Showing 9001 words to 12000 words out of 49932 words

Chapter 4 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf

nufar gida.
Sala tana biye da ita itama tana dariya da yi
mata kirari, "Abula tawa, kowa ya ja dake yaji
kunya. Mahassada kun sha kashi. Yarinya mai
tsada kalar manyan maza."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
KANO 11 GA WATAN 6, 1993.
Rayuwa mai sauyawa, sai dai ga Abu sauyi da
aka samu kalilan ne, domin dai cigaban nata bai
wuce na daina daukar abinci akanta,sai dai a
dorawa dan dako tana biye dashi ba, sai kuma
chalo da ta daina zuwa da dibar 'ya'yan jama'a
a tafi tsokanar fada duk ta daina. Sannan
kyawun ta da kirar da Allah yayi mata mai
daukar hankali sun fara bayyana. Sai kuma Abu
mafi girma da za'a idar bai wuce daina tallar
safe ba, saboda shugabar makarantarsu ta
budewa Abu wuta saboda jarabawa da aka yi ta
shiga aji biyu na sakandire amman sai ya
zamana Abu ce ta dauki na karshe a ajinsu,
sannan ko a jikinta (wai an mintsini kakkausa).
Abun ya konawa Hajiya Kubra rai, don haka ta
sanya aka tara mata duk wadanda suka zo na
karshe na kowanne aji, ta sanya su a gaba tayi
musu kaca-kaca, sannan tace lallai sai kowacce
tazo da mahaifinta domin tana son jin dalilin da
ya sanya basu mai da hankali akan karatun ba
har suka zo na karshe, dukkansu yaran jikinsu
sai kyarma yake yi kowacce a tsorace take
amman banda Abu dake ta murguda baki tana
magana kasa-kasa, sarai Hajiya Kubra ta ganta
amman sai ta rabu da ita da zummar idan
mahaifinta yazo za tayi mata hukunci a
gabanshi, haka nan suka tashi kowacce ta nufi
gidansu tun lokacin tashi baiyi ba. Abu tana
shiga gida babu ko Sallama bagazan-bagazan-
bagazan ta yadda jaka da hijabin tana fadin,
"Wallahi Sala ba zan kuma zuwa makarantar nan
ba, don na gaji da masifar shegiyar principal
dinmu, sai kace wata uwata haka kawai ta tsane
ni." Sala ta dubeta da kulawa tana tambayarta
"Mai tsada yaya akayi ne? Mai ya faru naga ko
lokacin tashi daga makarantar bai yi ba." Ta
tabe baki kana tace "Wai kawai dan munzo na
karshe shine ta sanyamu a gaba tanata

zaginmu, baki ga sauran ba jikinsu har rawa
yake yi, ni kuwa duk abinda tace sai na bata
amsa amman dai a hankali, kuma tama yi sa'a
dan 'yan arzikin a kaina da saina rama," "Kinyi
mini dai-dai, sai kuma aka yi yaya?" Sala ta
katse ta. "Wai kuma duk cin mutuncin da tayi
mana bai isheta ba wai lallai sai mun zo da
Babanmu, ni kuwa wallahi bata isa ba ai dai ba
karatun shiga Aljanna bane."
Sala ta amshe "Wannan tsabar rainin hankali
ne, haka kawai dan kunzo na karshe sai ace
wani sai kunzo da Babanku? To ai ba laifinku
bane sune basu iya koyarwa ba, ai zuwa
makarantar ba dole bane kiyi zamanki kin huta
da tashin safe ma." Wannan ne ya sanya Abu ta
share gindi tayi zamanta a gida har kusan sati
biyu bata je makaranta ba, sai rannan da Sadiku
ya shigo da hantsi wajen karfe goma, shima ya
dawo makaranta sai kuwa suka yi kicibis, yayi
kanta da masifa yana fadin mai ya hanata zuwa
makaranta. Ta zura dakin Sala da gudu dan duk
iskancin Abu tana tsoron Sadiku dan bai mata ta
dadi, dan babu wuya ya lakada ta. Sala ce ta
fito tana hargagi gami da sanar dashi yanda aka
yi. Ya kuma kulewa yace maza ta shirya ya
maida ta idan kuwa ba haka ba sai dai idan ta
daina fita ne wallahi sai ya karya mata kafar
talla. Sarai Sala ta san halinsa dan haka ta
lallaba Abu dake ta kunci ta fita suka nufi
makarantar. Sanda suka isa ofishin (principal)
shugabar makarantar ya dinga bata hakuri yace
Babansu ne baya gari shi ya sanya ba'a kawo ta
ba, shi kuma bai sani ba yana makaranta sai
yau da ya dawo ya taddata a gida. Da farko
Hajiya Kubra tace ba zata saurareshi ba sai dai
idan ya nuna mata katin shaidar cewar shi
dalibi ne I.D card, tayi mamaki sosai da taga
abinda yake karantawa (Law) amman kanwarsa
muguwar dakikiya. Ta bashi guri ya zauna
sannan ta sanar dashi irin mugayen dabi'un Abu
da kuma dakikancin ta. Yayi kwafa cike da
takaici yace "Babanmu yace a baki hakuri
sannan yace kafin na bar Ofis din na kiyi mata

bulala guda hamsin, kuma yace daga yau
kowane irin laifi tayi a daina korata gida tunda
ba fada takeyi ba dan bata son karatun, a dinga
bata horo mai tsanani kowanne iri ne." "Karya
kake yi wallahi, yaushe har kaga Baban mu daya
fada maka haka?" Ta katse masa magana da
rashin kunya da hargowa. Mamaki da takaici ya
kama Hajiya Kubra, wato bata bar na gida ba
balle na waje ma. Shi kuwa Sadiku saboda
tsabar takaici kasa magana ma yayi, sai dai yaga
wata bulala a kan teburin Hajiya Kubra dan haka
ya dauko ya hau zabga mata, tun tana ihu da
makaleshi har ta gaza bakin nan nata sai da ya
mutu, gashi babu Sala mai kwatarta ita kuwa
Hajiya Kubra dama a cike take da ita dan haka
ko uffan bata ce ba, daman duniya idan akwai
abinda take tsoro bai wuce dukan Sadiku da na
Malam ba, domin basa mata na wasa, gashi
sune kadai zasu daketa a duniya su daki banza
dan babu abinda Sala zata iyayi, sai dai tayi
hargaginta ta gama dan ba zata iya rama mata
ba, su kuma bata isa ta dauko musu 'yan sanda
ba kamar yanda ta saba.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yawan dukan da yayi mata ne ya sanya ran
Hajiya Kubra yayi haske, ta tabbatar lallai akwai
mai kwabar Abu jine kawai da bata yi. Bayan ya
jibgeta ya gaji ya dubi Hajiya Kubra yace "Hajiya
ki bata fartanya tayi noma da kuma wankin
bandaki." Abu dake kwance tana kuka ta kuma
kurma ihi tana fadin "Wayyo Sala na shiga uku
kizo da kanki,A zuciye ya kuma kai mata duka a
bakinta wanda ya sanya ta yin shirun dole dan
sai da bakinta ya fashe, amman bata daina
harararsa da murguda baki ba. Haka ya tafi ya
barta saida tayi noman nan da wankin bandakin
dalibai wanda yayi kaca-kaca da kashi babu

kyan gani, dan saida ta daure hancinta da
dankwalinta sannan ta iya wankewa, shi dai
Sadiku yayi tafiyarsa, amman yasan yau bala'i
sai yasha ya more gurin Sala. Ai kuwa haka din
akayi domin dai data dawo gida taga idonta da
bakinta sun kumbura ta zabura da sauri tana
tambayar abinda ya faru. Abu ta zube a tsakar
gida ta dora hannu a kai tana zunduma ihu
kamar wacce akayi wa mutuwa ko kuma a
sannan ake dukan nata tana fadin "Wayyo Sala
na shiga uku, wallahi bazan taba yafewa Sadiku
ba ko kabarinsa zai dinga balbala da wuta..."
"Wai me ya faru? na san za'a rina daman, me
yayi miki?" Sala ta tambaya a rude. Ta kwashe
duk yanda akayi ta sanarwa da Sala tana ajiyar
zuciya dan babu alamar hawaye ko kwalli a
idonta. Habawa ran Sala idan yayi dubu ya baci,
ta dinga sirfa masifa tana fadin "Ai makarantar
ba dole bace da har za'a kama ki da wannan
dukan a fasa miki baki da hanci, tunda kin iya
daurin dankwali ai magana ta kare, ladan ya isa
haka. Shi kuwa dan Baba zaizo ya sameni
wallahi sai nayi mummunan saba masa, sai ya
yabawa aya zakinta."
Haka nan ta wuni tana mita kamar zata ci babu.
Shi kuwa Sadiku yana sane yaki dawowa gidan
da wuri sai da ya bari dare yayi ya lallaba kicin
dan ya dauki abincinsa, ai kuwa tayo waje
daman lambo tayi tace dawa Allah ya hadamu,
donma dai ya wuce duka ne da ranar sai yasha
duka a gurin Sala, shi kam ko kala baice ba da
yaga ba'a ajiye masa abincin ba ya juya ya fice.
Ta bishi har zaure tana fadin "Babu zuciyar
nema sai ta ci, ita dai wacce ka tsana din ce ke
nemo abinda kake ci kuma wallahi ko ruwa ba
zaka sha a gidan nan ba, idan kayi zuciya ka
siya, wanda na san ko sisi baka da shi baya ga
tarin takardu da bakar zuciya." Shi dai dakinsa
ya shige ya kwanta ranar haka ya kwana da
yunwa, ita kuwa saida ta kusa kwana tana mita.
Wannan shine sanadiyyar daya sanya dole aka
daina tallar safe, domin dai Sadiku yace duk
sanda tayi laifi a daina turata gida tayi noma da

wankin bandaki, abinda ta tsana a rayuwarta,
ya kuma rantse idan ta daina zuwa makarantar
sai ya ballata yaga da kan da kafar da zata yi
tallan, dole kanwar naki aka hakura da tallan
safe dan ta dinga zuwa da wuri. Da farko Sala
tace bata yadda ba amman ganin da rana ma
ana samun ciniki mai yawa kuma ita Abu tana
tsoron bala'in Sadiku ya sanya dole suka
hakura, sai dai su Karima suyi tallan safen kafin
su tafi makarantar, amman ita da yake ba irin
halinsu daya da Abu ba takanyi hanzari ta saida
ta tafi makaranta, domin ita halinsu kusan irin
na Sadiku ne shiya sanya basa shiri da Sala
sosai kullum tana mata fada da cewar mai kan
kwantai.
Misalin karfe biyu na rana ta fito daga gidansu
dan dakonta yana dauke da fantekar abinci da
kwanuka da miya a kansa, ita kuma tana rike da
farin bokitin roba mai haske an yanka salak da
tumatir da albasa, daya hannun kuma kaji ne
soyayyu cikin irin farin bokitin, anyi wanka an ci
kwalliya, zanin nan an daurashi kwauri a waje
anja jagira lebe yasha jambaki da baki, sai dai
anyi kilin an daina dige-dige da kwalli, hatta
takalmi dan madina dake kafarta yasha wanki
sai sheki yake yi, ana tafe dagwas-dagwas
kamar mai jin tausayin kasa, domin tun can
daman Abu akwai tsafta da kwalliya balle yanzu
da aka fara zama 'yan mata, gwalli da feleke ya
karu, duk cikin kawayenta tafi kowa iya tsara
kwalliya, daman gata ba baya ba gurin kyau.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
zandakata a nan,insha Allahu Zuwa yamma
zamu dora,domindai aikin Littafin yayi bisa,Wata
tangarda ce ta hanani farayimuku a
ana,nagode..

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100



Idan Zuciya Tagyaru 1-02
Posted by ANaM Dorayi on 05:26 AM, 28-Jan-16
Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU
_________________ Na
________Fauziyya D Sulaiman____
Mustafa dake zaune kofar gidansu bisa farar
kujera karkashin bishiyar Umbrella, yana
karatun jarida kamshin Abu ya bugi hancinsa ya
daga kansa da sauri yana dubanta, kusan sati
guda kenan yake ganinta tana wucewa irin
wannan lokacin, kwarai yarinyar ta kwanta masa
a ransa, da kuma dai alamun ba za'a sha
wahalar samun kanta ba, kullum yana son yi
mata magana amman ya rasa ta yanda zai fara,
yau dai dabara ta fado masa dan haka ya fara
kwala mata kira. "Ke! Ke mai abinci! Kawo." Ta
tsaya turus gami da waigowa tana dubansa,
domin bata saba saida abincinta cikin unguwa
ba sai ta dangana ga tashar kofar wambai,
amman sai taga yayi mata kwarjini ba zata iya
kin saida masa ba, domin dai abincinta sai
wanda taga dama take saidawa, don haka ta
hau kwalawa almajirin dake dauke da abincin
kira "Kai Mudi! Kawo abincin za'a siya. Babu
musu yayo ribas ya juyo, ya isa gaban Mustafa
wanda ke zaune akan farar kujera mai tambarin
kamfanin coca-cola ya tsaya kerere. Ta galla
masa harara tana fadin "Kai fa tamkar jaki kake
komai sai ance kayi zaka yi ko? To sauke kayan."
Sannan ta dubi Mustafa tace "Malam na nawa
za'a zuba maka?." Yayi wani mayaudarin
murmushi yana mata wani duba na yaudara da
kwarewa a harkar iya soyayyar 'yan zamani yace
"Haba 'yan mata babu ko gaisuwa?" Tabbas yayi
masifar yi mata kwarjini, hasalima tunda suka
hada ido taji wani abu ya bugi zuciyarta wanda

ya sanya ba zata iya yi masa musu ba ko rashin
kunya, shi kansa ya gano hakan a kwayar idonta
ya kuma san haka nan Allah yayi masa kwarjini
da farin jini ga kowa, domin dai da wani ne
cewa zatayi, ban iya ba ko kuma tace baka kai
matsayin da za'a gaidaka ba din ne, amman shi
sai ta tsinci kanta da ce masa "To ina wuni?"
Yayi dariya yace "Ko ke fa, lafiya kalau, yaya
sunanki ne, dan kallon farko naga kin mini dari
bisa dari."
Ta kosa da zancan nasa ta daure dai tace "Ka ga
sauri nake kada rana tayi mini, na nawa za'a
baka? Dan kada kaja nayi kwantai." Ya kuma
murmushinsa dake kashe mata jiki yace "Haba
dai, ai kyawawa basa kwantai, ko domin kyanki
ai a sayi abincinki." "Ka ga nifa zan wuce kana
bata mini lokaci, wallahi dan kaine kawai na
tsaya." Ta fada tana yamutsa fuska. Ya kanne
mata ido daya yace "Haba dai ke kya soma
tafiya ban san sunanki ba? domin dai zaman
nan naki ne, dan tun randa na fara ganinki
Allah ya dasa mini tsiron sonki a raina wanda
kullum yake kuma girma, dan haka nake zama
kawai naga wucewarki naji dadi. Ta dubeshi cikin
ido, yanayin kallon da yake mata ya kashe mata
jiki ta gaza masa komai, amman sai ta dubi
Mudi da ya baza kunnuwa kamar na zomo yana
sauraran abinda suke fada tace "Mudi dauki mu
tafi yana bata mana lokaci." Mudi ya yunkura zai
dauka amman sai Mustafa ya dakatar dashi
yana fadin "Kai ajiye, maza nemo 'yan uwanka
almajirai ka raba musu, kyaky-kyawa kamarki ai
kin wuce tallan shinkafa, ke fa gimbiya ce."
Yana maganar yana dubanta da wani kallo daya
bambanta da wanda samarinta kucaku ke mata.
Mamaki ya cikata amman sai ta gaza cewa
komai tayi shiru kawai tana dubansa. "Kaje
mana ka kira 'yan uwanka ka raba musu ka
baza kunnuwa ka saki baki sai kuda ke fadawa."
Yace da Mudi wanda ya saki kunne da hangame
baki yana dubansu. Mudi dai gani yake kamar
da wasa yakeyi, amman da yaji ya doka masa
tsawa ya kuma nanata masa ya sanya ya fara

kwalawa 'yan uwansa kira. "Alalan Alalan
almajiri, Alalan Alalan kazoo kaci, Alalan Alalan
Alalan kai ba tumatiri." Ai kuwa nan da nan
gurin ya cika da almajirai, yace "To maza abi
layi." Ya kalli Mustafa dake kallon su. Mustafa
yace "Ka rarraba musu mana." Ai kuwa nan da
nan ya fara zubawa almajirai kafin kace kwabo
sai fanteka da bokitin salad. Abu na tsaye rike
da kugu cike da mamaki tana kallonsa, lallai
wannan mutumin dan rikice ne, ko tambayarta
kudin abincin baiyi ba yasa aka raba, zata yi
maganinsa kuwa yau, don wallahi sai ta tsuga
masa kudi masu yawa. Ya dubi Mudi yace "To
maza a hada kayan a koma gida uwar dakin
naka zata taho yanzu." Sai da yaga Mudi yayi
nisa sannan ya dubeta na dan wani lokaci tana
tsaye rike da kugu da alamun mamaki da
shakka a fuskarta. "Adon gari tunanin me kike
yi? Har yanzu baki fadi mini sunanki ba." Ta
yamutsa fuska tace "Sunana Abu......" "A'a
babban suna Zainabu Abu mai tagwayen suna
kenan, gaskiya Zainab baki dace da kalar tallah
ba, dubeki fine baby ace kina daukar tallah? to
gaskiya ni dai daga yau na soke tallar nan." Ta
dubeshi a tsiwace tace "Ka ji mu da mutum sai
kace wani Ubana? ko kai ne zaka dinga biyana
kudin da nake samu eye?" Yace "Eh mana zan
dinga biya ko nawa ne, don gaskiya bana son
rana tana taba mini kyaky-kyawar fuskarki,
kyanki hutu Zainabu."
Ta tabe baki don zancen bai gamsar da ita ba,
don tasan bai san yawan kudin bane shiyasa
yake wani cika baki amman yanzu zata yi
maganin firiritarsa. Don haka tace "Ka ga ka cika
ni da surutu bayan baka biyani kudin abincina
ba." Yayi dariya yace "Haba Zainab, baki yarda
dani ba naga alama, ko don kin ganni da dan
wando jeans da shet? kin san mu 'yan boko
bamu san kaya masu nauyi, amman nawa ne
kudin? Kila idan na baki hankalinki yafi
kwanciya." Ta murguda baki wanda ya zame
mata kamar al'ada sannan tace "Dari uku da
ashirin da biyar ne, sai nama na naira talatin da

biyu...." "A'a Zainab, duka zaki hade mini?" Tayi
dan duru-duru don tasan zulake tayi duka
kayan nata basu wuce na dari biyu da tamanin
ba, don haka ta kasa hadewa ta fadi don bata
iya lissafi ba (bata da Maths tab akin yara), da
ya fahimci halin da ta shiga sai ya zura hannu a
aljihunsa ya debo 'yan murtala (Naira Ishirin)
har na dari hudu yace, "Ga dari hudu ma ni na
kara miki." Mamaki ya cikata matuka, hannunta
har rawa yake yi gurin karba don tana ganin
kamar zai maida yace ya fasa ne. Sai da taji
dumin kudin a hannunta sannan hankalinta ya
kwanta ta dube shi da mamaki tace "To nagode!
Zan tafi gida." Yace "A'a ai dole na yiwa gimbiya
rakiya ko don naga gidansu." A wannan karon
bata yi masa musu ba don yayi mata ba zata,
don haka suka nufi hanyar gidansu, a kofar gida
yayi mata sallama yace sai gobe tace Allah ya
kaimu. Ta shiga gida da gudunta Sala na zaune
tayi tsuru cike da shakkun labarin da Mudi ya
bata, gaskiya tafi zargin bari kawai suka yi yace
wani wai juye wani saurayi dan gaye yayi mata.
Abu na shigowa ta mike da zakuwa tace, "Ke
maza sanar dani menene ya faru?" Abu tayi
dariya gami da nuna mata kudin da saurayin ya
bata, ta fizge daga hannun Abu da azama ta
hau kirgawa, Abu kuwa sai dariya takeyi. Sala ta
kammala lissafawa ne ta dubi Abu cike da farin
ciki tace "Diyar arziki yau kuma wane mai arziki
kika hadu dashi? Kai wannan diya da kan arziki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login