Showing 30001 words to 33000 words out of 49932 words

Chapter 11 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf

iyakacin dauriyarsa. Abin da
ya faru dashi tsahon wasu shekaru da yake
ganin a can baya mara amfani da muhimmanci,
har idan ya tuno abin yakan kira shi da tsuntsu
daga sama gasashshe, sai dai tunda ya yi nisa
abin ya fara damunsa, da farko yakan ga kamar
abin nan ne da Hausawa kan kira 'Sabo tirken
wawa' sai dai da yaga duk kwanan duniya abin
yana kuma tsiro a zuciyarsa har ya kai matsayin
da ya cika zuciyar tasa babu sauran wani gurbi
na tirjiya da dauriya. Ya yi kwafa a karo da
dama ya juyo yana kallon kayataccen falonsa
wanda ya sha kayan alatu kamar ba za'a mutu
ba, ya isa dan gurbin shan lemo, ya zuba lemo
a kofi ya hada da shandy ya cilla kankara ya
daga ya shanye wai ko zai ji sanyi a zuciyarsa,
sai dai har lokacin abin yana nan, sai yaga
kamar ma karuwa ya yi saboda mutuwa da
jikinsa ya yi sabon tunani ya shige shi. "Me ya
sa haka ne?" Yayi wa kansa tambaya, wadda
tsawon lokaci yake yiwa kansa, ya dauko taba ya
kunna ta ya bata wuta a hankali yana lumshe
idanuwansa amman har lokacin bai ji sanyi a
ransa ba. Ya jawo takardar da ya bayar da irinta
a Ofis dinsu jiya ta barin aiki yana kuma
dubawa, wayarsa ta fara kara ya dauka da kyar
yake magana, abinda aka gaya masa kamar kara
hasala shi aka yi don haka da zafin rai yake
magana cikin harshen nasara. "Eh! Ni ne na
rubuta dan na yanke shawarar barin aikin nan
don jama'ar kasata na bukatar gudummawa ta,
sannan iyaye na sun damu da su ganni,haba
Mustafa kada ka yi mana haka, idan albashinka
ne ya maka kadan zamu iya kara maka mu." A
ransa yace, "A wannan karon babu wanda zai
hana ni tafiya dan zan biyawa raina bukatarsa
ne, dan idan na cigaba da zama a haka zan iya
asarar farin ciki da kwanciyar hankalina."
Amman a fili sai yace, "Oga kuyi hakuri ba zan
iya janye kudirina ba a wannan karon na tafiya
ko da nawa zaku kara mini, nayi muku alkawarin
dai duk sanda na sami dama zan dawo muku

gaba daya, amman yanzu hankalina ya yi
kasata." Dan Baturen da suke maganar ya sare,
dan 'dan zaman da suka yi sun san Mustafa
mutum ne kaifi daya, idan ya sanya abu a
gabansa babu wanda ya isa ya hana shi
aiwatarwa, dan haka ma ya rike aikinsa da
gaskiya da amana, dan haka suke masifar ji
dashi, shine zai bare inji ba tare da ya tsaya ya
kalli 'yar takardar bayani ba ya maida ya hada
shi kuma ya tashi tsaf, ba kamar sauran
Turawan da sai sun duba ba a rubuce, ya dai
daure yace, "Shike nan Mustafa muna maka
fatan alkhairi, sai mun hadu a Ofis din. Ya yi
ajiyar zuciya ya ce, "Shike nan Oga sai mun
hadun." Ya kashe wayar tasa gami da lumshe
idanuwansa, wata rayuwa ta dinga bijiro masa
wacce ta wuce shekarun baya wacce a da can
yake daukarta shirme, sai dai yanzu ya tabbatar
ita ce rayuwarsa mai cike da ainihin farin ciki da
sanya shi nishadi da dariya, sai dai duk sanda
yake tunanin wani abin mai fadar da gaba kan
fado masa, sai dai yana addu'ar Allah kada ya
tabbatar da wancan abinda ke fadar masa da
gaban. Washegari jikinsa babu kwari ya fito daga
Ofis din nasu dan alhinin rabuwa da abokan
aiki, sai dai daman haka rayuwa ta gada dole
wata rana za'a rabu, walau ta gurin zama ko
aiki ko kuma ta har abada ma (mutuwa). Daga
nan kai tsaye gurin neman Visa ya nufa ta
komawa kasarsa ta haihuwa wacce rabonsa da
ita tsahon shekaru.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
KANO-NIGERIA: 15/10/2003.
Bayan ya sauka ya dauki shatar mota tun daga
filin jirgi har gidan Mahaifinsa. Maigadi ne ya
fara ganinsa don haka ya zuro da gudu cike da
murna da doki yana fadin, "A'a Alhaji Mustafa

yau kake tafe? Marhabun lale, sannu da zuwa."
Mustafa yana murmushi yake amsawa ya
sallami mai tasin, sannan ya dubi maigadin ya
ce, "Malam Bala a shigar da kayan ko?" Daga
nan ya shige cikin gidan kai tsaye, ya yi sa'a
kuwa jama'ar gidan duk suna nan domin la'asar
ce. Da Mominsa ya fara cin karo tana zaune a
falo tana karatun jaridar Leadership Hausa, tana
sanye da (Medicated glass), ya shiga da sallama
bakinsa a washe. Ta daga kai cike da tsananin
mamaki, suna hada ido dai ta tabbatar da lallai
shine, ta mike cike da murna tana fadin,
"Babana! Da gaske kai ne ka iso garin ba tare da
ka sanar da mu ba?" Ya isa gaban Mahaifiyar
tasa cike da farin cikin ganin Mahaifiyar tasa don
ya kwana da dama bai ganta ba, dan ma wani
lokacin ta kan bi Mahaifinsa suje ganinsa, don
shi tunda ya tafi bai kuma waigo wa Nigeria ba,
wanda shi wai nan dabara ya yi dan ya manta
da abinda ke damunsa a ransa, a cewarsa idan
ya yi nisa da abin zai samu sassauci koma ya
manta gaba daya, sai dai yanzu ya gano
dabararsa ba za ta kai shi ko'ina ba. Ya ce,
"Momi barka da gida, na same ku lafiya?"
"Lafiya kalau muke sai dai mamakin dawowarka
yanzu babu sanarwa, Allah dai ya sanya lafiya."
"Momi Lafiya kalau wallahi, na so kwarai na ba
ku mamaki ne dan na sha sanya rana zan zo
amman bana zuwa, dan haka nace wannan
karon sai dai ku gan ni kwatsam." "Lallai kam ka
ba mu mamakin, bari na je na samo maka dan
abin tabawa." Ta mike ta nufi kicin din gidan.
Tana isa kicin ta tadda 'yan matanta suna ta
faman kacaniyar girkin dare, ta ce, "Albishirin
ku?" Gaba daya suka ce, "Goro Momi." "To
yayanku ya dawo yanzun nan, yana falo dan
haka sai a hado masa abin motsa baki kafin a
kammala girki." Gaba daya suka yi falon da
gudu suna murna suna ihu, sun ma manta da
abinda aka ce su dauka, ta yi murmushi sannan
ta dauka ta tafi da shi.
Yana ganinsu ya ce, "Lallai 'yan matan Momi an
girma, kalle ku don Allah." Suka kalli juna suna

dariya.
Ya so tun daran ya fita ya fara aiwatar da
abinda ya kawo shi garin, sai dai gajiya ta hana
shi dan haka dole ya hakura har gari ya waye.
Washegari ya shirya cikin manyan kaya wadanda
suka kara fito da kimarsa da martabarsa, duk
da zaman da yayi kasar waje bai daina sanya
manyan kaya ba, musamman yakan aiko a yi
masa, idan ya sanya turawan suyi ta sha'awarsa
musamman idan zai je gidan biki ko wani fati,
yawaita sanya manyan kayansa tun yana nan
gida ya kara masa martaba a idanun jama'a har
suke ganinsa wani mai hankali da tsantseni.
Motar Babansa ya hau dan na shi yayo Odarsu
ba su karaso ba, yana tafe yana jin wakar Bob
Marley don mutuminsa ne, sai kada kai yake
cike da nishadi, yau ce ranar da zai cikawa
ransa burinsa, yau ne zai je ga Zainabu Abunsa
karo na biyu da sunan soyayya, idan ya tuno
abinda ya faru a baya sai ya dinga jin wani farin
ciki da nishadi. Sai dai abinda ke fadar masa fa
gaba idan ya tuna anya Zainabun tasa ba tayi
aure ba? Idan aka ce Zainabunsa ta yi aure
kuwa lallai yana cikin tashin hankali da rashin
nutsuwa, dan ya gano yanzu itace rayuwarsa,
sai yake ganin nisan gidan nasu da yake su sun
tashi sun koma cikin G.R.A. Ya isa kofar gidan
yayi fakin yana kallon gidan, kusan yanda ya san
shi haka yake yanzu, sai dai wasu sauye-sauye
da aka samu, mutane ne a kofar gidan can da
can suna cikin kwalliya. Gabansa ya tsananta da
faduwa da ya ga Sadiku sanye da manyan kaya
da gani sababbi ne sai daukar ido suke ya zama
babban mutum mai kamala, sai fito da abinci
yake shi da wasu cikin farantai. Ya zubawa
Sadiku ido har lokacin gabansa na faduwa, ya
zuge gilas din motar a hankali yana kara kallon
jama'ar dake kai kawo kofar gidan. Can ya
hango wani maroki yabi Sadiku yana masa kirari
ya sanya hannu a cikin aljihu ya dauko kudi ya
ba shi, da alama yana cikin farin ciki, daga
ganin alamun babu ko tambaya aure aka daura
sai dai bai san ko na waye ba, ya yafito wani

yaro da yazo wucewa ta kusa da shi yana kallon
motar. Yaron ya karasa yana kallonsa a alamun
rashin sani a fuskar yaron, "Dan Allah yaro
daurin auren wa aka yi a kofar gidan ne?" Ya
nuna kofar gidan da hannunsa. Yaron yace,
"Daurin auren wannan din nan aka yi 'yar gayun
nan mai kwalliya ni na manta sunan ta ma." Ya
rasa gane wacce yaron ke nufi sai dai
hankalinsa yayi kololuwar tashi don yana ganin
kawai Zainabun sa ce ma, ammai sai yayi ta
maza ya ce da yaron, "Na gode ka ji abokina, un
go wannan." Ya mika masa Naira dari biyu,
yaron ya amsa cike da murna ya tafi.
Yana cikin mota yana ta sake-saken yanda zai
yi, shin kundumbala zai yi ya futo ya tambayi
wacce aka daurawa aure ko kuma hakura zai yi
ya koma.Tunaninsa ya tsaya cak sanda ya hango
wasu hadaddun mata sun nufo shi, dayar
doguwa ce sosai fara amman da alama ta dan
kara da na kanti, sai dayar gajera ce amman ba
can ba, tana da wani irin kyau na daukar
hankali, daga shigar ta har tafiyarta sun yi
matukar burge shi, yana hango su suna doso
shi, sai yaga mara tsahon da yawa fuskarta tana
masa gizo kamar ya santa. Suka zo suka gota shi
suna taku sannu a hankali, gaba daya sun tafi
da hankalinsa, wani irin kamshi ya ji ya bigi
hancinsa san da suka wuce, ya lumshe idonsa
saboda kamshin da ya ji
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
"Anti Abu ga wayarki in ji Sala ta ce kin manta
ta." Wata 'yar yarinya da ta fallo da gudu ce ke
fadin haka. Mustafa ya bude idonsa da sauri.
Wacce tafi tafiya da hankalinsa yaga an mikawa
wayar, ta amsa ta sanya a jaka, yayi wata
sanyayyar ajiyar zuciya mai cike da rudani yana
fadi a ransa, "Yanzu wannan Abu ce da ya sani

a can baya 'yar mitsitsiya da ko kwalliya bata iya
ba, 'yar tallan abinci da ya wayar da ita, ita ce
ta zama wata irin tauraruwar mata ta wuce
yanda duk yake tunanin zai gan ta?" "Ya Salam"
Ya fadi a fili. Ko da wasa ko a mafarki bai taba
zaton Abunsa zata yi irin wannan wayewar ba,
ya daukarwa kansa zai dawo Kano na Nigeria ya
auri Zainabu, ba don tsananin kyau, ilmi ko
dukiya ba sai dai dan tsananin sonta kawai da
Allah ya jarabce shi, sai dai abun mamaki da
tsoro sai ya ga Zainabu ta sauya ta wuce
iyakacin tunaninsa gaba daya. Tashin motar da
yaga sun dosa ne ya farkar da shi daga dogon
tunanin da ya fada, ya tada ta shi ya bi bayan
ta sun sai dai ina sun riga sun yi masa nisa, dan
haka ko hangosu baya iya yi, dan hala dole ya
dauki hanyar komawa gidan su dan ya ji kiran
wayar Dadin su. Karfe takwas na dare ya kuma
dawowa kofar gidan su Zainabu, don yinin ranar
haka ya yi shi sukuku, ya dinga tuno yanda ya
ga Zainabu na tafiya da kamshinta na yanzu,
musamman yau Babansa bayan sun gaisa sai
yayi masa maganar aure dan sun jima suna
masa maganar yana cewa suyi hakuri har yanzu
baiga wacce ta yi masa ba ne. Cikin wata shigar
ya iso ya yi kyau matuka, shaddar har wani kara
take yi saboda tsabar bugu da ta sha, sai dai ya
tarar da cincirindon mata a kofar gidan, sai
motoci ne ke diban su, sai dai addu'arsa Allah
ya sanya ba Zainabunsa aka daurawa aure za'a
kai dakin miji ba. Yayi fakin ya fito ya jingina da
motar yana kallon matan dake kaiwa da
komowa cikin hasken fitilar da ya haske kofar
gidan. Har ya gama kalle-kallen sa bai hango
Zainabu ba, wata budurwa mai shegen yangar
tsiya da take ta wucewa ta gaban sa ko zai taya
ya daure ya yafito, babu musu ta nufe shi kanta
ya kuma fasuwa don ga dan gayu mai
hadaddiyar mota yayi kiran ta zata buda gurin
'yan matan gurin, ta nufe shi tana kara salon
tafiya tana wani girgiza, duk da ba wani kyau ta
cika ba amman daga gani tana ji da kanta.
"Barka da yamma adon gari." Ya fadi da wata

mayaudariyar muryarsa, yayi mata kuri da
idanuwansa wadanda ke ruda 'yan mata. Tayi
wani far da idon ta da kyar kamar bata son
magana ta ce, "Yauwa ya kake?" Yayi dan
murmushi yace, "Kalau nake. Na ce banga
amarya Abu ba ko har sun wuce ne?" Ya shirya
hakan ne don ya tabbatar da gaskiyar abin. Ta
yi masa wani kallo mai cike da mamaki sannan
ta ce, "Hala dai mantuwa ka yi naji kana cewa
Abu, dan dai na san Karimatu ce amarya ba
Abu ba, yaushe Abu zata yi aure ita da ta
daurewa bariki gindi?" Ta karasa maganar tata
tana yatsina fuska da alamun kishi a muryarta
jin ya ambaci Zainabu don ta zaci cewa zai yi
yana son ta. Ransa yayi wani wasai cike da farin
ciki da yaji ba Zainabunsa ce aka yiwa aure ba,
duk da bai ji dadin abinda ta ce din ba amman
sai ya dake ya ce, "Kai na shafa'a ne, yi hakuri
Karimatu nake so na ce miki na manta." Ta dan
saki ranta tace, "Babu damuwa idan gurin fatin
za ka mu zo ka rage mana hanya mana ni da
kawayena?" "Me zai hana, ki shigo na kai ki
mana." Ya yi haka ne dan yayi amfani da
wannan damar ya ga Abun a can.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347


Zaharaddeen Shomar
whatsapp 08168575100



Idan zuciya tagyaru 1-04
Posted by ANaM Dorayi on 01:13 PM, 30-Jan-16
Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU
_______IDAN ZUCIYA TA GYARU_____
_____________ Na

_______Fauziyya D Sulaiman______
Dadi ya cika ta ta yafito kawayenta da ke can
tsaye suna kallon su da mamaki da sha'awar ina
ma ace su yace yana so. Ta shiga motar tana
fadin, "Ga kawaye na nan zaka rage musu
hanya." Yace, "Su shigo mana." Dadi ya kuma cika
ta tace musu, "Ku shiga baya mana." Ta umurce
su sanda suka iso jikin motar. Ta so ya dan ja ta
da hira sanda suka hau kan kwalta don ta kara
budawa a gurin kawayen nata, sai dai shi kaset
kawai ya kunnan na mutumin na sa, yana gyada
kai zuciyarsa na can ga Zainabu Abu yana
kwadayin yanda zai ganta ko da sau daya ne. A
haka suka isa har inda za'a gabatar da fatin,
hotel ne hadadde, tun daga waje za ka san fatin
na manya ne dan manyan motoci ne a gurin.
Sisters night aka rubuta da kyalli baro-baro
wanda ke haske a gurin. Fatin Abu ce ta shirya
shin don taya kanwarta murnar biki, Malam ne
ya daura auren sannan 'ya'yansa suka shige
gaba gurin bikin dan duk yawancinsu suna auran
masu hali ne suna tukinsu, don haka a motocinsu
aka dinga dauko mata ma. Bayan yayi fakin
sauran 'yan matan suka fice da saurin su, ita
kuwa 'yar gwallin ta tsaya tana wani yauki da
fari, har zai ce ta fita mana sai ya tuna yanda
take masa wani yauki da yanga. Dan haka yayi
murmushi ya ce, "Ga shi har zamu rabu ban san
sunan Hajiyar ba." Tayi dariya mai cike da nishadi
ta ce, "Sunan ai ba wani na ku zo mu gani ba ne,
sunana Salimat." Yace, "Lallai nice name, suna
mai dadi." Ya zaro kudi a aljihunsa ya mika mata
ya ce, "Ga wannan kya yi liki kafin na shigo zan
ga wani abokin da bai karaso ba, idan na shigo
zan gan ki." Yayi mata haka ne dan ta rabu da
shi. Ta yi wani fari da idonta don ta yi zaton da
gaske yake musamman da taga ya bata kudi
masu yawa, dan haka ta ce, "Babu damuwa,
amman fa ban ji sunanka ba." Da sauri yace,
"Sunana Mustafa." Don ya gaji da ganin ta ya
matsu ta bashi guri ya shiga ya ga rabin ransa.
Ta ce, "Shi kenan na gode Mustafa sai ka shigo."
Ta fita tana wata yanga. Ya bita da kallo har ta

kule sannan ya yi tsaki yana fadin, "Ki ga mace
kamar an zana one amman sai wani firirita da
iyayi take, ita wannan ko a kafa aka daura mini
ita ai zan yage ta na zura da gudu ne." Ya kuma
gyara fakin ya kwantar da kujera gami da kara
sautin wakar da yake ji, ya kunna taba yana sha
yana kada kai kamar kadangare, ta cikin hasken
gurin yake karewa matan da ke shige da fice
kallo. Ya dan jima a haka sannan ya bude motar
ya fice ya kukkullo ko ina, sannan ya nufi inda ya
ji kida yana tashi na Mahmud Nagudu don shine
yake taya su shakatawa. Gurin ya tsaru matuka,
mawakin ya dage yana ta rera wakarsa cikin
tattausan lafazi, amarya da ango suna tsakiyar
makeken filin suna takawa a hankali, yana daga
inda yake tsaye ya gane Karimatu dan ya santa
tun tana karama, sai dai daman can ita tafi
Zainabu hankali da nutsuwa. Ya sakale hannuwa
a kirji yana ta waige-waige, bai kula da matan
dake ta kallon sa wasu ma har sukan yi masa
sigina. Can ya hangota ta shiga filin rawar tana
sanye da wani irin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login