Showing 39001 words to 42000 words out of 49932 words
Chapter 14 - Idan Zuciya Ta Gyaru Complete by Fauziyya D Suleiman .pdf
dina, bayan
sakamako ya fito babu lafi na samu admission a
FCE, domin a wancan lokacin ba'a tsaurarawa
gurin makin jarabawa, don haka da 2 credits 2
passes na sami admission. A wannan lokacin ne
na kuma wayewa na san lallai da kai na a duhu
yake, duk da dai ba wani karatun ne a gabana
ba, na hadu da malamai 'yan ban gishiri na
baka manda da taimakonsu na kammala. Dai-
dai lokacin da na kammala karatuna na hadu da
wani dattijo ma'abocin son holewa DPM ne a
wata karamar hukuma. don haka tunda ya
kyalla idon sa a kaina ya makale mini, shine dai
ya kawo min takardar fara aiki (upper) har gida
tun sakamako na bai fito ba, don haka na fara
aiki na, amman fa a kanyi wata banje Ofis ba
domin dai ina da manya a sama, sun ajiye ni a
cikin Sakateriya bangaren (Accountant), mai raba
kudi, don haka Salary bana wasa nake samu ba,
duk da ba abinda na karanta kenan ba kasan
Nigeria jaga-jaga inji wani mawaki, don wallahi
wadanda muka yi karatu dasu da dama basu
sami aiki ba har yau, kuma yawancinsu sune
masu kokarin sun fito da first class amman da
yake basu da wani a sama suna zaune, kai
Nigeria sai a slow wallahi." Ya yi dariya yana
fadin, "Wallahi ke din nan 'yar buyagi ce, ni
kaina wani lokacin tsoro kike bani, barin ma
yanzu, don haka ne ma na dinga jin tsoron
dawowa don kada kiyi mini buyagin naki." Ta yi
dariya gami da kai masa bugu na wasa, suka
kama dariya gaba dayan su, sannan ya gyara
zama yana kuma shinshinarta kamar wata diyar
mage sannan ya fara bata labari kamar
haka.Kamar yanda kika sani daran da yayanki
Sadiku ya yi mini wannan wulakancin na tafine
raina a tsananin bace, domin tun da nake ba'a
taba mini wulakanci kwatankwacin wannan ba,
don haka na kudirta a raina na hakura dake
tunda daman yace duk randa ya kuma ganina a
kofar gidan ku sai ya sanya an jefe ni, ni kuwa
bana son iyayena su san halin da nake ciki sam.
Sai da na koma gida ne ma sannan na tuna da
abinda ya kaini gurin ki, don muyi sallama ne ni
zan koma makaranta duk da na san ban taba
gaya miki hutu nazo ba. Sai da tafiyar ta kama
gadan-gadan sannan na ji wani irin masifaffan
son ki yana bijiro mini da kewar ki, amman na
dake don ina ganin da zarar na bar garin duk
zan daina ji, don haka na bar Kano da zummar
na bar Zainabu Abu na nufi birnin Califonia. Sai
dai tunda na isa garin na jini kamar wani mara
lafiya, surarki da kamar ki ta dinga bijiro mini
don haka na yi zaton ko kewar ki ce, don haka
na fara mu'amala da mata kala-kala masu kyau
masu ilimi har ma da masu dukiya, amman sun
gaza gamsar dani kamar 'yar kwaila Zainabu,
amman na dinga yaudarar kai na da lallai sai na
manta Zainabu, duk macen da na kalla sai naji
na raina ta burin yana ga Zainabu, na ki na
dawo hutu don ina ganin idan na dage zan
manta dake din, sai dai iyayena suzo mini hutun
can, har na kammala karatuna kina nan a raina
na kuma baiwa kai na wani lokacin na mantawa
da ke, don haka na fara aiki a can duk da ba
haka iyayena suka so ba, sai dai shi Mahaifina
mutum ne mai saukin kai da baiwa mutum
damar sa inda yaga babu cutarwa a kanta. Dare
daya na ji duk iyakacin dauriyata ta kare,
musamman da nake ta fama da yawan ciwon
kai da aka auna ni akace na rage sanya damuwa
a raina, na yadda muddin na cigaba da zama a
can ciwon zuciya yana gan da kamani saboda
yawan tunani, na yanke shawarar zan dawo
Nigeria na neme ki amman a wannan karon
auranki zan yi, don na gane kece kadai nake so
a rayuwa ta, na kuma yi kokarin jifan tsuntsu
biyu da dutse daya don daman iyaye na sun
damu da lallai na dawo nayi aure.Sai dai idan
na tuno ki sai naga kamar na rasa ki ko kin yi
aure, da zarar na tuno hakan sai naji duk
hankalina ya tashi, na yawaita sallah da rokon
Allah ya sanya baki yi aure ba, da wannan
shawarar na dawo gidan Nigeria, da zummar ko
a yaya na sameki zan aure ki, don ban yi zaton
Abun da na sani zata koma mace mai girma da
daraja da aji kamar haka ba, don dai a yanzu so
ne tsagwaransa a raina ba wata sha'awa ba. Sai
dai na sha mamaki a yanda na ganki a yanzu,
nasan tun a can baya kina da kyau don yana
daya daga cikin abunda ya sanya nayi mu'amala
dake, ga tsabta koda yaushe zaki wuce ta gaba
na sai na ganki tsaf dake, takalminki kamar ba
kya sakawa.Don haka Zainabu ba da wasa na
dawo ba da zummar na aure ki na dawo, don
haka bana son a dauki wani lokaci mai tsaho,
sannan dole ki daina kula 'yan iskan samarin
nan naki don ina da kishi mai tsanani, shi ya
sanya a wancan lokacin ma nayi kokarin ganin
baki kula kowa ba, don haka Zainabu gani
gabanki da kokon barata ina fata zaki amince da
bukata ta." Tayi dariya cike da jin dadi ta ce,
"Lallai Mustafa ka debo ruwan dafa kanka, ta
yaya zaka ce kai kadai zan dinga kulawa bayan
ba mijina kake ba? Ai hakan ba mai yiwuwa
bane ba." Ya mike zaune yana mata wani duba
idonsa fal da masifa ya ce, "Wallahi kina so ne
na fara rotse a kofar gidanku, don duk dan
iskan da yayi mini rainin wayo a kanki zan yi
maganinsa, da can sun yi yanda suke so, yanzu
kuwa mai guri ya zo kowa sai ya matsa ya bashi
gurin sa, duk mai neman kansa da arziki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta makalkale shi tana dariya ganin yanda yake
masifa kamar zai rufe ta da duka, suka kama
dariya don tana masa irin salon ta da take siye
masa zuciyarsa. Bugun kofar da akeyi ne ya
fargar da su, Zainabu ta mike da sauri tana
fadin, "Ina zaton shegiyar nan ce ta dawo." Ta
dubi agogo sha daya da minti uku, sannan ta
nufi kofar da sauri tana kokarin budewa. Asma
ta shigo da gudu tana ihu da dariya tana fadin,
"Shegiyar ashe akwai mai maganin iskancinki,
gaskiya Mustafa ka ci a baka na daya, ya ci a
sara maka wallahi, don kayi mana maganin mai
shegen taurin kan nan." Mustafa ya mike tsaye
yana dariya sannan ya ce, "Daman ke muke jira
mu wuce." Ya mika mata makullin sannan ya
dubi Zainabu ya ce, "Ke madam sai ki shirya na
sauke ki a gida ko, don na san idan na tafi
wannan dan iskan ne zai zo ya dauke ki." Suka
fashe da dariya ita da Asma har da tafawa, yayi
murmushi yana fadin, "Lallai kwa yi mini dariya
don kun san kun kama wuya na, ni kam na
wuce mota kya tadda ni a can." Har ya kusa
kaiwa kofa sannan ya tsaya yana fadin, "Ahaf!
Hajiya Asma na gode kuwa zan gan ki." Tayi
dariya tana fadin, "A'a don ni kada ka damu
babu damuwa ai duk yiwa kai ne, don bani da
kamar Zainabu duk Kano." Yayi murmushi ya
ce, "Na dai gode din sai mun sake haduwa."
Sannan ya fice. Asma ta kalle ta gami da
fashewa da dariya su dukan sannan suka tafa
Asma ta ce, "Wallahi kawata kin iya iskanci, ki
dubi yanda kika juyar da zuciyar dan talikin nan
a lokaci kankani don Allah, don Allah yaushe ne
zaki sanar da ni sirrin nan ne?" Zainabu ta tafi
tana fadin, "Sirri ne abin." Asma ta bita da gudu
tana fadin, "Haba kawar, ki taimaka mini don
Allah." Zainabun tayi dariya sannan ta ce, "Ki
bari sai mun hadu kinga yanzu lokaci ya kure,
don zumana yana jirana a mota." Suka kuma
fashewa da dariya, sannan Asma tace, "Lallai
Mustafa ya ciri tuta don ban taba jin kin ambaci
wani namiji da ko sunan da iyayansa suke gaya
masa ba, daga shashasha sai dan wahala ko dan
akuyan can, amman Mustafa yaci Zuma gaba
daya ma." Zainabu ta zame da sauri ta falla da
gudu tana fadin, "Malama ki kyale ni haka nan,
kina bata mini lokaci." Sanda suka isa gida duk
'yan biki sun gama watsewa sai dai sauran
kwadayayyu, sun jima a mota suna sallama
sannan ta fita tana takawa da tafiyarta ta
daukar hankalin 'yan maza, sai da yaga shigarta
gida sannan ya ja motar tasa cike da tsananin
sonta, da wani nishadi da farin ciki.
Tana shiga Sala ta kama yi mata sannu da
zuwa, ta sami kujera 'yar tsugunne ta zauna
don cike take da nishadi. Sala din ta kama
murmushu don ganin diyar tata a cikin farin ciki
sannan ta ce, "Hala yau diyar tawa ta hadu da
mai barin dala ne naga bakin naki ya ki
rufuwa." Ta yi 'yar dariya sannan ta ce, "Sala
kin san abun mamakin da ya faru kuwa tun
daran jiya?" Bata bari ta bata amsa ba ta dora
da cewar "Mustafa ya dawo." Da mamaki Sala
din tace, "Mustafa kuma? Waye me wannan
sunan, ba dan dan banzan yaron nan da ya
cuce mu shekarun baya ba can?." Zainabu ta
bata rai matuka kamar zata yi kuka, ganin haka
ya sanya Sala din ta tsuke bakin ta, don ta yi
zaton zata yiwa Zainabun gwaninta ne, don ta
san irin alwashin da taci akan Mustafa. Ita kam
mikewa tayi tana fadin "Ashe daukar hakkinsa
muka yi daman, don ba laifin sa ba ne." Ta sha
ruwa a randa sannan ta dawo ta gaya mata duk
yanda suka yi da Mustafan. Sala din tayi dan
murmushi tana fadin, "A'a lallai bashi da laifi to
mun yafe masa." Zainabu ta ji dadin abunda
Sala din ta fadi, don haka ta mike tana dariya
sannan ta ajiye mata damin 'yan dari dari na
dubu ashirin tace, "Sala gashi nan kya kashe."
Sala din ta dauka tana dariya sannan ta ce, "Ke
Zainabu ba kya gajiya? Na ga fa kin sha
kacaniyar biki kwanan nan." Zainabu tayi dariya
tace, "Ai Mustafan ne ya bada ya ce a baki kya
sha ruwa kafin yazo bada hakuri da kansa." Sala
ta fashe da wata wawiyar dariya sannan ta ce,
"Kayya ki gaya masa ya kwantar da hankalin sa
komai ai ya wuce gashi kin ce daman ba laifinsa
ba ne." Ita dai Zainabu daki ta shige domin tayi
baccin gajiyar kwanakin da bata yi ba can baya,
kafin yamma tayi su hadu da zuman nata
************
Cikin kwanaki kalilan soyayya da shakuwa ta
kuma shiga tsakanin su, duk da suna rikici duk
lokacin da Mustafa ya ga Zainabu da wasu
Musamman Alhaji.... Dan haka duk inda tasan
zata gamu da samarin ta kan guje masa don
bata son ace kullum suna samun sabani da
Mustafa dan yana da matukar kishi, su kuma
sun gaza hakuri dan duk kusan namijin da ya
fara mu'amala da Zainabu bai iya daina wa dan
ta fiye fitina da yawa, sai dai idan Allah ne ya
kwato shi daga hannunta. Shi kam Mustafa
kullum hankalin sa a tashe yake dan bai kaunar
ya ga Zainabu da wani, dan haka nema suka
yanke shawarar yin aure a wannan lokacin. Shi
kam yana shakkar tinkarar Momin sa da
maganar auren nasa don ya san ta bata san
wargi sam ita, ga shi daman kullum tana masa
maganar ya zabo mace cikin 'yan matan gidan
ko kuma ya duba cikin 'yan uwa masu tarbiyya
dan bata son yayi zaben tumin dare, sai dai shi
a iyakacin ganinsa daga 'yan matan dake cikin
danginsu har na waje bai ga wacce tayi masa
kamar Zainabunsa ba. Yau ya tadda Momin
nasa a karamin falo, 'yan matan ta suna
karamin falo suna kallo sai musu a keyi tsakanin
'yan matan, don gidan nasu bai rabo da 'yan
mata na 'yan uwa dan su basu da yawa su biyu
ne kacal, gashi Momin su tana da son jama'a
dan haka koda yaushe gidan a cike yake banda
masu zama dindindin, banda kuma wadanda
aka aurar, dan haka tunda ya ga take-taken
Momin na su na son ta hadashi da wata a
cikinsu shi ya sanya ba ko da yaushe yake sakar
musu fuska ba. Ya shiga falon da sallama, ita
kadai ce don ya baro Alhajinsu a falo da baki, ya
isa gaban ta ya gaishe ta, sannan ya koma
babbar kujera ya zauna, ya dubi tibin inda yaga
hankalinta ya karkata. Yakin Falastinawa ne dai
da Isra'ilawa wadanda kanwa uwar gami
America ke daurewa gindi, ana nunowa a tashar
C.N.N. "Kai wadannan mutanen wallahi
azzalumai ne, ka dubi yanda suke kashe farar
hula da basu ji ba basu gani ba, sannan su yi
farofagandar basa taba farar hula, Allah dai ya
bi musu hakkinsu kuma ya nuna musu karshen
su, Amin." Hajiya Kubra ke fada da bacin rai.
Mustafa ya ce, "Haka ne Momi, sai dai idan kika
duba daman can zaki ga abun nasu bawai suna
yi bane don wani abu sai don su yaki addinin
musulunci kawai, yanzu fa idan kika shiga
kasashen turawa da gemu sai kaga an mai da
kai wani abin tsoro saboda sunyi farofagandar
batawa musulmi suna a idon duniya, dan ma
yanzu Allah yana nuna musu ishara mutanan su
turawa sai musulunta suke, musamman
matansu kamar su Kristian Barkeu da 'yar uwar
tsohon shugaban kasar Birtaniya Tony Blair,
Laurent Bothh wacce ma'aikaciyar jarida ce, da
sauransu, shine fa muke dan samun sassauci a
gurinsu, abun nasu dai sai addu'a." Ta amsa da
"Amin, ina wai ka shiga ne?, tun da safe nake
saka rai da shigowarka amman shiru." Gabansa
ya fadi, don yanzu sam bai zama a gida kullum
suna makale da Zainabunsa, amman sai ya
dake ya ce, "Momi kin san ina fafutukar fara
aikin tun da sun bani (offer), takardar daukar
aiki, shi ya sanya yanzu bana zama." Ta ce,
"Lallai kam haka ne, Allah dai ya taimaka ya
sanya a fara a sa'a." Ya ce, "Amin." Sannan ya
kama inda-inda don ya rasa ta yanda zai gaya
mata. Hajiya Kubra ta dube shi tana dariya tace,
"Babana duk yanda aka yi da magana a bakin
nan naka." Da yake sunan Baban ta ne da shi.
Ya yi murmushi yana sosa keya ya ce, "Momi
sirika na yi miki shine nake kunyar sanar da
ke."tayi dan murmushi dan ba hakan taso ba
taso ace anyi 'yar gida, amman sai ta danne
dan tana son yayi auren, dan haka tace, "Lallai
kam kace yau zanyi kwanan farin ciki, a ina ka
samo matar taka ko a can American ne?" Yayi
dariya ya ce, "A'a Momi a can dai unguwar da
muka taso take, can kasan layinmu na da,
sunan ta Zainabu." Ta ce, "Lallai kam, Allah ya
tabbatar mana. Waye kuma Babanta, a wane
gida take ne ma?" Da sauri ya ce, "Sunansa
Malam Abubakar." Tace, ai shike nan bari Alhaji
ya shigo sai a sanar da shi, amman dani na so
ace cikin 'yan uwanka da suke gidan nan ka
zaba, amman tunda Allah ya kaddara matar
taka a waje take ba zamu ja da ikon Allah ba,
sai dai muyi addu'a Allah ya tabbatar mana da
alkhairi kawai. Ya ji dadin abunda ta ce, yayi
mamakin kuma saurin shawo kanta da ya yi,
duk da saurin daukar zafin ta. Daga nan suka
cigaba da hirar su a cikin hirar nema take cewa
tana fatan zainabun tasa mai hankali ce da
nutsuwa. Ya ce, "Momi ko ke kika ga Zainabu sai
kinyi sha'awarta, ta kammala diplomarta yanzu
haka tana aiki ne." Tace, "To ai shike nan, na
san dai sai Baban ku ya sanya anyi masa bincike
don kada ayi zaban tumun dare." Kirjinsa ya
bada ras-ras, amman dai ya dake yace, "Na san
ma babu wani aibu da zai tadda ga Zainabu in
dai ya sanya mutanan kirki a binciken ba
munafukai ba." Tun daga sannan ya ji hirar ta
fita daga ransa gaba daya, don bai san irin
abinda za'a ce akan Zainabunsa ba, shi kam yaji
ya gani dan haka koma me zai faru sai dai ya
faru amman shi dai da ikon Allah sai ya aure ta.
Da haka yabar dakin mahaifiyar tasa ya nufi na
shi, amman yana cike da tunanin abunda zai
biyo baya idan suka san wacece Zainabu.
Kwanaki biyu shiru babu wanda yace masa ko
kala akan maganar, shi kam ya damu kwarai ya
ji anyi masa zancan, dan Baban sa ma da suka
yi maganar da Hajiya Kubran abinda ta fadi ya
maimaita, cewar zai sanya ayi masa bincike
sosai. Ya sami wani tsohon abokinsa acan
unguwar da suka taso ya ce don Allah ya bashi
amana ya binciko masa labarin wata yarinya
Zainabu diyar Malam Abubakar kamar yanda
aka ce masa, sai dai abokin nasa ya dan sami
matsala da farko dan duk wanda yace wa sun
san Zainabu diyar Malam Abubakar sai suce
gaskiya basu san taba, mutum hudu ya tambaya
amman duk ba'a dace ba. Sai da ya isa
majalisar da yake zama ya fara kawo maganar
neman Zainabu da yake yi, sai wani cikin
abokan hirar tashi yace, "Ko dai Zainabu diyar
Baba Abbakar mutumin Sudan din nan ake nufi,
in dai itace kuwa bai yi mata ba, domin dai
kowa yasan karuwar gida ce, duk da babu kyau
suka akan maganar aure amman tunda dai
amana ya baka sai ka sanar da shi gaskiya in
dai ita ce din, da dai kanwarta da aka yiwa aure
kwanaki ce ma da sauki dan ba halinsu daya
ba." Nan suka hau sanar dashi irin halinta dan
gaskiya shi ma'aikacine bai fiye zama ba sai
karshen sati kuma