Showing 6001 words to 9000 words out of 49932 words
Chapter 3 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf
inci (ta kunduma zagi)." Ta isa
gabansa yana shan tabar wiwi sai wani lumshe
ido yake yana rere wakoki kala-kala na gambara
zuwa wakokin 'yan dambe da na barayi, kai
gasu nan dai barkatai. Abu ta rike kugu tana
wani karkada kafa tace "Kai barawo bani kudina,
rannan na zuba maka abinci ka gudu baka bani
kudina ba, to yau Allah ya kama ka, ko ka bani
kudina ko nayi maka rashin mutunci wallahi. Ya
dubeta yana murmushin mugunta yace "Banza
ke wallahi karamar arniya ce, har kin isa kiyi
mini wata barazana, to na cinye na karfi ne ki
kwata." Ta tafa hannu tana fadin "Kan Ubancan,
lallai yau ka tabo ma kanka, yau zan nuna maka
kai karamin dan iska ne, dan ko sama da kasa
zata hade sai ka bani kudina." Ta kama kwalar
rigarsa ta cukwikwiye tana cigaba da bala'i. Shi
kuwa sai dariya yake yana fadin "Yarinya kece
mai aikin yi, in dai nine wallahi mu kwana a
haka." Ya cigaba da zukar wiwinsa yana lumshe
idanu. Jama'a sukayo gurin suna bada hakuri,
Abu tace wallahi ba zata cikashi ba sai ya bata
kudinta idan kuwa ba haka ba zata dauko masa
folis ita kam Laraba da yake matsoraciya ce sai
hakuri take baiwa Abun. Maimakon ta hakura
sai ta doka mata tsawa tana fadin "Dalla can
malama gafara daga nan, Uwarsa ta kauye ce
take bani jari ko ubansa na karkar....." "Ke Abu
don kazanki ni kike zagi?" Rodimasta ya katseta
a hasale dan ya fara kufula da rashin mutuncin
da take masa. Babu tsoro balle fargaba tace "An
zageka din, kai wanene da ba za'a zageka ba
eye?" Ya kuma hasala da zafin rai yake fadin "Ke
wallahi idan baki sakeni ba zan tattakaki a gurin
nan na farfasa miki jiki." Tayi shewa "Ahayye!
wallahi Bismillah dan halak ka fasa, don ka sani
duk mari daya a folissitashan naira dari yake,
don wata kila sai an hada da gonar kauye
sannan za'a biya kudin marin....." "Ke Abu dan
Allah kiyi hakuri ki sake shi, wannan ai ba
mutuncin ki bane kina mace kina fada da
maza."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta kalli mai maganar tana fadin "Kaga Baba mai
taba ina ginin mutuncinka dan kana biyana
kudina ba irin wannan dan bashin ba, dan haka
kawai ka bar gurin nan sai ya biyani kudina zan
sakeshi." "Kinga ya isa sakeshi nawa ne kudin
naki na biya, tunda shima ya rantse ba zai biya
ba dan idan rigimar tayi zafi har mu zaku jawo
wa tunda dai haka 'yan sandan can ke so a fara
fada suzo kame." Ta murguda baki tana fadin
"Ai wallahi nima ba zan sakeshi ba sai dai idan
ka biyani, naira biyar ne dan haka sai ka biya."
Ya dauko naira biyar a aljihun gaba rigarsa yace
"Gata shike nan rigimar ta kare ko?" Ta saki
rigar Rodimasta tana fadin "Banza matsolo
matsiyaci, yau Allah ya rufa maka asiri da yau
kaga karshen rashin mutunci." "Ke! Ya isheki
tunda dai an biyaki kudinki 'yar matsiyata, dan
wallahi kika zageni sai na tattakaki." Ya fadi
yana nunata da yatsansa. Ta tsaya ta rike kugu
tana wani girgiza tana fadin "Wanda bai fasa ba
baya kaunar uwale da ubale..." Laraba ta
janyeta tana fisfisgewa da kyar aka samu ta
kama hada kayanta tana cigaba da bala'i ta bar
tashar. Tana isa gida ta dire fantekat kayan ta
mikawa Sala kudin wacce ke washe baki, ta fada
daki ta kwanta. Sala taji shiru ta leka dakin ta
ganta a kwance ta bude baki da mamaki tace
"Au Abula kwantawa kika yi? Ke da zaki je
makarantar allo? kada jarababban yayanki yazo
ya ishemu da mita." Ta mike gami da daukar
allo ta fice tana kun-kuni. Miskili kafi mahaukaci
ban haushi, Sala ta fada tana dariya. ta dora da
cewar "Abula diyar Salamatu wani lokaci idan
kina shan kunu ko miskilancin naki ya motsa sai
na ganki kamar wata diyar wani sarki, sai da
lallashi Abula ta." Bata dai ce komai ba ta
ficewarta.
Makarantar dake kusa da gidansu, dan
tsakaninsu gida uku ne, koda taje dinma hira ta
kamayi da kawayenta sai da malam din ya doka
musu tsawa sannan suka rude da hayaniya wai
su nan dole karatu sukeyi. Da ya kirawo ta ta
biya allonta kuwa inda-inda ta kama yi, nan fa
ya hauta da fada, tayi kum da baki kamar ba
Abula diyar Sala ba, dan idan akwai wanda take
tsoro da shayi a duniya bai wuce malam da
yayanta ba, dan malam din bai mata ta dadiba
tun tana 'yar mitsitsiyarta kuwa, gashi babu
yanda zasuyi dashi dan shine kamar matsayin
kakanta na gurin Uba, ya kuma maimaita mata
ta karanta kuwa tsaf. Domin dai duk iskancin da
takeyi tana sane don da ace tana maida hankali
akan karatu da mai kokarice ita dan
kwakwalwarta akwaita da saurin rike abu, sai
dai shiririta da wasa da ta sanya a ranta, dan
yanzu data koma gida zata fita yawo da wasa
dan da kyar gobe zata iya biya yanda ya biya
mata, rudewar da akayi da karatun tashi ne ya
kwace ta. Ana cewa fatiha kowa ya mike yara
suna ta waka suna fadin "Tashiiii." Su Abu da
zugar kawayenta kuwa tsayawa akayi ana maida
yanda aka yi, dan wai wata Lantana tayi
gulmarta, wai yau zasu dirji bakin Lantana da
rubabben kwai. Ai kuwa suka saka ihu aka
sanya Lantana tsakiya tana kuka, sai waccan
tace nima kince mini kaza kince mini kaza, sai ta
tabe baki tana fadin, "Laaa! Ni din?" Sai kuma ta
sanya kuka, Laraba ce ta kuma tunzura fadan
da tace "Eh, nima rannan kince mini wai Abu
tana zuwa gurin Dan Oga mai kyamis, Kutumar
uban can, lallai yarinya a gulmar taki har da ni?
dan ubanki?" Abu ta shiga masifa tamkar zata ci
babu, taci dammara da gyalanta tana cigaba da
girgiza gami da ambaton sunan iyayanta tana
kunduma musu zagi gami da dungure mata kai
da lakuce mata hanci, yara sai ihu suke yiwa
Lantana wacce banda kuka babu abinda take yi.
Malamin sune ya farga da abinda ke faruwa
yayi kansu da dorina, ya samu daya ya caula
mata ta gantsare gami da fasa ihu, abinda ya
ankarar dasu kowa ya bazama da gudu dan
gujewa bulalar malam, wannan ne ya ceci
Lantana daga fasa mata baki da akayi niyya da
rubabben kwai. Ana idar da sallah Abu ta fito
daga gida tana rera wakar kiran wasa don tunda
ta taso itace ke kiran 'yan wasa don ita ce boss
din, don haka ko yara ne ba'a gani ba gidansu
ake zuwa nemansu Sala tayi ta bala'i. Ta fara
rera wakar wasa kamar haka: "'Yan wasa ku
futo wasa, idan baku zo ba ubanku yazo, bani
na fada ba bature ne, baturen ma na kasar
borno. 'Yan wasa ku fito wasa." Ai kuwa sai sai
ga yara suna fitowa daga gidajensu da gudunsu
maza da mata.Yayanta Sadiku dake shagonsa
yana jinta, ji yake tamkar yaje ya shaketa, sai
dai yana gudun jarabar Sala ne, don shi a
zatonshi tun da ya samar mata makarantar
gaba da firamare zata daina wannan wasan
haukan, amman sai yaga babu abinda ta daina,
dan haka yayi niyyar hanata da tsiya amman
Sala tayi tsalle ta dire tace Wallahi bai isa ba ya
kyale mata yarinya ta wataya.
"Aljana a kwaba ba tsari, aljana a kwaba ba
tsari....." Wannan wakar ce ta katse masa
tunanin da yakeyi, ya mike ya leko da sauri don
yasan wa suke tsokana. Ai kuwa yana hango su
sunyi zuga suna biye da wata karuwa da taci
kwalliya da wani matsats-tsan siket kanta babu
dankwali balle mayafi, tana tafe da kyar da
sauri tamkar siket din zai yage, kanta tamkar
tozon rakumi ga takalmi sakadale tumeme da
kafarta, amman sunki saurara mata sai binta
suke suna mata wakar da ihu gami da bula
mata kasa. Can wasu dattawa wadanda ke
zaune suma suna zabga uban musu, dan sunan
majalisar tasu ma majalisar 'yan musu, suka yo
kansu sanda suka ankara da duka.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nan fa suka runtuma da gudu suna dariya, sai
da sukayi nisa sannan suka zube a kofar wani
gida sunata dariya. Can Abu tace "Laaa! Ku tsaya
kuji wallahi yau mu kai sumame gidan shegun
can Karuwai mun dade wallahi bamu je ba ko?"
Yaran suka amsa da "Eh! Wallahi mu badawa
shegu tiyagas din toka." Abu tace "To kowa ya
tsaya bari naje gida na samo toka da citta a
gurin Sala." Ai kuwa cikin kankanin lokaci suka
hada citta da barkono dakakku da kuma toka
cikin ledoji suka kulle da dutse a tsakiya suka
nufi gidan karuwai ta bayan layi don kada a
gansu. Sun yi sa'a kuwa da yawan karuwan
suna daki suna hira da lalatattun maza 'yan
uwansu, wasu kuma ma suna caca da masu
aikata babbar alfasha. Suka shiga cikin gidan da
sanda kamar wasu barayi, har tsakar gidan suka
isa, cikin daga murya Abu ta bada umurni, "A
fasa! A fasa!!.Ai kuwa ji kake tush-tush-tush,
nan da nan karuwai suka kama ihu da atishawa,
na daki suka yo waje da gudunsu wasu daga su
sai siket, wasu kuma sai zani, harda masu dan
kamfai. Su Abu suka fasa ihu suna dariya gami
da ficewa da gudu daga gidan dan kada a
kamasu, sai da suka isa wani kofar gidan can
nesa da gidan karuwan suka zube suna dariya,
suna hango yanda suke ta atishawa.
Hantsi ya dubi ludayi sanda Abu ta dawo daga
tallar waina. gashi anyi sa'a ranar babu
makarantar boko, dan haka ta zauna a tsakar
gida tana baiwa Sala labarin yanda sukayi da
karuwan jiya suna ta kwasar dariya, Sala kam
harda durkusawa tana rike ciki. Can suka jiyo
sallama, tun kafin sukai ga amsawa aka shigo,
mutane guda biyu da kayan 'yan sanda a jikinsu
riga da siket, sun daure kugunsu da bel. Sala ta
mike cike da mamaki tana tambayarsu "Yaya dai
bayin Allah lafiya ko? Don ganinki babu alheri."
Daya daga cikinsu ta fara magana "Hajiya munzo
mu tafi da 'yarki mara mutuncin can Abu,
domin dai ta addabi uban kowa a unguwar nan,
idan yaso idan munje folis sitashon kya ji abinda
ta yi." Abu ta mike da sauri tana tillika dariya
dan tasan kwanan zancen tana fadin "To muje
din mana, Sala kiyi zamanki yanzu zan dawo."
Sala tace "A'a ba zan iya bari ki tafi ke daya ba
muje." Ta dauko gyale akan igiya suka fice tana
fadawa Karimatu ta lura da abincin da ta dora
kafin ta dawo. 'Yan sandan suka fara kuluwa da
dariyar da Abu take musu, dan haka suka ce
wallahi idan bata daina ba zasu yi mata shegen
duka, ta gumtse baki tana yi a ciki don bawai
tsoronsu takeji ba, a haka suka isa har folis
sitashon din. Ganin karuwai sun jeru ne har da
'yan daudu ya sanya ta kuma tabbatar da
zargin da takeyi, kamar ta fashe da dariya
amman dan tana gudun sharrin 'yan sanda ya
sanya ta gumtse bakinta. Ta isa gindin kanta
inda wani dan sanda yake zaune da gashi buya-
buya a bakinsa wai shi nan sajan ne. Yana wani
muzurai ya dubi Abu yace "Ke mai ya sanya kika
je gidan wadancan masu zaman kansu kuka
barbada musu toka hade da yaji?" Abu tayi
shiru taki cewa komai, ya kuma maimaita mata
maganar amman taki tankawa. Wani kurtun dan
sanda dake tsaye ya daga kulki ya maka mata a
gadon baya, ta gantsare gami da fasa ihu tana
sosa gurin tana fadi "Wayyo Allah na na shiga
uku, wallahi idan ka karya mini kashin gadon
baya na bazan yadda ba." Ya kuma dagawa zai
maka mata amman mai mukamin sajan din ya
hanashi domin idan da sabo sun saba da halin
Abu, sannan ya maida dubansa gurin Abu ya
daka mata tsawa ya kuma maimaita tambayar
da yayi mata da gargadin idan ta kuma yin
shirun zasu saba mata. Ta murguda baki gami
da kallon sa kyar da idonta babu alaman shakka
ko tsoro tace "Wallahi ko zaku kasheni ba zan yi
magana ba sai dai muje gaban (D.P.O)." Sala
tace "Abu kiyi magana kada su tsamama miki
jikinki." Ta kuma hasala tace "Sala kiyi shiru,
haka kawai sai su kama dukana bayan basu
kama ni da laifin komai ba? Ai nasan 'yancina
dan haka ba zanyi magana ba sai dai muje
gaba." Ran 'yan sandan ya kuma baci suka yi
mata caa tamkar zasu cinyeta amman ko gezau
batayi ba, ana cikin haka sai ga (D.P.O) din ya
shigo,
Da mamaki ya dubi Abu yace "A'a, Abu lafiya na
ganki a nan?" Ai kamar jira take ya shigo sai ta
fasa kuka kamar wacce aka yiwa dan banzan
duka, amman fa idon nan nata babu alamar
hawaye ko digo sai dai burarin kawai da takeyi
tana rike bayanta . (D.P.O) din yace su shigo
daga cikin Ofishinsa su duka, Dan daudun dake
tare da Karuwan ya rike haba yana fadin "Oh!
Ni Hajiya Ladi yau na gamu da shegiyar yarinya
mai sharri, wallahi ko kwallaba nan ta ganki ta
kyale, ai wallahi ko mutuwa zakiyi ba kuka ba
sai kinci ubanki." Ya karasa maganar yana tafa
hannu da cinya. "Kai! keep quit kayi mana
shiru." Wani kofur ya doka masa tsawa. Yayi fari
da ido gami da fadin "Lalala! Ka manta wallah
Hajiya Ladi nake ba kai ba." Da haka suka shiga
ofishin D.P.O din. Mai tuhumar Abu Sajen
Barewa ya karantawa D.P.O tuhumar da ake
yiwa Abu, da kuma abinda ya faru. Ya dubi Abu
yace "Kina jin zargin da ake miki? haka ne ko ba
haka na ne?" Ta lankwashe murya cikin ladabi
tamkar mutuniyar arziki tace, "Yallabai karya
suke mini, ni jiya da daddare ma ina gurin
tallan gyada ta, har kazo wucewa kace na kai
maka gwangwani goma a majalisarku ko?" Ya
dubi karuwan yace "To ku kunji abinda wacce
ake tuhuma tace, ko kuna da wata hujjar da
zata nuna mana itace din ta bada muku toka?"
Hajiya Ladi ya tafa hannu yana fadin "La'ilaha
illallahu, Allah na yarda yarinyar nan shegiya ce
kwalba." "La-la-la ka zage ni?" Abu ta fadi ta
dora da cewar "Yallabai kana ji yana zagina a
gabanka hakama acan waje yayi ta zagina."
D.P.O ya doka masa tsawa yana fadin "Kada ka
kuma zaginta." Ya rike haba yana fadin "O! Ni
Hajiya Ladi na shiga uku, tuba nake Yallabai ayi
hakuri na daina zagin, amman kwaran-kwatsa
dubu jiya ina suyar doya na shiga bandaki dan
na rage marata, na jiyo hayaniyar su Abu, kafin
na farga har na fara tari da atishawa a cikin
bandaki da kokarin shidewa har zani na yana
faduwa, da kyar 'yar fisuwa ta kamoni ina
kokarin bankawa cikin masai. Ko ba haka ba
'yar fisuwa?" Ya kalli wata karuwa da taci uban
bilicin, kan nan tamkar tozon rakumi daga ita sai
gajeren wanda iyakacin gwiwa da riga tishet.
Tana tsaye rike da kugu tace "Haka ne yallabai,
tabbas yarinyar nan ce ta gayyato mana yara
suka watsa mana toka mai yaji, dan da muryar
ta ma muka gane ita ce" "Karya kike yi bani
bace, daga jin murya sai kice ni ce? Idan kuma
kin yarda ki rantse da Allah ko a kawo Qur'ani
ki dafa." Abu ta katse ta. D.P.O ya ce "Kunga
tunda dai abun nan baku da shaida zargi ne
kawai kuke yi, dan haka ki basu hakuri ke Abu,
idan yaso a gaba sai kuyi kokarin kama koma su
waye ke muku haka."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya dubi Sala ya cigaba da magana "Ke kuma kije
ki baiwa sajan din da ya karbi laifin kudin shan
ruwa, na kashe case din kowa ya fita." Sam ba
haka karuwan nan suka so ba, amman tunda
dai basu da cikakkiyar shaida dole suka hakura
suka fice, ita kuma Sala ta baiwa Sajan Barewa
Naira hamsin tace ya sha ruwa. A harabar caji
ofis din suka kuma cin karo da karuwan da
Hajiya Ladi suna mai da yanda aka yi.Abu ta
dubi Hajiya Ladi tana dariyar keta har da gwalo,
Hajiya Ladi ya dalla mata harara yana nuna ta
da yatsa alamun kashedi, ta kuma sanya dariya
gami da sanya hannu a wuyanta ta ja shi alamar
yanka, sannan ta nuna Hajiya Ladi. Hajiya Ladi
ya saka Salati "La'ilaha illallahu, ni zaki yanka?
Lallai yarinyar nan baki da mutunci, to gwara na
koma na fada su zama shaida tun bamu bar
gurin ba." Yana magana da karfi yana tafa
hannu da buga cinya, gaba daya hankalin
jama'ar dake gurin yayi kansu. Abu ta
marairaice tana fadin "Dan Allah jama'a wa yaji
sanda na yiwa mutumin nan magana balle har
nace zan yanka shi? to muje din mana a kwatar
mini hakkina tunda abin naka sharri ne, tunda
dai kowa yana ji anan bance da kai komai ba."
Sannan tabi bayan Hajiya Ladi da sauri dan su
koma ciki tare. Hajiya Ladi ya tsaya da sauri
sororo yana kallon Abu, domin dai lallai ya hadu
da wacce tafi shi sharri da iya iskanci. Da zolaya
Abu tace "Yaya ka tsaya mu tafi mana." Ya
dallawa Abu harara yana fadin "Kwalba uwar
sharri, kada ki kuma kirana da kai sunana Hajiya
Ladi, idan kuma jurinki iskanci zamu kuma
gauraya sai na nuna miki ke din baki isa komai
ba wallahi." Ya tafa hannu gami da bugawa a
cinya yana wani murguda baki da karkafa ido,
ya dora da cewar "Kun ga kuzo mu bar harabar
police station tun shegiyar yarinyar nan bata
haddasa mana ciwon zuciya ba, kunga tafiya ta."
Ya gyara daurin zanin dake bisa wandonsa gami
da dane hannu yana tafiya yana wani yanga,
suka rufa masa baya suna mai da yanda aka yi.
Abu ta kyal-kyale da dariya gami da