Showing 18001 words to 21000 words out of 38778 words

Chapter 7 - HAUWA KULU Yar Cikin Badala 4 Book By Sumayya TAKORI.pdf

dauki Waheedah da ya ajiye a
gado tana tsala kuka ba.
Dakin Sumayyah ya nufa, sai ya tarar da dakin a kulle. Wato ita kuma ta tafi ba izninsa. Ya
fiddo waya ya kira ta,
kina ina ne dakinki a kulle?
Wa? Ni? Bhaiya ai na tsufa a hostel, ba ni ba kara kwanan gidanka.
Sarham ya kara hassala fiye da farko, ya ma fasa gaya mata cewa ya zo da Hauwa don bai
ga amfani ba, ya ce,
In na kara cewa ki zo gidana Summy ki ce shege ne ni ba haihuwar Maisharia da Prof. ba.
Na yafe miki zuwa gidana daga yau har gaban abada.
Jikin Sumayyah ya yi sanyi, ta ce, Bhaiya
Ya yi maza ya kashe wayar, jikinsa yana tsuma da bacin rai, ba tare da ya saurare ta ba, ya
koma falo ya tadda Hauwa.
A yadda ya bar Hauwa a haka ya same ta a zaune a kan kujera ita ma ta kumbura tayi fam,
kiris ta ke jira ta fashe. Don bata taba jin cin mutunci akan lalurarta rabin wanda ta ji a bakin
Madinah yau ba. Hakika makanta abu ce mai saka karfin ji!
Ya yi kamar bai ga kumburin da ta ke yi din ba, ya dauki jakar kayanta ya kama hannunta ya

ce,
Taso ki biyo ni mu je ki huta.
Ta ja tunga a inda ta ke zaune ko motsawa ba ta yi ba. Ta kuma warce hannunta.
Yaya Doctor ni gida zan koma!.
Idanuwanta suka yi narai-narai cikin kwalla, wadda ba ta idasa zubowa ba.
Ya dube ta a matukar hassale itama, ya ce,
Ga hanya nan ki koma din, idan ba ku hadu ku ukun kun haukata ni ba, ba ku ci sunanku na
mata tumakai ba!.
Ya dauki jakarta ya nufi wani daki da ke rufe wanda ke kallon dakin Madinah, ta shirya dakin
ne don bakinta yan gidansu na Sorondinki in sun zo aikin Hajji su kan shigo su kwana, shi kuma
nan ya ga nan ya dace Hauwa ta zauna don girmansa daya da dakin Madina.
Dakin a gyare yake tsaf babu abinda babu na bukata, ga sabon bayi (toilet) makale a cikinsa.
Ya ajiye jakar Hauwa ya fito.
Daidai fitowarsa ya ga Madinah tana kwashe warmers din abincin da ta girka daga kan
dining table. Ta kwashe komai ta juye a leda ta saka a freezer.
Tana kallon Hauwa a zaune tana tsane ido da gefen mayafin abayarta, ta wutsiyar ido ta
harare ta, bayan ta gama kwashe komai ta shige dakinta ta kulle ta ciki.
Sarham ya dawo ya zauna daf da Hauwa, ya rasa ta ina ma zai bullo musu su duka. Hauwa
jin zamansa a kusa da ita sai ta kara sautin shesshekar kukanta, wai ita kawai ya maida ita
wurin Mama bazata kwana a gidan ba.
Ga gajiya, ga yunwa, ga bacin rai da suka tarun masa don haka bai kula ta ba. Ya fiddo waya
ya kira Abbansa yana maida fushinsa, ya gaya masa sun sauka lafiya, haka Mama ma. Bai ja
hirar da tsayi ba kuma ya kama hannun Hauwa ya soma janta ta karfi zuwa dakin da ya zabar
mata.
A gefen gadon dakin ya zaunar da ita, This is your room, in kin ga dama kuma ki kama
hanyar Kano a kafa daidai ne. zan je in yi sallah, muje ga toilet in nuna miki yanda yake ki gane
komai, ko kina son shiga.
Wannan karon ta bashi amsa cikin share ido jin yace su je kuma bai kama hannunta ba.
Idan na fadi fa, tunda ban san hanyar koina a gidan ba?
Tausayi ne mai tsanani ya kama shi, kawai sai Hauwa taji Sarham ya dauketa yana tafiya da
ita zuwa toilet din a hannayensa.
Kunya taji soai ta hau sunne kanta a kirjinsa. Daka barni na tafi da kafata don in gane hanyar
koina.

Dr. Sarham bai yarda ya direta ba sai a toilet din, ya nuna mata yadda za ta yi amfani da
komai na bandakin, ta hanyar dora hannunta akan komai yana bayani. A karshe ya nuna mata
(shower) ta wanka da yadda zata dinga kunnawa da rage zafin ruwan daga famfon kada ya
kona ta, ya nuna mata kunna (water heater) wadda yace in ta kunna ba sai ta kashe ba don
tana kashe kanta automatically.
Ita ba ta san dalilin yawan taba hannayenta da yake yi ba wai yana nuna mata abubuwa, nan
kuwa ba ya gajiya da touching dinsu ne sabida taushin fatar hannunta.
Na gane, ka je zan yi wanka!.

Kin fasa komawa gun Maman? Ya tambaya cikin gatse, yana janyota yana makalewa.
Hauwa ta tsuke fuska da baki, ta ce, Ya danganta da sunan da aka kara kirana da shi a gidan
nan. Ni duk duniya ba wanda ya taba ce min musaka. In ma musakar ce shin miskini ba mutum
bane? Ni dai na san;

Inna Akramakum Indallahi Atqakum.

Ta hakan ne ya gane cewa ta ji me Madina ta fada a kanta. Ita makanta da ma sanya karfin ji
ne da ita. Ya kuma san ba abinda ta tsana a duniya irin sunan da Madinah ta kira ta da shi, yau
mafi muni, don haka ya sassauta murya ya sake makalkaleta a jikinsa yana shafa gadon
bayanta, yace. Ki yi hakuri, ki kara yin hakuri, ki kuma koyi karbar ‘labelling’ na sunan lalurarki, hakan ne zai
sa ki zauna lafiya ko da wani ya fada ki daina damuwa irin haka da shiga bacin rai, ba lallai ne
kowa da niyyar gorin ido yake ce miki makauniya ba, wani kuma bada isgilanci bane, aah suna
ne da Malam Bahaushe ke kiran duk wani mai lalurar gani dashi don banbance lalurarsa. Ki koyi kauda kai a kan hakan muddin kina so ki rabu da bacin rai.
Ya kara sassauta murya, ya ce,
Ki gama wankan kiyi sallah mu je tare mu sayo abinci.
Saboda ya ga sanda matar gidan ta fito ta kwashe nata bakidaya, (amma bai fadi hakan ga
Hauwa ba ya barwa ransa).

Wannan ya sa Hauwa ta dan saki ranta, jin cewa za su fita su mike kafafunsu. Don dama
sai mutsuka suke mata na zaman jirgi.
To ka fita zan yi wanka
Allah ya yarje min inga komai na jikin matata Hauwa
Ya fada yana sirka mata ruwan wanka.
Saida ta hada da rokon shi Allah Annabi ya bata waje sannan ya fita ya rufo mata kofar.
Ta yi wankanta da kyau da ruwa mai zafi domin warware gajiyar da zaman jirgi ya haddasa
mata, tana wanka tana tunanin yadda zamanta da Maman Waheedah dinnan mara kirki zai
kasance a gidan, wadda a zahiri ba ta marabci zuwanta ba, kuma ba ta shirya zama tare da ita
ba, kafin maigidan ya kawo ta meyasa bai gaya mata matarsa bata da kirki ba, kuma bai nemi
yardarta ba ya daukota ya kawo mata gida?
Wannan ya nuna shi Sarham mutum ne mai yin abin da ya sa kansa a gidansa ba tare da
shawara da mata ba. Ita dai ta san za ta yi ‘tolerating’ komai, za ta yi wa Madinah biyayya
kamar yadda Mama da Inna suka nusarsheta, abu daya ne ba za ta lamunta ba, Madinah ta
keta rigar mutuncinta ko ta ci gaba da kiranta da duk sunayen wulakancin da ta ga dama Wata doguwar rigar atamfa Hauwa ta sanya Chiganvy da aka yi wa wani ubansun dinki
wanda ya fiddo kyakkyawar surarta sosai ba tare da ta san yadda kayan suka karbi jikinta ba, ta
dauki mayafin da Mardiyyah ta manna a cikinsu ta yafa.
Tana cikin fesa turare Dr. Sarham ya shigo sanye da farar sabuwar jallabiya mai matukar
tsada, sai tashin nasa kamshin na musamman yake yi.
Oya lets go, kin gama ai ko?
Idonsa ya kai ga dressing dinta ya kankance ido, Me-ji! Cire wadannan kayan maza-maza,

kin manta a Saudi-Arabia ki ke? Ko ba a can ba ne in aka ce ki fita da wannan dinkin jikinki na
juyawa a cikinsa sai ki fita don hankali ya wadace ki ko?
Hauwa ta hau shafa dinkin jikin nata wai ta ji me ye laifinsa.
Ka yi hakuri, ka san dai ba na gani.
Umh! Da wani ne ya fada da yanzu cibi ya zama kari, canza su maza-maza ina jiranki.
Ya ci gaba da tsayuwa kuma bai fita ba.
Hauwa ta rausayar da kai gefe, To a gabanka zan canza ne Yaya Sarham?
Ya yi wani dan murmushi cikin rashin jin dadi ya juya ya fita yana cewa,
Na ba ki wuri, Mrs., matsayina na Yaya har yanzu yana nan bai canza ba kenan ko?
Bai kuma tsaya sauraron amsarta ba ya juya zai fita tayi maza ta riko shi.
Za ta so kwarai ta ga fuskar likita Sarham a yau, ta tabbata wanka ya dauka ko daga
niimtaccen kamshin da yake zubawa a dakin.
Hauwa ta yi ajiyar zuciya tana ji a jikinta lalurar makantarta ta har abada ce ba ta da magani,
don ba ta taba ji ko ganin makahon da idonsa ya bude ba.
Don haka fatanta na ganin fuskar likita Sarham zai ci gaba da kasancewa fata (hope) irin
wanda har dan Adam ya koma ga Ubangijinsa bai samu cikarsa ba (actualizing of dream) dinsa.
Ta hau lalubar fuskar Dr. Sarham ta saka fuskar shi a tsakanin tafukanta biyu, tana shafa
tattausan sajen gefe da gefen fuskar tasa, ta ce You are my HUSBAND, not a brother, and my
everlasting dream is to see you with my naked eyes.
Sarham yayi maza ya hade bakin su wuri guda, yana sakar mata mata wata irin zazzafar
sumba mai tsayi da zurfi kusufa-kusufa lungu lungu sako sako a cikin bakinta.
Hauwa sai ajiyar zuciya take yi, kwalla ta taru a idonta, ta yi maza ta rike shi gamgam itama,
nan ya idasa rikitata ta hanyar kai bakin shi saman kirjinta, daga wannan lokacin suka lula a
wata duniyar maaurata mai ban mamaki da shiga rai. Hauwa na neman shidewa Sarham ya
dauketa a hannunsa zuwa gadon dakin, har da wata irin sheshshekar fita hayyaci yake yi a jikin
Hauwa kai kace bai taba rike mace ba, yana kiranta da sunayenta kala-kala. Wadanda take so
(Hauwau-Jiddah-Maijiddah) da wadanda bata so (Kuluwa ta, Kulun-Majadun dina, ni ina ganin
ki kuma ina son ki a hakan, ko baki ganni ba)”.

Tunda Madinah ta kulle kanta a daki ba ta kara ko lekowa falo ba, sai kukan Waheedah ka ke
ji yana tashi a gidan, wadda da alama ba ta samu lallashin uwa ba. Wannan kukan na Waheeda
har cikin kwakwalwarsa yake tabawa, kukan Waheedah shi ya ceci Hauwa a hannun Dr.
Sarham yau kuma, ba don haka ba da tuni ta amsa sunan sauran mata yan uwanta. Taimaka mata yayi ta canza kayan zuwa bakar abaya da mayafinta. Ya san da gayya ta kyale
Waheeda take jiniya don haka ya kama hannun Hauwa suka fito ya rufe dakin suka bar gidan.
Madinah na jin rufe kofarsa ta leka waje ta tagar dakinta. Nan ta hange su suna takawa a
kasa gwanin ban shaawa, ya rike hannun Hauwa cikin nasa. Ba ta san dai ina za su je ba,
amma jikinta ya ba ta ‘mudam (restaurant) da ke cikin estate din nasu za su je, wato wajen cin
abincin likitocin Saudi-German. Wani abu ne da za ta iya cewa tunda suka yi aure rabon Sarham da shi wato cin abinci a
Mudam, don ko ba ta dafa abinci ba zai wa cikinsa yan dabaru ne ya zauna lafiya. Sai ta shiga
tambayar kanta shin abincin da ta dafa ta kwashe don kar su ci ta kyauta? Lallai kishi mai
maida babba yarinya mai juya hankalin mai hankali. Kyabe baki ta yi, ta ce,

Ba hakkina ne ciyar da su ba daga shi har matar tasa.
Shi da ya ga zai iya wahala da makauniya sai ya fara tunda wuri, kafin wankin hula ya kai shi
dare don in yana zaton ni zan kula masa da mata ya yaudari kansa.

Suna tafe cikin tsanaki a gefen titi, Sarham na tausar zuciyarta a kan kalaman Madinah.
Ya ce, Ki daina damuwa don wani ya ce miki makauniya, ko mara gani. Makaho bai isa ya
hana alumma kiransa makaho ba, haka kurma bai isa ya hana alumma kiransa kurma ba. Thats
the same with gurgun mutum (physically challanged) bai isa ya hana a kira shi gurgu ba, but
accept it, like it, appreciate it. Accept your disability, enjoy it sai ta zame miki unique
identification ba tare da ranki ya baci a banza ba.
Ni idon nan da ana musanye da mun yi na huta da wannan bacin ran na GORIN IDO tunda
ban isa hana mutane kiran Hauwa-Jeddah makauniya ba.
Hauwa, ta daga manyan idanunnan farare kal, tayi harr! Dasu a kan Sarham da wani irin
murmushin jin dadi a fuskarta. Sarham ya shafa kansa zuwa keyarsa jin wani ignition na
fizgarsa, yace kada ki kashe ni da idanunnan Hauwa, I loved them, ina son daren yau in samu
Safiyyah ko Maimunatu mai irin su, daga daren farko mai albarka. Hauwa ta kai tafukanta ta rufe fuska cikin jin kunya da karuwar Son Sarham mai tsanani a
zuciyarta.
Daidai lokacin da suka isa mudam din suka shiga. Akwai tsirarun mutane, amma ba su da
yawa, ya samar musu waje can nesa da kowa ya zaunar da ita, sannan ya je ya yo musu order
din zazzafar kazar nan ta (Kentucky Fried Chicken) da aka fi sani da KFC da Chips, aka hado
da zazzafan coffee mara sugar aka kawo musu. Yau Hauwa sai ta samu kanta da jin kunyar cin abinci a gaban likita Sarham, ba su taba cin
abinci tare ba sai yau. Shi kuwa bai lura wai kunya ta ke ji ba ya dinga dauko tsokar kazar da
chicken nugget yana saka mata a baki ko ya tula mata tsokar a gabanta.
Ki ci ki koshi fa, kada ki ji yunwa cikin dare.
Ta soma ci a yangance ya ce, Maijiddah ni saurayinki ne ne da ki ke min wannan yangar
taunar yen-yen- alhalin na san yunwa ki ke ji?
Hauwa ta rufe ido tana yar dariya a haka ya saka mata nugget guda a baki ya cika mata
bakin taf, ta hau dariya tana tauna tana rufe ido.
Da suka gama suka tako zuwa gida kasancewar ba tazara sosai tsakanin flat dinsu da
mudam din.
Tunda suka dawo a falo ya zaunar da Hauwa ya fita ya rufe koina na gidan. Madinah dama ta
garkame dakinta tuni amma tana jin dawowarsu kuma lokacin ta gaji da kukan Waheedah itama
ta bata nono wanda hakan yasa Waheedah barci.
Suna falo tare har karfe tara na dare yana kallon labaran Aljazeerah kafin yunwa ta koro
Madinah daga daki zuwa kitchen.
Ta wuce su, ko kallo ba su ishe ta ba, shi ma ya kalle ta da wutsiyar ido ya kauda kai, yana
kokarin kashe talabijin ya ce da Hauwa, Mu je mu kwanta haka, don gobe insha Allah zan fita
da wuri na shiga asibiti.

Ya kama hannunta zuwa dakinta duk a kan idon Madinah. Wani zazzafan hawaye ya feso wa
Madinah. Suka shige ya rufo kofar harda key. A can baya idan wani ya gaya mata cewa Sarham

zai iya kama hannun wata mace a duniya bayan ita, za ta karya ta ne da babbar murya. Yau dai
ga shi tana ganin halin maza, ganin idanunta. Shin me ta yiswa Sarham data cancanci haka?
Tabbas duk wadda ta ce namiji uba ne ko abin yarda da baiwa amana akan SOYAYYAH ita
Madinah za ta kwana tana gaya mata itace marainiyar da ta fi kowa maraici. Sanin cewa hankalin Madina yana kansu sai bai jima sosai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login