Showing 1 words to 3000 words out of 30696 words
Chapter 1 - GOGA SHA FAMA Book by Mansur Usman Sufi .pdf
GOGA SHA FAMA 1
Cigaban
SARKIN SADAUKAI
Rubuta Labari
MANSUR USMAN SUFI
08137237071
BABI NA ƊAYA
Al'amarin su sarki uslaim kuwa lokacin da suka kammala fafata yaƙi da wadannan ayarin
gwaggwan birrai,
Sai sarki uslaim yayi umarni aka kafa tantuna domin ya da zango, nan fa kuyangi suka shiga
aikin dafa abinci domin yin kalaci,
Sarki uslaim ya shiga izuwa nasa tantin domin ya ɗan samu nutsuwa,
A lokacin boka ƙarzum ya kebance ana sa tantin domin shiga cikin halarar tsafin sa domin
gudanar da bincike na musamman,
Lokacin da ya baje alƙalumman sihirin yafara gudanar da binciken,
Abinda yafaru tsakanin sarauniya Nuwairat da boka Jadwar gami da su saurayi Hizmal ne
yafara bayyana a madubin tsafin,
Tun daga lokacin da waɗannan miyagun halittun ke biye da wannan kyakkyawar budurwa, har
izuwa lokacin da su Hizmal ɗin suka samu nasarar ceton rayuwar ta,
Sa'adda boka Jadwar yaga wannan al'amari sai kawai ya taƙarƙare ya kwarara wawan ihu
wanda ya firgita duk wata halitta dake filin sansanin kuma ya yi sanadiyar farkawar sarki uslaim
daga gyangyaɗin daya ɗauke sa,ya mike tsaye zumbur daga kan gadon sa,
Ya zare takobin sa ya ruga izuwa waje bisa tunanin cewa koda dakarun sumame ne suka kawo
farmaki
Ai kuwa koda fitar sa ya ruga izuwa kofar tantin da yaga dakaru na yin tururuwar shig,
Da isar sa izuwa wajen ya tusa kai izuwa cikin tantin
Nan take yayi arba da boka Jadwar zaune a bisa buzun tsafi fuskar sa a murtuke babu annuri,
Sarki uslaim ya dube sa cikin fushi yace yakai ƙarzum shin ina dalilin wannan kururuwa taka,
Koda jin wannan tambaya sai boka ƙarzum ya dubi Sarki uslaim cikin ladabi yace "Ka gafarce ni
ya shugaba na kayi sani cewa bakomai bane ya sanya wannan ihu ba sai bisa Abin da na gani
a cikin madubin tsafi na,
Abinda na gani ɗin kuwa shine abinda muka fito farauta wato yaro Humair makaho sun samu
nasarar ceton rayuwar wata jaruma da ake kira da suna Nihla,
Ya shugaba na kayi sani cewa a halin yanzu bincike ya tabbatar dacewa wannan budurwa itace
mace ta farko da SARKIN SADAUKAI Hibairu zai fara gani a rayuwar sa,
Kuma tabbas da zarar yagan ta zai kamu da matukar soyayyar ta
Haƙiƙa jaruma Nihla ita ce zata zamo tana sarrafa Hibairu tamkar yadda ake sarrafa masa akan
kasko saboda tasirin soyayyar ta a zuciyar sa
Wani abu daya kara dugunzuma hankali na shine al'ajanin dake ɗauke da su saurayi Hizmal
shine ke ɗauke da taswirar fadar Sarkin bokaye,
Babu wani mahaluki da ya isa yaje fadar Sarkin bokaye face ya mallaki wannan taswira,
Kaga kenan koda ace mun samu nasarar saduwa da Hibairu kuma ya amince zai ceto gimbiya
zarifa to fa tilas ne yazo muna ɗauke da taswirar fadar Sarkin bokaye,
Sa'adda sarki uslaim yaji wannan batu daga bakin boka ƙarzum sai hankalinsa ya dugunzuma
ainun fiye da ko yaushe,
Ya dubi ƙarzum cikin alamun tsananin damuwa yace yanzu mene ne abin yi ya masanin ilimin
tsafi,
Boka ƙarzum yace "Mafita ɗaya ce tabbas dole mu yi kokari mu riski su saurayi Hizmal,
Domin a halin yanzu kwanaki ƙadan ne suka rage su isa dajin Baitul-shamshan,
Kuma yanzu haka sarauniyar kyawawan duniya Nuwairat tare da boka Jadwar na biye da su,
Baya ga su ɗin ma akwai sarki shazwan tare da tawagar matsafan sun bazama farautar yaro
Humair tare wata hatsabibiyar jaruma mai Hushriba
Wacce takasance yar uwa ga jaruma Husnaila da ke tare da saurayi Hizmal domin tserar da
yaro Humair makaho
Tabbas masu iya magana na cewa A bari ya huce shine ke kawo rabon Wani
Kuma tabbas da zafi zafi akan daki ƙarfe domin a sarrafa shi yadda ake buƙata,
Tabbas wanda ya daɗe zai ga daɗau,
Sa'adda boka ƙarzum yazo dai dai nan zancen sa sai sarki uslaim yace "Haƙiƙa zancen ka
dutse ne ya dodon bokaye,
Yanzu dazarar mun yi kalaci za'a cigaba da tafiya ba zamu yada zango ba,
Koda gama faɗin hakan sai sarki uslaim ya juya ya fice da ga masaukin boka ƙarzum,
Wannan shi ne abinda ya faru da sarki uslaim da tawagar sa a lokacin da suka kammala artabu
da gwaggwan birrai,
A ranar da tafiya dajin Baitul-shamshan tazo tun sa'adda alfijir ya keto SARAUNIYA
ABIDATUL-AULIYA ta kammala shiri tsaf
Ta zauna tana jiran matsafi shubairu, tsawon daƙiƙa hamsin tana zaune a cikin wannan hali ne
kwatsam bazato babu tsammani sai matsafi shubairu ya bayyana a gare ta a cikin siffar wannan
kyakkyawan tsuntsun da bayyanar sa sai ya rikiɗa izuwa ainahin siffar sa,
Sa.adda Abidatul-auliya tayi arba dashi sai ta miƙe tsaye cikin matukar farin ciki taje ta tare sa
fuskar ta cike da annuri,
Matsafi shubairu ya dube ta cikin wani murmushi mai ɗimauta zuciyar duk wata ya mace mai
hankali ya buɗi baki cikin tattausar murya yace"Barka da wannan lokaci ya sarauniyar
kyawawan duniya Abidatul-auliya bintu shafwaz,
Abidatul-auliya fuska cike da annuri tace cikin zazzakar murya tace "Barka da zuwa JARUMIN
JARUMAI kuma sadaukin mazaje,
Tun tuni na kammala shirin komai kai kaɗai nake jira domin gudanar da gagarumar tafiyar mu ta
zuwa dajin Baitul-shamshan domin saduwa da jarumi Hibairu SARKIN SADAUKAI ko zamu
samu nasarar cika burin mu na mallakar tsumin tsafi dake fadar Sarkin bokaye domin warkar da
lalurar kuturtar tsagin jiki da ta same mu,
Dajin wannan batu daga bakin Abidatul-auliya sai matsafi shubairu yace"Ai bakomai ne yasanya
nayi jinkirin bayyana a gare ki ba sai domin a lokacin da kika fito ba lokacin sa'a a tafiya ba ne,
Bisa hakan ya sanya na jinkirin ta amma yanzu batare da bata lokaci ba zamu fara wannan
tafiya,
Koda gama faɗin hakan sai matsafi shubairu ya buɗe bakin sa ya karanta wadansu dalasiman
tsafi yake wani Dankareran tsuntsun tsafi ya bayyana a wajen,
Shi dai tsuntsun tsafin yakasance yana kama da mikiya sai dai kan sa irin na batoyi ne,
Koda bayyanar tsuntsun sai matsafi shubairu yayi wa sarauniya Abidatul-auliya nuni da ta hau
bisa tsuntsun,
Batare da bata lokaci ba ta hau ta zauna, Shubairu yayi koyi da ita,
Kawai sai tsuntsun tsafin ya kaɗa fuka -fukan sa ya tashi izuwa sararin samaniya ya na mai
keta gajimare cikin matsanancin gudu tamkar giftawar tauraruwa mai wutsiya,
Wannan shi ne abinda ya faru da sarauniya Abidatul-auliya ta birnin Tehran tare da matsafi
shubairu daya bayyana a agare ta da siffar kyakkyawan tsuntsu.
Lokacin da sarauniya Nuwairat da boka Jadwar suka bi sahun aljani Marhutul-Azab dake ɗauke
da su yaro Humair makaho,
Sai suka wanzu suna tsala gudu a cikin gajimare bisa kan Dardumar sihiri
Tafiyar Sa'a biyu da daƙiƙa hamsin kacal suka yi su na wannan gudu,
Su na cikin wannan tafiya ne sarauniya Nuwairat ta dubi boka Jadwar tayi gyaran murya tace
"yakai Jadwar shin nan da wani lokaci ne za mu iya cimma su saurayi Hizmal?
Da jin wannan tambaya sai boka Jadwar yayi shiru gami da runtse idanun sa,
Daga can sai ya cire kai ya dubi sarauniya Nuwairat yayi gyaran murya yace"ya shugaba ta
haƙiƙa cimmu su a wannan lokaci abu ne mai matukar wahalar gaske domin kuwa aljanin dake
ɗauke dasu shine aljani mafi tsananin karfin gudu a cikin jinsin aljanu,
Sai dai duk da hakan akwai yiwuwar zamu iya cimmu su a lokacin da zasu yada zango,
Koda jin wannan batu daga bakin boka Jadwar sai sarauniya Nuwairat ta cika da matukar farin
ciki
Daga wannan furuci ne kowa yayi shiru babu wanda yakara cewa kala,
Wannan shi ne abinda ya faru da sarauniya Nuwairat da boka Jadwar akan hanyar su ta
farautar budurwa Nihla wanda ke tare dasu yaro Humair makaho,
---
Kamar yadda gimbiya Hushriba ta tsara haka al'amarin yaksance wato tun da duku-dukun
safiya fadar sarki shazwan ta cika ta batse da al'umma maza da mata yara da manya suka yi
cincirindo babu masaka tsinke,
Duk inda Mutum ya kalla babu abin da zai gani face kawunan bil'adama rututu,
Tamkar dandazon kiyasai, tsawon daƙiƙa Ɗari biyu da ɗoriya ana jiran fitowar sarki shazwan
tare jama'ar sa,
Ana cikin wannan hali ne kwatsam sai aka jiyo bugun tambura da bushin algaita,
Sai aka hango sarki shazwan tare da bakuwar jaruma Hushriba da tawagar bokaye,
Nan take fadar ta rude da shewa da jinjina kuma kowa ya mike tsaye daga wajen zaman su
domin girmama ga sarki,
Sai da sarki tawagar sa suka zauna abisa kujerun su,
Bayan yan majalissa sun kammala kwasar gaisuwa,
Sai sarki shazwan ya mike tsaye daga kan karagar mulki ya fuskanci jama'a kuma fadar tayi tsit
tamkar mutuwa ta kawo ziyara
Sannan daga bisani ya buɗi baki cikin kakkausar murya yace"Da farko ina yiwa dukkan
waɗanda suka hallara a wannan fada mai albarka barka da zuwa
Bayan haka kuma ina taya al'ummar kasa ta alhinin abinda yafaru damu na ibtila'in GOBARAR
DAJI,
Yaku jama'a ta kuyi sani cewa ina mai farin cikin sanar ɗaku cewa a yau ne zanyi gagarumar
tafiya domin samo maganin dazai kare wannan birni namu daga sharrin bayyanar SARKIN
SADAUKAI,
Sannan ina muku albishir dacewa bakuwar jaruma Hushriba zata baku wani muhimmin sirrin
tsafi dazai kare ku daga sharrin GOBARAR DAJI har izuwa lokacin da zamu dawo daga abin da
suka fita ne ma
Sa'adda sarki shazwan yazo nan a jawabin sai fadar ta sake rudewa da shewa a karo na biyu
kuma jama'a suka cika da matukar farin ciki maral misaltuwa.
Batare da bata lokaci sarki shazwan ya ɗora waziri Rufyan a matsayin halifan sa,
Bayan ya shiga izuwa gidan sarauta yayi bankwana da yar sa gimbiya sulairat,
Sai aka dunga aka fito izuwa wajen fada, batare da bata lokaci jaruma Hushriba ta buɗe bakin
ta takaranto waɗansu dalasiman tsafi,
Tsawon daƙiƙa goma, tana gama rufe bakin ta nan take wani irin haske kore ya bayyana a
wajen ya duka shiga jikkunnan jama'a,
Cikin Abinda bai gaza daƙiƙa Ɗari ba ya shiga jikin duk wani mahaluki dake wajen,
Sannan haske ya dawo ya cure waje guda ya tashi izuwa sararin samaniya ya tsaya cak,
Sai gashi yana bayar da wani irin haske tamkar fitila,
Koda kammala hakan sai sarkin bokaye Dargas ya kwalla wa aljani Haulatul-infal,
Jim kadan sai ga sa ya bayyana a wajen ya faɗi ƙasa ya kwashi gaisuwa,
Cikin azama sarki shazwan ya hau kansa ya zauna,
Sarkin bokaye Dargas, gimbiya Hushriba, sarkin yaƙi tare da tawagar bokaye biyar suka yi koyi
dashi,
Cikin sadaukantaka aljani Haulatul-infal ya naɗa fuka-fukan sa ya luluƙa izuwa cikin gajimare,
Tun jama'a na hango su har yazmana sun ɓace ɓat tamkar basu taɓa wanzuwa,
Wannan shi ne yafaru da su sarki shazwan bayan su saurayi Hizmal sun samu nasarar shiga
gidan tsira,
Turƙashi ana wata sai ga wata, yanzu dai gashi manyan sarakuna
Sarki shazwan na birin zawatul-ifdal, sarki uslaim na birin Istanbul, sarauniya Abidatul-auliya ta
birnin Tehran, sarauniya Nuwairat ta birin Garul-mausul.
Da matsafan duniya sun bazama farautar yaro Humair makaho domin saduwa da SARKIN
SADAUKAI Hibairu,
Tabbas farautar wadannan abubuwa biyu dai dai yake da neman jaki mai ƙaho.
---
A birnin Rum dake yammacin duniya anyi wani gawurtaccen sarki da ake yiwa laƙabi da
Baddadul-ulƙas
Sarki Baddadul-ulƙas yakasance gabjejen kato mai kirar samudawan farko mutum mai tsananin
jarumtaka tagaban kwatance,
Ya bunƙasa a sihirin tsafi da da tarin dukiya,
Bokayen duniya da masu hasashe sun tabbatar dacewa a wannan ƙarni babu wani sarki mai da
ya kai sa tarin dukiya dangin lu'u lu'u da zinare gami da dabbobin ni'ima,
Baddadul-ulƙas ya samu nasarar tara wannan dukiya ne saboda wata gasar jarumtaka da ake
shirya wa a wani birni mai suna madinatul- shaja'a ma'ana BIRNIN MAZAN JIYA,
Fiye da sukaru goma sarki Baddadul-ulƙas ne ke cinye wannan gasa saboda jaruman da yake
kawo wa sun kasance hatsabibai a fagen fama,
Duk jarumin da labarin jarumtakar sa ya shahara sai sarki Baddadul-ulƙas ya mallake sa kodai
ta hanyar siyan sa da dukiya mai tarin yawa ko kuwa ta karfin tsiya,
Domin dai kawai ya saka sa a cikin gasar jarumtaka,
Duk sarkin da ya lashe gasar ana naɗa jarumin sa a matsayin GOGA SHA FAMA na shekara,
Wata rana sarki Baddadul-ulƙas na zaune a lambun shaƙatawar sa,
Sanye yake cikin shiga irin ta sarauta zaune abisa kujera ta ƙasaita gudanar da bincike bisa
halarar tsafin sa abisa madubin tsafin sa,
Kwatsam sai yaga wani al'amari da ya sanya shi farin ciki kuma ya dugunzuma hankalin sa
Abin da ya sanya sa farin cikin shine akwai wani boyayyen jarumi da ake kira da suna Hibairu
SARKIN SADAUKAI,
Wanda yake a halin yanzu babu wani gwarzon mayaki kamar sa,
Abin da ya dugunzuma hankalin sa kuwa shi ne ta wace hanya zai mallaki SARKIN SADAUKAI
Hibairu domin ya shiga gasar jarumtaka dashi,
Bayan cewa A halin yanzu Hibairu baya jin Yaren mutanen duniya baki ɗaya shi yana amfani ne
da wani yare na musamman,
Wani abu da ya fi dugunzuma hankalin sa shine haƙiƙa sauran Yan uwan sa sarakuna abokan
gaba zasu iya cin nasara akan sa matsawar su ka riga sa mallakar SARKIN SADAUKAI,
Sa'adda sarki Baddadul-ulƙas yazo nan a tunanin sa sai ya sake zurfa fa izuwa cikin Kogin
tunani domin samun mafita,
Daga bisani ya samu mafitar, mafitar kuwa ita ce tun da a halin yanzu saura kwanaki ɗari biyu
SARKIN SADAUKAI ya kammala karanta ɗalasiman tsafin dake jikin ZOBEN SHIRIn sa sannan
ya fito daga dajin Baitul-shamshan to yazamana wajibi na yi ma za na ɗebi runduna ta domin na
je bakin dajin Baitul-shamshan na kafa sansani har izuwa lokacin da SARKIN SADAUKAI zai
bayyana
Fatana shi ne Hibairu ya samu nasarar cinye gasar jarumtaka ta duniya ya zamo GOGA SHA
FAMA,
Sa'adda sarki Baddadul-ulƙas yazo nan a tunanin sai ya sake nutsawa bisa halarar tsafin sa
domin yakara samun haske akan al'amarin,
Yana cikin wannan bincike ne sai kawai ya a bushe da dariyar farin ciki maral misaltuwa tamkar
ba zai taɓa daina wa ba,
Bakomai ne yasan ya shi a cikin wannan farin ciki ba sai domin ya gano cewa HUBAIRU
yaksance ɗa a wajen babban maƙiyin sa Barde Shabbaru
Wanda a halin yanzu yake bauta a ƙarƙashin masarautar sa,
A salin Shabbaru mutumin ƙasar Misra ne kuma sarki Baddadul-ulƙas ya farauto sa ne bisa
yarjejeniyar cewa idan ya samu nasarar lashe gasar jarumtaka ta GOGA SHA FAMA zai raba
dukiyar da ya samu ya basa kaso biyu kuma zai nada shi wazirin sa,
Bayan Barde Shabbaru ya samu nasarar cinye gasar ne, sarki Baddadul-ulƙas ya ci amanar sa,
Kuma yayi umarni a hallaka matar sa domin bincike ya tabbatar masa dacewa jaririn da zata
haifa ne zai kawo karshen mulkin sa,
Lokacin da sarki Baddadul-ulƙas yaga wannan al'amari sai ya sake cika da mamaki,
Amma sai ya tambayi kansa a cikin ransa yana mai cewa ya a kayi matar Barde Shabbaru ta
rayu har ta haifi abinda ke cikin ta ?
Wani ɓangare a zuciyar sa kuma na cewa dashi yanzu ai zaka yi amfani da wannan dama ne
wajen jifar tsuntsun biyu da dutse ɗaya,
Wato zakayi amfani da Barde Shabbaru wajen mallakar SARKIN SADAUKAI,
Koda cewar bata ganin bil'adama ballantana ya tuna wane mahaifin sa,
To amma soyayyar uba da ɗa ba wasa ba ce tilas zata yi tasiri,
Zaka samu nasarar sarrafa Hibairu yadda kake so har ya kai ga lashe maka gasar jarumtaka ta
duniya,
Dazarar ka cimma burin ka sai ka hallaka su baki ɗaya da uba da ɗan na sa,
Sa'adda sarki Baddadul-ulƙas yazo dai dai nan a tunanin sa sai ya sake bushe da dariyar farin
ciki tamkar bazai daina ba.
Tun a daren wannan rana sarki Baddadul-ulƙas ya fara shirya rundunar mayakan sa ta haɗar da
dakarun bil'adama da aljanu haɗe da miyagun dabbobi
Alfijir na ketowa ya tashi hankalin rundunar sa ya durfafi dajin Baitul-shamshan,
Tirƙashi gaskiya masu iya magana da suka ce ba'a rabu da bukar ba an haifi habu,
Gashi duk waɗannan sarakuna da jarumai sun bazama farautar Hibairu tare da nasu
hukumomin,
Jaruma Husnaila, saurayi Hizmal da aljani Marhutul-Azab suna tare da yaro Humair wanda
shine kaɗai ya iya magana da Yaren Hibairu SARKIN SADAUKAI,
Sarauniya Nuwairat kuwa tana son kasance mace ta farko da Hibairu zai fara arba da ita domin
ya kamu da ƙaunar ta domin ta iya sarrafa sa yadda take so,
Yanzu kuma ga sarki Baddadul-ulƙas wanda ya tawo tare da