Showing 12001 words to 15000 words out of 37792 words
Chapter 5 - Rainon Soja Part 3 Complete Book By Maman Teddy .pdf
banza Sojan wofi
a yanzu fighting ake yi against love ba maganar soja ba . Babu wanda ya isa yayi mun iko da
Ma'eesha tawa ce! Duk wanda yayi yunƙurin rabani da ita wallahi ba zan bar shi ba.
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un kalmar da Mami ta furta kenan tana Girgiza Ma'eesha tare da
kiran sunan ta da ƙarfi“ Ma'eesha............”
[1/24, 6:01 AM] Real~Mamanteddy: *(Book 3 three)*
*Love and Amazing story*
*Written....✍ Aysha Mamanteddy Mrs Usm*
_________________________
*RAINON SOJA*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story*
*Littafin na kuɗi ne please ban yarda wata ta karanta mun ba tare da Ta biyani ba , regular
group ₦500... Vip group ₦1000... SPC payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha
keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932# .*
50~51
_________________________
“.......Ma'eesha.....! Mami ta fara kiran ta tana Girgiza ta ganin yanda Ma'eesha tayi lamɓaassss
ko numfashi bata fitarwa . Da sauri Daddy yakai hannun sa yana shirin Ɗaukar ta Ali ya riga shi
, yana mata ɗaukar nan nasa da ya saba . Juyowa suka yi suna kokarin fita harabar gidan ,
Suka yi kiciɓussss da Dr Sa'id Wanda shi yake duba jikin Daddy . Alhamdulillah ” kalmar da
Daddy yayi kenan yana furta “ Maza Ali mu koma ciki kaita Bedroom ɗina doctor ya duba ta
yanzu . Bana son Wani tsaye tsaye idan ka kaita ka sauko ina son magana......Bai tsaya jiran
me Daddy zai ce ba da sassarfa ya wuce , yayin da Mami ke bin su tana ƙwallah Khalil kuwa
riƙo Hannun Dr Sa'id yayi yana cewa “ Taho da Sauri Doctor ka duba ta please ”. muje
muje........Su Mom Hajara da suke falo su dai sun ga sun dawo ne Yuuuu duka suna nufar ciki .
Caɓe baki Mom Hajara tayi tana kallon su kana ta kalli Maryan dake rusa , kuka Jidderrrrrr na
furta“ Tun da ta shigo rayuwa ta kullum a wannan kukan nake. Yanzu Mom taimako ɗaya zakiyi
shine kiyi gaggawar komawa gida ki sanar mawa da Hajiya kaka wannan auren don a dakatar
dashi , tun da Daddy ya shiga tsakani to fa babu wanda ya isa ya dakatar sai ita.
Kallon ta Mom Hajara tayi kana tace “ Ai dakaytarwa dole , zama kuma ai ban ga ta zama . Tun
da har Ali akan wannan yarinya ya nemi mun tsayayya wallahi ba zan bari ya Aure ta ba ko ta
halin ƙaƙa . A taƙaice na tsani ma yarinyar baki ɗaya.... Cikin Muryar Kuka Maryam tace “ Mom
Ki taimaka mun kar Khalil ya Aureta , gwara Su Adams ɗin su Aure ta ........Wani irin haushi ne
ya kama Jidder don ita kallo ɗaya da tayi ma Adams taji yayi matuƙar burgeta , wato ta kamu da
Soyayyar sa a Zuciyar ta.... topa!
Don Allah ke Maryam ki bar wannan magana ai shirme ma kenan! Babu wanda zata Aura cikin
su ,ai sai dai ta Auri ɗan dako ko Masu yankar fulawa . Me su Adams zasu yi da ita?......wuce
su Mom Hajara tayi tana furta “ naku wasa ne , Bara ku gani”.
Daddy na tsaye Mom Hajara ta wuce shi ko tankasa bata yi ba ta yi shigewar ta mota . Bai bi ta
kanta ba , don tuni ya gama kiran su Alhaji muddasir ƙanin sa da Alh Kawu da Sauran Wanda
yake son su Amsa Wannan Auren , da shima ya yanke hukuncin sa lokaci daya, don a ganin sa
hakan shine natsuwar ita kan ta ma'eeshan , ko mutuwa sukayi sun san tana hannun wani
babban bango jijjige na rayuwarta , dama ya daɗe yana fatar ɗaya daga cikin yaran nasa su
aure ta sai kuma gashi .
Juyawa yayi yana shiga moton sa tare da Ma drivan umarni suna ficewa daga gidan......!
**
Wani irin rawa da juyi Hajiya Atika ke yi , ganin yanda Alhaji ya sukurkuce a kan ta. Cikr da
takon ta ta fara nufo Ɓangaren su Rabi don ta bata ƙyautar ta sannan ya sake turata zuwa ga
Bokan nasu . Sasan ma'aikatan cike ta gansu , anyi dafifi ana furta ku bata ruwa ruwa ruwa. Da
Sauri ta ƙarika zuwa inda Yan Aikin suke , Rabi ta gani kwance tana ihu a galabaice tare da
furta “ Wayyo ciki na! Wayyo Ciki na! Suna shaƙe mun wuya da kachaaaa wayyo Cikina suna
ɗibar munnnnnnnnn Wayyyo...... Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un ” tabawa ta furta kamin tace “
Allahu Akbar, Allah me yanzu yanzu. Shikenan Rabi . Zare ido Hajiya Atika tayi kana tace “
Ban gane ba , me kike nufi? . Tabawa ne ta ɗago tana share hawaye kana tace “Hajiya baki
gane ba? Ai Rabi Sai dai muce ALLAH yayi mata Rahma babu ita ”. Wani irin zabura Hajiya
Atika tayi tana yin baya tare da Furta “ na'am tabawa”.
**
Nasreen ne ke bin Hajiya Falmata da kallo , kamin tace “ Mommy kiyi Haƙuri ki zauna kici Abinci
......Ke Nasreen bari , Ai wallahi yau ba zan rintsa ko naci komai ba , sai naji labarin mutuwar
duk wacce tayi mun Wannan Aiki da Har Adamu zai ci muun mutumci . Tabbas basu san da
Wacce suke kishi ba! Su abun nasu shirme ne , Ni nayi kisa babu iyaka indai akan Abin duniya
ne . Don haka gwara ma su bar mun duka . Ta furta tana cigaba da kaiwa da dawowa tare da
jiran jin umarnin Bokan nata na biyu wanda zai bata , tayi Aiki dashi yanzu a tsaye. Wayar ta na
handsfree tana sauraren Umarnin sa .
**
Ƙarfe biyar a wannan lokacin Ma'eesha ta farfaɗo don har an mata aluran barci , har kuma a
lokacin gidan cike yake don a yanzu har da Hajiya kaka Mom Hajara ma ta dawo . Da kuma
iyayen Maryam mahaifiyar ta wacce tazo kun san yan boko ba kunya wai taji a wani hali ake ciki
game da Auren yarta . Shikam Daddy an kira shi babu iyaka ba'a samun shi , har an gode
ALLAH . Don Hajiya kaka ta furje ido akan babu jikanta da zai Auri Ma'eesha a fara sanin
Asalinta da toshenta tukuna .
Suna zaune ne suka fara jin shigowan Daddy Alhaji muddasir Alhaji kawu , Da Abba Auwalu
dukan su Cike da kamala kai da gani kasan ƙusoshin ƙasa ne. Duka bin su da kallo suka yi ,
Yayin da suma ke kallon su Mom Hajara da kowa na falon fuskar su na fidda Annuri . Saurin
miƙewa Aliyu yayi don ya fara tunanin Ma'eesha na iya kuɓce masa a ko wani hali a kuma ko
wani lokaci a yanzu .
Wani irin Dariya Daddy yayi kana yace “ Ƙwantar da hankalin ka Aliyu , ma'eeaha ta zama
matar ka a Yau an ɗaura maka Aure da ita Da misalin ƙarfe hudu na yammacin nan.............!
Tirƙashi
Yanzu wasan zai fara✍ . Ko ya kuke ganin wannan tafiyar zata kasance? Meye ra'ayin ku a
wannan Auren na Haidar mugu da Ma'eesha . Shin ita kan ta ma'eeshan na son shi ma
kuwa? Ko dai watan cin Wahalar Aliyu ne ya tsaya? Khalil zai bar ma ɗan uwan nasa? Ya
Areeef kuma? Sannan ina Adams? Jidder ya nata Al'amuran zasu kaya? Ku cigaba da biyo
mmnteddy mai alƙalamin zinare yanzu aka fara morning ️ . Page 46~47 bonus ne zaku
iya sharing nashi zuwa wasu grps naku na gode ......!
[1/25, 8:05 AM] Real~Mamanteddy: *RAINON SOJA*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story.*
52~53
Aure!
Muryoyin matan Falon ya amsa a tare kana Aliyu ya saki Wani irin Ihun farin ciki yana furta
kalmar godiya ga mahaifin nasa tare da cewa “ That's my Dad! Daddy na gode ka bani duk
Abinda nake so tun daga yarinta na har girma kana faranta mun , Allah ya kare ka daga dukkan
sharri ya kuma bamu ikon biyayya a gareku. Na gode Dad . Juyawa yayi yana kallon su Alhaji
muddasir da Alhaji Kawu kamin suma ya fara kokarin yi masu tamkar zai zube yayi sijjada
Saboda tsaban Farin ciki . Wani irin farin ciki ne ke ratsa Zuciyar Mami da Daddy , Tabbas a yau
sun yarda Ma'eeaha rayuwar Ali ce gaba Ɗaya . Gaba ɗaya ya Saki ya dawo tamkar bashi ba ,
wannan jin kan da Miskilancin babu sai zallar Annuri dake fita daga fuskar sa . Dad! Muryar
Khalil ya katse su cikin sanyi , Wanda hakan yasa duka kowa mai da kallon sa gare shi. Gaba
ɗaya ya sauya fuskar sa babu Walwala , Ga tarin damuwa ƙwance cikin wata irin nannauyar
murya ya furta “ Shin Da Gaske ne Wai Ali ne kuka ba shi Auren kamilar Yarinya ƙarama kamar
ma'eeaha? Why baku Aurar da Jidder wacce ta kere mata Ashe karu nesa ba kusa ba ?
Wannan ba kuyi san kan ku ba kuwa duka saboda ɗan ku ya gyaru kuka yi hakan ba don kuna
ƙaunar ma'eesha ba!
Ali....Al...Muryar Daddy ne ya fara kyarma so yake ya kira sunan Khalil amma kuma maganan
sa ta sanya ɗaguwar hankali da mamakin furucin nasa sai yana kiran sunan Aliyu instead ya
kira sunan Khalil . Fahimtar Sunan shi ɗin yake SO ya kira yake kiran na Aliyu yasa ka Khalil
girgiza kai tare da cewa “ Of course yes Daddy! San Kai kuka yi. Waye bai san Halin Aliyu ba
tun yana ƙarami? Baya ji ....Sannan mazinaci ne mai lalata yaran mutane Sannan yanzu kun
ɗauki ƙaramar yarinya Which she's not up to 15 Kun bashi .....Wato idan ya kashe ta Ai babu
mai Asara . Sannan sha'awar ta yake ba Sonta yake ba i have since observe this......Ku mai
yasa baku fahimta hakan ba Daddy kuka...........Ya isa Khalil, Ranka zai mummunar ɓaci yanzu!
Muryar Mami ya katse su cike da doka Wani irin rikirkitaccen Tsawa . Kallon shi take yi cike da
ɓacin Rai tana Wani irin Girgiza kai na tama rasa mene zata ce .
Ka ƙyauta! Mami ta furta kawai tana kai hannun ta tare da Ɗauke ƙwallar da suke zubo mata .
Koma Meye Ni Alhaji Sale na yanke Wannan hukuncin , kuma ma'eesha ƴa ta ce naba Ali
haidar Auren ta , idan ya cuce ta ko ya zalunceta Amana ce Allah zai saka mata bamu ba.
Daddy ya furta yana kallon kowa na Falon, Inda Alhaji muddasir ya fara magana da cewa “ Wai
meke faruwa ne cikin gidan nan? Shin da gaske ne Kalamar Da Khalil yayi akan Haidar? Idan
kuwa da gaske ne to tabbas da Aƙwai tarin matsaloli. Wanda bata tunanin a ɗauki yarinya ƴar
teenage age a bashi . Shima bai gama hankali ba , don mai hankali ba zai zina ba.
Rintse ido Mami tayi tabbas ba zata yi shaidan Ali ba. A hankali cike da Sanyi Alhaji Kawu yace
“ A'a Ni sam ban yarda da Wannan Al'amari ba , Ali yaron kirki ne .....Ga Abin da Yayan sa ya
faɗa wanda suke tare tun daga Karatun Soja har yanzu , yafi mu sanin Waye Aliyu , Sannan
tausayin yarinyar yasa shi faɗin haka . Dole aƙwai lauje cikin naɗi. Muryar Alhaji muddasir ya
katse su cike da Zafin nan nasa . Don shi mutum ne mai Masifar faɗa , kowa tsoron shi yake yi ,
idan yace abu ba mai tsallake masa .
Maryam Jidder Hajiya kaka da mom Hajara su dai tun da suka zauna suka ji labarin an ɗaura
Auren Ali da ma'eesha motsawa dayan su babu wanda yayi duka sun kasa.
Cikin Tsawa Alhaji muddasir yace “ Ali buɗe baki kayi mana magana shin da gaske ne kana
lalata yayan mutane? Faɗa mun yanzu naji muna saurarenka”. Dammmmm Ƙirjin Mami ya buga
da ƙarfi don tabbas ba zatayi shaidar Aliyu ba , sannan kuma ta san shi baya ƙarya ko da kuwa
za'a kashe shi ne , yana da Wannan taurin zuciyar .
Areeef da Adams Sada kai sukayi ƙasa , don a yanzu Khalil sam bai ƙyauta masu ba . Kuma
basu ji Daɗin Wannan Abu ba , saboda sun san Aliyu Wallahi ba zai ƙarya ba koda za'a mutu
sai ya faɗi gaskiya ”.
Ɗago da Lulun idanun sa yayi na rashin tsoro yana zuba su bisa Na Alhaji muddasir da Sauran
kowa na falon . Gyaɗa kai yayi yana motsa laɓɓansa zai yi magana kenan Muryar ta ya katse
su tana cewa.....................
*Morning ️ .*
*Don Allah kar ki karanta ba tare da kin biya ba . Regular payment ₦500 Vip group ₦1000 SPC
payment ₦1500 via 6037312299 mohammed Aisha keystone bank ko katin MTN ta Wannan
number 08081202932#Antymmnteddy*
[1/25, 8:56 AM] Real~Mamanteddy: *RAINON SOJA*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story.*
54~55
*Littafin na kuɗi ne please don Allah kar ki karanta indai baki biya ba . Regular payment₦500
Vip payment₦1000 SPC payment₦1500 via 6037312299 mohammed Aisha keystone bank ko
katin MTN ta Wannan number 08081202932 idan Vtu transfer ne sai ki tura ta wannan number
09061466409....✍#Mamanteddy#mrsusm.* #General Sale famly.#Hajiya Atika#Nurse Nareet ....the Dairy.
Ku mance da Waye Uncle Aliyu! Forget about all his good character or bad , I love him and a
shirye nake zan Zauna dashi har na mutu har Abada! Not even because I love him No! Ba don
wannan ba kawai saboda shi yabani rayuwar sa. Ko da Zan Aure shi ya kashe Ni zan zauna
dashi kuma zan bishi . Shiruuuu Wurin yayi , Kalmar Ma'eesha dake fitowa daga bakin ta jin su
suke yi tamkar a mafarki ,don ba haka bane a Zuciyar ta suma sun san hakan , amma kuma
menene ya sauya ta at just a one time ? . Saurin ƙarikowa mami tayi zuwa inda Ma'eesha take
Gyefen ta Doctor Isma'il ne don da lamarin yayi ƙamari shi mami ta kira bayan tafiyar su Daddy
, idan mutuna shine Family Doctor ɗin nasu tun suna yara shi ne mai duba lafiyar ko wannen su
.
Ɗago da fuskar ta mami tayi tana cewa “ Ma'eesha kin tabbata Zaki zauna da Aliyu? ”. Koda Ya
Aliyu yana Abinda yafi Wannan muni ne zan Zauna dashi har iyaka Rayuwata! Ta furta wasu
hawaye na kwanciya saman idanun ta . A hankali ta zame hannun ta da jikin ta daga Mami tana
juyawa tare da barin falon tana komawa Bedroom ɗin Daddy inda take ƙwance.
Hummmmm lallai Wannan shi ake kira da bariki , yarinya ƙarama tana goge mu tasssss Abun
gunun mamaki Ashe itama Auren take so! Jidder ta furta tana tafe hannu . Uhmmmm lallai kam
Tom Ni ban yarda da Wannan Auren ba Alhaji saleh zamu zauna . Muryar Hajiya kaka ya katse
su cike da girma da natsuwa wanda sai a yanzu suka ji bakin ta ,don Duka an manta ma da ita
a falon .
Wani irin kallo Aliyu ya watsa mata na jika da kaka , kana yace “ Da yake kece zaki zauna da ita
ai dole Kice wani Za'a zauna , To daga yau an gama zama a mun wani magana akan ma'eesha
babu Ruwar Kowa da Rayuwar mu! Buɗe baki Hajiya kaka tayi kamin tayi magana tuni ya
juya cikin takon sa mai ɗaukar hankali ya wuce daga falon, don sosai ya shaƙa da maganan
Alhaji muddasir kuma ya so ya faɗa masa yana yin Duk abin da Khalil yace yana yi amma kuma
mene? Baya tunanin akwai wanda ya isa ya raba shi da Ma'eesha sarki ko alƙali kuwa.
To mashaallh kowa zai iya zama ko ? Muryar Alhaji Muddasir ya katse su bayan Tafiyar Aliyu
ciki.
Wani irin kallo Khalil ya bishi dashi , kana ya juya yana barin falon , da ido suka suka bi shi , har
da sirikar tasa da Maryam , A hankali suma Adams da Areeef suka sulale suka gudu , Jidder
kuwa iyayen Rashin kunya , miƙewa Tayi tana gyara hular kan ta ,kana tace “ A'a ku zama ya
gani , me zamu zauna muyi bayan Kunyi Abin da duka yayi maku. Kun shigo mana da Guba
cikin Ahali . Wallahi Wallahi wallahi Ma'eesha ta shiga uku , yanzu ne ya kamata ta sani babu
sauran Hutu da jin dadi a rayuwar ta . Na tsane ta kuma ba zan taɓa san ta ba. Fuuuuuuuu ta
juya tana ficewa daga falon ba tare da ta jira jin cewar ɗaya daga cikin su ba .
**
#Hajiya Atika
Kaiwa da komowa Hajiya Atika take yi tana salallami kana ta fara sambatu da cewa “ Rabi ,
Rabi Rabi ce wai ta mutu? , tana zancen tare da kaiwa da komowa....Yanzu Waye zai kaini
wurin bokan nan da yake yi mun Aiki ta hannun Rabi ? Har gida ya fara zama a hannunsa,
yanzu kuma Tayaya zan bari ya kuɓce mun ? Gaskiya mutuwa baki mun Adalci ba da ki ka
dauke rabi ba tare da na san wannan boka ba.
Dole na bin ciko n kuma san inda Rabi ke zuwa .
Tana zancen tare da wani lanƙwasa hannun ta tamkar zata karya su saboda damuwa .
**
#Nurse Narret
Cike da mamaki Doctor Bulama ke bin nurse Narret da