Showing 42001 words to 45000 words out of 49932 words
Chapter 15 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf
yawanci hirar siyasa suke yi
da matsalar da kasar ke ciki. Ba shi da wani ja
Zainabu diyar Baba Abbakar ce dai dan abokinsa
yake nema, dan haka ya je ya sanar dashi
yanda suka yi, daga karshe har kofar gidan su
Zainabun suka zo tare ya nuna masa. Haka nan
Alhaji Abdullahi ya koma gida jikin sa sanyi
kalau, domin dai ya tabbatar da lallai itace
wacce dansa ke so, shi kuwa duniya sam bai san
ya takurawa dan sa, yaso ace Zainabu da dan
sa yake so ta kasance kamila ce ba lalatacciya
ba, kafin ya shiga sallar Magariba ya kirawo
wayar Mustafa yace lallai idan an idar da sallah
yana son ganinsa,babu bata lokaci Mustafa ya
iso gidan dan kusan tare ma suka yi sallar Isha'i
da Baban nasa, ya dade a raka'ar karshe yana
addu'ar Allah ya sanya Zainabu ta zama
rabonsa, don yaji muryar Mahaifinsa kamar da
zafi shi ya sanya duk ya kidime. Ya riga Baban
nasa shiga gida, Momin nasa ta zuba masa
abinci amman ya gaza ci duk da uwar yunwar
dake addabarsa, dan kada ma Momi ta zargi
wani abu ya sanya ya dinga tsakurar kadan
yana ci har ma taso ta gane. Ta dubeshi da
kulawa ta ce, "Baba anya wani abu baya damun
ka? Na ga kwana biyu duk ka wani shiririce,
balle yanzu ka gaza cin abinci sai tunani." Ya
kakalo murmushi yana fadin, "Laaa! Momi me
kika gani? Babu komai gajiya ce dai kawai."
Ganin tana son ta gano shine ya sanya ya saki
jikinsa yaci abincin sosai, har Baban nasa ya
shigo, ya shige sashinsa ya kira Hajiya Kubra ta
wayar gida (land line) ya ce, "Baba ya shigo ne?
Idan ya shigo kuzo tare ke da shi." Ta amsa da
"Ya shigo, ga munan zuwa." Bayan ta ajiye
wayar ta dube shi duk ya sha jinin jikinsa ta ce,
"Alhaji yana kiranka." Sannan ta mike ta nufi
sashin Maigidan nata yana biye da ita a baya
har suka isa. Mustafa bai zauna akan kujera ba
a kasa ya zauna ya sunkuyar da kansa yana
gaida Baban nasa, fuskar sa babu annuri yake
amsawa, ba kamar yanda ya saba amsa masa
da sakin fuska ba, hakan ne ma ya sanya gaban
Mustafa ya cigaba da faduwa dan yana ganin
lallai wani abu yana shirin faruwa. Sun jima a
haka yana cigaba da duba jaridar leadership da
suka taddashi yana dubawa, labarin ya dauke
masa hankali wanda aka ce wai waye ya haifi
Obasanjo, sai da ya karasa shafin da yake
sannan ya daga kai yana duban Mustafa kur da
idonsa, abinda ya kuma fadar da gaban
Mustafa. Can ya daure ya ce, "Baba ka ce
yarinyar da kake nema acan kasan layin da
muka taso take har ma ta kammala karatunra a
F.C.E ko?" Bakinsa yana rawa yace, "Haka ne
Baba." Alhaji Abdullahi ya kuma gyara zama ya
ce, "To nayi bincike kamar yadda addini ya
umurci muyi a duk sanda aka tashi neman aure,
sai dai abun takaici duk mutanen da aka
tambaya wadanda ba zasu yi karya ba sun
sanar dani ko wacece Zainabu, dan haka sam
ban yarda da tarbiyyar ta ba da ta gidansu ba
ma gaba daya, don haka kaje ka nemo wata, ba
zan maka auren dole ba amman ya dace ace ka
samo mace mai mutunci da daraja a idon
duniya." Hankalin Mustafa ya yi mugun tashi
ransa ya baci, makwallaton sa sai kaiwa da
komowa yake yi, duk da sanyin A.C da fankar
dake dakin basu hana shi yin gumi ba, da kyar
ya iya bude bakin sa yace, "Baba kayi hakuri
bawai zan maka musu bane, ni na san Zainabu
diyar kirki ce, ka san halin mutanan yanzu ba
duka ne ke fadar gaskiya ba, dan haka ma
yanzu idan za'a yi aure ba'a cika zuwa a
tambayi mutanen unguwa ba, dan basu kaunar
wani ya cigaba, dan haka nasan zasu iya yiwa
Zainabu sharri dan haka ina neman yardarka
akan na auri Zainabu, watakilama ba wacce
nake so aka gaya maka ba." Alhaji Abdullahi yayi
dariya dan shi yana da hakuri da bin komai a
sannu ba kamar Hajiya Kubra ba mai saurin
daukar zafi ba da saurin fushi, sannan ya ce,
"Baba bana shakkar ba Zainabun da kake nema
aka sanar dani ba, amman bari nayi maka wasu
tambayoyi idan har ba ita bace shike nan." Ya
goge zufar dake tsats-tsafo masa ba tare da ya
iya cewa komai ba Baban nasa ya fara jeho
masa tambaya"Asali Abu ake ce mata sanda
tana yarinya, yanzu ne ake ce mata Zainabu
ko?" Ya ce, "Haka ne." "Kuma da can tana tallar
abinci da gyada da dai sauransu ko?" Ya hadiyi
wani yawu dan dai ya san lallai Baban nasa ita
ya gano, da kyar ya iya cewa, "Haka ne." "Tana
da wani Yaya mai suna Sadiku wanda shi ba irin
halinta gare shi ba, da kuma wata kanwarta da
aka yi mata aure kwanaki ba ko?" Yayi shiru bai
bada wannan amsar ba dan dai ya san Babansa
yayi bincike matuka akan Zainabu. Alhaji
Abdullahi ya cigaba da bayanin sa duk da bai
bashi amsa ba, "Babanta mutumin Sudan ne,
sunan shi Baba Abbakar, kuma ana kiran
Babarta da Sala....." "La'ilaha Illallahu! Yanzu
wannan karuwar yarinyar kake so Baba?" Hajiya
Kubra ta amshe zancen tun bai kai ga bada
amsa ba. Jikin sa ya kama rawa da rawar murya
ya ce, "Momi ba karuwa bace, don dai tana
aikine a (Local Govt.) ne shi ya sanya ake mata
kallon 'yar iska, wallahi ina sonta Baba kayi
hakuri don Allah, sharri kawai aka yi mata."
Hajiya Kubra ta amshe, "Sharrin gidan Uwar wa?
Ai ni sai yanzu ma na gane da ka fadi sunan
Mahaifinta Abbakar da sunan Babarta, yarinyar
da tun tana 'yar labubuwarta take iskanci, har
ciki aka zubar mata tana da shekara sha hudu a
duniya." Mustafa ya ce, "Kin ji ba Momi, sharri
ne aka yi mata dan ana....." "Sharrin Uwarka? to
tsaya ka ji na sanar da kai, na san Zainabu
shekarun da suka wuce, yarinya ce mara
mutunci kuma mara kunya dakikiya, ta addabi
kowa, duk wannan lami ne ma akan iskancin da
take yi." Ta dubi mijin nata tana magana, "Alhaji
idan baka manta ba na taba baka labarin wata
'yar iskar yarinya shekarun baya da tayi mini
rashin kunya har cikin Ofis dina, lokacin ina
makarantar 'yan mata ta Dala (G.G.C DALA), dan
ranar da tayi mini rashin mutuncin nan kasa
bacci nayi, don har sai da jinina ya hau, har yau
ina addu'ar Allah ya hadani da yarinyar nan
nayi mata rashin mutunci amman har yau Allah
bai hada mu ba, sai daga baya ma na ji 'yar
unguwar da muka baro ce a bakin wata 'yar
ajinsu, sai yanzu zaka ce kana son ta wai kuma
da aure ma? Ai ko da ku biyu kuka rage a
duniyar nan ba zaka aure ta ba muddin ina
raye." Ya dafe kansa idonsa ya kada yayi jajir
yana fadin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."
Dan ya riga ya gano Momi ta san komai, ta san
Zainabu farin sani, ashe ita ce wacce take bashi
labari din nan, sai dai ya rasa ta yaya zai sanar
da su wannan cikin da take tsanar Zainabu
saboda shi dan ta ne yayi shi, ta yaya zai ganar
da su shine ya fara lalata Zainabu tun a wancan
lokacin da take zarginta, duk da ya tadda
Zainabu da wasu muggan halaye amman shine
ya koyar da ita kashi saba'in cikin dari. Ya yi
tsamo-tsamo da shi kamar wanda kaza ta
fashewa a cikin sa, bashi da damar da zai kuma
musa musu abinda suka fadi, don idan yace na
Babansa sharri ne to na Momin sa fa wanda
Zainabu da bakin ta ma ta bashi labari, a sanda
take bashi labarin bai yi zaton Mahaifiyarsa bace
dan shi ko tambayar ta makarantar da take bai
taba yi ba balle har ya gano hakan ba. Alhaji
Abdllahi ya katse masa tunaninsa ta hanyar
fadin, "Baba ka sani ba wai muna kin Zainabi
akan kanta bane, A'a muna kin Zainabu saboda
halinta, don babu wanda zai so ace yau ya hada
zuri'a da lalatacce, da ace irin halin kanwarta
gareta babu abinda zai hana mu kyaleka ka
aure ta, dan haka ina baka shawara da lallai ka
koma ka sake nemo matar aure dan wannan
bata yi ba."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Idan Zuciya Tagyaru1-05
Posted by ANaM Dorayi on 08:00 PM, 03-Feb-16
Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU
_____________ Na
________Fauziyya D Sulaiman_____
"Yo to banda abunsa ma a gidan nan wacce irin
mace ce babu kuma masu tarbiyya da kyau idan
ma shine ya rufe masa ido, don haka ka kwantar
da hankalinka ka zabi wacce ta dace da kai duk
'yan uwanka ne." Alhaji Abdullahi ya amshe, "Ki
na ji Kubra, ba wai dole sai anan gidan zai zabi
mata ba don zai iya yiwuwa bai ga wacce ta dace
da ra'ayinsa ba, ya je ko ina ya samo mata in dai
diyar musulunci ce kuma mai tarbiyya." Shi kam
duk bai fahimtar duk abinda suke fada don sam
hankalinsa baya jikin sa, ji yake kamar ya dora
hannu a kansa yayi ta zunduma ihu kawai ko ya
ji sanyi a ransa. Alhajin na sa ya ce, "Ka tashi ka
tafi Allah ya zaba maka abinda yafi zama
alkhairi." Ya mike da kyar yake iya daga kafarsa
yana hada hanya tamkar wanda ya sha giya ko
kwayar sanya maye, idanuwansa sun kada sun yi
jajir da su kamar gauta, har ya fice basu ce
komai ba illa binsa kawai da suka yi da kallo.
Hajiya Kubra ta ja tsaki tana fadin, "'Ya'yan yau
ba'a iya musu, banda haka daga ganin yarinya
baka san halin ta ba ka dage sai ka aure ta, ni
abun ma mamaki yake ba ni, yaushe har ya
dawo garin nan suka kulla soyayya da
hatsabibiyar yarinyar nan har ta dauke masa
hankali haka? Duka baiyi ko cikakkaken wata
guda a garin nan ba, ni ko bayan raina ba zan so
ya auri diyar nan ba, Wallahi Alhaji dan baka san
ta bane sam bata da kunya da ladabi ko miskala
zarratin, tuntuni na tsaneta wallahi." Alhaji
Abdullahi ya kuma gyara zama cike da tashin
hankali dan dai yana tausayin dan sa, don ya
gane ba karamin so yake yiwa Zainabu ba ya ce,
"Ai haka Allah yake ikonsa, shi kadai yasan a inda
suka hadu, sai dai muyi masa addu'ar samun
mace ta gari, da addu'ar ita kuma Allah ya shirya
ta." Hajiya Kubra ta ce, "Amin dai." Shi kam
Mustafa da kyar ya iya kai kansa sashinsa saboda
tsananin tashin hankalin da yake ciki, dan Allah
ya sani duk duniya baya ga iyayansa babu
abinda yake so sama da Zainabu, ya sani
Zainabu wata tsoka ce a cikin jikinsa mai yawo da
jininsa, a da can baya yana daukar son Zainabu
shirme kuma shiririta a zuciyarsa, sai dai a yanzu
ya sani muddin bai auri Zainabu ba lallai kam
rayuwarsa tana tare da hatsari. Ya kwanta
rigingine a gadonsa ya rintse idonsa, ina ma zai
iya kuka da lallai yayi ko ya sami sassauci a cikin
zuciyarsa. "Zainabu! Zainabu!" Ya fadi a hankali
ko ya ji sanyi a zuciyarsa, ya sani hakkin Zainabu
da sauran matan da ya cuta ne Allah ya saka
musu ya jarabce shi da son macen da ya raina a
da can, lallai da iyayansa sun san irin yanda yake
son Zainabu da sun barshi ya aure ta ko yaya
take. Haka nan ya dinga juyi a gadonsa bai san
sanda bacci barawo ya silalo ya dauke shi ba,
don yana cikin tsananin tashin hankali. Da asuba
da kyar ya iya tashi dan jikinsa duk ya masa
nauyi, a masallaci ya jima yana addu'ar Allah ya
karyo da zuciyar iyayansa su amince ya auri
Zainabu, har gari ya waye yana ta lazimi, sam ya
manta da zuwa Ofis dan haka sai da ya makara.
Ko da ya isa dinma kasa tsinana komai ya yi,
banda kallon hoton Zainabu dake bisa tebur
dinsa babu abinda yake yi, ya sani muddin
iyayansa suka hana shi ya auri Zainabu to kuwa
lallai zai jima bai yi aure ba, kai babu ma rana.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya nufi kujerar da ke Ofis din doguwa ya kwanta
yana neman layin wayarta, bugu daya ta dauka.
Ita ce ta fara magana, "Hello My honey, Zuma
ta."Ta fadi da wata irin murya mai tsananin fisgar
hankalinsa, wacce ta ke siye zuciyar 'yan maza da
ita. Ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "Zainabu ina
tare da matsala mai girma, na rasa yanda zanyi
da rayuwata ba ni cikin hayyacina da walwala ta."
Ta ji gabanta ya fadi amman sai ta dake ta ce,
"Ayya Zumana ka kwantar da hankalinka komai
zai zamo da sauki Insha Allah, ka na ina ne
yanzu?" Ya lumshe idon sa kana ya bude ya ce,
"Ina Ofis yanzu amman na gaza komai, ji nake
kamar bani da lafiya ma." Ta kuma kwantar da
murya ta ce, "Kana jina ko zumana, ka kwantar
da hankalinka gani nan zan zo yanzu Ofis din
naka don bani son bacin ranka....." "A me zaki zo
ne?" Ya tambaye ta da sauri. Ta yi murmushi don
ta san Mustafan ta da shegen kishii ta ce, "Ka
kwantar da hankalinka zan zo a shatar tasi ne,
don nima ina Ofis yau." Ya ce, "Yayi kyau, ina
jiranki kada ki jima." Ta dubi abokin aikin nata da
yake kallonta tamkar maye sai dai duk iyakacin
jarabarsa da gulmarsa ya gaza jin abinda take
cewa, ta galla masa harara kana tace, "Wallahi
Oga kai mugun dan saka ido ne, wannan kallon
da kake mini fa kamar maye?" Yayi dariya yana
sosa keya ya ce, "Ke din Zainabu da tsokano
mutum kike, banda ni waye zai daure zama da
zukekiyar mace irinki yana kallonta..... yanzu dai
ina zaki naga kina shirin fita bayan yanzu D.P.M
yayo waya zai zo." Ta yamutsa fuksa tana fadin,
"Idan yazo kace masa na fita idan da dama zan
dawo." "Zainabu ki yiwa Allah ki tsaya idan
ba....." Ko kuma bi ta kansa bata yi ba ta fice
abunta ya bita da kallo yana girgiza kai sannan
ya ce, "'Yar jidali, yarinyar nan kina gara zama
wallahi, ko da yake kin isa ne." Ta isa Ofis din
nasu cikin wani ubansu leshi, zanin ya zauna
dam a kugunta rafa ne,rigar bata fiye girma ba
don da kadan ta iya wuce cibiyarta, sai dai
hannunta dogo ne, yanayin kirarta ta kalangu ya
fito sosai duk wanda ya kalleta sai ya kara sai dai
mai karfin zuciya, kamshinta ka dai zai iya sanya
ka kalle ta balle kyau da tsarin tafiyarta.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta murda kofar Ofis din ta yi sa'a kuwa a bude
take don yasan zata zo, ta san Ofis din dan kusan
tare suka tare ma, ta shiga da sallama, yana bisa
kujera yayi tagumi, har ta isa inda yake bai motsa
ba sai dai idonsa yana kanta har lokacin. Matuka
kwalliyar ta burge shi, ta isa ta zauna bisa
cinyarsa ta janye hannunsa daga tagumin da ya
yi, ta shafi gurin tana magana kasa-kasa,
"Zumana waye ya taba mini kai?, hankalina a
tashe na iso Ofis din nan." Ya daga idonsa yana
dubanta, abinda ya kuma bata tsoro don ganin
idon yayi jajir da alamar tashin hankali, ta kuma
shafar fuskar sa abinda ke sanya shi jin sanyi a
ran nasa ta ce, "Zumana ka sanar da ni abinda
ke faruwa wallahi hankalina a tashe yake." Ya
lumshe idonsa sannan ya fara magana har
lokacin tana shafar fuskarsa yace, "Hajiya Kubra
tsohuwar Shugabar makarantar ku ta G.G.C Dala
wacce kika yiwa rashin kunya itace Mahaifiya
ta....." Ta mike a zabure gami da dafe kirji tana
fadin, "Innalillahi wa inna ilahihi raji'un, na shiga
uku, Mustafa yanzu Hajiya Kubra Mominka ce?
Wayyo Allah na yanzu ya ya zan yi? Ina fatan
baka sanar da ita ko ni wacece ba?"Ya ware
idanuwansa wadanda suke jawur yana fadin,
"Zainabu babu hanyar fita, Momi ta sanki farin
sani kuma tasan kece Zainabun da nake so yanzu
a raina, Baba na ya sanya anyi masa bincike a
kanki matuka, ina sonki Zainabu amman iyayena
sun hanani auranki, abunda basu sani na yanda
Zainabu take haka ma dan su yake, amman na
rasa ta yanda zan sanar dasu abinda suke gudun
Zainabu saboda shi na dansu ne." Jikinta ya
dauki rawa dan ta shiga tsahin hankali matuka,
ya kamo ta ya tallafe ta a jikinsa yana shafar ta,
ta yi lamo a jikinsa tana ajiyar zuciya tamkar
diyar mage, ta ayyana a ranta wannan wace irin
masifa ce ta doso su, yanda suke son juna ace an
haramta musu auran juna, don dai duniya bata
da abin so kamar Mustafa, ta gama sallamawa
kanta a yanzu shine bango majinginarta, don ta
gaji da walagigin yawon iskanci da shan bakar
azaba ta saida mutunci a gurin maza, domin dai
ta lura yanzu ta sani babu abinda ke tattare da
bin maza sai bata da sai da mutuncin kai,
amman gashi wani katon abu na neman ruguza
mata wannan burin nata. Ta san halin Hajiya
Kubra mace ce mai kafiya da dagewa bisa duk
abinda ta sanya a gaba, wuya da dadi basa
sanyawa ta sauya daga kan ra'ayinta, bata manta
kirarin da malamansu ke mata lokacin tana
makaranta, "Mace mai kamar maza kwari ne da
babu." Sun yi shiru na tsahon lokaci kowa da
abinda yake sakawa a zuciyarsa, sun gaza sanya
kansu farin ciki kamar yanda suka saba a duk
lokacin da suka hadu don basu gundurar
junansu. Ita ce tayi karfin hali tace, "Musty