Showing 21001 words to 24000 words out of 132190 words

Chapter 8 - Matar Makaho Compelet Book by Rukayya Ibrahim Lawal.doc

cikina"

Subhanallah Sumayya cikin ne Al'ameen Daya Mike cikin tsananin tashin hankali yake lalubarta ,

Khadija ma da saurin ta ta iso ni,sannu Aunty take fada idon ta ya jika da hawaye

*****Nikam.na kasa Bata amsa kuka kawai nake hankali tashe

Khadija tashi kije ki Kira doctor eiiii sauri

Toh yaya tace tana mikewa da saurin ta

Al'ameen Kam hannun Sumayya ya Kama sai sannu yake Mata a hakan likita yazo ya sameta a halinnan

Da sauri shida nurse suka rufu a kanta tare da K'ura Khadija da Al'ameen waje,allurai sukai Mata harda na bacci lokaci daya bacci ya dauke ta,

Khadija da Al'ameen na tsaye a bakin kofa likita ya fitoh ya kira su zuwa office,

Malam Al'ameen majinyaciyar ka tana cikin condition Mai muni ya kamata ka samo kudin aiki nan da awa uku ba wallahih kome zai iyya faruwa,

Innalilahih wainnailaihir rajuun kawai suke fada,

Suka mike zuka fita a office in Khadija Kam kuka ta fara abin Yama Al'ameen yawa ta Ina zai fara anya zai yafewa kansa kuwa in yar mutane ta mutu ata dalilin rashin kudin aikin da Bai samo ba,

Yaya ya kamata Aunty tasan abinda ke faruwa muje ka fada mata ta Kama hannunsa sukayi dakin

Suna shiga suka samu Sumayya na bacci ..........

Yaya Ammar innan yazo baka nan ya bawa Aunty kudi Amma Taki karba tace na baka

Allah sarki Ammar yazo ne?

Eh yaya kana fita Yana shiga, yace ma Wai Daman Yaso kuyi sallama tafiya ne ya kamasa, na gaggawa,

Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari Yan kiyaye sa aduk inda yake,

Ameen yaya

Khadija Miko min kudin na hada da dari biyar in hannu na naje na Basu Koh zasu mata daidai a Nemo sauran su bimu bashi,

Uhmm lallai yaya kadai San asibiti bata ma matum aiki ba tare da kudi bak'oh?

Khadija bara dai naje na gwada Koh Allah zaisa a dace tunda kinga hour uku aka bamu kuma yanzun bacci take, bara naje na dawo ya fada Yana karban kudin da khadijar ke mika Masa,


Yana fita yaje wajen biyan kudi,

don Allah Dan uwa kayi hakuri ga dubu goma da dari bayar a fara mata aikin in yaso za'a cikita muku daga baya Dan Allah ku taimaka min matatace ba lfy kuma hour 3 aka bani ake son mata operation?

Amma Kai *makahon* nan Ina ga baka zuwa asibiti ne taima?

Ina zuwa ranka shi Dade sai dai ban taba kawo majinyaci irin wannan ba

Toh gaskiya ka gannin nan Koh biyar naci a cikin kudin da nake karba wallahih Sai an daure ni

Kuma anan in baka biya kudiba wallahih baza'a Mata aiki ba Koh mutuwa zatayi gwara kaje ka Nemo duk in da kudi ya shiga ya fita shawara nake baka,Amma zance a taimaka maka toh hadai asibiti ba


Shikam tsabar damuwa har jiri yakeji yana ibansa ,a rayuwar yanzun in baka dashi kana ji kana gani harka mutu indai baka da kudin jinya ba Mai taimakon ka, zama yayi a bakin barandan pharmacy in yayi shuru cikin tashin hankali da alhini,


Bayan fitar Al'ameen khadija na zaune har lokaci hawaye baibar zuba ba sai ta gogi wani ya zuba, har hour 1 yayanta Bai dawo ba,

*** A hankali nabude idona na sauke akan Khadija dake ta hawaye ido harya kumbura abinka da farin fata fuska tayi ja" khadija lafiya kuwa meya faru Naga kina kuka"??

Babu Aunty Daman na tsorata ne danaga cikin ki ya Tashi Ashe haka kike fama da Jin jiki sannu,

Murmushi nayi "haba Khadija Menene na kuka baki ga naji dauki ba"

Toh Aunty,

"Yauwa khadija nikam likita ya fadi abinda ke damuna ne, Koh yake sani ciwon cikin nan"?

Kafun ta bude baki ma sai ga doctor ya shigo,Wai har yanzun baku samo kudin aikin ba Koh bakuji condition inda nace muku tana ciki ba Wai ina MAKAHON yake ne?

"Doctor ban gane mikake nufi ba" nace ina kallon sa?

Au baku fada mata bane? Yana kallon khadija alamar tambaya

Eh doctor bata sani ba khadija ta bashi Amsa,,

"Wai meke faruwa ne kun sani a duhu" waza'a ma aiki??

Kece appendix ya kumbura sosai tun jiya na sanar dasu Amma haryau shuru Basu biya kudiba yanzun haka hour 3 na Basu su kawo kudin Dan kina bukatan aiki gaggawa Amma an share hour 1 shuru, Banga alaman zasu biya ba

Da mamaki nake kallon khadija"yanzun khadija Ina fama da wannan babbar matsala irin wannan Amma kuke mini Wasa da rayuwa Ina da kudin da Zan iyya biya ba bandashi ba"

Kiye hakuri Aunty Daman Yaya ne yace shi yake son biya

" Koh ance lallai sai yayanki ne ya wajaba ya biya ai ni Karan kaina nasan Bai dashi don Bai biya ba ai bazai zama wani abu na daban ba" menene riban ya fita yana neman bashi alhalin Ina da kudi"??

Kiye hakuri Aunty,ta fada jikinta a sanye ganin Raina ya baci

"Nawane akace kudin aikin"?

......50k ne

"Khadija tashi ki dauki key kije gida ki dauko mini jakana wani yellow a cikin whtdp nawa ki dauko mini jakan akwai kudi a ciki"

Toh Aunty ta fada tana mikewa daukan key in tayi a jakan kayana ki hadamin da wayata ki dauko darduma babba da filo, ga kayan da nacire ma kikai mini gida kisa a basket in bayan kofa"

"Kihau nepep ya kaiki kofar gida ki shiga in kin dauko kudin saiki shiga ya dawo dake ki basa 1k ya d'auki kudinsa karfa kice Zaki tafi da kafa"??

Toh Aunty ta d'auki kayan nawa ta fita a dakin, doctor Kam Dan kallo ya zama Daman tun da ya ganni yake ganin alamun Jin Dadi a tare Dani Amma abinda ya daure masa Kai mutanen da suka kawo ni asibitin abin yana bashi,mamaki harda Nurses Amma basuga fuskar tambaya ba

**komawa nayi na kwanta shima doctor fita yayi


Tsabar rudewa Khadija Koh yayanta Bata Lura dashi ba akan baranda ta wuce,

Shikam ganin lokaci na wucewa yasa ya Tashi ya shigo dakin,da sallama a bakin sa,

**Amsa Masa nayi Ina kallon sa yazo ya zauna a kujiran gefena,

Sumayya,yakira sunana

"Na'am" na amsa Masa

Kiye hakuri Sumayya na kasa kula dake wallahih nayi iyya kokari na Amma ban samu kudin ba Daman appendix ne ke damunki Kuma ya kumbura, shine ake son Miki aiki kuma........

**Da nayi niyar rufesa da matsifa Amma sai jikina yayi sanyi Jin bayanin da yake mini" ban bare ya karasa ba na katse sa"ba kome, me amfanin Ina dashi kaje kana,.. baran attaimaka maka kazo ka biya mini kudin aiki"? Karka sake mini irin wannan banaso duk abin da zai taso a waje na Koh Khadija Koh Kai, in baka dashi karka sake zuwa gun wani da sunan ya taimaka maka indai abin baifi karfina ba pls"

Kiye hakuri insha Allah bazan sake ba,

**Shuru na Masa
Jin Bata amsa ba ya sashi yin shuru


Khadija na Isa gida ta samu jama'a na cike a kofar gidan dam alamu dai wani abinne ya furu don harda motar police ga jama'an unguwan makil...............








*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* =؃?


Contact them vie
>؀?08028827241 or 09033791049
IG @umsadincense






>؀?my WhatsApp number
>???
>د? *MATAR MAKAHO* =?h?
>د?
~ Na ~


('Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa=?L?
free book >?'?

Page1?? 6?? &1?? 7??
Shigowa d'akin nayi cikin hanzari na karasa kusa da abie na banyi wata wata ba na rungume sa na fashe da kuka maicin Rai,,,,

Ji kawai nayi momy ta dakawa abie tsawa,

Kai Abdulsalam mainace maka akan yarinyar nan?,

Ai da sauri Naga Abie ya hankad'ani a jikinsa ya mike tsaye cikin wani irin hada fuska Wanda. Bansan abiena dashi ba Naga ya mike cikin hargage yake magana Sumayya fita a dakin nan banason ganin ki banace Miki bake bani ba Koh bance ki zauna a dakin kiba,

"Abie Kai nazo gani don Allah Abie Koh kowa zai juyamin baya Kai karka Bari a rabamu don Allah Abie," nace Ina fashewa da kuka,

Waye uban naki?? keh daga yau niba ubanki bane bansan wata y'a Sumayya ba kaf zuriyan shugaba babu yarinya Mai suna Sumayya ki fita a gidan nan da zuriyan mu bake bani Koh mutuwa nayi banason ganinki akan gawata,yace idanunsa na taruwa da hawaye daga Gani dai maganar fatar bakine bana zuciya ba,

"Amma abie menene nai maka da har zaka yanke dukkan alakar ka Dani har haka atunani na Koh kashe mutum nayi bazaka yanke alaka Dani ba abie ka rabani da mahaifiyata tun bansan kaina ba yanzun Kuma ka sallamawa duniya ni" wa nake dashi in ba kaiba kaf duniya nan abie why Abie why"=?-?=?-???

Nafada Ina kallonsa gani nayi hawaye nabin fuskar sa,ya daga ido Yana kallon momy,

Toh munafuki kallon me kake mini,Ke Kuma wuce ka sata a gaba tabar Mana cikin gida yanzun,

Nikam mutuwar tsaye nayi nashiga uku yaushe abie ya zama haka zaushe ya koma yaron momy,abie da na sani ne kuwa kafun na bar gidan nan Koh maganar banxa momy Bata Isa tamin a gabansa ba bare yau har tana basa umurni ya koreni,

Ban farga ba naji an janii kiiiiiii!!! Anyi hanyar steps Dani,

Cikin mamaki nake kallon abie yau ni yake ja Kamar wata saniya zai koreni a gidan sa lallai fa,

Jana yake tayi har Muka sauko falo abin gwanin tausayi,nikam kuka nake Kamar Raina zai fita gabaki d'aya naji duniya tamin zafi,
Ganin abie ya nufi kofar fita falo Dani yasa Khadija tasowa ta biyomu a baya Yan falonka da ido suka bimu wasu na dariya ganin yanda uba ke fincikar yarsa

Fincike hannuna nayi na dawo cikin falon na tsaya a gaban babuji (kanin babana) " babuji abani ducument Ina, Ina bukatar su,"


Don ubanki lokacin da uwarki ta haife ki da results ta haifiki ne,,,,,


Don haka baza'a bayar ba koma bara ma kiji daga yau Koh a kasuwa ne karki sake hada sunanki da family shugaba,

"K'warai kayi gaskiya babuji ba'a haifini da results ba Amma da kudin ubana na same su in Kuma hassadace yasa kuka k'wace karfa ku manta arziki nufin Allah ne in Allah ya tsaga da rabonka sai kayi arziki ruwa da iska Koh guguwa bazai Hanaka samuba",

"Ba karatu bane kadai abinda ke sa bawa arziki rabonsa baya wuce kansa"

"Baiwa ta jarina"sannan wannan tsinannen gidan naku wallahih ku rubuta ku aje sai yafi muku prison ganin..................

Tassss naji saukar wani azabebben Mari a kumatu na Wanda yasani sumar wucen gadi,ba kowa bane yamin Marin nan sai sahabi yaron babuji,

Ke karamar Yar iska watoh kema harkin zama Yar bariki irin mutanen gidan da kike Koh zakizo nan ki gwada Mana kin falle toh baki Isa ba ki tsaya kina gayama ubana magana in barki ya fada Yana fincikata juyawa nayi Ina kallon abie Wanda ke tsaye kansa a duke,

Bai tsaya aku Ina Dani ba har Saida ya dangana da get turani yayi waje Yana ma Mai gadi warning daga yau in ya sake barin Mai Kama Dani ya shigo gidan nan a bakin aikin sa,Yana fadan haka ya juya abinsa yayi cikin gida, ya dauko jakana da takalmi ya watso mini a jiki,

Baba buzune ya fitoh yazo inda nake zaune tunda ya jefoni ban matsa ba mamaki tsoro da kuma wani irin tsana naji ya tsargan mini na family mu duka ban cire kowa ba, aciki nayi alkawari daga yau na yanke duk wata alaka da shugaba family house,

Kayi hakuri yaro haka rayuwa take kaji,
kayi zaman auren ka ka rike mijinka Allah zai baka mafita kaji hajiya Sumayya,kayita addu'a kaima Allah ya tsareka gidan nan yanzun sai abinda matar babanka yace,
ya fada cikin tausayi,nidai Ina duke dakai sai kuka nake inda Allah ya Soni ma unguwan mu ba irin sintali bane nan kowa na cikin gidan sa Babu mutane a waje,

Jin ana kamani anason mikar Dani yasa na daga kaina Khadija ce wance bansan yaushi ta fitoh ba ,Ashe tun Marin da aka kwada mini ta ruga tayi waje tazo ta Saya,...


*******""""

Banyi musu ba na nike tsaye Kayana ta hau karkade mini nidai sai kuka nake Kamar zararriya gashi bamuda Koh sisi da zamu tare abin Hawa ya kaimu gida gashi Koh a gidan ma bani da kudin da Zan biyasa Kuma banda tabbacin yayan Khadija na dashi, yasa na Kama tafiya da kafa Ina kuka,

Dukawa Khadija tayi ta dauki jakana Dana Bari,sai hakuri take bani Amma nai Mata banza a haka muka fara fasa hanya,

Mota na gani Tasha gaban mu tayi packing Abdul ne ya fitoh a ciki ya nufe mu,

don Allah Sumayya kiye hakuri da abinda kikaje Kika tarar a gida wallahih yanzun gidan mu sai addu'a abin sai gaba gaba yake, Kuma na rasa me yasa duk gidan mu ke suka tsana,

*****Kala bance Masa ba don shima wani tsanar sa nakeji a Raina Sam yanzun naji banason ahalina kwata kwata na yanke duk wata alaka dasu daga yau Kamar yanda Suma suka yanke Dani,

***Kaucewa nayi na fara tafiya bance Masa kala ba,

Biyo ni ya sake Yi Yana mini magiya, Sumayya don Allah badon ni ba kizo ki hau na kaiki gidanki Kinga yamma yayi bazaki samu Keke napep ba anjima anan,

Wallahih Abdul Ina Ganin kimarka Inka kuskura ka kaini bango Zan maka abinda bazaka manta Dani ba Kai asuwa zakazo ka tsaya kana bani umurni wallahih daga yau Babu ni Babu Kai Koh a hanya ban sanka ba na tsaneku mugaye kawai azzalumai wallahih ku jira karshin ku,


Habba Sumayya menene laifina in sun Bata Miki ni meyasa Zaki had'a Dani,..

"Ai Wanda suka Bata mini su waye ne a gunka"?na tambaye sa Ina kallon sa ido cikin ido,

Iyayen mune da Yan uwan mu,ya bani Amsa,

"Iyayen kadai da Yan uwanka daga yau bana D'aya daga cikin family shugaba in baka sani ba ka sani yanzun ka fita harka ta "

Sumayya kada bacin Rai yasa ki ringa furta maganganu da Basu dace ba,


"Na furta Abdul Koh kaima dukana zakayi" na fada Ina wuce sa

Shikam mamaki ne yake son kashesa Anya Sumayya da ya sani ce wannan shuru shurun ashe haka take ganin bazata yarda tahau motarba yasa ya zare kudi a Aljuhunsa ya mikawa Khadija gashi Yan Mata kuhau Keke Koh ya fada Yana duban Khadija,..

"Wallahih Khadija Kika karbi kudin nan sai na nuna Miki true colour na"

Khadija Kam ta tsorata da sauri tayi gaba kamar yanda taga nayi,

Muka barsa a tsaye kamar gunki,


Tafiya muke har lokacin hawaye baibar zuba a. Idanuna ba wani irin zafi nakeji a Raina a haka muka ringa fasa unguwa unguwa muna wucewa tafiyarda tunda nake. Bantaba yin irinsa ba yau shi nake kafafuna duk sun kumbura na rashin sabo, Amma yanda zuciya ke cina Bai bare naji wahalar ba, Khadija kam Koh a jikinta,


Har mangariba yayi bamu ma kusa Isa sintali ba

Aunty Koh z???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?amu tare kekene in munje gida Yaya ya biya Kinga fa mangariba yayi ga hadari sosai? Khadija tace

Kala bance Mata ba tafiya kawai na cigaba dayi don nasan Koh na hau munje bazamu samu kudi ba tunda cinikin nasa duka ya hada ya bani Ina zai samu wasu dari da hamsin,

Tafiya mukaci gaba dayi ga yunwa don rabona da abinci tun ruwan shayen safe Amma bacin Rai baisa naji ba har aka Kira Isha adaidai lokacin aka fara yayafi sai ruwa ya sauko Kamar da bakin k'warya ganin mun iso bakin kasuwa yasa ban tsaya wani labewa ruwa ya dauke ba tunda dare ne Babu Wanda zai gane mu gashi NEPA sun dauke a haka ruwa na dukan mu muka shiga sintali hanyar gidana muka nufa tun daga nesa Muka hangesa


Al'ameen ne a tsaye a kofar gida ruwa na dukansa daga ka gansa kaga Wanda hankalin sa yake tashe,

Muna Isa Khadija ce ta fara Masa magana nikam cikin gidan na nufa don bana bukatar Jin kome,

Yaya ya Naga kana tsaye a cikin ruwa haka gashi duk ka jika lafiya Kam?

Ina Naga lfy Khadija baku dawo ba Ina Aunty take Allah dai yasa Yan gidan su basuce bazata dawo ba wallahih naji tsoro Khadija karsuce zasu rabamu?


Hhhh habba Yaya bafa wani abu da zai rabaka da matarka insha Allah sai mutuwa Kama daina mugun tunani irin wannan,

maganan dadewa Kuma abin hawane bamu Bamu ba da wure, shiyasa naso ma mu kwana Amma Aunty tace mu dawo kar hankalin ka ya Tashi(Tamar karya don ya kwantar da hankalin sa)

Shap in kuka kwana ai nashiga uku kenan ,

Amma me yasa baku Kama hanya da wure ba kuka bare sai yamma kuka fitoh,gashi ruwa ya muku duka,

..Kai Yaya abinci fa muka tsaya muka ci,
Yauwa Yaya kasan me yau ran aunty a bace yake don Allah ka bita. A hankali inda Hali ma karka Mata magana yanzun ka Bare sai da safe ka Mata magana in ma kaga change a tare da ita ka Mata uzuri,

Meya faru Khadija?

Ba kome Yaya kawai dai sun D'an samu matsala da yaran gidansu ne sai Randa ya baci,


Bai yarda ba don yasan halin Khadija akwai surutu akwai boye abinda ba'a sata fada ba,shiyasa kawai ya shanja zancen,

Toh khadija muje ciki in ruwan ya tsakai ta sai na raka ki gida

Ah ah Yaya dare yayi fa yanzun ana neman 8:00 na dare nikam Zan koma Goggo zatayi fada,

Muje na rakaki gida sai nama Goggo bayanin dalilin jimawar ki karta Miki fada,

toh yaya,ta fada tana Kama hannunsa suka nufi layin su Goggo Amina,

Nikam

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login