Showing 36001 words to 39000 words out of 49932 words
Chapter 13 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf
mai taswirar
birnin London, da silifas na fata a kafarsa dan
gasken, sai agogo na azurfa da wani kwalelen
zobe shima na azurfar, ya yi kyau matuka. Suna
hada ido da Asma ta yi ajiyar zuciya sai taga yau
yafi kyau ma fiye da jiya, dan ta kuma yadda irin
gogaggun mazan nan ne ma, ta kwantar da
murya tana fadin, "Yallabai barka da isowa." Ya yi
murmushi gami da fadin, "Yauwa kawarmu ya
gida?" Tana amsawa ta bashi hanya ya wuce ciki,
sannan ta kulle. 'Yar buyagin tashi tana zaune
tana ta busa hayakinta bata ko kalli inda suke ba
balle ma ta gane waye ba. Ita ma Asma tana
shigowa kiran wayar Alhaji Buba ya shigo wayar
ta, yace ga direba nan ya turo su taho, dan shi
baya zuwa da kansa dan kada masu ganin sa da
daraja su ganshi girma ya fadi, dan haka sai dai
duk sanda ya bukace ta ya turo direbansa a kaita
can gidan sa ta kwana, dan haka dakin ta ta
wuce ta hado 'yan kayanta. Har ya isa kusa da
ita ya zauna bata san ya zo ba, dan tabar
shaidan din ta fara gaya mata karya, ta jingina
da kujera ta lumshe idanuwanta tabar tana
tsakanin hannunta.A hankali ya zare tabar dake
tsakanin hannunta, kamar wacce ya tsikarawa
allura ta bude idonta firgigit ta ware manyan
idanuwanta a kansa suka yi ido hudu, sai ta yi
zaton ko gizo yake mata kamar yanda yake mata
tun dazu. dan haka ta mai da idanuwanta ta
lumshe wai ta daina ganin gizon sa, sannan ta kai
tabar ta bakin ta da zummar ta kuma zuka,
amman sai taji wayam babu komai, ta bude
idonta da sauri a kansa, shine din dai da gaske
yana taya ta shan tabar tata. Haushi da takaici
ya cika ta tama rasa yaya za tayi masa, amman
ta san ba kowa ne yayi mata wannan iskancin ba
illah Asma, dan haka ta mike da bala'inta ta nufi
dakin kwanan Asma din, sai gata sun ci karo a
hanya, ta ci uwar kwalliya sai kamshi take zubawa
rataye da jaka a jikin ta. Ta rike kugu tana
harararta, ita dai Asma dariya ta sanya sannan ta
nufi Mustafa ta cilla masa makullin tana fadi cikin
harshen turanci "Take care, good night." "Wai
Asma wannan wane irin iskanci ne?" Zainabu ta
tambaya a kule. Asma ta daga kafada alamar Oho
sannan ta fice da saurinta tana dariya. Ta kulu
matuka, ta mai da kallonta ga Mustafa dake
kallonta yana murmushi ta ce, "Wai kai kana gani
kayi mini dabara ne, to ka sani a yanzu na girmi
wayo da dabararka, sanda ka yi kaci nasara dai
ka yi amman ban da yanzu, don haka sai ka
zauna ka jire mata gida." Ta dauki dan yalolon
gyalenta da jakarta ta nufi kofa. Sai dai ina ya
rigata dan mikewa yayi da azamarsa ya sanyawa
kofar makulli ya cilla makullin cikin aljihun
wandonsa. Ta yi tsaye tana kallonsa cike da
takaici da masifa, ya isa gaban ta ya tsaya cak ya
zira hannuwa cikin aljuhunsa ya ce, "Ga ni
gabanki kiyi mini hukunci daidai da laifina zan iya
dauka, amman ki yi mini alfarma ki daina gudu
na sannan ki dai na mini kallon kiyayyar nan dan
yana bakanta mini raina, domin Allah ya
jarabceni da son ki Zainabu, na gaza kallon
kowace mace da daraja a rayuwata, ki taimaka ki
yafe mini laifin da nayi miki nasan mai girma ne,
amman na yi ne ba da son raina ba." Ta rike
kugu tana kallonsa idanuwanta sun sauya launi
zuwa jawur, duk wannan farin da kyallin babu
saboda tsabar dacin ran da take ciki, tayi wani
yake wanda yafi kuka ciwo sannan tace, "Mustafa
na sanka tuntuni gwani ne kai gurin iya yaudara,
da irin wadannan kalaman ka sami nasara a
kaina a wancan lokacin hadi da kuruciya da
talauci da son kudi irin na Mahaifiya ta, sai dai ka
sani a yanzu Zainabu Abu ta wuce duk iyakacin
tunanun ka, baka da sauran kalmar da zaka iya
yaudararta da ita, baka da kudin da zaka iya
yaudararta dasu, domin ina mu'amala da
wadanda suka fika kama daga Gwabnoni sai
Sanatoci da Ministoci zuwa manyan 'yan kasuwa
dake rike da akalar Nigeria, dan haka yanzu ina
da kudi da farin jikin da nafi karfinka, a yanzu
idan na buga waya kadai duk abinda nake nema
zan samu, dan haka kaga baka da makamin da
zaka yaudari zuciyata a yanzu, duk da kana
takamar kaine silar fadawa ta a wannan muguwar
harkar da kullum nake tsinewa mara albarka."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya kuma kwantar da murya ya ce, "Zainabu
tunda na diro garin nan na ganki nasan lallai ba
Abun da na sani da can bace, kuma ban dawo
rayuwarki dan na nuna miki kudi ko kyau ko
mukami ba, na zo ne da sunana Mustafa
masoyin ki nida zuciya ta kadai ina fata zaki yafe
mini abinda nayi miki can baya, sannan na mai
da matsayina da martaba ta a zuciyarki kamar
da, koma yafi haka don a yanzu Mustafa bai zo
da zummar fasikanci ba sai dai da zummar auran
Zainabu, domin a yanzu Ubangiji ya jarabi zuciyar
Mustafa da tsananin son Zainabu." Ta kalleshi a
lalace tamkar ta ga mahaukaci sabon kamu tace,
"So! So! Lallai ka hadu da mugun ciwo idan har
da gaske kake, balle na san karya kake yi, domin
kai mutum ne mai yaudara da karya, don haka
ka bude mini kofa na fice kawai, dan bana son ko
kallon fuskar ka domin kai ne mutumin da ya
sanya rayuwata a cikin fargaba da tashin hankali,
nasha azabar da har abada ba zan manta da ita
ba dan haka bude mini kofa na fita ko na daina
ganin azzalumar fuskarka!" Ta karasa maganar
tana hargowa. Ya hadiyi wani miyau mai daci,
maganganunta suna yi masa zafi da suya a cikin
zuciyarsa, dan haka da kyar ya iya buda baki
yace, "Zainabu ba zan bude miki kofar nan ba
har sai kin amince dani kin yarda yanzu ni ba
mayaudari ba ne..." "Ba zan taba yadda da kai
ba, ka bude mini kofa kawai na fita tun ban
maka rashin mutunci ba wallahi." Yana tsaye
kyam babu alamun zai ko motsa, ranta ya kuma
baci matuka, ta ga lallai da gaske yake dan haka
ta nufe shi da azama ta kama kokarin kwatar
makullin, nan fa suka fara kokawa amman ina
namijin duniya ne maji karfi dan haka ta gaza kai
hannunta balle ta iya dauka har karfinta ya kare,
tayi kokarin janye jikinta amman ya hana ta
hakan dan ta tuno masa da wani lokaci da wasu
al'amura da ke masa dadi da sanya shi nishadi a
duk sanda ya tuno. Tayi kokarin ta kwace amman
ta gaza sai ma wani abu da yake shirin jawo
mata dan shin din daban ne a zuciyarta ya san
kanta da yanda yake samun ta a sama, daman
haka yake so ta shiga jikinsa dole sai ta sakko
don dai shine ya santa ya san wacece ita, tayi luf
a faffadan kirjinsa mai kirar zaki ta gaza kasa
aiwatar da komai. Ya sami yanda yake so dan
haka yake da salon yaudarar da sace zuciya,
yanzu kam ya soma nasara a kanta dan tana jin
zafinsa a ranta amman tana matukar son sa, dan
haka komai ya kwance mata, Mustafa ne namiji
daya tal da idan tana tare da shi take manta
kowa, amman duk sanda take tare da wani sai ta
tuno shi da soyayyarsa, don haka bata da karfin
halin da zata kwaci kanta duk da haushinsa da
take ji, dan haka sai ta fashe da kuka kawai.
Jikinsa ya dauki rawa don yasan ba karamin abu
ke san ya Zainabu kuka ba, don tana da taurin
zuciya, dan haka cikin tausasa murya da rada ya
ce, "Zainabu don Allah ki yi hakuri ki yafe mini na
tuba....."."Me ya sanya ka tafi ka bar ni sanda
nake tsananin bukatar ka a rayuwa ta eye?" Ta
tambaye shi tana kuka. "Ki yi hakuri na san nayi
miki lafi, sai dai na yi miki alkawarin ba zan kuma
barinki ba har abada, ni din naki ne ke kadai, ba
zan iya kuma barinki ba Zainbau, ni kaina na sha
wuya, na yi miki alkawari." Ta yi luf ta gaza cewa
komai dan yayi mata yanda ba zata iya kuma
musa masa ba, anan suka baje suna shashancin
su. Sai karfe goma na safe suka sami sukunin
tashi suka fada wanka sannan suka yi sallah,
sannan Zainabu ta fada kicin da sauri don ta
samar musu abin da zasu karya dan yunwa suke
ji matuka. Ya bita kicin din tana sanye da wani
dan guntun siket, tare suka yi aikin suna ta
dariyarsu. San da suke karyawa yayi mata kuri da
ido yana kallo don Zainabu ta bashi mamaki, ta
wuce duk yanda ya santa, gaba daya ta gama
haukata shi a daran jiya, yanzu abu daya ya rage
masa ya auri Zainabunsa ya huta, kullum yana
manne a jikin ta shi kadai, sai ya ji wani kishi ya
kama shi mai tsanani dan bai san iyakacin adadin
mazan da ta yi mu'amala ba, sai yake da na
sanin tafiya da yayi ya bar ta, da shi kadai ya san
abarsa. Ita ma wani irin farin ciki take ji a cikin
zuciyarta, dan ta sha karo da maza kala-kala a
yawon iskancinta, amma bata ji wanda ya taba yi
mata dai-dai da Mustafa ba, don haka tana yin
bariki ne bawai dan dadi ba sai don neman abun
duniya(Allah ya kyauta), Zainabu hatsabibiya ce
ta kin karawa, dan haka maza da dama ke shan
wahala a kanta, yanzu ma mikewa tayi tsam ta
isa inda yake ta zauna cinyarsa, ta sakala
hannuwanta a wuyansa ta mika masa bakinta wai
ya sammata abin da yake taunawa (wainar kwai),
bai yi mata gardama ba dan shima gwani ne, dan
haka ya hada bakinsa da nata yana ciyar da ita
abinda ke bakinsa, da haka ta dinga kara susuta
shi tamkar wani karamin yaro ta mai da shi.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan sun kammala cin abincin suka yi masauki a
doguwar kujera mai cin mutum uku. Ta kwanta
lamo a kirjin sa tana shafar sa tamkar mage,
cikin kunnensa ta ce, "Musty wai me ya sanya ka
tafi ka bar ni sanda nake tsaka da bukatarka?"
Yace, "Sai kin sanar da ni irin wahalar da kika ce
kin sha sannan zan sanar dake nima." Ta yi kwafa
tana fadin, "Labarina mai cike da abun tausayi ne
da takaici, domin daga ranar da na nemeka na
rasa na shiga tashin hankali, naje har gidanku
aka ce mini daman hutu kazo wai a kasar waje
kake karatu, na shiga tashin hankali da ciwo mara
misali, abu fa kamar wasa sai ciwo ya dinga yin
gaba, da farko na zaci ciwon soyayya ne, sai da
abu yaci tura aka gano ashe ciki ne dani....." "Ciki
da gaske Zainabu ko na wasa?" Ya tambaya da
sauri. Ta yi dariya tana fadin, "Da gaske Musty
wallahi ciki ne na gaske, kai ai munga tashin
hankali ni da Sala a wannan lokacin." "To yanzu
ina abun da kika haifa din?" Ya kuma tambaya.
Ta tabe baki tana fadin, "Cabdijam, ai tuni muka
zubar da shi." Ya dafe kai yana fadin, "Ya salam,
ai sam ban san kina da ciki ba, har na ji ina son
abuna wallahi Zainabu." Ta warware masa duk
abin da ya faru sannan ta dora da cewar, "Bayan
mun gama da wannan muna murna mun dawo
gida da kwanaki kuma sai ciwon ciki ya balle mini
ga zubar jini kamar jinina zai kare, amman da
muka je gurin shegen likitan da ya zubar mini da
cikin ya caje mu kudi masu yawa gashi a lokacin
bamu da komai duk mun saida 'yan
kadarorinmu, don haka yace ba zai taba ni ba,
sai nurse din da tayi mana hanya ce tace muje
asibitin kuroda tun da dai yanzu ba zubar da ciki
bane zasu karbeni, gahi an kwana biyu da zubar
da cikin sai nace ina da aure bari na yi, sai ta
shige mana gaba da sunan ni 'yar uwarta ce daga
kauye aka kawo ni. Amman duk da na Gwabnatin
ne ma sai da aka rubuta mana magunguna masu
tsada ga karin jini, sai yaya na ne ya bada jininsa
aka diba, sannan Sala ta je ta ciwo bashi aka sayi
magunguna, lokacin adadin kudin kusan dari
shida ne. Bayan na warke muka fara tunanin
inda zamu samu kudin da zamu biya dan daman
irin kayan nan na bashin watan nan ta amsa ta
karyar da su ta saida sannan aka sami kudin, don
ma matar tana shakkar Sala ba tayi magana ba,
da na samu sauki sosai Sister din nan ta bani
shawarar na dinga fita good evening (karuwanci),
cikin kankanin lokaci komai ya sauya domin dai
kasan ni ta daban ce." Suka yi dariya gaba
dayansu sannan ta cigaba da maganar, "Yaya
Sadiku kamar zai shake ni ya kashe ni don tsabar
tsana da yayi mini, don har cewa yayi da ya san
ci gaba zanyi da iskanci da bai yadda an kara
mini jininsa ba, gwara na mutu kowa ma ya huta,
sai da Sala ta tsawatar masa harda barazanar
zata tsine masa idan bai fita harka ta ba sannan
ya saurara mini. Sister ce tace na koma karatu
domin rayuwa babu ilmi tana tawaya don haka
Sadiku na komawa ya maidani makaranta wacce
na yi kusan wata shida banje ba, da farko yace
ba zai maida ni ba sai da nayi masa alkawarin ba
zan kuma yawo ba sannan ya yadda ya kwashi
katina da zai tabbatar da bani da lafiya ne
sannan muka wuce makarantar. Sanda muka isa
Principal dinmu ta ce ba za ta amshe ni ba
domin dai nayi wajen wata shida ban zo ba 'yan
ajinmu har sun zana jarabawar sake aji . Sadiku
ya marairaice yana bata hakuri, ji nake kamar na
harbe shi don haushi, daga karshe ya dauko kati
ya bata don ta tabbatar bani da lafiya ne. Ta
ware idanuwa domin dai duk da bata fahimci
abinda likitan ya rubuta ba ta fahimci kalmar
(bleeding after abortion), wato zubar jini bayan
bari, ta daga katin cike da tsana da takaici take
kallona sannan ta fara magana.
"Lallai yarinyar nan kin cika tantiriyar 'yar iska,
bayan iskancin da rashin kunya har karuwanci
kike tabawa, kamar ki ace an zubar miki da ciki?
Kai tir da halinki, Allah ya wadaran halinki." Sai
ta jefeni da katin akan fuska ta. Sadiku ya mike
jikinsa yana rawa domin bai san likitocin da
suka yi mini karin jini sun rubuta bari nayi ba
don bai san karyar da muka shirya ba, sannan
bai tsaya ya duba katin ba duk da ba komai zai
gane ba ma, ya fara magana da rawar jiki, "Don
Allah Hajiya kiyi hakuri kaddara ce da
tsautsayi....." "Da kuma sakaci da rashin
tarbiyya." Ta karbe daga bakinsa, sannan ta
dora da cewa, "Wallahi ka ji na rantse yarinyar
nan ta gama zama a makarantar nan, alfarma
daya zan iya yi maka na rubuta maka takardar
(transfer) canji zuwa wata makarantar, don ban
ga amfanin zama da daliba irin ta ba, ita ba
kokari ba sannan ga shegen iskanci ta addabi
dalibai da malamai tun yanzu tana matsayin
kwaila, ina ga ta zama babbar mace? (No i
can't) ina ba zan iya ba." ta karasa maganar a
hasale. Ni kuwa ina gefe na cika nayi fam,
domin Sadiku ya gaza rama mini cin mutuncin
da matar nan take mini, don haka na mike daga
tsugun nan da nake yi na dole, domin tun a
gida ya gargade ni na durkusa da munje kuma
na gaida ta don ta san na yi hankali. Ke! Ma ya
ishe ki haka, haka kawai zaki sanya ni a gaba
kina zagina kamar wata uwata? Ko abun da yafi
ciki nayi ina ruwanki, idan ba zaki karbe ni a
makarantar ki ba kawai kice ba zaki karbeni ba
amman kin saka ni a gaba kina zagina, ke
wayasan iskancin da 'ya'yanki suke..... Marin da
Sadiku ya dauke ni dashi ne ya sanya ni yin
shirun dole, na dinga dubansa da jin haushi
kamar nayi masa Allah ya isa, amman tunda
lallabashi nake yi ya sanya na hakura ina ta
kunkune dai. Kana ji a gabanka tana zagina ma
ko? To maza ku bar mini Ofis dina tun ban hada
ku da (security) ba, ta fadi a hasale. Ya dauki
katin da yake a kasa yace, Malama nagode, kiyi
hakuri hali ne kowa da irin nasa, sannan ya
dubeni yace idan kin ga dama sai ki taho mu
tafi. Bai jira abinda zan ce ba ya fice daga Ofis
din. Na dalla mata harara ina fadin, "Allah ya
sanya ba kece kika kawo ilimin boko duniya ba,
sannan Mangwafak ba dan gidanku ba ne, don
haka zanyi karatu a wata makarantar ko kina so
ko baki so....." "Ki fitar mini daga Ofis dan
ubanki ko na sanya a zane mini ke ko na hada
ki da 'yan sanda su kulle mini ke wallahi
shegiyar yarinya mara kunya kawai karuwa.....
Na ce, "Kin ga karuwa dai a gidanki ba niba."
Ina gama fadin haka na ficewata ina hangota
sanda ta zauna a kujera cike da bacin rai da
bakin ciki mara misaltuwa, na dai ji dadi don na
rama wulakacin da tayi mini. Bayan mun dawo
gida Sadiku ya yi kamar ya cinye ni don bala'i,
yace kuma babu ruwansa da ni, don haka na
rasa yanda zan yi na koma karatun, don na
gane idan mutum yana zuwa makaranta yakan
rage 'yan sa ido. Daga karshe dai Sister Asibi ce
ta yi mini hanya na koma Sheka da karatuna,
acan dai na kammala Secondary