan ya kalli Shatu dake danna wayarta tana kallon hotunan da sukayi yanzu yace.
"Aunty Amarya Hamman namu yana nan ne, ayi mana iso wurin shi mu kwashi gaisuwa".
Shiru ta ɗanyi tare da kallon Ummi.
Da sauri Hibba tace.
"Eh yana nan yanzu ya shiga".
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
"To Aunty Sayyada ayi mana sallama dashi ace ɗaliban shi ne, Affan, Yusuf, Arya,".
Cikin tsoron kada Shatu ta kuma zuwa ɗakin abun da ya faru jiya ya sake faruwa Ummi tace.
"Ai yana bacci ne yanzu ko".
Da sauri Affan yace.
"No ba matsala in ance masa Yusuf ne, tashi kice muna sallama dashi."
Cikin murmushin jin Yusuf da Aryan sunce.
"Eh gsky gwara mu gaidashi kada ya gammu a wurin sukuwa yace bamu nemi izininshi ba".
A hankali tace.
"To bari a gaya mishi".
Ta yunƙura zata tashine Ummi ta riƙe hannunta tare da cewa.
"Shatu kadafa".
A hankali tacewa Ummi.
"Ba komai fa Ummi".
Ganin hakane yasa Ummi ta sake mata hannun tare da cewa.
"To Allah yasa".
Amin Amin Juwairiyya da Hibba sukace.
Shi kuwa Affan cewa yayi.
"Allah bazaiyi faɗaba in yaji mune".
Kai Ummi ta gyaɗa sabida basu san me take tsoron ba.

Ita kuwa Shatu a hankali ta nufi Side ɗinsa.

Su kuwa hirarnsu sukaci gaba dayi a falon.

A hankali ta tura ƙofar falon nashi ta shiga.
Shiru babu kowa babu komai sai sautin ac dake tashi fuuuhhh.

A hankali ta lumshe idonta kana cikin sanyi ta nufi ƙofar ɗakin nashi.
Tare da cewa.
"Salamu alaikum! Salamu alaikum!! Salamu alaikum!!!".
Shiru babu motsin komai, hakane yasa a hankali tasa hannun hagun ta dafa ƙirjinta dake bugawa.
Kana tasa hannun damanta ta tura ƙofar Bedroom ɗin.
Sai kuma gashi ta buɗu ƙofar.
Wani sassanyan ajiyan zuciya ta sauƙe jin wani irin masifeffen ƙamshi da sanyi daya ratsa mata jiki da zuciya.
Sallama ta kumayi shiru ba amsa.
A hankali ta cusa kanta cikin ɗakinta da yake duhu.

Wani irin bugawa ƙirjinta keyi kana.
Kanta na sarawa da masifan ƙarfi.
A hankali ta juya gefen mashigar ɗakin hannun tasa ta lalubi abin kuna wutan ɗakin danna ɗaya daga ciki tayi,
hakan yasa ƙoyin wutan ɗaya mai kalar Sky blue ya kawo wuta.
Sanadin hakane ɗakin ya kawo wani irin haske mai ƙayatarwa.
Yanayin wutan ɗakin labulayen da kayan jikinta dana jikinshi sukazo iri ɗaya.
Juye- juye tayi tare da cewa.
"To ina yak".
Shiru tayi bata ƙarisa rogowar mgnar ba hangoshi can ƙasa yana konce rigingine yayi pillow'n da tafukan hannunshin.

A hankali tayi taku uku zuwa biyar ta matso kusa dashi cikin sanyin da ya fara yimata yawa ga cikinta dake tsuma a hankali tace.
"Salamu alaikum".
Ko motsi baiyiba bare tayi zaton zai amsa.
Sallama ta kumayi shiru ba amsa.
Ganin hakane ta matso a hankali take takun saɗab-saɗab take taka sawunta a hankali har ta isa kusa dashi.

Da sauri ta zubawa ƙafar damanshi ido.
Ajiyan zuciya tayi mai sanyi tare da mgnar zuciya.
"Uhumm ashe dama yana komciya a ƙasa haka babu shimfiɗan komai ba pillow, da kuma ƙaramar riga da wondo iya guiwa."
A hankali ta iso gab da kanshi,
Cikin yin numfashi a hankali wai karya jita, ta rusuna ta zauna bisa sawunta irin zaman yin tahiyan salla.
Cikin ƙurawa babbar yatsar ƙafar damanshi inda ta rinƙa biyo wannan zanen macijin dake kwance lib a ƙafarshi.
Da ido tabi zanen har kan guiwarshi inda iya nan wondon 3 qtr ya rufe.
A hankali ta ƙara sunkuyowa ta kurawa wurin ido, tare da mgnar zuciya.
"To iya ina wannan zanen tafiyar macijin ya tsaya ne a jikinshi?".
Jim kaɗan tayi kana a hankali.
Ta miƙa hannunta, cikin sanɗa a hankali hankali tasa yatsunta biyu ta kamo bakin ƙafan wonɗon ta ɗan jawoshi a hankali tayi sama das...!




Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 in Kuma special Group kikeso wanda a mako biyu ake gaba part 1 kuma abiyu za'a gama Part two da izinin Ubangiji yimin TRANSFER ɗin 1k ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. sai ki turo screenshot shaidar biyanki ta wannan number 09097853276.



By
*GARKUWAR FULANI*Ta ɗan ja tayi sama da bakin ƙafan wonɗon wanda yake na robane bakin a tsuke yake.
Da sauri cikin tsoro da rawan jiki ta saki robar.
Pat ya fetti a jikinshi.
Ganin ya motsa.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wani sassanyan numfashi ya ja mai tsawo tare da fesoshi a hankali kana, ya mirgina a hankali ya juya ya kifu cikin kasalan nauyin bacci ya ɗaura kanshi bisa cinyarta,
Kana ya ware hannayenshi da sukayi ɗan tsami sabida pillow'n da yayi dasu.
Ware hannayen yayi tare da miƙarar dasu.
Ya zama tana tsakiyar hannunshi kana kanshi na kan cinyoyinta.

Haɗe hannuyen nashi yayi ya sarƙafe yatsunshi wuri ɗaya, ya zama ya zagayeta tako ina yayi mata ƙawanya.
Ya cusa hancinsa cikin mayafinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinta dana kayanta.
A hankali ya kuma gyara kwanciyarshi da kyau kana yaci gaba da sauƙe sassauƙan numfashin.

Ita kuwa Shatu wani masifeffen tsalle da bugu zuciyarta keyi tamkar zaiyi tsalle ya fito woje.
Gaba ɗaya ida nunta kan sumar kanshi ta zubasu.
Tare da kallon tattausan sajenshi dake kwance lib-lib a gefen fuskarshi.

Wani sassanyan numfashi ta sauƙe tare da lumshe idonta cikin zuciyarta tace.
"Allah shi ƙara".
Sai kuma tayi sauri ta buɗe idonta tana tambayar kanta.
"Allah shi ƙara me ɗin? Ya ƙara ruggumata ko meyeye".
Cikin kauda zancen a ranta ta ɗan muskuta dan janye jikinta. Amman sai ta ji ya riƙeta gam-gam, yana ƙara cusa kanshi cikin jikinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren jikinta.

Cikin tsoro murya na rawa a hankali tace.
"Yah Sheykh!".
Karab sautin muryarta ya ratsa kunnuwanshi.
Sai dai ko motsi baiyi ba,
A hankali ta kuma ce.
"Yah Sheykh! Yah Sheykh!!".
Shiru babu amsa sai numfashin da yake fiddawa a hankali yana kuma shaƙan ƙamshin jikinta.
Cikin sanyi ta ɗan ɗago hannunta a hankali tasa taffin tattausan hannunta, ta ɗan rinƙa buge gefen fuskarshi a hankali a hankali tanayi tana cewa.
"Yah Sheykh! Yah Sheykh! ! Tashi wai Affan dasu Yusuf sunzo, shine Affan yace inzo in tasheka".
A hankali ya buɗe idonshi,
Yanayin yadda take ɗan marin gefen fuskarshi da hannunta wanda ke ɗaure da agogo.
A hankali ya ɗago hannunshi ya ɗan kan hannunta ya kamoshi ya riƙe, cikin tsoro ta fara kiciniyar kwace hannunta,
Sai kuma tayi zuru, jin ya ja hannun da ɗan ƙarfi ya kawoshi dai-dai saitin fuskarshi.
Idonshi ya zubawa yatsun hannunta da kullum in ya gansu da jan lalle yake tuna mishi baya.
Da sauri tace.
"Wash Allah na".
Jin ya murɗa hannun ya juyo da fuskar agogon inda zai gani.
Ƙarfe biyu da miti arba'in da ɗaya.
Du-du baccin 40 minutes yayi tazo ta tasheshi.

"Harda zuba min maruka".
Ya faɗa a ransa.

Ita kuwa kan tattausan suman ta ajiye sinsiyar hannunta.
tana jin kanta na sara Especially in ta kalli saitin ƙasan gadonshi."

A hankali ya sake hannunta kana ya yunƙura ya juya rigingine,
ya fuskanci sama, ita kuma tana zaune tana kallon ƙasa hakanne yasa suna fuskantar juna, cikin wani irin yanayi ya zuba mata ido na wasu sakanni.

Shigarta tayi masifar mishi kyau. Kodan tasa kalan kayan da yafi sone.
Cikin muryar bacci yace.
"Shine harda dukana? Meyasa ne ku mutanen garincan kuke son dukan mutun da kallon jikinsa?".
Cikin tura baki tace.
"Cinyana, nagaji kanka nauyi".
Bai janye idonshi a kantaba ya yunƙura ya tashi zaune tare da juyowa ya fuskanceta.
tanƙwashe sawunshi yayi tare da cewa.
"Me zaki kalla a jikina? Woto Kin zama kamar ɓarauniya ko? Me kike son gani? Wani abu kike sone?".
Cikin tura baki tace.
"Nifa tada kai a bacci kawai nayi".
Hannunshi yasa ya riƙo hannunta, yatsunta ya zubawa ido, cikin wata murya mai sanyi yace.
"Masha Allah, kinyi kyau."
Wani irin sanyi taji kalmar tashi tasa mata a ranta, ido ta ɗan ɗago ta kalleshi.
Shima ita yake kallo, ido ya lumshe jin sautin zazzaƙar muryarta a hankali tace.
"Nagode".
Tonƙoshe kansa yayi bisa kafaɗa kana hankali ya sake hannun nata.
Fuskarta ya kalla tare da taɓe baki yace.
"Waya koya miki irin sa lalle Mammeyyyyy nah!? Dan tafi ko wacce mace iya lalle".
Cikin sanyi da nazartar yadda ya kira sunan Mammeyyyyy da yadda lokacin ɗaya idonshi suka fara sheƙin tsastsafo da zafafan hawayen da ba zubowa zasuyiba.
Cikin son gano meke cikin zuciyarsa tace.
"Ummeyy nah ce ta koya min tun ina ƙaramar".
Yatsunta ya jujjuya kana ya miƙe tsaye.
A hankali ya juya ya nufi bathroom sabida baya son ta hango wutar ƙunar dake ransa.
Ita kuma binshi da ido tayi,
tare da langoɓar da kanta tana kallon sharabansa da gargasa yayi musu ƙawanya.

A haka ta shiga wani nazarin tana mai maimaita sunan da taji ya kira da cikekken so shaƙuwa ƙauna tausayi rauni shogoba *Mammeyyyyy.* Ta maimaita sunan a fili.

Shi kuwa Sheykh Jabeer al'wala yayi kana ya fito.
Yayi mamakin ganinta a zaune bata fita ba.

Hararanta yayi ganin yadda taketa kallonshi. Jallabiyar shi ya zura, kana yasa al'kyabbar, tare da sa Hiraminshi.
Sannan ya fesa turare.

Duk inda yayi tana binshi da ido.
Wayarshi da yafi yawan riƙewa ya ɗauka ya zura a al'jihunsa.

Sannan ya nufi bakin ƙofa inda takalminshi suke yana cewa.
"Wannan kallon maitan fa".
Da sauri ta janye idonta.
Cikin daƙilewa yace.
"Kada ki cinyeni da ido fa. Bana son kallo, ko kina bina bashine?."
a hankali ta miƙe tare da lumshe ido ta biyu bayanshi.
Tana gyara mayafinta tare da cewa.
"Ni ban kalleka ba".
"Uhummm." yace a taƙaice.
Kusan a tare suka fito.
Yana gaba tana bayanshi,
Suka fito tsakiyar falonshi.
Tsayawa ya ɗanyi ya gyara masaƙalin Al'kyabbar tashi.
Shiyasa ya zama a jere suke tafiya tana gefen damanshi.
A haka suka fito cikin corridor'n.
Suka doshi Falon cikin kwarjini da dacewa da juna sai ƙamshi da sheƙi zallan kyau sukeyi.

Da Sallama a bakinshi suka kutsa kai cikin falon.
Wani irin dariyar jin daɗi Affan da suke can Dinning area yayi, suna cin abinci da Ummi ta matsa suci.
Wani irin murmushi Yusuf da Aryan ma sukayi tare da miƙewa suka nufi inda uban gidan nasu ke tsaye da kekyawar tauraruwarshi mai haskawa.
Affan kuwa wayarshi ya zaro yana kekkebta musu hoto tare da cewa.
"Ga amarya, ga ango, suna carabki da zallan kyau da ƙamshi".

Murmushi sukayi dukansu, ita kuwa Shatu tana tsaye gefenshi.

A haka su Affan suka iso.
Suna Isa Affan ya ruggumeshi shima Sheykh ruggumeshi yayi tare da make ƙeyarsa.
Da sauri ya janye kanshi tare da cewa.
"Wayyo Allah na yanzu Hamma Jabeer na girma harda yaran nawama ban wuce dukaba".
Murmushi yayi tare da, Ruggume Yusuf da Aryan Allah ya sani yana masifar son yaran nan har gobe bashi da ɗalibai sama dasu yana sonsu so na musamman, duk sanda ya gansu yakan tuna ƙuruciyarsu tun suna yan shekara goma sha biyar-biyar yake tare dasu shi ya horas dasu.
Yana tura irin tarin ƙalubale da suka fuskanta a gasar Polo da kuma irin nasarorin da suka samu Especially Yusuf nashi yana tuna yadda yaran suke sheƙiyanci in sun haɗu, yana jinsu tamkar su Jamil.

Cikin murmushin ya shafa kansu tare da cewa.
"Sannunku da zuwa".
Cikin jin daɗi sukace to.

Bisa kujera ya zauna su kuma suka zauna a ƙasa a gabanshi kan carpet.

Ita kuwa Shatu a hankali ta juya ta nufi kitchen ganin Ummi ta nufi can.
Hibba kuwa na gefensu tana gayawa su Jalal ga Ya Affan fa.

Da gefen idonshi ya bita da kallo.
Har ta ɓacewa ganinsa, Allah ya sani yana son abu blue baya iya cire idonshi kan abu mai kalar shiyasa yake jin baya gajiya da ganinta, da zai samu kada tayi nesa dashi, dan tayi mishi kyau sosai farar fatarta ta fito fes kamar balarabiya ji yake tamkar ya bita duk inda tayi.


Cikin murmushin ya kalli Aryan yace.
"Aryan Ina su Yusuf ƙaramin".

"Alhamdulillah suna lfy Malam".

Kai ya jinjina tare da cewa.
"Masha Allah".
Sai ya kuma kalli Yusuf yace.
"Ina mai sunana baka zomin da shiba".
Murmushi Yusuf yayi tare da cewa.
"Malam baka tambayi Aryan ƙaramin ba da yakeso ya zama kamarka sai ka tambayi mai sunanka".
Dariya sukayi kana yace.
"Ayyah my Aryan, sun kusa tafiya ai in sha Allah Jami'atul Madina zaiyi karatunshi".
Da sauri suka juyo suka kalli Jalal da Jamil da suka shigo da sauri.
Ruggume Affan sukayi suna cewa.
"Oyoyo ya Affan".
Hannu ya basu suka tafa kamar sa'ao',insa ne su.
Cikin dariya yace.
"Tun ɗazu nake kiranku bakwa ɗagawa.
Nace waɗannan ana can cikin hayani ".
Murmushi Jamil yayi tare da miƙawa Yusuf hannu wanda ke cewa.
"Oh wato Affan kawai kuka gani mu ko oho ko".
Cikin ɗan sakin fuska Jalal yace.
"Afwan Hamma Yusuf ya Aunty Zahra da Mama".
"Suna lfy. Sun gaidaku". yace tare da bashi hannun.

Kana suka gaisa da Aryan.
Sannan suka miƙe sukace bari suje wurin Aunty Mami.
Cikin dariya Affan yace.
"Eh kujema kuzo da ita taga matar babban yaya".
Da sauri Jamil yace.
"A a ka kawota da kanka dai".
Ya ƙarshe mgnar suna fita.

Su kuwa cikin yin ƙasa da kai Yusuf yace.
"Uhum dama Malam zamu ɗan shiga wasan daba ne in batsala".
Murmushi mai faɗin Sheykh yayi tare da cewa.
"Wato ku dai har yanzu baku girma da batun doki ba".
Shiru sukayi sai Affan ne yace.
"Tab Yusuf kuma da in ya ga doki bai hauba jikinshi har rawa yakeyi".
Murmushi Sheykh yayi kana yace.
"To muje muyi salla. Tukun tunda sai anyi sallan la'asar za'a fara ko".
To sukace tare da miƙa ganin ya miƙa dan tuni uku da kwata ta wuce.
Affan ne ya kira Ummi tare da cewa suzo zasu tafi.
A tare suka fito kitchen.
Sabbin kuɗi rafa yan dubu-dubu Yusuf ya miƙawa Hibba ƙulli ɗaya dubu ɗari kenan yace.
"Gashi miƙa wa Ummi ta raba muku."
Affan ma ya basu.
Hakama Aryan.
Hibba sai tsalle take tana cewa.
"Yessss my brother's Allah ya ƙara buɗi Amin Amin sukace kana suka juya zasu fita.
Cikin tsare girma Shatu tace.
"Mun gode, a gaida gida".
Gida zaiji sukace kana suka fita suka tafi.

Suma su Ummi wucewa sukayi yin al'wala.

Ana idar da salla kuwa aka fara hawan daba, hawan sarki dama duk sauran shagulgula na gidajen masarautun gargaji yayin wurin taron bikin salla.
MASARAUTAR Joɗa ta cika tayi maƙil da bani Adam.

Haka dai akayi taron lfy aka tashi lfy sai kuma gobe in Allah ya kai rai.

Washe garin ranar da sassafe.
Sheykh ya tafi asibitinshi.
Ko karyawa baiba.
Sai kusan sha ɗaya ya dawo da alamun yunwa da gajiya tare dashi.
A falon ya zauna suna gaisawa da Ummi dan basu gaisaba ya tafi daga masallacin can ya wuce.
Ummi kuwa tasa Shatu ta kai mishi breakfast ɗin shi da yanzu kam in yacima ya zama lunch ne.

Hibba kuwa na can ɗauki tana ƙenƙesa ado.

Cikin isa da ƙasaita Gimbiya Saudatu ta shigo tsakiyar falon babu ko sallama.
Haɗe fuska Sheykh yayi tare da cewa.
"Wannan banzan ɗabi'a na arnatakun baya, dan ko arna yanzu suna cewa konkon, mutun kamar shanu ko mahaukaciya".
Cikin isa ta iso tsakiyar falon.
Dai-dai lokacin kuma Shatu ta fito falonshi.
Cikin shigar doguwar riga mai ruɓi biyu.
Kanta ta ɗago ta kalli Shatu kana ta kalleshi cikin yin dariyar mugunta tace.
"Eh kam tabbas tunda ka auro mahaukaciya dole kasan hali da ɗabi'un mahaukata ai.
Zuwa gaba kaɗan kaima zaka fara ihu da kuka da sume-sume irin na wannan al'janar fulanin daji daka auro ɗin".
Cikin tarin mamaki Ummi ta kalli Shatu ta kuma kalli Hibba da yanzu ta fito, cike da al'hinin ta yaya taji wannan batun ya fasa Masarautar Joɗa yes in dai Gimbiya Saudatu taji to ai shike nan kowa ma zaiji.

Shi kuwa Sheykh ba gane inda soki burutsunta ya nufaba yayi.
Ita kuwa cikin watsa musu kallon ku sakarkaru ne tace.
"Kuna mamakin ta ina naji, cewar ji shekaran jiya iwar haka dai wannan matar tashin tana yashe a sume da ido a wulkice tana ƙarkarwa farfaɗiya kamar mazari ne.
To ai Ni duk wanda yaci tuwo dani miya yasha.
Inada tawa a cikinku duk motsinku ina dashi a tafin hannuna.
Nan gaba kaɗan zamu samu riƙeƙƙiyar mahaukaciya a masarautar Joɗa".

Cikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login