Showing 138001 words to 141000 words out of 180927 words
Chapter 47 - GARKUWA Book 1 Original Pdf By Garkuwar Fulani.txt
ce mata.
"In Allah ya kaimu gobe iwar haka ƙarfe goma na dare zuwa sha ɗaya jirginmu zai tashi Umaymah".
"Kai da waye zaku tafi ne?".
"Nida Dr Aliyu, da Barrister Kamal, sai kuma Ya Hashim da Galadima, da Wambai da Abba na da cimgan ɗin shi".
Da sauri tace.
"To wai kana nufin kai bazaka je da taka cingam ɗin bane?".
Cikin sanyi yace.
"Kiyi haƙuri Umaymah dan Allah na roƙeki kada kice inje da kowa, dan Allah a barni mana in huta in na bar ƙasar kam".
Shiru Umaymah tayi saida taji ya kai ayane tace.
"Shi kenan Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy, kuma muna nan tafe".
Amin Amin yace kana sukayi sallama.
Washe gari kab mutanen masarautar Joɗa masu zuwa Umrah sun gama shirin su.
Bayan ansha ruwa anyi sallan isha'i ne suka shiga kitchen dan aikin sahur, koda ta ɗauko Foodflaks ɗin da akasa mishi abin buɗa baki ko buɗe su baiba.
Hakane yasa Ummi tace to maza ta dafa mishi wani abun.
To tace kana ta juya ta ɗauko, kaza, kwai, dankalin turawa kaɗan, maggi, gishiri, tattasai, attaruhu al'basa mai Curry,
Duk ta matso dasu kusa.
Sai kuma ta ɗebo Kabeji karas.
Ta miƙawa Saratu tace.
"Yauwa Sara goga min su ƙananan, kada ki haɗasu wuri ɗaya, kana ki yayyaka min al'basa sannan ki jajjaga min wata."
Ta faɗin tana tura mata Attaruhu da al'basan.
Cikin nitsuwa Saratu tace.
"To Aunty ba matsala".
Ita kuwa Ummi meda hankali tayi kan girkin sahur ɗin.
Wanke rabin kazar tayi, tare da sata a tukunya ta watsa al'basa da maggi da tafarnuwa da citta da kanamfari kaɗan.
Sannan ta rufeshi. Tasa wuta yadda ya kamata.
Kana ta jawo robar dankalin ta fara ferewa tare da cewa.
"Allah aikin nan yana yawa Ummi, kusan wuni muke a kitchen mu kuma kusan kwana shima wai bazaici abuba sai sa mutane aiki".
Tayi mgnar cikin gajiya da kuma iya gskyar ta, dan muddin kasha ruwa tafa burinka ka samu ka huta.
Juyowa Ummi tayi ta ɗan kalleta tare da cewa.
"A'a ai bakya son hutun tunda kikaje kika samu Juwairiyya kikace ta huta taji da aikin gidanta, nan zaki rinƙa yi, sannan in Hajia Maman ta aiko ki kora Hadiman dashi, ko kisa Hibba ta kaiwa bayi shi.
Kinga duk sun gaji sun daina kawowa, sai Na Gimbiya Aminatu, shi kuma Sheykh yace a dena kawowa tunda kice zaki iya da aikin.
Yanzu da kin bari suna kawowa dai da wata ranama sai munga dama mushiga madafa".
Sunkuyar da kanta tayi tare da yin shiru kamar bata nan.
Yes ta san duk abinda Ummi ta faɗa hakane.
Ƙarisa feree dankalin tayi kana ta wonƙeshi fes ta ɗaurashi a wuta, ya dafu sosai kana ta sauƙeshi a gefe.
Zuwa lokacin kazar ma tayi lugub, haka yasa ta sauƙeshi ta juyeshi a plate, zare ƙasusuwan tayi duka, sannan ta ajiyeta gefe kusa da dankalin.
Jajjageggen Attaruhu da al'basan da Saratu ke miƙa mata ta amsa.
Cikin plate ɗin dafeffen dankalin ta juyeshi kana tasa kazarma a ciki.
Sannan ta jujjuyasu ta caƙuɗasu da kyau, kana tasa Maggi gishiri ɗan ƙanƙani, sai kuma Curry.
Kwan dake gefe cikin ɗan wani kwanon tangaran ta jawo, ta fasa kwan ta juye cikin haɗin kaza da dankali da jajjagen ta ɗan gwarayasu.
Hibba data shigo yanzu ne tace.
"Yauwa My Aunty dama kwaɗayi ne ya koroni nazo in shiga kitchen."
Murmushi tayi tare da cewa.
"To matso ki tayani aikin ɗan zuba min ruwan zafi kan Karas ɗincan.
In yayi ɗumi ki juye ruwan cikin kwandon kabejin nan ruwan zafin ya ɗan razana ganyen, sai ki miƙo min shi nan".
To tace tare da fara aikin.
Ita kuwa Shatu ɗiban haɗin ta rinƙayi tana mul-mulawa kamar Yan boll,
saida ta gama sannan, ta ɗaura man gyaɗa.
yayi zafi ta fara suyasu,
saida ta soyasu duka tasa a Foodflaks kudun kada yayi sanyi ta matsar dashi gefe.
Kana ta matso ta ta amshi Kabeji da Karas ɗin.
Mai tasa kaɗan a tare da al'basa, kana tasa jajjagen kaɗan, ta soyasu, sannan ta ɗauki sauran murmusheshen kazar tasa a ciki kana ta juye Kabeji ta Karas ɗin, sanna tasa Maggi, mintuna biyu zuwa uku ta sauƙesu.
Ta zubawa Hibba da Ummi kana tasawa Sara.
Sanin ya dawone yasa ta shirya mishi komai a tray'n.
Kana ta nufi Side ɗinshi.
Ummi kuwa da Hibba a falon suka zauna suka fara ci suna santi.
Ita kuwa Saratu tattare wurin tayi ta kimtsa komai ta goge sauran kwanuka kana ta tafi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, tuni ya gama kimtsa komai da zai buƙata in yayi tafiyar.
Bai wani ɗauki abu da yawa ba.
Komai na ɗauki shi ya kimtsashi bisa tsari.
A hankali ya taso daga bakin gadon hannu yasa ya shafa cikinsa,
Yunwa yakeji kuma ya gaji da masan shiyasa yau bai kulaba.
Folon ya nufo tare dasa kuɗin dake hannunshi a al'jihun jallabiyarsa.
A hankali ya tura ƙofar ya fito.
A dai-dai lokacin itama ta turo ƙofar shigowa falon .
A hankali ta shiga
Tsakiyar falon ya nufa,
bisa kujera ya zauna, ita kuma kanta a sunkuye ta iso inda yaken.
Ɗan sunkuyowa tayi ta ajiye tray'n kan santa table ɗin, gabanshi.
Kana a hankali ta fara miƙewa zata tashi.
Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta, da yatsarshi ya nuna mata ta zauna.
Cikin kwaɓe fuska tace.
"In zauna?". Kanshi ya gyaɗa mata alamar eh.
Cikin turo baki ta harari gefen fuskarshi, kana ta ɗan rusuno a hankali ta zauna.
Bakin kujerar dake bayanta.
Cikin muryar ƙunƙuni tace.
"Bacci nakeji".
Bai kulata ba, sai ma gyara zamanshi da yayi ya nuna mata plate ɗin gabanshi.
"Cikin cinna bikin sama tace.
"Bana gane kurmanci".
Juyowa yayi ya watsa mata narkakkun idanunshi da bata iya gano meke cikinsu cikin nata.
Karon forko kenan data ga zahirin yadda kalar ƙwayan idonshi suke, sosai kwarjinshi da haibarshi ya danne tsiwarta, a hankali ta matso kusa da inda yake.
Rusunawa tayi har ƙasa a hankali ta buɗe plate ɗin data shirya mishi Chechen balls da ganyen Fork ta ajiyeyi mishi gefen plate ɗin kana tasa hannun zata ɗauki flaks alamun zata samunshi tea a cup ɗin.
Yatsarshi manuniya ya ɗan ɗaga tare da kaɗa mata ƴatsar alamun bai sataba.
Yamutsa fuska tayi tare da turo baki cikin yin ƙasa da murya can cikin maƙoshinta tace.
"Karkaci ma in kaga dama".
Ta gefen idonshi ya kalleta ba tare da ya juyoba yana kallon yadda takeyin mamul-mamul da lips ɗinta,
Gyara zamanshi yayi tare dasa hannun ya ɗan ɗauki Fork ɗin Chechen ball ya ɗan soka
kana ya ɗago alamun zai kai bakinshi sai kuma ya maida cokalin ya ajiye.
Ɗago kanshi yayi ya zuba mata ido na 3 second kana ya nuna mata idonshi tare da lumshesu alamun ta rufe idonta tako gane abinda yake nufi.
Cikin gunaguni tace.
"Nifa zan tafi bacci nakeji, ba sai na rufe idona a nanba zan tafi kaci abinci k".
Shiru tayi ganin kallo da yake mata da mayun idanunshi.
tura bakin tayi tare da sunkuyar da kai kana ta murguɗa bakin.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, numfashin ya ɗan fesar kana a hankali ya muskuta ya gyara zamanshi, kaikaicewa ya ɗan yi yasa hannunshi cikin al'jihun jallabiyarsa. rafan dubu-dubu sabbi dal-dal ya fito dasu guda shida.
Miƙo mata su yayi.
Hannunta ta miƙo a hankali ta amshi kuɗin.
Gyara zamanshi ya kumayi kana yasa yatsunshi biyu ya jawo ɗaya plate ɗin ya rufe ɗayan.
Tsuke fuskarsa yayi da kyau tare da kafeta da ido cikin kakkausar murya yace.
"Yau zanyi tafiya daga yanzu, zuwa ƙarfe biyu. Duk inda naje inada lbrin gidan nan duk abinda zakiyi zan sani, duk motsin masarautar Joɗa.
Saboda haka ki kiyayi kanki da yiwa mutane tijara,
Bana son fitsara da rashin sanin darajar manya, ki tsaya matsayinki, bana son shishshigi cikin al',amuram rayuwata.
Ki kuma kiyayi murguɗa wannan bakin fitsarar in ba hakaba wata rana in kin murguɗa minshi bazai dawo dai-dai ba haka zai zauna a murguɗe a karkace, Allah ya nuna miki matsayi da darajar miji."
Ƙasa tayi da kanta tare da cewa.
"Kuɗin na meye ne".
A daƙile yace.
"Na yagawa ne, kije ki yaga ki zubdasu".
Kallonshi ta ɗan yi ganin hankalinshi baya kantane, ta miƙe tsaya ta juya ta fita.
Shi kuwa bayanta yabi da wani irin kallo.
Sosai yaci Chechen balls ɗin dan yayi daɗi sosai, kuma gashi rabanshi da abinci tun jiya iwar hakan, dan haka yaci iya abinda zai iya ci, kana ya miƙe yaje yayi wonka ya fara shiryawa.
Ita kuwa Shatu tana fitowa a falo ta samesu gaba ɗayansu harda Ya Jafar da Aunty Juwairiyya da kuma. Su Jalal da Hajia Mama.
ganin hakane yasa ta ɗan juya ta nufi falonta bedroom ta wuce taje ta ajiye kuɗin sannan ta fito.
Gefen Ummi ta zauna kusa da Hibba suka ɗan fara hira da Hibba ko inda Mama take bata kallaba.
Can ya fito cikin shigarsa ta yau da kullum.
Da sauri Jalal ya miƙe ya amshi ƴar Kekkyawar jaka ta maza dake hannunshi.
Dai-dai lokacin kuma Ya Hashim ya shigo tare da cewa.
"Sheykh mu tafi lokacin yana ƙurewa".
To yace kana ya kalli Ummi, Mama, Aunty Juwairiyya, Hibba, yace.
"To zamu tafi".
Kusan haɗa baki sukayi wurin cewa.
"Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lfy ya dawo daku lfy".
Amin Amin sukace.
Ƙwayar idanunshi ya ɗan juya ya kalli inda take ba tare da kowa ya gane ya kalletanba, kana suka juya suka tafi nan su Jalal Jamil duk suka fito dan sune zasu kaisu Airport.
Daga nan suka tafi sha biyu dai-dai jirginsu ya tashi a international airport Ɓadamaya.
Sai kusa ƙarfe ɗaya su Jalal suka dawo,
Sosai suka mamakin wannan karon Ya Jafar bai ce zaibi Sheykh ba.
Haka dai rayuwa tai-ta juyawa sa'a da wuni yau azumi ashirin ne aka kai wanda bahaushe ke cewa an gama goma na wuya za'a shiga na ɗokin salla.
Tunda Sheykh ya tafi baiyi mgnar da kowaba a cikinsu har yau kwanansa biyar.
Yana can ƙasa mai tsarki ibada tayi daɗi baya tuna kowa baya tuna komai sai kusanci yake nema da yardar mahalinsa.
Ko bacci Allah ya yaye mishi sai yayi baccin awa ɗaya zuwa biyu a wuni daga wannan kuma ya gamsu.
Kullum a a masallaci yake kwana.
In gari ya waye sai yayi walahanshi yayi karatun awa biyu, sai ya tafi gidan ƙanan Sitti dake nan Madina wanda shidasu Baba Kamal duk nan suka sauƙa.
to a nanne zai ɗan yi bacci.
To yau kuma shine daren da za'a fara tuhajjudi kuma sannan yaune suka baro Madina suka iso makka.
Kai tsaye gidansu Sitti suka wuce.
Nan suka samu itama Sitti da ahlinta sun iso, Umaymah ma da Haroon yau suka iso.
Kana Ibrahim ma da ahlinshin sun iso daga ƙasar Cairo sosai Sheykh Jabeer yaji daɗin hakan.
Yau ɗin kuma
Yana ɗaya daga cikin dararen da ake tsammanin laylatul Ƙadir.
Kasan cewar babbar zuriya yake.
Sheykh Jabeer Ali, ɗane ga Sheykh Ali jikan Sheykh Abdulkareem kenan,
Wanda sunanshi aka sawa Jabeer.
Yana matuƙar son Jabeer sosai.
Hakan yasa tare suke shiga harami tare suke fitowa.
A nan gida Kautal kuwa hada-hadan jama'ar musulmai na tafiya bisa tsarin addinin musilunci kowa na shirin salla da kuma tarban wannan kwanaki goma na ƙarshe.
Yau miyar shuwaka sukayi da tuwo.
Suna gama kimtsa komai ne suka dawo falo.
Tv suka kunna suna kallo, suna ɗan hira.
Gyara zama Ummi tayi tare da cewa.
"Lallai yau in munyi garaje zamu makara".
Da sauri Shatu tace.
"In sha Allah bazamu makara ba, wannan uban bindigar da kukace in lokacin sallan Tuhajjudi yayi zava bugata ai zata tashemu".
Hibba ce ta ɗan gyara kwanciyar ta, tare da cewa.
"Kalli lokacin shabiyu saura yanzuma za'a fara, Ummi kai mana Tashar Saudi".
Ta ƙarshe mgnar tana kallon Ummi da Rimote ke hannunta.
To Ummi tace kana ta. Juya musu tashar.
Inda suka samu tuni sun fara sallan Tuhajjudi.
Inda ake nuna harami kai tsaye.
Shiru sukayi suna kallon yadda haramin ya cika yayi maƙil da al'ummar Annabi.
Kab an nitsu bakajin komai sai sautin muryar limamin dake karatun al'ƙur'ani cikin zazzaƙar murya mai daɗin sauraro.
Koda aka tafi ruku'u gaba ɗaya a tare aka sunkuya hakan yasa abin yayi wani irin kyau mai ɗaukar hankali.
Sun jeru tamkar zanen fefeyi.
Hakama da suka tafi sujjada.
Musamman da yake cameran ɗaukar sama akayi.
Suna ɗagowa kuma aka juya cameran ya fuskanci limamin da sauran mamu na sahun forko wanda duk manyan malamai ne.
Cikin wani irin kallo Hibba ta miƙa da ƙarfi tare da...!
Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 ko kiyi min TRANSFER din 1k Dan samun Special Group ta asusuna na 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276.
ByTare da cewa.
"Lahh Ummi kalli Hamma Jabeer kusa da Uncle Jabir Ali ɗin can".
Cikin Murmushin Ummi tace.
"La ai kuwa, Allah sarki masha Allah, tabarakallah. Allah ka ƙarawa Annabi daraja, Allah ka ƙara bamu hasken addini da imani a zuƙatanmu."
Amin Amin Hibba tace.
Tare da juyowa ta kalli Shatu da tayi kamar bata jisu ba,
Sai tea ɗinta take zuƙa a hankali.
A zahiri zakace idonta kan cup ɗin yake, amman a baɗini kan allon TV'n idonta yake, ta zubawa fuskarshi ido. Duk da bawai kai tsaye shi kaɗai ake ɗaukaba, limamin dake jansu ake ɗauka hakan yasa suma suka fito da yake yana cikin mamun limaman sahun forko.
Sosai take ƙare mishin kallo tare da tsarin shigarsa dana mutanen da yake cikinsu.
Sam bazaka iya bambance shi da suba, Especially ma Sheish Jabir Ali da yake matuƙar kama dashi.
Haka nan taji wasu irin zafafan hawaye masu ɗumi suna tsastsafo mata cikin jijiyoyin idonta.
Ta kuma kasa janye ƙwayar idanunta kanshi. Tana kallon tsarin shigarshi da kullum take ganinshi a matsayin takura.
Lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su.
Ummi ta kalla wacce farin cikin ta ya fito fili.
Hakama Hibba. Sai murnar abun takeyi tamkar tayi tsalle ta shiga cikin TV'n,.
Ganin sun sunkuya kai ruku'uh da zasu tafi sujjada ta biyu ne, kuma an ɗaga camerar an maidata ɗaukar samane.
Yasa ta miƙe a hankali bisa santa table dake tsakiyar falon ta ajiye cup ɗin kana ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi kinji masallacin Joɗa ma sun fara sallan kuma muna zaune".
Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa.
"Farin cikine ya rufeni Shatu,. Muje muyi al'walan mu tafi".
Uhum tace ta juya ta nufi falonta tana mai share hawayenta da har yanzu suke zubowa, tanajin zuciyarta na amsar wani nannauyan abu a kan Sheykh, ta yarda ta gamsu cewa mutun me ibada da imani da ilimi abin sone a zuciyar kowane mutum na gari.
Bayan sunyi al'wala ne suka fito cikin manyan jihabai ƙatti har ƙasa suka nufi woje.
Ananne Shatu tai mamakin ganin yadda kusufa-kusufa matan masarautar ke fitowa, duk suka nufi hanyar zuwa masallacin ta ƙofar dasu Lamiɗo ke bi.
Suna fitowa jikin masallacin sai ga wani ƙaton rumfa na ƙara an lailayeshi da wani irin yashi fari ƙal-ƙal kana ga hasken wuta a cikinsa.
ko wacce da sallaya a hannunta tuni wasu kuma sunma shimfiɗa sallayunsu sunbi jam'i hakanan matan maƙota da sauran matan bayi da hadimai duk nan suke zuwa.
A jeru gaba ɗaya ananne ga kafaɗar matar sarki gata baiwa.
Babu matsayi ko milki bare isa ko ƙasaita.
Haka dai suka bi jam'i sai ƙarfe uku aka idar akayi addu'o'in kana akashafa aka kai sujjadar ƙarshi ta witirin.
Kana akayi taiya akayi sallama duk kowa ya nufi gidanshi.
Daga nan kuma aka kama aikin sahur.
Suna dawowa Hibba ta kuma kunna TV nan ta samu su tuni su sun idar. Wasu nata ɗawafi ne sai addu'o'in ake jerawa.
wanda sai kaji tsikar jikinka na tashi sabida yadda yake ratsa zuciya da jini.
Washe gari da bayan sallan isha'i da asham, yanzu Jalal da Jamil ne kaɗai ke zuwa dan Imran da Sulaiman ma dasu aka tafi.
Haka yasa yanzu duk suna zama a Dinning table suyi buɗa baki a tare.
Jalal ne ya ɗan kalli Ummi cikin cin Beans salad da Shatu tayi musu.
Hibba ce keta santi tana cewa.
"Alhamdulillah yanzu dai saura mana azumi tara ko takwas".
Murmushi sukayi, ita kuwa da sauri tace.
"Kai takwas nema in sha Allah".
Jamil kam tuni yake dariya tare da cewa.
"Tara ne".
da sauri ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi wai haka ne?".
Cikin dariya tace.
"A a ban saniba Hibbat."
Plate ɗin data zuba ferfesun jan nama ta jawo tare da fara ci tana lumshe ido tace.
"Takwas ɗin nema in Allah ya yarda".
Allah yasa haka Shatu tace.
Sai yanzu Jalal ya ɗan kallesu tare da cewa.
"Ashe dai duk kanwar jace".
Murmushi Ummi tayi kana sukaci gaba da cin abinci.
Yau dai ana zaton salla saura kwana biyar ko shida.
Da hantsi suna zaune dan yau sun tashi da wuri.
Aunty Juwairiyya ce tayi sallama tare da shigowa, Bayan Ummi ta amsa mata.
Gefen Hibba ta zauna tare da cewa.
"Alhamdulillah Ummi ɗinkunan mu sun dawo, yanzu KB ya kawosu ya shigo ko?".
"Eh ya shigo mana".
Juyawa tayi ta kalli Hibba tare da cewa.
"Je kice ya shigo Hibba yana nan zaki kanshi cikin baƙar mota".
To tace tare da miƙewa da sauri.
Jim kaɗan suka shigo tana gaba da jaka a hannunta yana biye da ita a baya da ƙattin jakunkuna guda biyu da wani yaro shi shima da manyan jakukkunan biyu.
A tsakiyar falon bisa carpet suka aniye jakunkunan kana, ɗaya yaron ya juya ya fita.
Shi kuwa Kabir ya zauna a ƙasa bisa carpet ɗin tare da cewa.
"Barka da hantsi Ummi".
"Barka dai Kabiru, munyi Sa'a an cika mana al'ƙawarin ko".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Sosai ma kuwa Ummi aini telane mai amana".
Hibba ce ta ɗanyi murmushi tace.
"To ka bari a yebeka mana".
Cikin dariya ɗan matashin yace.
"A a ai duniyar yanzu kawai ka yabi kanka, dan ba lallai bane wani ya yaba maka".
Dariya sukayi duka.
Kana ya fara firfito da kayayyakin.
Ko wanne da sunan maishi a jikinshi.
In ya fito dana Ummi sai ya miƙa mata, in ya fito dana Aunty Juwairiyya da yaranta sai ya miƙa mata.
Hakama na Hibba yana fitarwa yana miƙa mata.
Shatu da yanzu ta fitone, ya kalla tare da cewa.
"Barka da safiya Sayyada Shatu".
Murmushi tayi Allah ya sani in sun ce mata Sayyada dariya suke bata wato irin ita matar Al Sheykh ko.
Cikin nitsuwa da danne dariyarta tace.
"Barka dai".
Sai kuma ta ƙara so ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi waye ne shi?".
"Telan mune". Ta bata amsa a taƙaicd.
Cike da mamaki tace.
"To ina ya sanni?".
Hibba ce ta amshi zancen da cewa.
"A hoto ya sanki, da mukaje kai ɗinkunanki hotonki kawai aka nuna mishi, ya ɗinka kuma kinga komai yayi dai-dai ko".
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Lallai kam yayi ƙoƙari".
Cikin dariya yace.
"Uhum ai na iya aikina sosai Sayyada".
Yanzu kam dariya sukayi duka.
Kana ya zaro kayanta a ƙalla kala takwas ya miƙa mata.
Amsa tayi tare da cewa.
"Sannu".
Hibba kuwa irga kayan tayi tare da cewa.
"Kb saura kala bibbiyu a