Showing 12001 words to 15000 words out of 49932 words

Chapter 5 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf


kike, shi ya sanya aka tsangwameki a unguwar
nan, ki dubi yadda su Sarai da Sakina kawayenki
suke kwantai kullum sai sun dawo da ragowar
abinci, sai dai a cinye ko kuma akai dakalin 'yan
kwantai da daddare abincin naira biyu a karyar
dashi naira daya koma sis daya. Abu tace "Bari
ke dai Sala, ni tunda nake ma ban taba haduwa
da mutum mai ban mamaki irin wannan ba."
Sala tace, "Yaya ne sunansa?" Ta tabe baki tace
"Oho!!! Ni ko tambaya ma banyi ba." "Kiji
sokuwa, arziki yana kiranki kina masa kutufo, to
gobe ki tambayi sunansa kuma ki saki jikinki
dashi, kin san su irin wadannan basu son ki

dinga dari-dari da su, idan abin ma gaba
daya....." Abu tayi dariya gami da shigewa
dakinta. … Allah ya shirya.
Washegari ma haka ce ta faru, Mustafa yayi
mata juye ya rako ta gida, sai dai wannan karan
ya tsaya sun dan taba hira duk da ya lura
sokuwa ce sam bata waye ba, da kuma alama
girman jiki ne kawai da ita babu shekaru, sai dai
ko menene shi dai yaji ya gani yana kuma so a
haka.
Yau da gobe sabo da shakuwa ya shiga
tsakaninsu har ya zama an daina fita da abincin
ko ina sai dai a bawa almajirai a gida. Abu an
daina fitowa kamar yadda Mustafa yace bai son
kyaky-kyawar fuskarta ta baci da zafin rana don
haka tana gida kullum. Wani abu kuma da
Mustafa ya koya mata shine cin dadi, yanzu
abincin kala-kala take ci ba irin wanda take ci
ada can ba, ga kaya da yake kawo mata na
kwalliya da na sanyawa, sai ga Abu ta kuma
futowa fes da ita kuma yanzu da motar Babansa
ma yake zuwa zance gurinta ko ta Mamanshi
don haka cikin motar suke zancensu. Ta futo
daga wanka tana tsakar gida bisa tabarma da
kayan kwalliya a gabanta ana ta kwalliya da
hasken wutar nefa, dan Mustafa na gab da
zuwa, Sala ta zauna daga bayan ta tana kallonta
cike da murmushi tace, "Kai diyar nan wallahi
akwai ki da kwalliyar daukar ido, dubeki kamar
wata sarauniya. Ai ba don bamu gama cin kudin
ba da kin auri yaron nan don ya dace dake, ga
kyau ga kudi, sai dai na lura kamar dai iyayensa
ne masu kudin ba shi kansa ba ko?" Abu ta
tabe baki tace, "Oho! Ni ban sani ba, ke idan
banda abinki ma Sala yaushe na isa aure? Ni
yanzu ma sai nayi digiri, don Mustafa yace mace
idan tayi ilimi wai tafi kyau da tsada. Ni fa yanzu
Sala dan-na-sanin talla ma nake yi, ki dube ni ki
gani yanzu kamar wata diyar wani basarake."
Sala tayi shewa gami da rangada guda tace, "Kai
Allah nagode maka, ai abinda nake ta nusar
dake kenan tun da can, ki sami samarin da zasu
dinga kashe miki kudi mu huta da tallan, yanzu

ba gashi munyi kyau ba? Ga kudi suna shigowa,
wannan shegen yayan naki yana saka mana
ido." Ta ja tsaki, "Mtsw! Wallahi idan ya sake sai
nayi masa baki, wai har ni zai kalli idona yace
mini sai Allah ya tambaye ni duk abinda muke
aikatawa, wai don kina zance a mota, wai 'yan
unguwa sai zarginki sukeyi gashi kin daina talla
ma a ina kike samun kudi yanzu? Nace a gidan
ubansa. Sai fa da nayi masa wuta-wuta sannan
na samu ya fice daga gidan nan, kuma nayi
masa barazanar duk randa ya kuma shiga
shirginki sai na tsine masa, idan muka biye ta
tashi zamu rayu ne? Da yanzu mun mutu,
Mtsw!" Ta kuma jan tsaki. Abu ta hasala ta
murguda baki gami da tsiro shi gaba tace, "Ki
fita harkarsa kawai Sala, na lura talauci ne ke
damunsa, kuma wallahi yayi sa'a shi yayana ne
da wallahi 'yan sanda zan dauko masa." Sala
tace, "Ai bake ba ni kaina ba don gudun abin
kunya ba da saka ido irin na tsinannun mutanen
unguwar nan, da wallahi sai na hadashi da 'yan
sandan sun lallasa mini shi." Sallamar da wani
yaro yayi ce ta katse musu hirar tasu tamkar
wasu kawaye, su kuwa sauran kannan nata duk
sun bazama tallar gyada a can kofar gida. "Kai!!
Meye ka ishemu da sallama?" Sala ta katse shi
cike da haushin katse musu hirarsu da yayi ba
tare da ta kai aya ba don ko amsa sallamar ma
bata yi ba. "A'a daman wani ne a mota ke
sallama da Abu..."
"Au! Yi hakuri na hauka da fada, kace tana zuwa
dan albarka, ka ji?" (HMMM) Yaron ya fice yana
fadin to. Ta dubi Abu da ta mike ta nufi daki
don sanya kaya tana dariya tace, "Yau dai naga
kwalliyar nan ta daban ce, kiyi sauri kada ki
bata masa lokaci." Ita dai bata ce komai ba ta
shirya ta fito sai kamshi take yi, kai tsaye ta fice
ta nufi gurin da Mustafa yake, yana hango ta ya
bude mata gaban motarsa wato kusa dashi sai
wani malalacin murmushi yake mata na
tsananin yaudara irin na gogaggun samari, ita
kuwa sokuwar sai wani kara zobara baki takeyi
tana wani yauki har ta shiga ciki ta zauna tana

wani fari kamar 'yar tsana. Ya shaki kamshinta
gami da lumshe ido, cikin mayaudariyar
muryarsa yace, "Kai Zainabu, kin yi kyau kamar
wata sarauniya." Tayi dariya cike da jin dadi
tace, "Haka ma Sala tace wai nayi kyau sosai."
Yayi murmushin jin wautarta, Ya riga ya gama
karantar halin Abu da Sala, don haka ya san ba
zai sha wahala gurin samun hadin kan Abu ba,
don haka ya mika hannuwansa ya kamo hannun
Abu yana wasa dashi yace, "Kai yatsunki akwai
ban sha'awa, dube su zara-zara. Dadi ya kuma
cika ta na yabon da yake mata tace, "Haka kowa
ke cewa, wai yatsuna da na hannu da na kafa
suna da kyau kamar ba nawa ba." Yayi dariya
yace, "Gaskiya haka ne, amman kyanki ai yaci
suma suyi kyau." Cikin dabara ya jata jikinsa
yana fadin, "Ya dace dai yau na shaki kamshin
nan naki da kullum ke ruda ni." Ga mamakinsa
sai yaga Abu ta saki jikinta har ma tana kokarin
taya shi, abin ya bashi mamaki don yayi zaton
sai yasha wuya zai sami kanta, sai gashi ya
same ta a ruwan sanyi, amman sai ya danne ya
dinga aiwatar da mugun nufinsa da zuciyarsa ke
ingiza shi. (Allah ya kiyashe mu da aikin assha.
amin).
Da ya tabbatar ba zai sami wata matsala da Abu
ba, sai ya lankwashe murya yace, "Abu ko zaki
rakani wata 'yar unguwa?, daga can kin ga sai
mu wuce nayo miki siyayya ko?" Tace "Babu
damuwa muje kawai." Ya dubeta ta dan hasken
dake cikin motar na farin wata da ya shigo yace,
"Kina ganin babu matsala idan Sala ta aiko bata
ganki ba? dan kada tayi fada." Ta tabe baki tace,
"Kada ka damu ba zata ce komai ba tunda dai
ta san siyayya zaka yi mini, kuma ta san ai
muna tare." Yaji dadin abinda tace dan haka ya
tada motar gami da karo sautin wakar dake fita
a cikin rediyonsa, muryar Bob Marley ce a
wakarsa ta One Love, duk da Abu bata jin
turanci wakar tana mata dadi musamman da
yake koda yaushe za kaji kaset din Bob Marley
Mustafa ke sanyawa, har ma ta iya bin wakar
tana girgiza kai duk da ba daidai take fadin

wasu kalmomi ba. Suna tafe a hanya suna hira
har suka isa wani hotel, kasancewar kaurin
sunan da hotel din yayi baka ganin jama'ar kirki
a cikinsa domin kada sunansu ya baci, wannan
ya kara baiwa 'yan iska damar cin karensu babu
babbaka, gurin shiru babu alamun jama'a, sai
ka shiga daga ciki zaka ga kamar tsakiyar rana
ce dan haske da tashin kida. Ya dubi Abu yana
murmushi yace, "Zainabu ya dace mu dan tsaya
a nan musha lemo mu huta, kafin na wuce yi
miki siyayyar domin har dan kunne da sarka na
gwal zan sai miki, kema ki shiga sahun manyan
mata ko?" Yana mayaudarin kallonsa yake
maganar. Tayi dariya cike da jin dadi tace "Babu
damuwa." Ya sami guri ya faka motar tasa, ya
bude ya fito sannan ya bude mata ta fito suka
jera, Abu jin kanta take yi da girma saboda ta
fito daga mota, a ganinta ta gama cinyewa.
Sanda suka isa cikin reception din hotel din sai
ta kama zare idanu cike da kauyanci, domin
tunda take bata taba ganin guri mai kyawun
wannan ba, ta saki baki galala tana kallo ga
hasken wuta ga fankoki suna juyawa ga A.C da
Tibi, ga 'yan mata nan kala-kala kowacce da
shiga ta rashin mutunci, sai taji ta raina kanta,
lallai ta yadda da Mustafa da yace zai nuna
mata rayuwar 'yanci da wayewa, gashi kuwa ta
fara gani. Sai ta kama muzurai kamar ta koma
gida ta sanyo atamfarta Wagambari da tafi
kowacce kyau da tsada, amman sai taga ai ko ta
sako ba zata yi kyawun wadannan ba, ta
shagala da kallonsu tana fadin dama itace
wannan, can kuma idan taga wata sai taji tafi
waccan tace, kai waccan zan zama, shi kuwa
yana can yana biyan kudin dakin da zai kama
musu. Ya kammala ya amshi makulli ya nufe ta,
sai yaga sam hankalinta baya tare da ita har
hannu take sanyawa tana taba duk abinda ya
burgeta, ya kama hannunta suka nufi dakin da
ya kama musu. Sanda suka shiga dakin kuwa sai
labari ya sha bamban, sai taga ai can wajen ma
ba'a sanya komai na more rayuwa kamar nan
ba, ta fada kan tumemiyar kujerar dake falo da

karfi tana fadin, "Kai bari muga za ta loma
kuwa?" Ta saka wata dariya ganin ko motsi
sosan baiyi ba, can idon ta ya hango mata wani
gilas dake dauke da ruwa da kifaye da wasu
'yan kananan bishiyoyi, ta mike da sauri ta isa
gurin, ta saki baki tana kallo da shafawa, can ta
kuma fashewa da dariya tana fadin "Wallahi
kifin da ransu kuma yawo suke kamar a teku."
Shi kam Mustafa yayi tsaye yana dubanta,
hannuwansa cikin aljihu yana dariya saboda
ganin irin kauyancin da take yi, lallai ya kuma
tabbatarwa Abu sokuwa ce mara wayo, sai dai
rashin kunyar, domin da ace tana da wayo ba
zata yi wannan kauyancin ba, ko kuma dan bata
da wasu shekaru da yawa ne? Can ya hango ta
tana kiciniyar bude wata kofa sai turawa take
iyakacin karfinta.
Ya karasa yana dariya yace "Dakin bacci ne, bari
kiga yanda ake budewa." Ya kama marikin kofar
ya murda a hankali sai gashi ta bude. Ta kuma
bude baki cike da mamakin ganin wani irin
katon gado kuma dan karami ba irin na Sala mai
rumfa ba, ta nufi gadon da gudu tayi tsalle ta
fada tana kyalkyala dariya har da rike ciki tana
kuma birgima. Can kamar wacce aka kuma
tsikara sai ta kuma mikewa da sauri saboda
hango wata kofa da tayi ta san lallai wani abin
kallon zata kuma gani, wannan karon bata sha
wahala ba ta bude domin taga yanda ya bude
waccan, ta rufe bakinta cike da tsananin
mamaki taca cewa "Na shiga Uku ni Abula,
menene wannan kuma?" A cikin kunnenta taji
yana mata rada, "Wannan bandaki ne gurin
wanka irin na 'yan gayu, idan kina son irinsa zan
gina mana." Ta juya tana dubansa da mamaki
dan bata yarda da abinda yace ba, yaya ma
za'a yi aga bandaki a cikin daki kuma ga wasu
irin abubuwa a ciki kamar daki ma? Ya daga
mata kai alamar haka ne da gaske, ta nufi gurin
kwamin wanka ta shiga sai ya sakar mata
shawa, ta firgita ta fito da gudu tana ihu,ta
kankame shi domin ta firgita, ya fashe da
dariya. Lallai Unguwarsu da manyan gidaje

amman bata taba shiga ciki taga yanda suke ba,
domin ita kam bata iya jure wulakanci ko kaka
yake, su kuwa 'ya'yan masu kudin unguwarsu
wulakanci ne dasu, sam basu kula su ko fita
zasu yi ma sai dai a mota, shi kansa Mustafa
sanda ya fara cewa yana sonta tayi mamaki
sosai, sai daya dinga yi mata kalamai masu dadi
da yaudara sannan ta yarda, har yana cewa
shifa so babu ruwansa da mai kudi da talaka
duk yana shigarsa, da haka ya samu kanta dan
wani lokacin har mamakin kanta take yi data
afka son wanda ta tsana a da can. Tasha yiwa
motocin jama'a faci domin ta tsani gudun da
sukeyi a layin suna kade kaji da akuyoyi wani
lokaci harda mutane, idan anyi magana sai su
biya dan suna da kudi, sai da takai duk kofar
gidan da aka ganta sai an koreta domin idan ta
kullawa mutum duk sanda taga mota a kofar
gidansa koda ta baki ce sai ta koma gida ta
dauka kibiya ta kitso ta sossoka a tayoyin, dan
masu gadin da sun ganta zasu bita da bulala. Ya
janye ta yana dariya saboda yanda ya ga ta
tsorata yace "Bari naje na samo mana abinci da
dan ruwan lemo." Bata ce masa komai ba illa
tafiya da tayi gurin wani abin tana tabawa. Ya
dawo dauke da wani katon faranti mai dauke da
abinci da manyan kwalabe na giya (wa iyazu
biLlahi) ya ajiye bisa tebur din dake falon kana
ya shiga ya kirawo ta, da kyar ya samu ta baro
bandakin tana cewa ya tsaya tana kallo, yace In
dai kina son kallon kullum zan dinga kawo ki."
Dadi ya cikata, da wannan dabarar ya samu ta
futo. Abinci ya mika mata mai dauke da naman
kaza zuku-zuku, ta amshe kuwa da azama ta
fara ci, shima yaja nasa farantin yana ci yana
kallon ta yana dariya ,Can ya dauko kwalbar
Shandy dinsa ya bulbula a kofi ya kafa kai ya
kyankyama ya dire kofin. Ta dubeshi da mamaki
a tsorace tace, "Kai Musty (haka take ce masa)
Giya ce fa? ba zata bugar da kai ba? Naga dan
tasha idan ya sha yayi ta maye har kwata yake
fadawa." Yayi murmushi gami da lumshe
idanuwansa kana ya bude a hankali, "Ai shi

karamar giya yake sha wato burkutu shi ya
sanya yake maye, amman wannan original ce
wato mai kyau din ce, bata sanya maye bari na
zuba miki ki sha kiji." Ta manne kafada da sauri
tana fadin "Kai bana sha tsoro nake ji ni dai."
Yace, "Haba dai tawan don Allah kisha wallahi
ba zaki bugu ba sai dai kiji karfi." Da kyar ya
samu ta sha kofi guda, can kuma sai ta wawuro
kwalbar ta kafa kai ta dinga kyankyama, ta dire
kwalbar bisa tebur din. Ya fashe da dariya gami
da tafa mata yana fadin Wonderful, wato
mamaki ta burge shi, ya zira hannu cikin
aljihunsa ya zaro tabar shedan wato wiwi) ya
kunna ta ya zuka kana ya mika mata, wannan
karon batayi gardama ba ta amshe da azama ta
zuka domin bata cikin hayyacinta, sai dai zuka
daya ta kware ta kama tari, ya tashi da sauri ya
nufe ta yana rike ta har tarin ya lafa.
Amman don ta saba maimakon ta hakura sai ta
kara zuka don abin ita sha'awa ma ya bata, don
ta dade tana sha'awar yanda ake shan taba
musamman idan taga wanda ya kware mai
fesar da hayaki ta baki ta hanci. Dadi ya kama
Musty sai ya kuma zaro wata cikin aljihunsa ya
kunna ta ya hau zuka. Ta fashe da dariya karan
tabar na tsakiyar yatsunta guda biyu shima ya
taya ta suka dinga dariyarsu da zukar tabar
shedan din har suka gama, sannan ne kuma
Abu ta soma tangadi tana zage-zage da yarfe
hannuwa. "Wallahi karya ne! Babu wani sauran
shege da zai raina mana hankali wallahi! Ha-ha-
ha." Ta fashe da dariya. Ya isa inda take da
azama yana fadin "Kwantar da hankalinki
yarinya." Ta fada jikinsa shabar tamkar kayan
wanki, ai kuwa ya sami yanda yake so don haka
ya shiga aiwatar da mugun nufin da zuciyarsa
ke kintsa masa, da fari bai samu matsala ba sai
da abu yayi nisa data fara jin zafi sannan ta
nemi kwace kanta, amman da yake a buge take
hakan bai samu ba har sai da ya cimma burinsa
a kanta (Wa'iyazu billahi). Duk irin iskancin Abu
da gantalinta namiji bai taba aike mata kai tsaye
ba don tana tsoro da gudun kar aji mata ciwo,

ko su Dan Oga da dan tasha da suke siyan
abincinta, basu taba samun hadin kanta haka
kai tsaye ba sai Musty, yau ya samu daga sama
don haka shine mutum na farko da ya fara
sanin Abu diya mace, abunda ba zata taba
mantawa ba a kundin tarihin rayuwarta. A nan
bacci ya dauke su don duk cikin su babu wanda
ke cikin hayyacinsa. Basu ankara ba sai da gari
ya waye tangararau, sannan suka farka a firgice
Abu ta saki kuka da ta tuno abinda ya faru a
daren jiya, shi kuwa Musty kwantar da kansa
yayi ya dinga bata hakuri harda guntun
hawayensa, karshe dai yayi mata alkawarin kaya
da zai sai mata kala-kala har ya samu ya shawo
kanta don ya lura muguwar kwadayayyiya ce, ya
samu ya lallaba ta ya hada mata ruwan dumi
cikin bahon da tayi kauyanci daran jiya ta shige
ciki. Shigar ta bandaki da kuma tuno irin
alkawarin kayan da yace zai siyo mata ne ya
faranta ranta har ma ta daina ganin aibun
abinda suka yi din, don haka da kwarin
gwiwarta ta fito shima ya shiga don ya shirya.
Sanda ta kammala shiryawa ne gabanta kuma
ya soma dafuwa tana tunanin me zata ce da
Sala yanzu don ta Babanta sam bata jinsa,
domin sam ba zai lura bata gidan ba, domin bai
shigowa gidan sai dare ya raba, haka nan daga
gurin Sallar Asuba yake wucewa majalisarsu,
idan ka ganshi a gida da rana to lallai Alhazan
da suke wa a dawo lafiya sun kawo musu zakka
zai zo yaci abincin rana a kudinsa, yakan ce sai
ya ci guminsa wai, sai kuma jarababban yayanta
da take tsoro kada ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login