Showing 132001 words to 135000 words out of 180927 words

Chapter 45 - GARKUWA Book 1 Original Pdf By Garkuwar Fulani.txt

28 Aug 2025

1833

kana tace.
"Um bari inje inyi salla".
Sai ta kuma kalli Hibba dake lankwabe tace.
"Sannu Hibba kwanta ki huta".
Jalal da yanzu ya shigone ya ɗan taɓe baki tare da cewa.
"To me tayi da zata huta tunda fa gari ya waya in anga ta tashi dai yin salla ne, tun tuni birgima take a tayis wai sanyi take nema".
Dariya sukayi mata baki ɗayansu,
Ita dai Shatu ciki ta wuce.
Salla tayi kana ta fito. Koda tazo kitchen ta samu Hibba na suya musu Arish ɗin, tayi mamaki.
Cikin wasa tace.
"Kawo in karɓeki jeki kwanta".
Cikin sanyi tace.
"Ai Hamma Jabeer ne yace min in ina aiki bazanji wuya ba, zanfi ganin lokaci ya gudu".
Dariya sukayi mata kana kowa yaci gaba da aikinshi.
Ita Shatu miyar sahur na asuba ta ɗaura musu.

Cikin ikon Allah shida dai-dai suka gam kan aikinsu.
Bayan Shatu'n ta taya Hibba suya kwai daban, ta jerasu a Foodflaks, in ta ajiye fefeyin soyayyan ƙwai da yaji haɗi da diddigin kifi, sai ta zuba soyayyan Arish a kai kana ta kuma rufeshi da fefeyin kwai haka ta rinƙa jerasu saida ta cika kulan.

Ummi kuwa ta sawa Saratu komai nata.

Sannan suka kimtsa wurin fes suka fito da komai suka jera a dinning table.

Nan duk suka wuce ɗauki.
Wanka sukayi, kana sukayi al'wala sannan suka fito falo. A nan suka samu Imran, Jalal, Jamil, Sulaiman.
Cikin gajiya Ummi tace.
"Yauwa Jalal ku ɗauki manyan kulolin nan ku kai masallaci.
Sauran madaidaitan kuma ku ajiyewa sarkin bayi.
A bawa bayi da hadimai".
Murmushi Jamil yayi tare da cewa.
"Eh lallai bana bayi sun samu uwar gijiyar data tuna dasu, bayan kuma anayi musu nasu na daban".
Cikin lumshe ido Shatu tace.
"Eh suma suci abinda muke dafawa da kanmu, ba sai na gandun nasuba".

Miƙewa sukayi suka ɗauki kulolin sun zo falon kenan Sheykh na shigowa, wani hadimi na biye dashi da manyan ledodi cike da ƴaƴan itatuwa.
Kusan a tare suke mishi sannu da dawowa.
Murya a bushe alamun ƙishi yake amsa musu kana ya nunawa Ummi leda ɗaya yace.
"Ummi a wonke wannan a haɗa da dabino mudu uku a basu su kai masallaci".
Ya ƙarishe mgnar yana wucewa.
Da sauri Ummi tace to.
Ta miƙe kenan Shatu tace.
"Ummi zauna bari in wanke sun".
To tace kana ta koma ta zauna.
Ita kuma taje ta wonke ta zubasu a tray kana ta ɗauko plates and cups masu yawa, tazo ta miƙawa Imran.
Da sauri suka amsa suka tafi.

Jim kaɗan suka dawo, cikin gajiya Jamil yace.
"Ummi ansha ruwafa mun samu Ladan na cin dabino".
Da sauri Hibba ta miƙa tare da cewa.
"Su ladanannan haka suke basa kiran salla sai sun sha ruwa."
Dariya sukayi mata kana suma suka miƙe sukabi bayanta.

Zama sukayi bisa kujerun kowa da abin yake hari.
Sai dai kab ɗibsu da dabino suka fara.
Ummi ce ta kalli Shatu tare da nuna mata babban tray'n da aka shirya komai na buɗa cikin Foodflaks guda 3 madaidata masu kyau, sai plate ɗin da aka shirya fruits masu ɗan karen sanyi, tupa, inabi ,kankana, abarba, gwanda, Lemu, ayaba, kana da dabino, da kwakwa,
Sai goran zam-zam madaidaci, kana sai cup da tea spoon a ciki, sai fork and knife a gefe da gefen plate ɗin dake cike da fruits ɗin komai biyu akasa.
Kulolin kuma ɗaya masane a ciki, ɗan namiyar kuma miyar Masar ne, sai ɗayan kuma, soyayyan ƙwai da dankalin, ɗayan kuma ferfesun kayan cikin ne.
Cikin nitsuwa Ummi ta ɗago tray ta miƙa mata tare da cewa.
"Yauwa gashi kai mishi lokacin shan ruwan na tafiya, yanzu zakiga ya fito".
Cikin sanyi da gajiya ta amshi tray'n kana ta nufi falon nashi, cikin nitsuwa take takun, a hankali tayi sallama tare da kutsa kai cikin falon.
A can bisa Dinning area ta hangoshi yana zaune, kan kujera ɗaya, ya kuma jawo ɗaya kujerar ya ɗaura sawunshi a kai ya miƙesu, System ɗinshi na bisa cinyarshi.
A hankali take takowa saman steps ɗin tare da ratsa cikin jeren ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu darajar sheƙin Daimond sai sunkuyar da kanta tayi sabida ɗauke mata ido da suke.

A hankali ta isa kusa dashi, cikin tura baki tare da ɗan murguɗashi ta ajiye tray'n, a tsakiyar table ɗin.
ɗago kanta tayi da niyar ta ɗan juya, ta fita.
Wani irin buɗe idanin tayi gaba ɗaya tare da zubasu, bisa sharaban ƙafarsa ta dama, wanda sanaɗin zaman da ya ɗan yi ya miƙe ƙafafuwan nashi bisa ɗaya kujerar ne yasa suka ɗan baiyana, wani irin kallo mai cike da ɗimuwa takeyiwa zanen dake bisa ƙafarshi ta dama, da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannun hagun ta kama kanta sabida wani irin sarawa da ya farayi da ƙarfi.
Cikin sauri ta juyo tare da miƙa hannun damanta ta sauƙeshi kan...!





Akwai kayan gyara na amare da uwar gidaye da masu jego, ga mai buƙatar saya ga number ta 09097853276



By
*GARKUWAR FULANI*Ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu darajar sheƙin Daimond da yayiwa wurin labule.
Yayin da kuma hankalinta da idonta duk suke kan ƙafar tashi tana kallon zanen da take gani har kamar motsawa yakeyi a jikinshin, da kuma suffar macijiya.
A hankali ta ɗago ƙafarta tare da take step ɗin forko, hankalinta kuwa duk yana baya, har ta juya kanta gaba ɗaya sam ganinta baya gaba.
Cikin rashin sa'a kafar ta tsallake step ɗin forko bata isa kan dandamalin ta biyu ba, ta sauketa, cikin akasi ƙafar ta sule tare da yin shuuuuu tayi gaba.
Wani ƙara mai ɗan karfi irin na maiyin azumi ta sake tare da rumtse idanunta da ƙarfi tana jiran taji ta ina ɗin ta zai karye.
Wani irin ihu ta kuma sakewa, lokacin da taji ta faɗi gib a kan stpes ɗin kanta ya bugi dandamalin sama.

A hankali ya juyo kanshi ya kalleta a fakaice,
Ba tare da yace mata ko ƙalaba ya juyar da kanshi ya fuskanci tray'n data ajiye mishi, plate ɗin fruits ya ɗan buɗe kana, ya ɗauki Fork ɗaya, janye ƙafafuwan shi, yayi ya sauƙo dasu ƙasa kana ya gyara zamanshi ya fuskanci Dinning table ɗin da kyau.
Fork ɗin yasa ya fasa cikin dabino da yake irin na kwali nanne mai laushi ne,
ture ɗan yayi gefe kana ya soki dabinon a hankali ya kai bakinshi, bayan yayi addu'o'in buɗa baki.
Ido ya lumshe jin lokacin da sanyi da zaƙi da ɗanɗanon dabinon ya game mishi baki.

Ita kuwa Shatu kuka tasa tare da riƙe ƙugunta, da kanta cikin muryar kuka take cewa.
"Wayyo Allah na. Wayyo Ummey na, bayana ya karye ƙuguna ya ɓalgace, kaina ya fashe ƙeyana ya tarwatse".
Ta ƙasa Glass ɗin table ɗin ya ɗan kalleta, kana ya maida kanshi yaci gaba da cin dabino, yana maijin wani irin masifeffen dariya na taso mishi jin raki da Shatu ke zubawa.
Saida yaci ƙwaya bakwai, kana a hankali ya fara tsira Fork ɗin kan ƴaƴan inabi masu masifar sanyi da daɗi, ci yakeyi yana jin ƙishin daya addabi moƙoshinsa na wucewa.
saida ya tsinke nonon inabin kab ya cinye, kana ya fara soka kankana da akayiwa ƙaƙanan yanka kana aka barbaɗa garin madara a samansu, shima shanye rabinshi yayi.
Wani sassanyan gyatsa yayi tare da ture tray'n gefe.

Ita kuwa Shatu sosai taji zafin faɗuwan ga azumi ga gajiyan aiki ga faɗuwa ga haushin yadda duk ihun da tayi babu wanda ya kulata, bare a kawo mata agaji, abun ya haɗe mata sai hawaye share-shere ta tabbatar da a gidansu ne tayi wannan ihun da gaba ɗaya iyayenta da yayunta da ƙanwarta duk suna kanta, da tuni an ɗagata a wurin ma.
Bege da kewa da kukan rashin yan uwanta da watseman ahlinsu ne ya tunzura hawayenta.
Ta kasa tashi sabida jikinta duk rawan yunwa da gajiya yakeyi ba ƙarfi sam.

A hankali ya miƙe tsaye bayan ya sha ruwan zam-zam mai ɗan sanyi kan ƴaƴan itatuwan da yaci.
System ɗinshi ya ajiye kan Dinning table ɗin, tare da wayarshi.
Gefenta ya ɗan ratsa ya fara taka steps ɗin tare da kallonta a fakaice.
Yana gab da sauƙane ya ɗan motsa lips ɗinshi tare da cewa.
"Kaɗan kenan in dai baki dena samin ido a jikina ba,
Faɗuwa harda kareireyewa zakiyi in baki kiyayi yimin kallon ƙurillaba, na lura ku mutanen wancan dajin bakuda abinda kukafi so sama da kallon killataccen wuri na jikin mutun.
Muddin baki dena satan kallon jikina ba, sai waɗannan mayatattun idanun naki sun tsiyaye kin huta ki zama makauniya babu ɗan jagora.
Kiyi dai a hankali ko kya samu ki mutu da idonki,".
Ya ƙarishe mgnar yana tafi kamar bashi yayi mgnar ba.
Ita kuwa Shatu hannun tasa ta sharce hawayenta tare da rakashi da hararan kai mugune.

A falon ya samu su Ummi sunata dariya.
Cikin sauri ya kalli su Jamil yace.
"Kai wannan dariyar na menene, ku taso mu tafi masallaci".
Cikin dariya Jamil yace.
"Allah ko Hamma Jabeer ina zaton Hibba bata taɓa azumi ba sai bana.
Ga yadda ta dawo wuni ɗaya, wai a haka kuma har ta fara lissafin wai yauwa yau mun kai ɗaya mun rage".
Ɗan gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Muhibbata tashi kije kiyi salla sai ki ɗan konta ki huta kafin a kira isha'i ko".
Cikin sanyi tace.
"To Hamma MJ".
Jalal kuwa cikin yin ƙasa da murya yace.
"Gobe ma zakiyi ne ko zaki huta".
Cikin kwaɓe fuska tace.
"Zanyi Umaymah tace, bana ko ɗaya in nasha sai na biya".
Murmushi ya ɗan yi tare da cewa.
"Ashe dai kin girma".
Da sauri ta sunkuyar da kanta, shi kuwa yabi bayansu Jamil.

Duk sukayi gaba, Sheykh kuwa na bayansu.
har yaje tsakiyar falon sai kuma ya ɗan tsaya jin Ummi na ce mishi.
"Shetu fa".
Cikin saurin tafiya masallacin yace.
"Tana can ta faɗi wai ko ta karye ne naji tana cewa ban dai san mataba".
Yana kaiwa nan ya fita, ita kuwa Ummi da sauri ta miƙe cikin zaro ido tace.
"Karaya kuma? Innalillahi yaushe".
Tayi maganar tana nufar falonshi,
A bakin ƙofar shigowa sukayi kiciɓis da ita, da sauri ta tareta tare da tallabota, jin yadda jikinta ke rawane ta jawota suka fito falon cikin tausayawa tace.
"Sannu Shatu".
Cikin tausaya Hibba taketa jera mata sannu.
Ajiyeta bisa kujera Ummi tayi tare da cewa.
"Baki sha ruwan ba ma ko?".
Kanta ta gyaɗa mata alamar eh.
Hakane yasa Ummi tacewa Hibba ta ɗebo mata, abin shan ruwan a take kuwa ta kawo mata.

Bayan tasha ruwanne duk suka nufi cikin ɗaki dan yin salla.


Daga yin sallan magriba su Jamil suka dawo sukaci abinci kafin aka kira sallan isha'i, kana suka koma akayi sallan isha'i da asham sannan suka nufi harkokin su.

Shi kuwa Sheykh Jabeer daga Masallacin gidan Radio Ɓadamaya ya wuce, wurin yin shirin Fatawa.

Sai tara dai-dai ya dawo, gida.
A kitchen ya jiyosu.
Bisa alamu duk girkin abincin sahur sukeyi.

Shi kuwa bayan ya shiga, wonka yayi-yayi shirin bacci kana ya fito falonshi.

Soyayyan Arish da kwan ya ɗanci tare da tarfa ferfesun ya ɗan ci. masa biyu.

Jin cikinsa yayi tib ne, ya miƙe ya dawo falon.
zama yayi bisa kujera yana kiran Umaymah,
tana ɗagawa tace.
"Jazlaan ina autata, ya azumin yau dai?".
Gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Umaymah autarki akwai raki, yau ita har ta fara lissafin an kai ɗaya saura 29/28".
Dariya ta ɗanyi tare da cewa.
"Kaɗan ma daga aikin Hibba".
Sai kuma tace.
"Ina ɗiyata kuma, ya azumin?."
Kanshi ya ɗan jingina da kujera kana yace.
"Alhamdulillah". Jin muryar Haroon na cewa.
"Wai ɗazu ina ka shigane inata kiran wayar ka baka ɗagawa".
Gyara zamanshi yayi tare da kurban coffee ɗinshi kana yace.
"Na bar wayar a gida, da ɗaya na tafi na Fatawa".

"To ya Amarya?".

"Ban sani ba".

Cikin dariya Haroon yace.
"Allah baka haƙuri".

Amsar wayar Umaymah tayi sukaci gaba da mgnar kan tafiyarsu Umrah.
Daga bisani sukayi sallama, ya miƙa ya nufi ɗakin baccinsa.


A kitchen kuwa, bayan sun gama komai na sahur ne.
Ummi ta cewa Shatu taje ta ɗauko Foodflaks ɗin dake falonshi.

To tace kana ta juya ta tafi.
Koda ta shiga ɗan kalle-kalle tayi ganin baya nan, yasa ta harari falon ma gaba ɗayatare da cewa.
"Mugu". Sannan ta ɗauki kwanukan ta fito.

Duk sauran abincin Saratu suka haɗawa ta kai musu ita da sauran hadiman.
Wanke-wanke tayi kana ta tattare komai sannan ta wuce part ɗin su.

Su kuma ganin har goma tayi ne, yasa sukayiwa juna saida safe duk suka shiga.

Yauma kamar daren jiya haka sukayi.

Washe garima haka suke tafiyar da rayuwarsu. Cikin tsari da kuma samun damar hutu da ibada dan ribatar watan Ramadan ɗin.

A hankali aka fara nisawa cikin watan Ramadan, kwanaki suna ɗan mirginawa da kaɗan-kaɗan.

Yau wunin azumi na biyar kenan.

Da hantsi bayan sunyi walaha sunyi karatun al'ƙur'ani.
Sanin yanzu Ummi na jin tabsir ɗin da yakeyi a masallacin Masarautar Joɗa ne yasa, Shatu tana gaisheta ta fito.

Hibba kuwa Side ɗin Aunty Juwairiyya ta nufa.

Ita kuwa Shatu falonta ta fito.
Bisa kujera ta zauna, tare da kiran
number Junaidu wanda Rafi'a ce, ta batashi data tare da bata haƙurin bazata samu zuwaba, sabida yayanta yazo sun koma jiharsu tare.

Ringing ɗaya ana biyu Junaidun ya amsa kiran ganin sabuwar number ne ya sashi cewa.
"Ban gane wake mgna ba".
Cikin jin daɗin yadda taji muryarshi ras alamun ya samu lfy tace.
"Junaidu Adda Shatu ce fa".
Da sauri ya tashi zaune bisa kekyawan gadon asibitin da yake kai tare da cewa.
"Laah Adda Shatu kece? Wlh ban gane muryarki ba, Adda Shatu ya gida ya kwana biyu, ya kewan gida, ya lbrinsu Junainah".
Cikin sauri tace.
"Kai Junaidu duka wannan tambayoyin, ka bari mana in tambayeka ya jikinka, yasu Iri da Laure da Innaji da jikin".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah Adda Shatu duk jikinmu da sauƙin wasuma duk an sallamesu, yanzu nida Hamidu da Adamune kaɗai muka rage, kuma jikin da sauƙi sosai.
Sai dan Baba Madune yana shan wuya,
Satin daya wucema an sake yi mishi aiki".
Cikin sanyi tace.
"To yanzu su waye ke kula daku".
Kanshi ya rausayar tare da cewa.
"Uhumm mufa yanzu bamu da matsalar komai Adda Shatu kwantar da hankalinki, mun samu gata da kulawar wani babban likita mai mutunci.
An canza mana asibiti ma an kawomu wani asibiti kamar na ƙasar woje".
Cike da jin daɗi tace.
"Alhamdulillah, dama dukkan tsanani yana tare da sauƙi".

Dogon numfashi Junaidu yaja tare da cewa.
"Adda Shatu, ashe mun samu nasara, an kora mana mugun babarbarenen nan,".
Uhum tace a taƙaice.
Shi kuwa Junaidu cigaba da mgna yayi.
"Adda Shatu Ya Salmanu ba lfy, yazo dubamu da jiki shima an kamashi gado.
Shi yake cemin wai su Bappa sun tafi Lardi. Ayyah Adda Shatu yanzu sai yaushe zasu dawo? Kina mgna dasu ne?".
Cikin dariya tace.
"Faɗi gsky dai Junainah kake son tambaya dai. Junaidu.
Suna lfy ina mgna dasu. Sai bayan salla zasu dawo."
Da sauri yace.
"Dan Allah Adda Shatu turo min number su".
To tace tare da gyara konciyarta.
Nan dai suka ɗan yi hira, kana sukayi sallama.
Sannan ta tura mushi number su ɗin.


Suna gamawa ta kira Number Bappa.
Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga.
Cikin jin daɗin jin muryarshi tace.
"Ina kwana Bappa na".

"Lfy lau Alhamdulillah Shatu ya Azumi, da baƙon wuri".
Cikin sanyi tace.
"Alhamdulillah, Bappa yaushe zaku dawo".
Dariya yayi mai ɗan sauti kana yace.
"Bayan salla".
Cikin lumshe ido hawaye na zuba tace.
"Bappa ina jin kewarku, bani da kowa nawa kusa dani.
In na tuno su ya Giɗi hankalina na tashi Bappa inyi ta kuka babu mai sanin irin ciwon da nakeji a raina".
Cikin sanyi yace.
"Kwantar da hankalinki Shatu, su Ya Giɗi suna raye, sai dai suna cikin mawuyacin hali, suna buƙatar addu'o'in ki musamman a cikin wannan mata mai alfarma, na sanki bakya wasa da riƙo da ibada, amman ki ƙara kan yadda kike, in sha Allah wata rana zasu dawo garemu, cikin sauƙaƙƙiyar hanya, addu'a itace abinda suke so, shiyasa na gaya miki abinda Allah ya nuna min a mafarki a kansu".
Cikin sassanyan kuka murya can ƙasa tace.
"Zanyi Bappa zan ƙara zan dage, kuma zan roƙi a tayamu addu'o'in a masallatai da wurin tabsir."
Cikin jin daɗi yace.
"Yauwa Shatu na, ki kwantar da hankalinki, ki zauna lfy da mutanen da kike tare dasu, kiyiwa mijinki biyayya, kiyiwa mayanshi biyayya bana son musu in babba ya gaya miki abu matukar bai saɓawa shariyar musulunci ba."
Cikin sanyi tace.
"To". Da sauri yace mata ga Junainah".
Cikin jin daɗi tace.
"To a bata waya".
Tsalle Junainah tayi tare da cewa.
"Adda Shatu, kizo Lardi garin da daɗi kullum sai an gasa mana zabbi ko Tattabaru, insha nono da zuma inci naman insha zuma, inci su inabi sai na ƙoshi".
Cikin so da ƙauna da shaƙuwar ta da yarinyar tace.
"Allah sarki Junnu ke ko kewata bakiyi bako?".
Dariya tayi tare da cewa.
"Nayi kewarku mana harda Ya Junaidu ma nayi kewarshki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Na bashi number ku, zai kira ku gaisa".
Tsalle tayi tare da nufar ɗakin Ummey.
Ita kuwa Shatu cikin dariya tace.
"Azuminki nawa".
Da sauri tace.
"Azumi na ɗaya ranan nayi rabi daga safe zuwa azahar jiya kuma na ƙarisa rabin daga azahar zuwa mangriba".
Wani irin dariya ne ya rufe Shatu dariya takeyi sosai.
Kewa da bege da son ƙanwar tata ya rufeta.
Da Sauri ta tsagaita da dariyar jin Junainah na cewa.
"Adda Shatu Bappa yayi aure an samo mana wata Inna mai kirki".
Cikin mamaki tace.
"Ke Junnu ƙarya ba kyau fa".
Da sauri tace.
"To ga Ummey ki tambayeta kiji".
Ajiyan zuciya ta sauƙe jin muryar Ummey cikin sanyi da jin daɗi tace.
"Ina kwana Ummey na ya gida, ya Junnuna nayi kewarku, Ummey wai da gaske Bappa yayi aure".
Murmushi mai faɗi Ummey tayi tare da cewa.
"To duk Alhamdulillah muna lfy eh Bappa yayi aure an bashi ƙanwar innarku, Indo kin santa ai ita take bin innarku, Bata taɓa haihuwa ba, to ashe mijinta ya rasu.
Shine yanzu aka aura mishi ita. Kuma tanada hankali kamar innarku".
Cikin sanyin jiki tace.
"Eh na san Umma Indo tanada kirki, to Allah ya baku zaman lfy yasa kuyi irin zaman da kukayi da Inna".
Amin Amin tace kana tai mata nasiha Sannan sukayi sallama.

Daga nan ta miƙa ta nufi ɗaki dan yin salla.

Ana idar da salla suka fito, kitchen suka nufa ita da Ummi da Saratu da tun ɗazu tana nan.
Suka fara aikin buɗa baki sunayi suna kimtsa komai.


Kafin shida ta cikama sun gama komai.

Yanzu in sun zo buɗa baki ita da Ummi da Hibba tsakiyar falon suke dawowa.
Jalal, Jamil, Imran, Sulaiman, kuma su zauna a dinning table.

Ya Jafar kuwa wani lokacin har can falon Sheykh zai wuce suyi buɗa baki a tare.
Kana su tafi masallacin.

Haka dai komai yaketa wakana cikin aminci da tsari.
A wurin al'ummar Annabi kowa ya nitsu ya maida hankali kan ibada domin neman rabauta.


Ƙarfe takwas dai-dai suka shiga kitchen dan yin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login