Showing 21001 words to 24000 words out of 49932 words

Chapter 8 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf

ki barni,
na shiga uku ni Salamatu." Baba Abbakar ne ya
dinga lallabata da kwantar mata da hankali,
zuwa gurin asuba kuma sai Abu ta fara suma,
dan haka gari yana dan kara haske aka samo
mota suka kwashe ta sai asibitin murtala
(Murtala general hospital). Sun yi sa'a suna
zuwa aka karbe ta, nan da nan aka rubuta musu
abinda zasu siyo, Baba Abbakar babu ko sisi a
jikinsa don haka ya zame ya gudu, Sala ce ta
kwance jakarta ta dauko kudin ta bada, nan da

nan aka daura mata karin ruwa, sai da babbar
leda ta shiga jikinta sannan ta fara dawowa
hayyacinta. Cikin ikon Allah kafin azahar ta
dawo hayyacinta, da taimakon Allah da
taimakon karin ruwan da aka yi mata. Sai
washegari da likita ya dawo yaga jikin ya dan
fara kyau ya rubuta mata gwaje-gwaje bayan
'yan tambayoyi da yayi mata, gwaji kala uku aka
rubuta mata, akwai na taifot da na maleriya sai
kuma wanda yake tantama a kansa dan ance
masa budurwa ce, amman dai ya zama dole a yi
din don ya tabbatar da binciken sa gwajin masu
ciki. Sala ce ta taimaka mata suka nufi dakin
gwaje-gwajen aka auna komai aka basu
sakamako cikin ambulan, suka ce ta kaiwa
likitan da ya turo su, suka koma dakin da aka
kwantar dasu suna jiran zuwan likitan. Sai da ya
gama ganin marasa lafiya sannan ya dawo dakin
nasu, ya fara bin gadaje yana dubawa har ya zo
kan na Abu. Ya gyara gilashin din idonsa gami
da kara tambayarta jikin nata, Sala ce ta amsa
sannan ta bashi sakamakon dake cikin ambulan.
Ya amsa ya farke yana dubawa, ya kuma gyara
gilashin din dake idonsa yana kallon Abu,
sannan yace da Sala, "Baba kika ce budurwa ce
ko?" "Fil ma kuwa a ledar ta. Don ko kudin toshi
ba'a kawo ba balle a sanya rana balle kuma ta
kai ga biki ba." Sala ta bashi amsa da sauri. Ya
girgiza ka ya ce, "Haka ne." Yace, "Baba ku
same ni a ofis dina yanzu zan baku sallama dan
ta warware." Bai jira jin amsar su ba ya wuce
gado na gaba. Sun dade tsugunne a kofar ofis
din nasa da kayansu a zube suna jiransa, har ya
zo ya bude ya shiga suka rufa masa baya, ya
nuna musu gurin zama sannan ya dauki wata
takarda ya fara rubuce-rubuce a cikinta



Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Idan zuciya ta gyaru 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 07:50 PM, 28-Jan-16
Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU
_________________ Na
________Fauziyya D Sulaiman_____
Bayan ya gama ya daga kansa yana kara kallon
Abu wacce tayi wuki-wuki, ya ma rasa ta inda
zai fara, can dai ya daure yace, "Baba wannan
diyarki ce?" Batayi mamakin tambayar ba don
jama'a da dama kanyi mamaki idan aka ga
'ya'yanta wanda sam basa kama da ita, dan
kamar mahaifinsu suke yowa wanda idan ka
gansu tamkar Larabawa suke, ita kuma gata nan
bakikkirin, don haka baki a hangame tace, "Ka
ga bamuyi kama ba ko? Ai mutane da dama na
mamakin ace 'ya'yana ne don idan suna yara
suna kuka a gidan biki har cewa ake na
maidawa uwarsu sai anga na ciro mama ina
basu tukunna ake yarda nawa ne, ai diyata ce ta
biyu. Ha ha ha" Ta saki dariya daga karshe.
Ya girgiza kai cike da takaici ya ce, "A yanda na
gani a jikin kati yanzu shekararta goma sha
hudu ko?" Ta kuma yin dariya tana fadin, "Haka
ne likita ka ganta gaba-gaba haka nan take da
girman jiki babu shekaru, ka ganta kamar 'yar
shekara ashirin ko? Girman jikin ne kawai
musamman yanzu da take cin kayan dadi sai
tayi wani fari da kiba kamar diyar wani
basarake, bul-bul da ita gwanin sha'awa."
Likitan yayi murmushi don ya gano inda Abu ta
samu matsala, wato rashin uwa tagari ne, dan
haka babu wani boye-boye ya ce, "Hajiya ke da
yarinyarki ta sauya kin tambayeta dalilin da ya
sanya ta sauya?." "Haba dai likita wace irin
tambaya ai jin dadi shi ke sanya mutum ya
sauya, ka ga dai yarinyar nan kullum da sai ta
dauki talla safe da dare, yanzu kuwa ta samu
mai ba ta kudin sai dai taci ta kwanta sai dai
makaranta." Ya girgiza kai cike da takaici ya ce,
"Haka ne, to tsaya na gaya miki diyarki tana
dauke da juna biyu, ma'ana ciki, dan haka
wannan sauyawar da tayi ba wai ta jin dadi

bace illah ta ciki....." Sala ta mike da tashin
hankali ta dafe kirji cikin karaji tana fadin, "Me?
Likita cika fa kace? Lallai baka san aikin ka ba,
dubi Abulan duka nawa take da zata yi ciki? Kai
dai ka kara dubawa ka gani ko katin wata ka
dauko." Ita ma Abu dake zaune tana jin caftar
da Likita da Sala ta dafe kirkji da sauri tana
fadin, "Na shiga uku ciki ne dani." Sai ta saki
kuka. Sala ma ta sanya kuka tana fadin, "An ya
likita ba karya ka fadi ba? Ko kuma aljanu ne
suka hura mata ciki ka ga kamar ciki ne da ita,
dan yaushe ma ta fara al'ada duka, ka dai sake
dubawa." Shi dai rubutunsa kawai yake yi akan
wata takarda, sai da ya gama sannan ya daga
kansa ya mika mata kayin yana fadin, "Ko ki
yarda ko kada ki yarda 'yarki tana da ciki, dan
haka idan baki yarda ba sai kije wani asibitin a
duba miki ita, na gama daku sai ku tafi, a gaba
a dinga kula da tarbiyyar yara." Ta kuma
fashewa da kuka tana fadin, "Don Allah likita ka
taimake mu, yanzu yaya zamu yi da wannan
abin kunyar? Na shiga uku ni Salame....." "Kinga
Hajiya ku fita can kuyi kukanku don na tashi zan
kulle ofis dina." Ya mike yana hada kayansa. Ta
tsagaita kukan tana fadin, "Likita yanzu babu
wani taimako da zaka yi mana?" "Kinga Baba
babu wani abu da zanyi bayan addu'a Allah ya
rabata da shi lafiya, kuje waje zan kulle ofis dina
nace." Yana magana yana kallon agogonsa. Haka
nan suka fice daga Ofis din Abu tana kuka Sala
kuma duk ta gigice, suka yi zaune turus a gaban
kayansu kowacce tana kuka, har yazo ya wuce
su bayan ya kulle Ofis din nasa. Can dai Sala ta
daure ta ce, "Wai ni Abula garin yaya kika yarda
har yayi miki ciki ne ma? Ai da kince yayi wasu
'yan dabarun da bazaki samu ciki ba" (Fauza
tace, kuji fa jama'a bata bakin ciki da lalata
mata diyar da aka yi sai ra samun cikin, shima
don tana jin kunyar idon jama'a ne, kai tir da
irin wadannan iyayen). Abu ta cuno baki gaba
tana wani kumbure-kumbure tace, "To nima na
san zan sami cikin ne Sala? gashi yanzu ya gudu
ya barni da ciki. Kuma na san 'yan gidansu ba

zasu yadda shi yayi ba, na shiga uku yaya zanyi
da gorin 'yan unguwarmu? Ga shi dama sun
tsane ni, yanzu idan suka ji ina da ciki zasu
dinga tsokana ta."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Sala ta fyace hanci wanda ke kwaranyo da
majina ga hawaye sun hadu sun cakude sannan
tace, "Au!! Gaya musu zamu yi? ai kama
bakinmu za muyi muyi shiru, ko Abbakar ba
za'a gayawa ba, dan kada dadin hira ya kwashe
shi a majalisarsu ya kwaza, kin san shi da
shegen surutu, kija bakinki ki yi shiru har mu
zubar da shi....." "Zubarwa Sala?" Abu ta fadi a
kidime. "Eh mana zubarwa zam yi, dan da
kunyar duniya gwara ta lahira, kuma ma ai ma
tuba kafin mu mutu. Goge hawayenki ni na san
ta inda zan bullowa al'amarin, ki sha kuruminki,
bari na samo mana mota mu tafi gida." Ta fita
ta samo musu mota suka loda kayanzu suka
nufi gida da sunan Abu ta warke. Tana isa gida
ta sanya aka samo mata madaci ta hada da
darbejiya da omo da kanwa ungurnu ta dafa su
suka dahu sannan ta kawo wa Abu daki. Tana
kwance lamo ta ce, "Abula na tashi ki kafa kai
maza ki shanye wannan." Ta mika mata kwanon
dake dauke da hadin. Babu musu Abu ta karba
ta kafa kai ta kama kyankyama tana rintse ido
saboda rashin dadinsa da daci kamar zai yanka
mata harshe, ko kofi guda bata sha ba amai ya
ciyo ta, ta yadda kwanon ta kama amai, gaba
daya hadin ya zube, wanda ta sha kuma ta
dinga dawo dashi tamkar zata amayar da
'ya'yan hanjinta. Sala tana tsaye ta yi tagumi,
sai dai tana ganin aman ya lafa ta kuma dauko
wani kwanon cike da maganin tace, "Maza Abula
na daure ki shanye wannan....." Ta girgiza kai
cike da fargaba tana fadin, "A'a Sala gaskiya

babu dadi, hanjina kamar zasu tsinke ji nake
kamar zan mutu." Sala ta waro ido waje tana
fadin, "To dama waye yace miki dadi ne da shi,
eye? Daman ai za ki sha ne dan ki rabu da
wannan jarabar dake tare dake, da don dadi ne
yaushe zan baki? Da dadi nake so kiji sai na sayo
miki kaza da madara, amshi ni ki sha tun raina
bai baci ba ko asirinmu ya tonu ba." Abu ta
amsa idonta na fidda hawaye ta amsa ta kafa
kai tana sha, ai wannan karon ko rabin kofi bata
sha ba aman ya kuma dawo wa, ta dinga
yunkuri kamar za ta amayar da 'ya'yan
hanjinta, hankalin Sala ya kuma tashi, haka nan
suka hakura dan babu yanda zasu yi suka yi
zugui-zugui da su cike da tashin hankali. Sadiku
ya shigo gidan da Sallama, Sala tace da Abu,
"Maza kwanta ki rufe idonki zan ce bacci kike yi,
Waye......? Tsaya ina zuwa." Bakinta yana
kyarma take fadin, ta fita da sauri tana kokarin
gyara daurin zani dake shirin faduwa. Ya dubeta
da mamaki dan ganin yanda ta fito a firgice,
idanuwan nata duk sun yo waje. Ya kalle ta da
damuwa a ransa ya ce, "Lafiya Sala ko ba ki jin
dadi ne?" Da sauri Sala tace, "Lafiya ta kalau me
ka gani? Jiya ne dai 'yar uwarka ta tashi da
ciwon kai har muka kai ta asibiti kana
makaranta, amman yanzu jikin da sauki dan har
an sallamo mu." Yace, "Allah ya sawake." Ya
dauki bokiti ya zuba ruwa ya shiga bandaki, ta
yi tsaye tana muzurai wai dan kada ya shiga
dakin, har ya gama ya futo daga bandaki. Sanda
ya futo har tsoro ya ji dan ganin yanda ya bar
ta haka ya tadda ta tana tsaye, ya dube ta da
mamaki ya ce, "Sala yaya dai, lafiya?" Ta gatsina
fuska ta ce, "Lafiya kalau, ina shan iska ne
kawai."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Ya dubeta sosai ya ji gabansa ya fadi dan ganin
yanayin ta, amman sai ya dake kawai ya wuce,
har ya isa soro sai wani tunani ya darsu a ransa,
sai ya juyo har lokacin tana tsaye tana dubansa.
Ya kalle ta da kyau yace, "Sala kunje asibiti kika
ce? Me suka ce yana damunta?" Munje mana da
Baba Abbakar muka je ma jiyan ta sami sauki
yanzu haka bacci take yi. Bai yadda da abun da
tace ba, dan haka ya ce, "Ki bani katin na duba
ko da wani abu da suka ce." Kululululuuu!
Cikinta ya duri ruwa, amman sai tayi saurin
yanko karya tace, "Laaa! Ka ga sai yanzu ma na
tuna da katin, ai mun baro shi a can asibitin
wallahi, ai tama warke idan ka ganta kamar bata
yi ciwon ba ma." Kamar ya kuma yin magana,
amman sai ya ga rashin dacewar yi din dan
haka kawai ya juya ya fita ya nufi dakinsa, sai
dai ransa cike yake da zargi kala-kala amman
yana ta addu'ar Allah ya sanya abin da yake
zargin ya zama ba gaskiya ba ne. Sai da Sala
taga ya shige dakinsa sannan tayi ajiyar zuciya
gami da shiga dakinta da sauri tana fadin, "Oh!
ni Salame yaro sai shegiyar tambayar tsiya
kamar dan jarida? Koda yake an ce ai karatun
Lauya yake yi sun iya sharri, ai da na gaya masa
abinda ya faru na shiga uku da surutunsa
kamar wani ubana." Kusan daran nan a zaune
suka kwana suna sake-saken abinda zai fish-she
su, daga karshe dai sun yanke shawarar
komawa asibitin watakila su sami wanda zai
zubar musu da cikin tunda an ce ana zubarwa.
Amman sun yanke shawarar ba zasu je asibitin
Murtala ba za suje Kuroda ne dan kada Likitan
jiya ya tona musu asiri. Sanda suka isa asibitin
suka bi layi har ya kawo kansu suka shiga,
bayan sun zauna likita ya dubesu yana
tambayar abinda ya faru. Sala ce ta fara
kwantar da murya tana fadin, "Wallahi likita
tsautsayi ne ya faru da yarinyar nan, yarinya ce
'yar albar....." Ya dubi katin yana magana,
"Hajiya kece Zainabun ne?" "A'a ba ni bace gata
nan." Ta nuna Abu. Ya maida dubansa ga Abu
ya ce, "Zainabu me ke damunku?" Idonta ya

kawo kwalla ta dubi Sala tana matse idanu, Sala
ta daga mata kai alamar ta yi magana, ta
kwantar da murya ba kamar da ba da take
magana a tsiwace tace, "Daman kaina ne yake
ciwo da ciki na da kuma amai....." Ya dubeta da
kyau sannan ya maida kansa ga katin yana
rubuce-rubuce, ya daga kansa bayan ya gama
ya ce, "Hajiya zaki kai ta ayi mata gwajin fitsari
da jini." Ya dubi wata ma'aikaciyar jinya (nurse)
yace, "Sister nuna musu dakin gwajin jini."
Ma'aikaciyar jinyar ta mike tana fadin, "Hajiya
taso muje mana."
Abu ta kalli Sala wacce ko motsawa bata yi ba,
Sala kam wani busashshen yawu ta hadiya da
kyar sannan tace, "To likita ai daman a babban
asibiti anyi mata gwajin, an gano tana da ciki
ne.... Daman zuwa muka yi ka taimaka mana
kamar yanda Allah ya taimake ka ka zubar...."
"Me?" Likitan ya tambaya da mamaki, ya dora
da cewar, "Hajiya an gaya miki muna zubar da
ciki ne mu?" Bai bari ta bada amsa ba ya cigaba
da maganarsa, "To ki sani mu bamu zubar da
ciki a nan, idan kika kuma kasadar zuwa wani
asibitin na gwamnati da sunan a zubar miki da
ciki za'a iya kama ki a daure, wato kina jin
kunyar duniya ba kya tsoron Allah ko? Wato
kinfi jin kunyar duniya ba kya tsoron Allah ko?
Me yasa kika yi sakaci da tarbiyyar 'yarki har
tayi ciki? A ce kamar wannan karamar yarinyar
da bata gama sanin kanta ba balle ma ta san
mecece rayuwa ta yi ciki....." "Ai dai kaddara ce
ba ta wuce kanka ba kai ma." Abu ta katse shi
tana murguda baki da wani kyafta idanuwa. Sala
ta kai mata duka tana fadin, "Kin ci Ubanki
nace, ana neman ya raba ki da wannan kajagar
kina masa rashin kunya?" "Kin ga Hajiya ku tashi
ku fita na gama da ku, don ina da marasa lafiya
dake jirana." Likitan ya katse mata maganar.
Sala ta gurfana bisa gwiwowinta za ta fara roko,
amma ya katse mata hanzari ya daga mata
hannu yana fadin, "Hajiya I said get out of my
Office, (Na ce ki fita daga Ofis dina)." Jikin Sala
ya yi sanya ta mike duk da bata ji abinda yace

ba ta gane korarsu yake yi, Abun ce ma ta dan
gane wani abu tunda ta san (get out) dan haka
suka fice babu shiri. A bakin titi suka yi tsaye
cike da tashin hankali, dan duk iyakacin
dabararsu ta kare. Abu ta fashe da kuka tana
fadin, "Yanzu Sala shi kenan gorin da nake yiwa
Ladi mai danwake ta haifi shege nima haka za'a
dinga mini? Kin gani har hana ta fitowa muke
muna bula mata kasa idan ta fito, gaskiya
Mustafa ya cuce ni, Gashi ya gudu ya barni da
abin kunya." Sala ta matse ido cike da takaici
tace, "Bari ke dai diyar nan, na rasa inda zan
tsoma kaina da wannan abun kunyar, wallahi
yaron nan ya shammace mu, da ina ganin sa
yaron arziki ashe dan tsiya ne." Tayi kwafa gami
da fyace majina da hawayen dake zubo mata da
gefen gyalenta.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Abu ta dube ta tace, "Sala yanzu gida zamu
koma?" Sala tace, "Eh, to! Ko dai zamu je gurin
bokan can na kan tudu mu gani ko za'a sami
maganin zubar da ci....." "Sannu Hajiya." Wata
murya ta katse mata magana daga bayanta,
gaba dayansu suka juya da sauri dan ganin mai
musu magana. Ma'aikaciyar jinyar nan ce da
suka gani a dakin likita, wadda ya ce ta raka su
dakin gwajin jini. Ma'aikaciyar jinyar ta fara
magana, "Ina ta addu'ar Allah ya sanya daman
baku tafi ba, na dan tsaye bata lokaci ne dan
kada likitan ya gane ku na biyo. Ai shi na gaya
muku dan ka'ida ne ba ya zubar da ciki, yana
wani fama da gemu kamar gaske. Don ma bai
kama yi muku wa'azi ba, shi ya sanya sam
bama shiri da shi, amman daman ka'ida ce duk
asibitocin gwamnati ba'a zubar da ciki idan na
da matsala ba, sai dai zan taimake ku yanzu dan
kun bani tausayi, bai dace yarinya karama

kamar wannan rayuwarta ta lalace tun yanzu
ba." Fuskarsu ta fadada da fara'a Sala ta ce,
"Kai amman likita mun gode miki kuwa, Allah ya
sanya ki gama da duniya lafiya." Ma'aikaciyar
jinyar tace, "Amin." Sannan ta fara yi musu
kwatancen wani asibiti mai zaman kansa inda
za'a cire musu cikin. Sala ta dinga godiya kamar
ta kwanta don durkuso tana godiya.
Ma'aikaciyar jinyar ta ce, "Babu komai idan baku
gane ba dai ku fada mini, sai dai yanzu rana ta
yi gobe da sassafe za kuyi sammako kuje." Sala
tace, "Mun gane ma." Haka nan sukayi Sallama
suka tafi suna ta godiya. Daren ranar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login