Showing 30001 words to 33000 words out of 65645 words

Chapter 11 - GARKUWA Book 3C Original True Book By Aisha Aliyu Garkuwa.txt.txt

28 Aug 2025

1072

abun bai damunta har ta gayawa Bappa, so ya bata ƙarfin guiwa da yin addu'a.


*Ba'ana*
Zaune yake gaban yaransa cikin rauni da yanayin damuwa yace.
"Nanda wata uku masu zuwa zan koma ƙasar Nigeria zanyi yaƙin neman Shatu koda zan rasa rainane, zan koma gareta.
Zan gaya mata ko mutuwa nayi sonta ne ajali na".
Cikin bashi ƙarfin guiwa ɗaya daga cikinsu yace.
"Zama kayi nasara".
A hankali yace.
"Babu tabbas, domin tunda na rasa Shatu nakega nayi rashin babbar nasara".
Sai kuma ya miƙe ya shiga cikin ƴar ƙaramar bukkarsa.

Murmushi Baron yayi tare da katse kiran da yayi Sheykh yana jin duk bayanan Ba'ana.
Dan shi Baroon yanzu ya zama ɗan aikin Sheykh dan tun zuwansa lokacin ciwon hannun Shatu.
Da fari har yasa a kirasa daga baya yasa aka dawo dashi.
Ya biyashi kuɗi masu tarin yawa, yayi mishi duk bayanin ɗaya nema, kana yasashi ya koma wurin Ba'ana kuma ya naɗo mishi rahoto da duk wani motsin Ba'ana yana turo mishi.
Alhamdulillah kuma yanzu duk shirin kama Ba'ana yakeyi.

Washe gari ranar asabar yau babu aiki.
Da misalin ƙarfe goma na safe jirginsu Abboi ya sauƙa cikin birnin Ɓadamaya.

Kai tsaye Salmanu yayi musu jagora zuwa Rugar Bani dan a take suna sauƙa wasu tsala-tsalan motoci guda biyar suka iso wanda dama su tun jiya suka iso.
A ƙasan plate number motocin akwai tambarin hatimin kan shanu a ƙasa ansa Abboi, irin tambarin dake jikin jiragen Abboi kenan.

Suna zuwa kuwa babu ɓata lokacin suka isa har cikin gida.
Inda nan Arɗo Bani da kanshi da sauran dattawan sukazo.
Bayan sun gaggaisane Abboi ya ɗan yi gyaran murya tare da cewa.
"Toh Alhamdulillah lallai komai yayi forko to tabbas yana da ƙarshe, to bayan bincike da bin diddigi dai mun gama fahimtar inane asalin wannan baiwar Allah'n kuma munada yaƙinin daga masararutar Joɗa ta fito.
To yau dai kam ranar data kamata mu shiga da ita ciki da yardar ubangiji tazo.
Kamar yadda muka tsara, yanzu zamu tafi".
Cikin tsananin jin daɗi da kuma fargabar ko ya al'amarin zai kasance Bappa yace.
"Alhamdulillah mu duk a shirye muke, fatanmu Allah yasa ina munje ta tuna baya, ta tuno ita wacece".
Da sauri Arɗo Bani yace.
"In Sha Allah ma zata tuna Malam Babayo".
"Allah yasa haka".
Al'ameen ya faɗa.
Amin Amin sukace kana duk suka miƙe suka fito.

Kana Bappa yazo yacewa Ummey da Dedde su fito.
Nan suka mara musu baya.

Mota ɗaya Bappa da Abboi da Arɗo Bani suka shiga.
Ummey da Dadde da Al'ameen kuwa suma mota ɗaya suka shiga.
Sauran kuma ƴan tsaronsu ne a ciki sai motar Yah Salmanu da Hafsi ƙanwar Shatu a haka suka fito daga Rugar Bani suka nufi Masarautar Joɗa.

A hankali Ummey ta jingine kanta da jikin kujera tare da dafe ƙahon zuciyarta a hankali ta furta innalillahi wa innailaihi rajiun".
Sabida tsananin tsinkewar da zuciyarta keyi Dedde kuwa hankalinta naga makiyayan dake zirya.


A nan cikin birnin Ɓadamaya a tsakiyar Masarautar Joɗa kuwa.

Gaba ɗaya su Umaymah suna falon Shatu.
Aunty Rahma ce da su Sara a kitchin, Aunty Juwairiyya tana part ɗinta da Hibba.

Junainah da Ishma kuwa suna kitchen tare da Aunty Rahma.
Kowa sabgar gabansa keyi.
A hankali Shatu ta miƙe ta nufi ƙofar falon Sheykh da sallama a bakinta.

Shiru ba kowa a falon tray'n breakfast ɗinshi shida Haroon ta ajiye bisa Dinning table.
Ganin ba kowane yasa ta turo kanta cikin bedroom ɗin.

Shiru ba kowa a hankali ta ƙara so ciki tana cewa.
"Salam Yah Sheykh". Ƙofar bathroom ta matso a hankali ta tura ba kowa a ciki komai yana kimtse tsab-tsab.
"Toh ina yaje kuma yau Lahadi kuma ai babu inda zaije".
Shiru tayi tare da juyowa ta matso tsakiyar ɗakin jujjuya kanta tayi ba mutun ba alaman mutun a ɗaki.
Har ta juya zata fita, sai kuma tayi sauri ta juyo tazo bakin gadonshi, abun data hanƙo ƙasan pillow'nshi ne yasa ta sunkuyowa da sauri hannunta tasa ta zaronshi.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Ta faɗa jiki na rawa tare da sakin fuskar robar da Sheykh ake amfani da ita a matsayin Jahan.
Da sauri ta juyo da nufin zata fita, sabida tsoron daya rufeta.
Sai kuma tayi sauri taja da baya tare da zare idanunta dai-dai lokacin da ta iso jikin marfin wodurob ɗin sa
Wanda yayi dai-dai da lokacin da Sheykh ya turo marfi ya fito.
A gigice take jujjuya kai tare da zaro ido.
Sai kuma ta juya da sauri ta kalli fuskarnar da ƙarfi ta buɗe baki tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun Yah Sheykh".
Da sauri yasa hannunshi ya kamo nata ya fizgota jikinshi cikin haɗe fuskarsu wuri ɗaya yace.
"Na'am Aysha please kada kiyi ihu tsaya nitsu nine Muhammad Jabeer Yah Sheykh mijinki Abu Afreen".
Cikin yanayi kaɗuwa tace.
"Yah Sheykh kai mutum ne ko al'jan".
Da sauri ya kamo hannunta suka iso gaba durowar.
Buɗe ƙofar yayi, kana a hankali yasa hannunshin ya ture, al'kyabbas ɗin shi dake jere a hanga a saƙale, sai ga wani ƙofa mai kamar glass.
A hankali yace.
"Aysha nitsu ki jini kinji ko".
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Toh".
Kanshi ya gyaɗa kana a hankali yace.
"Kinga wannan wurin ko?".
Da sauri tace.
"Eh naga kamar ƙofa ne".
Jawota yayi suka ɗan matso hannunshi yasa ya tura ƙofar da sauri tace.
"Lahh".
Sabida ganin wata ƴar siririyar hanya mai tsawo.
A hankali yace.
"Ni mutum ne Aish yanayin tsarin masararutar Joɗa ne yasa dole nake amfani da wasu ababen.
Kinga wanan hanyar har cikin bedroom ɗin Lamiɗo da Abba na duk akwai su.
Muna haɗuwa dasu a ɗakin Lamiɗo lokuta da dama.
In kina so anjima zan nuna miki, dan yanzu Lamiɗo ya rufe ƙofarsa ne da yanzu zamuje".
Da sauri tace.
"Me kukeyi a ɓoyen".
Jawo ƙofar yayi ya rufe kana a hankali yace.
"Ina wani aikine Aish Kuma aikin sirrine, tsawon shekaru inayi babu wanda ya sani sai Lamiɗo da Abba na da Umaymah sai yau kuma da kika zama ta uku".
Ya ƙarashe mgnar yana jawota suka zauna bakin gado.
A hankali ta sauƙe numfashi ido ta zuba mishi a hankali tace.
"Kai SS ne ko Yah Sheykh?".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ba'a faɗa kiyi shiru kada wani yaji kinji ko sirri ne Boɗɗo na".
Murmushi mai cike da jijjina tayi mishi.
Shi kuwa ruggume ta yayi ya koma baya ya kwanta.

Dai-dai lokacin kuwa motar Salmanu dake gaban motocin su Abboi ta kusa kai cikin matsarautar Joɗa bayan an wangale musu gate.

Wani irin rumtse ido da ƙarfi Ummey tayi tare dasa kanta bisa guiwowinta sabida wani irin masifeffen tsarawa da kanta yayi da azaban ƙarfi.

Kai tsaye bakin part ɗin su Sheykh Salmanu ya nufa dasu sai dai Motar Abboi da sauran duk a can baya bakin fada suka tsaya inda Bappa ya nuna musu.

Yadda suke ƙara kusanto Part ɗin su haka sarawa da bugun zuciyar da Ummey keyi yake ƙaruwa.

A can cikin falon Shatu ma, da sauri Umaymah da Mamma Suka kalli juna sabida masifar bugawa da ƙirazansu sukayi.

Sheykh kuwa da ƙarfi ya ruggume Shatu sabida ji yayi tamkar zuciyarsa zata faso ƙirjinsa ta fito woje.
Jalal da ke Part ɗin Yah Jafar da sauri ya rumtse idanunshi shida Yah Jafar ɗin.

Hakama Jamil dake tare dasu Gaini.

A hankali motocin sukayi parking.
Ummey kuwa wani irin ƙara rumtse idanunta tayi da masifan karfi.
Dedde kuwa a hankali ta buɗe ƙofar.
Ta sako ƙafarsa cikin shigarta ta al'farma.

Shi kuwa Al'ameen da sauri ya zagayo ya buɗe wa Ummey kofar tare da cewa.
"Ummey mun iso bismillah".
Cikin tsananin danne sarawar da kanta keyi ta ɗago jajayen idanunta a hankali ta zuro ƙafafuwan woje.

Ras ras Din dab din dab haka zuciyarta ta bada wasu tagwayen bugu.
Da sauri tasa hannunta ta dafe ƙirjinta.
Dedde kuwa a hankali ta zagayo inda take.
Shi kuwa Al'ameen a hankali yace.
"Bismillah ku shiga ga ƙofar".
A hankali Dedde tace to kana ta nufi ƙofar.
Ita kuwa Ummey cikin rawan jiki ta ɗaga ƙafarta ta dama ta ɗaura kan barandar tare da ƙara dafe ƙirjinta da rumtse idanunta sabida jujjuyawan da kanta ya fara.
Shi kuwa Al'ameeen bayansu yabi.

Shi kuwa Salmanu a hankali ya kalli Hafsi ƙanwar Shatu dake bin Khadijah.
Cikin yin ƙasa da murya yace.
"Ko in ɗagaki ne in kaiki".
Cikin jin kunya tace.
"A a Yah Salmanu zan shiga da ƙafata".

Su Bappa kuwa Sarkin ƙofa ne yayi musu iso zuwa cikin fada.

A hankali Dedde ta kai hannunta ta kama handil ɗin ƙofar falon ta murɗa tare da turawa kana tasa ƙafarta ta dama ciki bakinta ɗauke da sallama.

Aunty Rahma dake fitowa daga kitchen Junainah na biye da ita da sauri ta ɗan juyo ta kalli Dedde tare da cewa.
"Wa alaikassalam".
Ta ƙarashe amsa sallamar tana matsowa dan ganin wani irin fitinenne kama da Dedde keyi da Shatu.

Da sauri ta juyo bayanta jin Junainah na cewa.
"Lah Oyoyo Dedde".

Dai-dai lokacin kuma Ummey ta ƙarasa shigowa ciki wanda hakan yayi dai-dai da bugawar da kanta yayi wanda saida tayi sauri sa hannunta duka y ta damƙe kanta da masifan karfi tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Da ƙarfi wanda haka yasa Dedde juyowa ta fuskanceta sanadin juyawar da Dedde tayi kuma ya bawa Aunty Rahma da Junainah damar ganin fuskar Ummey da kyau.
Wani irin sauri Junainah tayi ta nufi inda suke ganin yadda gaba ɗaya jikin Ummeynta yake karkarwa da tsuma.

Aunty Rahma kuwa cikin wani irin tsananin firgita da kaɗuwa ta zazzaro idanunta waje har kamar zasu faɗo.
Wani irin taku mai cike da firgici tayi tana matsowa gaban Ummey dake jujjuyawa tana mai-mai-ta.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil".
Wani irin matsowa kusa da ita Aunty Rahma tayi tare da buɗe baki da ƙarfi tace.
"La ha ila ha illahu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallama. Aunty Mamey!."
Ta ƙarashe kiran da azaban ƙarfi da rakaɗi.
Ummey kuwa.
Kiranta da Aunty Rahma tayi yasata ƙara gigicewa.
Karkar haka jikinta ke rawa.
Cikin wani irin gigitaccen murya Aunty Rahma ta fara rabkawa ahlinta kira.
"Umaymah! Mamma Jazlaan ga Aunty Mamey ta dawo da izinin ubangiji Jazlaan, Jafar, Jalal, Jamil, Umaymah. Kuzo ga Aunty Mamey...".
Wani irin azabebben zabura...!





Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k ne kacal zaki turo ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Normal group Kuma 300 zaki turo ta asusuna ɗin sai kuyi screenshort na Debit Alert din ku turo min ta whatsApp 09097853276.




By
*GARKUWAR FULANI*
4/6/21, 4:15 PM - &: "Aranar wata jumma da da wanna Zazzafar ƙaddara ta rufta damu shekaru goma sha uku baya."
Sai kuma ya ɗan tsakaita
tare da jan
sassayan numfashi ya gyara
zamansa tare dasa tafin hannunshi ya share hawayensa.
Yayin da gaba
ɗayansu kacokam
suka mai da hankalin su kansa,
Duk sun ƙagu suji yadda a kayi a wannan ranar da basu manceba.
Shi kuwa Yah Jafar wani numfashin yakuma.
Saukewa kana yaci gaba da cewa.
"Ranar da dare bayan anyi sallan isha'i duk muna falon Mamey dani dasu Jalal Jamil Affan da Ummi da Imran yana ɗan sheksru takwas lokacin.
Anan mukaci abinci kana muka zauna muna hira.
Kasan cewar akwai shaƙuwa mai tarin yawa tsakanin Mamey da Affan da yake tana da son yara.
Amman son Affan da banne a wurinta har su Jamil kance wa Affan na hannun daman Mamey.
Takanyi Dariya tace.
"Eh ɗin ai ya fiku nitsuwa".
Muna zaune sai hamma Mamey keyi tare da miƙa da lumshe idonta hakane yasa tace mana.
Duk ta sallamemu saida safe tanajin bacci.
Ummi tace.
To.
Still Kuma sai mukaci gaba da hira.
Da ido muka bita ganin ta miƙa cikin sanyi tace.
"Kai zanje inyi bacci wlh wani irin bacci mai nauyi nakeji yana fuzgata tamkar zan faɗi.
Ni na shiga saida safenku".
Allah ya bamu al'khairi mukace dukanmu kana ta shiga.
Tana shiga kwanta ko second uku batayi da kwanciya ba tayi bacci.
Mu kuwa muna gama hira muka watse.
To su Jalal ne ƙarshen fita ashe basu tasheta ta rufe ƙofarta ba a famintata kenan fa?".
Ya ƙare mgnar yana kallon su Jamil.
Da sauri Jamil yace.
Eh.
Cikin sanyi ya kalli su Lamiɗo kana yaci gaba da cewa.
"Ina komawa ɗaki na kira Juwairiyya muka fara hira a waya kamar kullum.
To bayan mun gama
waya da Juwairiyya
har na kwanta sai na mike na nufi
ɗakin Mamey dan
inaso nayi mata magana a kan Juwairiyya fa tasanar wa mahaifin su maganar auren mu da ita, tun da lokacin takammala
karatun ta dan haka itama ta gayawa Abba na ayi batun aurenmu dan nima tuni lokacin na gama karatuna har na fara aiki.
Kuma a kwanakin ne aka bani sarautar Galadima wanda da mijin Gimbiya Saudatu ce mai matsayin to daya rasune Lamiɗo ya maida mulkin kaina.
A zatonshi ta hakane zaisa yaranshi bazasuyi faɗa da junaba tunda bazasuce ya baiwa wane ya hana waneba.
Ni a lokacin dagani har Mamey da Jabeer da baya ƙasar ma ba son wannan mulkin mukayiba bisa dole aka bani ita.
Sai kuma ya jingina bayanshi da kujera kana yaci gaba da cewa.

Ina isa bakin kofar
Mamey natura kofar da sallama nashiga ɗakinta.

Da sauri naja natsaya nan bakin kofar.
Can na hangi Mamey na kwance.
Bisa gado tana bacci da alamun baccin mai nauyi ne.
Hajiya mama kuwa na tsaye a kanta da wata iriyar shiga da tafi kama data bokaye ko ince matsafa.
Da mamaki nake kallon
Hajia Mama dake tsaye bakin gadon sanye da wasu irin jajayen kaya tun daga samanta har ƙasa,
kanta babu ko ɗan kwali
hannunta rike da wani ƙwarya.
Tana yayyafawa Mamey
wani ruwa dake cikin ƙwaryar tare da yin wasu surutai da sukafi kama da surkullen matsafa.

"Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un, nafurta da karfi.
Da sauri nanufo in da Hajia Mama'n ke tsaye cikin ruɗani da kiɗima ina faɗin.
Meye hakan Hajia Mama? me kike mata? me kike zuba mata a jiki haka?.
Dasauri tajuyo kaina tasaka hannunta cikin ƙwaryar taɗibo ruwan tashiga watsamin tana ƙara matsoni,
kaucewa nashiga yi ina matsowa in da Mamey take kwance kamar gawa ko matsi batayi,
itako Hajia Mama masoni tarikayi tana watsamin ruwan,
Baki na buɗe da karfi sabida wani irin masifeffen suka da naji duk inda ruwan ya taɓa a jikina yanayi.
Ƙara watsomin tayi wanda yasa na ƙara kaucewa da sauri tare da buɗe baki da nufin yin ihun zafin da nakeji da kuma fargabar halin da Mamey na ke ciki.
Sai kawai naji harshena yafurta Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un,wannan kalmar narika nanawata da karfi madadin inyi ihu."

Ita kuwa Hajia Mama da sauri tajuya cikin alamun tsoron tonuwar asirinta.
dan lokacin dare baiyi nisa sosai ba misalin ƙarfe goma ne,
da gudu tafita a ɗaki dan jin yadda na kara sautin salatin da nake.


Ita kuwa Hajia Mama tana fita part ɗinta ta nufa direct bathroom ɗinta ta shiga gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi number'n bokan ta takira yana ɗagawa cikin haki da fargabar a bin da zaije ya da wo tace.
"Boka yanzu nafito daga ɗakin matarnan na samu tayi bacci kamar yadda kace, kuma na watsa mata ruwan bata farka a sai daifa wani yaganni lokacin danake yayyafa mata ruwan maganin nan babban ɗanta Galadiman Masarautar Joɗa kenan ya ganni".
Wani irin dariya irin nasu na hatsabibai bokan yayi kana yace.
"Toh daya ganki me yakeyi? me kuma yake cewa?".
cikin rawar baki da soron da ya ziyarce ta gudun kada ai kin ya ɓaci tace.
"Sunan Allah yaketa ambata salati yaketayi babu ko kakkautawa da wasu addu'o'i".
Cikin ɗan tsagaita dariyar mugayen bokan yace
"To aiki kam zaici amma dai akwai nakasu aciki, amma kada kidamu yanzu shi yaron zamu rufemasa baki zai dauwama kurma ba mgna a bakinsa bazai iya yin maganaba bazai iya furta komai ba haka zai dauwama ba mgn saidai yayi ta mai-mai-ta abinda yake cewa.
Sannan daga nan tagwayen kuma zamu haɗa ɗaya da bin mata ɗaya shaye-shaye shi kuma babban kinga zai zama kamar Mahaukaci, shi kuma wancan Jabeer ɗin na gaya miki tun yana ƙaramin akwai sihirin da wani yayi mishi kada ki damu dashi bazai taɓa yin aureba har gaban abadan ko an mishi bazai zauna da matarba, kinga kenan duk sun zama suna da matsalar da dole baza'a basu mulkiba sai dai a bawa ɗanki Affan tunda kinga shi Imran ɗan ɗaya kishiyar taki shine ƙarami kan Affan."
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Yauwa boka na gode ni dama fatana ɗana yayi mulki dan bana son mulkin ya bar ɗakina tunda dai kace min tabbas cikin yaran Habibullah ne mijin wani zai gaji kakansa sarauta.
Dariya yayi tare da cewa.
"Kada ki damu mulki na gareki da ɗanki".
Wa iyazubillah kaɗan kenan daga sharrin tsinannun shaiɗanu maƙiya Allah da Manzonsa bokaye taɓaɓɓu masu sa mai binsu ya taɓe ya gaza sauri a ranar da muminai ke sauri a bisa siraɗi.

Acan cikin ɗakin Mamey kuwa.
Sosai sautin addu'a da karatun da Jafar keyi yatsanan ta yana kankame da Mamey, wacce ke ƙwance ida nunta a rufe, har lokacin bata farka daga.
Baccin sihirin da akasa takeyi ba saboda nauyin. Baccin da suka je fata ciki.
Sheko bakinsa baya iya furta komai sai addu'o'in sai kuma hawaye da keta tsatstsafowa daga cikin ida nunsa sabida fargarba da kuma zafin da yakeji,
Abba kuwa dake can part ɗinsa da yake Part ɗin shi na natsakanin na matan nashi ne.
Yana cikin ɗakinsa dake sama.
Haka yasa yarinƙa jiyo muryar Jafar da irin addu'o'in dayake cikin kiɗima, da kajin addu'ar kasan acikin tsananin firgici da tashin hankali yake yinsa,
Wuf yamike yanufo part in Mamey kasan cewar babu wata tazara sakaninsu.
Gudu-gudu sauri-sauri ya isa.
Cikin hanzari yatura kofar bedroom ɗin Mamey cikin sananin tashin hankali da kaɗuwa ganin yadda Yah Jafar ke rungume da Mamey sai innalillahi yake da karfi hawaye yagama wanke fuskarsa idanunsa sun yi jazir saboda kuka da zafin da yakeji da fargabar ganin tamkar Mamey a mace take a kiɗime yanufo in da suke yana faɗin.
"Subahanallahi kai Jafar meya farune me ya sameta?".
Yayi tambayar hankali a tashe, tare da miƙa hannu ya ɗago kan Mamey dake kan kafar Ya Jafar yashiga girgizata yana kiran sunan ta.
"Aisha! Aisha!! Ummu Jabeer!.
Gani shiru bata ko matsi sai dai tana numfashi ya tsananta firgicinsa.

Hankali a tashe yakuma kallon ya Jafar wanda keta addu'o'in babu ko kakkautawa.
Mai da kan Mamey'n yayi ya kwantar kan cinyar kafar Jafar.
Kana ya juya a kiɗime ya fita a ɗakin da sauri ya nufi sashin mahaifinsa Lamiɗo.

Shi ko ya Jafar cigaba da maimata innalillahi yakeyi yana zubda hawayen.

A can ɓangaren Hajia Mama kuwa.
fitowar ta daga ɗakinta kenan cike da jin daɗin yadda bokan ya karfafa mata guiwa tanajin daɗi a ranta yanzu komai zai tafi mata yadda take bukata zata rabu da zugar yayan Mamey da ita duk kowa ya huta, tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login