Cikin yanayin tashin hankali yaci gaba da cewa. "Me na tsare mata nida matata da ɗan cikin ta me suka tsare miki me jaririn da baima fito duniyan ba yatsare miki? da har kike ikirarin kasheshi". Wani irin numfashi mai zafi yafesar kana yamai da kansa kijin kujera yakwantar tare da lumshe idanunsa, kana ya kuma buɗewa a hankali. Kamar an sikareshi haka ya miƙe da sauri ya fara tarkata ƴan ƙananan kayyakin ai kinsa da suke baje bisa table ɗin yana gamawa. Ya fito tare da jan ƙofar Office ɗin ya rufe. A can sashin Gimbiya Aminatu kuwa. Bayan Hajiya mama suka bi da kallo cike da mamaki ganin yan da tafita a firgice, Gimbiya Saudatu kuwa ido takurawa cikin Shatu da wani irin tsananin mamaki kai tagirgiza kana itama ta jujjuya kai tanufi kofar fita. Shatu kuwa ko a jikinta saima gyara zamanta tayi suka shigaisawa da Gimbiya Aminatu kana tayi mata ya jiki. Ummi ma zaman tayi tagai sheta takuma yimata yajikin, daga nan kuma hira suka ɗan farayi. Wanda gaba ɗayansu ko wacce da abinda ke ranta. Gimbiya Aminatu da Ummi su shiru kawai sukayi suka ƙi yin wata mgna akan fita da yanayin da Hajia Mama tayi wai dan kada su nuna firgici su yasa hankalin Shatu tashi. Sun ɗan jima anan sashin nata suna ɗan hira. Cikin kula Ummi ta kalli Shatu daketa sauke hamma da lumshe ido alamun baccin ya fara cika mata ido. Dan yanzu baccin rana yazame mata wajibi idan bata yishiba bata jin daɗi jikinta, jin baccin yayi mata nauyi sosai a ido ne yasa tace. "Ummi mu tafi zanyi bacci". Da sauri Ummi tace. "Toh muje kam gashi kinata hamma". nan sukayiwa Gimbiya Aminatu sallama suka koma part ɗin su. Suna shiga kai tsaye bedroom ɗinta ta wuce. Tana shiga ta faɗa saman bed ai ko ba jimawa bacci yayi awon gaba da ita. Itama Ummi nata ɗakin ta wuce. Yah Sheykh kuwa a hankali ya dai-dai-ta parking kana yafito anitse yake ɗaga kafarsa laɓɓansa na mosawa a lamun tasbihi. Shiru falon nasu babu kowa ba motsin komai Side ɗin nasu, alamun duk suna bacci. Cikin sanyi ya juya ya nufi falon Shatu. Nan ɗinma shiru ba kowa, a hankali ya kutsa kai ya nufi Bedroom ɗin ta. A hankali ya zauna a bakin gado kusa da ita, Kwance take rigingine, bacci takeyi mai daɗi sai numfashi take sauƙewa a hankali, A hankali ya ƙara juyowa ya fuskanceta da kyau, hannunshi yasa ya ɗan jawo rigarta ya ɗan yi sama dashi. Ido ya lumshe jin wani sassayan numfashi data fesar. Alamun baccin nayi mata daɗi. Ɗaurin zaninta dake bisa ɗan cikin nata ya ɗan murza yayi ƙasa dashi. Tafin hannunshi na dama ya kife bisa fatar cikin nata. A tare suka sauƙe numfashi. A hankali ya ɗan sunkuyo cikin rauni da tarin son abinda ke cikin mata. Murya can ƙasa yace. "Ana Uhubbuk ya habibi. Ina sonka ina sonka ina tsoron abinda zai cutar min da kai da Amminka.". Shiru Shatu tayi da yanzu ta farka sai dai bata bude idanunta ba. Cikin sanyi shi kuma ya sunkuyo ya manna bakinshi kan fatar cikin nata yayi kissing nashi, kana a hankali ya fara karanto addu'o'in yana tofawa kan fatar cikin yana murzawa da tafin hannunshi. Wanda haka yasa wani bacci mai cike da salama ya kwasheta. Shi kuwa cikin sanyi yake cewa. "Yah Allah Kaine mai rayawa mai kashewa. Kaine mai badawa mai hanawa. Kaine mai jarabtan bawa da cuta kuma kaine mai bada waraka. Yah Allah dan tsarkin al'ƙur'ani da girman kujerar al'arshi da soyayyarka da Manzon Allah Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama ya Allah ka raya min wannan cikin ka inƙanta minshi ka tsare minshi ka bashi lfy ka fito min dashi duniya lfy ka al'barkaci rayuwar sa ka tsare minshi da tsarewarka shi da mahaifiyarsa". Ido ya lumshe kana ya sake mannawa cikin kiss sannan ya gyara mata konciyarta sannan ya fita ya nufi side ɗin sa. Hajia Mama ce zaune gaban. Wani mummunan mutun mai mummunan kamanni da shigar sutura, cikin murya mara daɗin amo yace. "Na gaya miki ki kiyayi cikin wannan yarinyar raba kanki da son cutar da cikin nan domin, komai zai lalace miki muddin kika taɓa cikin nan, tsohon asirin dake binne tsawon shekaru da dama zai tonu, duniya zata gano ainihin kamanninki". Cikin masifa tace. "Kai boka GILMAU ba cewa nayi ka karya min ƙwarin guiwata ba, zuwa nayi gareka dan mu nemi mafita. Kaida bakinka kace min muddin wannan shegiyar yarinyar ta haihu cikin masarautar Joɗa komai zai lalace min to kuma ta yaya zaka cemin in bar cikin jikinta ta haifeshi. Wlh bazata yiwu ba, dole in zibdashi yabi kororo ko kuma nasa Jahan ya burmamim cikin shegiyar bafullatanar dajin nan da wuƙa ya zazzago da cikin, ko kuma na hayo ƴan daba su zo su kashe min kowa na zuriyar Aisha". Wata muguwar dariya boka GILMAU ya kece da ita dariyar da tasa tsaunuka da kwazazzaɓan da wurin da kogon da suke ciki ya amsa da azaban ƙarfi wanda saida Hajia Mama ta firgita. Ido ta fara zazzarowa ganin wani irin masifeffen hayaƙi mai azabar duhu ya turniƙesu tako ina. Cikin dakiya da kafurar zuciya tace. "Yauwa kira muggan al'janunka ka gaya musu buƙatarsa suje su zuƙe min jinin waccar ja'irar yarinyar ya bare, su gaya min duk abinda sukeso zan sama musu". Da sauri ta gyara zamanta jin muryar bokar ta sauya cikin ƙarfi yace. "Kada ki damu Hajia Halima, zaki samu cikar burinki. Amman sai kin ajiye mana kuɗi kimanin Naira Miliyan ɗaya. Sannan zamuyi miki wannan aikin". Da sauri ta jawo jakar kuɗinta ta zuge rafofin kuɗin dake ciki ta juye a gabanshi wanda sunfi one million, da sauri tace. "Gasu nan ni dai a hallaka min cikin da ita mai cikin. Sannan a sabauta min Jafar ta yadda bakinsa zai bar karatun nan dan ta nan kaɗai ne zan samu nasarar binne tsohon sirri". Dariya yayi kana hayaƙin ya ɓace. Yana mai cewa. "Wannan fa faɗa ne tsakanin ƙarya da gsky tsakanin duhu da haske". Da sauri tace. "Su waye ƙaryan da duhu su waye haske?". Yana mai gaba tafiya yace. "Wanda ke riƙe da Allah da Manzonsa sune gsky kuna haske". Shiru tai ta zubawa bikin ido. Shi kuwa Boka cikin alamun canzawar murya yace. "Ni dai babu ruwana kan aikinki amman tunda baƙin mayen al'janin ya amshi aikinki ku kuka sani ina dai da tabbacin duk wanda ya riƙe ibada ko kunyi nasara a kanshi bazaiyi tasiri ba shekara nawa muna yaƙi kansu har yau mun kasa cikin galabarsu sabida su Allah suka riƙe". Da sauri tace. "Ni na gamsu". Daga nan ta miƙa ta fito, ta fara tattaki cikin dajin da ciyawi da ƙayoyi. Tafiya mai tsawo tayi kana ta fito bakin titin birji inda tabar motarta sai haki takeyi da numfarfashi dan azabar tafiyar da ta sha dan yin zalumci da muguwar zuciya da taɓewa a gajiye ta shiga cikin motar tata taja ta tafi. A ranar misalin ƙarfe goma na dare. Hajia Mama tsaye a can bayan side ɗin ta cikin bishiyoyin dake wurin da duhu. Cikin tarin bayyana ainihin tsana ziryan ta kalli Sheykh dake tsaye gabanta, cikin irin shigar Jalal. Riga da wondo ne 3 qtr rigar kuma mara hannu. Kana yasa fuskarshi ta roba wacce mutanen duniya suka sanshi da ita da sunan Jahan. kallo ɗaya zakayiwa askin kanshi zaka bashi sunan taƙadiri mugu dan yadda akayi fuskar ba annuri. Cikin tashin hankali tace. "Jahan na gama samun mafita, baƙin al'janin boka GILMAU wanda mayene ya amshi aikinna zai zuƙe jinin cikin dama ita kanta fitsarerriyar ƙauyen". Wani irin sassanyan ajiyan zuciya ya sauƙe a cikin ransa tare da yin mgnar zuci. "Ɓatacciya mai ɓataccen tunani nafi tsoron kiyi tunanin sawa Shatu guba akan bokayenki. Wanda na sani in sha, Allah. Bazasuyi nasara a kaina da ahlinna ba in sha Allah bazaki samu nasaraba dan Allah yana tare damu". A zahiri kuwa cikin sauya murya ya juyeta eh zuwa muryar ƴan daba yace. "Uhum rana dubu ta ɓarawo ko rana ɗaya kuma ta mai kaya". Da sauri tace. "To waye ɓarawon waye mai kayan?". Da sauri ya canza akalar zancen da cewa. "Yoh kece mai kayan mana tunda kece uwar gidan Habibullah, ita waccar balarabiya tazo ta aure miki miji tai ta zazzago ƴaƴa maza harda tagwaye. Kinga yanzu zamu samu nasarar kauda ahlinta, inma bokayen sunƙi yi mana aiki ko ni zan gama da wannan cikin Hajiyar mugunta". Dariyar jin daɗi tayi dan in yace mata Hajiyar mugunta tasan. Duk duniya shi ɗaya ne yasan asalin ainihin muguntarta sai bokanta. Takanji ta gamsu da kanta da ta iya sirranta muguntarta a ranta har tasa yardarta a zuƙatansu". Ganin yadda tai murmushi ne ya sashi yin ƙasa da kai tare da yin murmushin kana yace. "Toh ni zan wuce gida babyna tana jirana". Cikin gamsuwa da tasan yakan nuna mata yanada mata. To tace kana yabi can bayan bishi yoyin ita kuma ta dawo cikin Part ɗin nata. Sauri-sauri ya iso bakin Part ɗinsa, Agogon hannunsa ya kalla tuni goma ta wuce. haka yasa da sauri ya kutsa kai cikin falon. ba tare da ya cire fuskarba. Ba kowa a falon. Haka yasa da sauri ya gilma. Shatu da fitowar ta kenan daga ɗakinta cikin shirin bacci. Ta hangi gilmawar mutun amman sai taga kamar Jalal ne. Da sauri tabi bayanshi tana cewa. "Jalal lfy kuwa". Bai kulata ba, sai saurin daya ƙara, itama saurin ta ƙara dan a zatonta ko wani abune ke faruwa. Tana shiga falon shi kuma yana shiga bedroom. ya juyo da nufin rufe ƙofar ne ta hango fuskar. Da karfi ta dafe ƙirjinta tare da cewa. "Jahan". Shi kuwa Sheykh da sauri ya cire fuskar ya sata a inda yake ɓoyeta. da sauri ya zaro ɓaƙar jallabiya ya zura kan kayan jikin nashi. Kana ya nufi falon da sauri yana cewa. "Aishhhhhhhh mene". Da sauri ta juyo daga fitar da zatayi cikin tsoro tace. "Yah Sheykh Jahan". Ganin yadda jikinta ke rawa ne yasa yayi saurin ruggumota dan baison abinda zai firgitata. Cikin sama mata nitsuwa yace. "Nine Jahan ɗin ko". Da sauri tace. "Allah ya shiga ɗakinka". Kanta ya tallabo tare da cewa. "Aish nine fa, inaga idonki ke miki gizo, zo-zo-zo nan inyiwa babyna addu'a". Cikin binshi da kallon tsoro tace. "Yah Sheykh mu tafi ɗakina mu kwana a can". Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. "Toh muje can ɗin in zaki samu nitsuwa". Ya ƙarashe mgnar suna nufar ɗakinta. Bayan ya rurrufe ko inane. Ya jawota jikinshi a hankali yace. "Zan gaisa da Baby." Ido ta lumshe cikin ɗan sauran ruɗanin tace. "Uhummm". A hankali ya kwantar da ita, kana ya sunkuyo kanta rigar baccin nata ya ture sama, kana ya fara sumbatar cikin tako wanni sashi yanayi yana wasa da caɓɓullenta. Daga nan salon Ya sauya. A hankali ta fara ɗan rakin nata, tare da tureshi. Murmushi yayi kana ya jawota yace. "Taso muje muyi wonka". Cikin gajiyar daya tara mata ta narke jikinsa. Hakanne yasa ya tallabo ta, suka faɗa Bathroom. A hankali ya zare mata yar rigar jikin nata. kana yace. "To kiyi wonkan ina jiranki". Kai kawai ta gyaɗa sabida gajiya. Wonkan tayi kana ta fito. tare suka fito. Wata rigar ya bata ta saka kana ta koma ta kwanta. Shi kuwa ya shiga yayi wonka. Yana fitowa ya haura kan gadon kusa da ita ya zauna. A hankali ya jingina kanshi da jikin gado kana ya miƙe sawunshi tayi pillow dashi. Shi kuwa ture rigar yayi ya fara karanto addu'o'in yanayi yana tofawa bisa fatar cikin. A haka har tayi bacci. Kana daga bisani shima ya kwanta. A haka dai kwanaki sukayi taja. Komai na tafiya dai-dai cikinta na cikin lfy da salama bisa yardar Allah da kariyarsa al'farmar al'ƙur'ani. Sabida Sheykh ya dage da addu'a babu kama hannun yaro, bini-bini zai buɗe cikin yayi ta mata tofi a kai, kuma baya taɓa yarda ya barta ta zauna babu al'wala. Ya hanata kallo sai jin ƙira'a. Hajia Mama kuwa a ƴan kwanakin taje gidan bokanta yafi sau biyar. Har dai Abba ya fahimci fitar nata yayi yawa kuma sam yaga bata cikin nitsuwa. Batool kuwa yanzu ta gama gano komai bisa wannan dalilin ne ta tattara ta koma garinsu. Abban kuwa da gaiya yake barinta fita anguwar. Yauma zaune take gaban bokanta. "Kada ki damu ciki kam muna nan muna masa shiri. In ma bamu zibdashi ba wurin haihuwa zamu kashe uwar da ɗan ta hanyar ɓallo mata jini shi kuwa yaron mu bugi hannun mai yanke cibiya ya wuce misalin bakin gaɓa daga nan jinin zai malala duk su mutu". Cikin gamsuwa da hakan tace. "Hakanma yayi amman ni babu abinda ke samin ƙuncin duniya sama da ita da mijinta da wannan shegen cikin". "Kada ki damu ai tunda kina damu baki da matsala, ke dai tashi ki tafi kawai". Murmushi Sheykh wanda ke jin komai. bisa na'urar irin bi diddigi daya liƙa mata a zoben Daimond da ya saya mata tun shekarun baya. Alhamdulillah yanzu cikin Shatu ya cika wata bakwai cib. Yanzu ya ɗan fito ya girma dai-dai misalin cikin fari dai. Zaune suke a falon, Ummi na tubke mata sumar kanta. Ita kuwa waya takeyi da Ummeynta. Cikin tsananin jin daɗi tace. "Kai Ummey sati mai zuwa zaku dawo da gaske?". Cikin murmushin jin daɗin ba zatan da sukayi mata Ummey tace. "Sosai ma kuwa Shatu na. In Sha Allah ranar Alhamis zamu dawo da izinin ubangiji. Dan tun jiya ma, makiyayan dabbobin da Abboi ya sake ɗibarwa Bappanku sun taso. Da yake su tafiya ƙaface, kin san zasuyi. Kwana biyar a hanya kafin su isa. To munfi son sai sun isa mu kuma mu taso, tunda mu tafiyar jirgice". Wani irin tsalle mai cike da zallar jin daɗi tayi tare da juyowa ta kalli Ummi murya cike da farin ciki tace. "Alhamdulillah Ummi, su Ummey na sun kusa dawowa. Kai Alhamdulillah Wayyo Allah daɗina Junainah na zata dawo kusa dani". Murmushi mai nuna jin daɗi Ummi tayi tare da cewa. "A a kai masha ALLAH Alhamdulillah, Allah ya dawo dasu lfy". Amin Amin tace cikin jin daɗi kana ta meda hankalinta kan wayar jin Junainah na cewa. "Adda Shatu muna dawowa zanzo gidanki nida Ummeynmu, ki dafa mana abin daɗi". Cikin dariyar jin daɗi tace. "In sha Allah kuwa my Junnu sarkin kwaɗayi zan dafa miki duk abinda kikeso." Dai-dai lokacin kuma Sheykh ya shigo falon. wanda dawowarsa daga aiki kenan. Jalal da Jamil na biye dashi a baya wanda suma daga aikin suka dawo. Shi Sheykh Side ɗinsa ya wuce. Su kuwa su Jalal tsakiyar falon suka tsaya. Da sauri Shatu ta miƙe tare da yar sassarfa ta biyo bayanshi. Kamar ba mai babban ciki ba. Cikin sauri Ummi tace. "A a Shatu ki bar gudufa". Yana gab da shiga falonshi yaji Muryar Ummi na faɗin hakan. Da sauri ya juyo, ai kuwa da sassarfa ya hangota ta nufoshi. Cikin tsoro yace. "Aish me haka dan Allah ki tsaya". Ina kafin ma ya rufe baki ta isoshi ta faɗa jikinsa. Ta ruggumeshi gam-gam. Dole shima ya ruggumeta. Cikin meda numfashi da haki tace. "Yah Sheykh al'bishirinka". Cikin haɗe fuska yace. "Kafin ince goro, dan Allah Aish ki dena min gaganci da cikin nan, dan Allah ki rufa min asiri ki rainar mana shi da kulawa". Shiru yayi sabida fahimtar bata fahimtarshi, a fili zaka iya ganin zallar farin cikin dake kwance a fuskarta, kalmar al'bishirinka take ta mai-maita mishi. Dole ya ruggumota suka shiga falon zama yayi bisa kujera kana, ya zaunar da ita kan cinyarsa ido ya zuba mata tare da cewa. "Goro-goro-goro fari ƙal Aish gaya min me muka samu ne?". Cikin tsantsar farin ciki ta manna mishi kiss a goshi kana tace. "Um.. Ummee.. Ummey na da Bappa na da Junainah da Innarmu zasu dawo Rugar Bani kwannan Hamma Jabeer". Karo na forko kenan data kirashi da wannan sunan. Haka nan yaji wani irin masifeffen jin daɗi mai sa nitsuwar zuciya cikin kekkyawan murmushi yace. "Alhamdulillah Allah ya kawo mana su lfy Aish na". Da sauri tace. "Amin Amin, Hamma Jabeer. Gobe zan koma ko, sai in share mana gidan in gyara mana kafin su dawo ko". Da sauri ya zaro ido tare da cewa. "Ki koma kuma Aish rufa min asiri mana". Cikin fidda ido itama tace. "Yah Sheykh to ai zan komai haihuwa ne tunda zasu dawo. In haihu a can a kusa da Ummeyna tamin wonkan jego". Cikin yanayin gsky da gsky yace. "A'a wlh Aish babu inda zakije wani haihuwa bazan iyaba dan Allah kadama ki sake faɗar hakan. Wlh bazan iyaba. Ga Ummi zatayi miki komai Umaymah ma zata zo". Cikin tsoro tace. "To Yah Sheykh Amman ai zan je kam in sun dawo ko?". A hankali yace. "Eh wannan dai kam zakije, nima zanje in gaida Ummeymu". Da sauri tace. "To zanyi wata ɗaya a can ko?". Cikin zazzaro ido yace. "A'a Aish kiyi haƙuri wlh ko sati bazan iya barinki kiyi ba". Cikin shogoɓe fuska tace. "To dan Allah kwana nawa zanyi. Fisabilllahi fa shekara guda ban gansuba basu ganniba". Cikin nitsuwa da son sama mata nitsuwa yace. "Kada ki damu zakije kiyi kwana uku in na iya daurewa. Ammanfa sai in kina bani abun daɗi kullum har su dawo". Ya ƙarshe mgnar yana cusa kanshi cikin wuyanta. cikin farin cikin da take ji ɗin tace. "Me zai hana in bawa Hamma na kayan daɗin shi, in samu ya barni inje wurin Ummey na." Ta ƙare mgnar tana sa hannunta tana buɗa al'kyabbar jikinshi. shi kuwa Sheykh hannunshi ya tura, cikin rigarta. ya fara sarrafa caɓɓullenta. kirjin ta daɗa turo mishi sosai. ɗan sunkuyar da kansa yayi ya manna bakinsa kan caɓɓullenta. Ya fara yimata wani sahihin salo, A idonta ta rumtse tare da fidda wani irin nishi ashhyyyy, sai kuma ta dan turo kirjinta kana ta ɗaura hannunta a kansa ta cusa yasunta cikin lallausan suman kansa tana Ƙara manna kansa da kirjinta, cike da wani irin salo na musamman take yawo da yasunta cikin sumar kansa. A hankali taɗan ɗago kansa ta zare bakinsa da ke kan caɓɓullenta tamike tsaye hannunta taɗaura kan kafa ɗarsa tayi ƙasa da al'kebbar sa ta zareshi a hankali ta sunkuya ta durkusa bisa sawunta. tun daga kan faffaɗar kirjinsa take manna mishi wasu irin kyawawan kiss har zuwa kan mararsa, yayinda tasa hannunta cikin rigarsa ta ɗan ɗagashi tayi sama dashi. shiko hannun yakai yarike rigar yaɗan yi sama dashi har kan kirjinsa. cikin wani irin salo tarika kissing nashi tako ina cike da shauƙi da zallan farin cikin da take tare da shi. A sannu tarika yin kasa da hannunta, tana mai isar mishi da kekkyawan saƙonni, bisa Sheykh ɗinsa dake cike da zalama sai yana neman masauƙinsa muhalli sa. Shiko Sheykh ƙara matsowa yayi bakin kujerar. A hankali tasauke lips ɗin ta kan Sheykh harshenta manna kan lollypop ɗin a hankali cikin wani irin salo na musamman salo mai sanya wadda ake yimasa yalula duniyar taurari salon da tasan zai sashi farin ciki kuma da burinta kenan sabida ita kam yau farin cikinta bazai misaltuba. Wani irin numfarfashi mai haɗe da ƴar karamar kara yake fiddawa. Jiki na rawa yariƙo kanta da hannayen sa duka biyu yana ƙara lasa mata lollypop ɗin. Sosai tadage tana sarrafa shi da harshenta salonta ya gigita shi yasan yashi cikin wata duniya na musamman. ɓari da kemar jikinsa yake ta ko ina janyo ta yayi jikinsa gaba ɗaya yarungumeta gam-gam murya na rawa can ƙasan maƙoshi yake cewa. "Masha Allah, jazakillahu khairan Mar'atussaliha." A hankali ta gyara zamanta kan cinyarsa, tare da samar da kekkyawan kusanci a tsakaninsu. Ta tabbatar da ziyararta ta riskeshi a ba zata. Hannunsa tariƙo tajanyoshi jikinta, wani irin kyarma jikinsa keyi da tsuma miƙe sawunshi yayi da kyau. Tare da ƙarasa zare boxes sai wani karkarwa jikinsa yake yakai kololuwa wajen felling cikin tsananin bukatuwa ya masota tare da gyara zamanshi bisa kujerar da kyau. Hannunta tasa ta kamo saman kujerar. Shi kuwa Sheykh tafin hannunshi ya kife kan cikinta dake lafe a jikinta ɗan cas dashi. Cikin yanayin happy take sarrafa alaƙarsu har tsawon 15min. Shi kuwa Sheykh gaba ɗaya ya gama gigicewa. A hankali yake shafa cikin dan tsoron duk abinda zai cutar dashi yake. Ya kuma lura yau Shatu farin cikinta yasata, ƙarin ƙaimi. A hankali ya kai bakinshi kusa da kunnenta cikin daburtacciyar murya mafi rauni yace. "Hashhhhh thanks my dear Aish. Babyna fa". Tsawon lokaci kana ta narke a jikinshi cikin tarin gajiya da maida numfashi. Murmushi mai cike da jin daɗi da tarin gamsuwa yayi. Kana ya shafa fuskarta sannan ya tallabeta suka wuce bedroom ɗin sa. Shi ya fara shiga yayi wanka ita kuwa tana konce, saida ya fito ta shiga tayi tuni lokacin kuma magriba tayi. A can ƙasar Cameroon kuwa, ɓangaren su Junaina kuwa kallon Ummey tayi jin yadda take jiyo hayaniya da dariyar mutane da muryar Ummu dake cewa Shatu kada ki gudufa. Mikawa Ummey wayar tayi tana cewa. "Ummey sai dariya suke yi". karɓar wayar Ummey tayi takashe, kana ta miƙa dan yin al'wala. A ɓangaren su Shatu kuwa washe garin ranar ma tashayar da Sheykh zallar madarar daɗi dan kuwa yau kusan ita tayi tukin. Washegari Dasafe Sheykh yashirya cikin shigarsa ta al'farma yanufi General Hospital Ɓadayama wanda dama yake zuwa duk ƙarshen mako. Yau kuma saura kwana biyu su Ummey su dawo. Alhamdulillah tuni su iro sun iso da garken shanun da Appa Alhaji Abboi kenan ya sake haɗawa Bappa kama daga shanu tumaki awaki. Raƙuma da dawakai. Sai kaji da zabbi da aka sassakasu cikin kwandunan saƙar mari aka ratayesu a jikin dawakai. Alhamdulillah Arɗo Bani da Alhaji Haro da Alhaji Umaru da dai sauran daddatawan garin su, suka tarbi su iro suka nuna musu tsohon garken Bappa, nan suka sauƙa, kana suka gyara duk wani abu daya kamata su gyara. Arɗo Bani kuwa da kanshi ya turo uwargidansa Maman Ya Salmanu, da kuma matar Alhaji Haro Maman Junaidu sukazo suka buɗe gidan Bappa suka kimtsa musu komai suka share komai yayi gwanin ban sha'awa. Kana daga gidan Arɗo Bani ake kawowa su Iro abinci, in sunyi tatsa kuma sadaka suke rawaba al'majirai na cikin Shikan. Alhamdulillah a can Kamaru kuma su Ummey da Bappa da Inna amaryar Bappa da Junainah duk sun gama shirinsu. Tuni Al'ameeen ya gama musu komai na tafiya. A ɓankaren Shatu kuwa itama sai shiri take tayi, Sheikh da kansa ya gayawa Umaymah nan ita kuma ta gayawa Lamiɗo. Yau Al'hamis. Kuma yaune su Ummey zasu dawo. Sheykh ne zaune a office ɗin shi na Valli. Haka nan yaji zuciyarsa na sinkewa. Gaba ɗaya sai hankalinsa ya koma kan zantukan Hajia Mama. Ajiyan zuciya mai nauyi ya ɗan fesar, kana ya jawo wayarshi. Ɗan lallatsawa yayi kana ya karata a kunne. Shatu dake tsaye gaban dreesing mirror'n tana kimtsa kayyakin kolliyar ta, cikin yar ƙaramar jakane alamun shirin tafiya, jin wayarta na ringing yasa tasa hannu ta ɗago ganin sunan dake saman wayar. Habibi Da'iman, murmushi tayi tare da amsa wayar kana ta kara a kunne, cikin sanyi tace. "Assalamu alaikum Yah mu'allim". Sassanyan numfashin ya fesar tare da sauƙe ajiyan zuciya kana yace. "Wa alaikassalam Mar'atussaliha, kina lfy ko". Kai ta gyaɗa kamar tana gabanshi kana a hankali tace. "Lfy lau Alhamdulillah" Da sauri yace. "Baby nafa". Murmushi tayi kana tace. "Alhamdulillah Doctor duk muna lfy, sai dai muna kewarka Yah Sheykh". Cikin lumshe ido yace. "Ina nan tare daku". Cikin ta ɗan shafa kana tace. "Hamma Jabeer nifa na gama shirina". Ƴar karamar dariya yayi fahimtar duk sunan da zata kirashi dashi yanada ma'anarsa namusannan kuma ko wanne suna a gaɓar daya dace dashi take kiranshi. Takan ce mishi Doctor a duk lokacin da yake bincikar lfyarta ko kuma takejin wani abu nata na mata ciwo, to kai tsaye da Dakta take kiranshi da yaji haka kuma yasan akwai abinda zatace mishi na damunta. Kana duk sanda zata ce mishi Hamma Jabeer takanyi mgna dashi kai tsaye a matsayin Garkuwanta kuma ƴaƴanta ɗan uwa yadda da yaji haka yasan zatayi mishi mgn kan nuna shi matsayin ƴan uwansa natane ƴan uwanta nashine, kuma a kan danginshi zatayi mgn ko nata. In Kuma yaji tace mishi. Malam to yasan akan abinda ya shafi addini zatayi mishi mgn ko tambaya da dai makamantansu. In kuwa yaji Yah Sheykh to yasan fagen da ake ya lura tana jin daɗin sunan, dan takan kira sunan ne cike da shauƙi mai ratsa zuciya. A hankali yace. "To Boɗɗon Ummey ki shirya da kyau, dan nima zaki shirya min dare nan ki bani kyautar kwana ukun da zakiyi". Murmushi tayi tare da cewa. "Kai Hamma Jabeer bazan hutaba". Da sauri yace. "Zaki huta mana". Uhum kawai tace. Shi kuwa cikin nitsuwa yace. "Aysha manna wayar a jikin cikin namu ko". Da sauri tace. "Toh Malam ayi addu'ar da ni". Tayi mgnar sabida sanin addu'a zaiwa cikin. Ai kuwa tana manna wayar a cikinta ya fara addu'o'in masu ratsa jiki. Wani irin murmushi tayi tare da cewa. "Laaah Malam kaji Baby tana motsawa". Murmushi yayi shima kana yaci gaba da Addu'o'in. Saida ya ida kana sukayi sallama. Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k wanda anfi yawan posting in kunaso kiyi min TRANSFER 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa sai kiyi screenshort na Debit alert ɗin ki ki turomin 09097853276 ta whatsapp sai in saki a group akwai Normal group Kuma 300 ne kuma ta ac ɗin zaku biya in baki da halin biya ta ac ki sayi katin Mtn na ɗari uku kacal ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276. *Yahunde International airport* By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Ƙarfe huɗu dai-dai, na yamma, wasu irin motoci ne masu masifar kyau da tsaruwa. Suke kutsa kai cikin airport ɗin, wanda a ƙalla sun kai bakwai. bisa alamu duk akwai cikekken nasaba da dama, dan har can asalin wurin da jirgi yake biyu daga cikin motocin suka wuce. Kana biyar kuma suka tsaya a ainihin harabar. A hankali aka buɗe motocin. Alhaji Abboi ne ya fara fitowa. Sai Bappa kana Al'ameen da wasu matasa uku masu kama da Al'ameen sai wata kekkyawar budurwa mai kama da Shatu sak wacce take riƙe da hannun Junainah. Sai Ummey da Inna Amarya da suka fito. Bisa alamu duka, sauran rakiya sukayiwa su Bappa. Gyara tsayuwarsu sukayi dan ganin matafiya nata shiga cikin jirgi, wanda yake ɗauke da tambarin Abboi. Cikin murmushi Appa ya miƙawa Bappa hannu sukayi musabaha kana a hankali yace. "Toh Malam Babayo Allah ya maidaku lfy ya kiyaye hanya". Cikin jin daɗi Bappa yace. "Amin Amin Abboi Ubangiji ya saka maka da mafi kyawun sakamako". Cikin jin daɗin Addu'a Al'ameen da saura zaratan samarin nan sukace. "Amin ya Allah". Sai kuma sukayi shiru jin Appa na cewa. "In kun isa ka gaida min Parvina da kyau, kana aci gaba da ɓoye mata abinda mu muka fahimta, har sai lokacin da ido zaiga ido muna da kekkyawan yaƙinin duk sanda taga wasu cikin masarautar Joɗa mu samman in ya shafi ahlinta in sha Allah zata iya tuno komai na baya". Ya ƙarashe mgnar a hankali yadda ko su Al'ameen basu jiba bare su Ummey. Cikin gyaɗa kai Bappa yace. "Inama ji a jikina komai ya kusa zuwa ƙarshe da izinin ubangiji. Dan yanzu dai nasan muna komawa Shatu zata zo, to inma batazo da waniba ina zaton zata zo da mijin nata, kuma inma bata zo ɗinba idan ta haihu shine shirinmu ta sanadin haka Ummeynta zata shiga masarautar Joɗa ba tare da an zargi komaiba". Kai Appa ya gyaɗa tare da cewa. "Tabbas komai ya kusa zuwa ƙarshe". Yar Kekkyawar budurwar nan kuma mai kama da Shatu hannun Junainah ta sake ganin Bappa na miƙo mata hannu alamun tazo su tafi. Cikin sanyi Khadijah tace. "Ayyah Junainah zamuyi kewarki." Da sauri Junainah tace. "Adda Khadijah ina in Adda Shatu na ta haihu zakizo keda Dedde ko?". Kai Khadija ta jinjina tare da cewa. "In sha Allah kuwa, zanzo ki gaida min ita da kyau kinji ko my Junnu kice mata duk Ahlin Abboi muna kewarta." Da sauri tace. "To zan gaya mata, bey-bey Adda Khadijah sai kunzo". Tana faɗin haka ita da Bappa suka nufi cikin jirgi. Ita kuwa Khadijah ruggume Ummey tayi tana zubda hawaye tace. "Ummey zamuyi kewarki, dake da Junnu". Hannu Ummey tasa ta share mata hawayenta kana tace. "Nanda wata biyu dai Shatuna zata haihu zakuzo mu gana". Da sauri Ummey da Inna Amarya suka nufi cikin jirgin bayan sunyi sallama da Abboi. Basu tafiba saida sukaga tashin jirginsu. Ƙarshe biyar da rabi jirginsu ya sauƙa cikin Ɓadamaya International airport. riƙe da jakukkunan kayansu suka fito, Junainah na gaba. Tanata murmushin jin daɗi. A haka suka iso asalin inda masu taryar matafiyan suke. Yah Salmanu ku wanda shida Junaidu ne sukazo taryarsu cikin motar Yah Salmanu wanda tuni shima ya samu aikinsa, cikin Ɓadamaya an bashi gida da mota. Wani irin tsalle Junainah tayi tare da rabkawa Junaidun kira wanda ta hangoshi yanata ɗan dube-dube alamun neman ta inda suke. Jiyo muryar ta, A tare suka juyo shida Yah Salmanu. Wani irin murmushi mai cike da tarin jin daɗin Junaidu yayi tare da nufo inda suke gadan-gadan. Ita kuwa Junainah da gudu ta iso gabanshi, sai kuma ta tsaya tare da sakin murmushi bata abka jikinshi ba kamar yadda takeyi da can baya. Wani irin murmushi Yah Salmanu yayi tare da cewa. "Oyoyo My Junnu Allah sarki nesa mai raba masoya, watoma Junaidu kawai kika sani banda ni ko?". Cikin jin kunya alamun shekara ɗaya nan data ƙara cikin shekarunta yanzu ta zama yar shekaru goma sha uku hankali da nitsuwa da kunya sun fara zuwar mata, cikin jin kunya tace. "A a Yah Salmanu na ganka mana". Sai kuma ta kalli Junaidu daya karkata kai yana kallonta cikin sanyi yace. "I miss you very very sorry so much my Junainah". Cikin rufe ido tace. "I miss You to Yah Junaidu, ya jikinka ka worke ko?". Da sauri yace. "Alhamdulillah garauma kuwa". Shi kuwa Salmanu da sauri ya isa gabansu Bappa jakukkunansu ya amsa, haka yasa shima Junaidu yayi maza ya amshi na hannun Ummey tare da cewa. "Oyoyo Ummey na Bappanmu Inna Amarya sannunku da hanya". Kusan a tare sukace yauwa. "Sannu Junaidu". Sai kuma Bappa ya kallesu tare da cewa. "Masha Allah Junaidu na ya girma." Ummey kuwa Salmanu ta kalla tare da cewa. "Kai sannu Salmanu ya bayan rabuwa?". Cikin girmamawa yace. "Alhamdulillah Ummey na munata kewarku Rugar Bani gaba ɗaya". Bappa ne ya jinjina kai tare da cewa. "Muma muna cannedai Amman munata kewarku". Ɗaga nan suka nufi inda motar Salmanu take. Suna shiga suka nufi Rugar Bani. Kafin a kira mangriba dai sun isa. Anayin sallan magriba da isha'i matan Rugar Bani suka rinƙa shigowa sunayiwa su Ummey sannu da dawowa da ganin amaryarsu. Junaidu kuwa ana idar da salla ya dawo nanfa yaja Junainah gefa kaɗan cikin gidan sunata hira, tana bashi lbrin ahlin Abboi yayinda sosai yanzu faransaci ya kama bakinta. A nan masarautar Joɗa kuwa. Ana idar da sallan isha'i suna fitowa a kan hanyar komawarsu cikin gidane. Lamiɗo keyiwa Sheykh batun zuwansu Rugar Bani da Umaymah ta gaya mishi. Ɗan juyowa yayi ya kalli Lamiɗo jin yana cewa. "In Allah ya kaimu goben da safe fadawa da bayi zasuyi muku rakiya, ka kuma ɗauki Jalal da Jamil da Umminku". Cikin kwaɓe fuska yace. "Bana wani buƙatar rakiyar bayi da fadawa da hadimai. Kuma Jamil da Jalal duk yanzu bana son yawonsu na aamu suɗan fara meda hankalinsu sosai kan aiyukansu sun rage zaman gida da yawace-yawace kuma ma ni tafiyata ta sirrice, bana ma son asan Aisha bata gida bare asan inda take, sabida gsky wanna Hankakar Hajia Mama mai farin gaba bakin baya sata iyasa aje can Rugar ayi mata komai, badon dole bama bazata jeba, sabida rugar ba tsaro." Jinjina kai Lamiɗo yayi cikin gamsuwa da zancenshi yace. "Eh to wannan ma hakane ba matsala kuyi tafiyar sirrin ammanfa zakuje da Ummi". Kai ya gyaɗa alamun to daga nan sukayi sallama. Yana shiga falon ya samu ba kowa. Falonshi ya wuce a nan ya samu Shatu kwance bisa kujera. Matsawa kusa da ita yayi tare da cewa. "Ya dai Aish lfy kuwa yau ba hira ina Ummi ina Juwairiyya?". Ido ta lumshe tare da cewa. "Wlh Ummi zazzaɓin mura ke damunta". Cikin kula yace. "Assha subahanallahi tasha mgni kuwa?". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Eh tasha har tayi baccima". "Toh Allah ya sauƙa". Yace yana zare al'kyabbar jikinshi. Amin Amin. Tace tana tashi zaune. Gefenta ya zauna ganin haka ta ɗan gyara zamanta tasa mishi abinci ya fara ci. A hankali ta kalli wayarta dake gefenshi ganin ta kawo haske alamun ana kiranta. Miƙo mata wayar yayi. Junaidu tace tare da amsa kiran. Cikin dariya yace. "Adda Shatu na rigaki ganinsu yau kam gani ga Junainah na, ga Ummey ga Bappa munata hirarmu sanyin hunturu na kaɗamu ga farin wata, Adda Shatu farin cikin Rugar Bani ya dawo kamar yadda kika sani a da can baya". Cikin tsananin jin daɗi tace. "Alhamdulillah Junaidu nima in sha Allah gobe iwar haka muna tare da yardar Allah, ina my Junnu". Da sauri Junainah dake c jinsu tace. "Gani nan Addana". Murmushi tayi kana tace. "Ina Ummey na?". "Gata can cikin baƙi" Junaidun ya bata amsa. Daga nan ta katse kiran. Ta juyo da sauri ta kalli Sheykh dake cin abinci. "Alhamdulillah Hamma Jabeer su Ummey sun iso". Cikin sakin fuska yace. "Masha Allah, Alhamdulillah". Da sauri tace. "Gobe sammako zamuyi ko". Ajiye spoon ɗin hannunshi yayi sabida ya ƙoshi gyatsa yayi tare da hamdala kana a hankali yace. "Aishhhhhhhh ya za'ayi muyi sammako, kin matanta gobe jumma'a ne? Sai munyi sallan Jumma'a sai mu tafi ko? Please kada kice komai kin ji kiyi haƙuri sai munyi sallan". Cikin rashin iya masa jayaya tace. "To Allah ya kaimu Lokacin". "Amin Amin". Yace Daren ranar sosai Shatu ta sama mishi gamsuwa iya gamsuwa. Sai da komai ya lafa kuma ta narke mishi, tare da kamo hannusa ta ɗaura kan ɗan cikin nata daya tattare ya koma gefe ya bawa iyayen nashi dama. Da sauri ya tashi zaune yana sauƙe numfashin. Tafin hannunshi ya kife kan cikin. tare da fara murza wurin a hankali yana dai-dai-ta kwanciyar yaron yana mgn a hankali. "Afwan Ƴar al'barka gyara kwanciyarki ko, kada ki wahal da Amminki, yauwa yarinyar kirki, Allah ya miki al'barka ya fito dake duniya lfy ya tsareki da kariyarsa ya al'barkaci rayuwar ki ya raya mana ke bisa imani yauwa Kekkyawar jikar Mamey da Ummey". Murmushi sosai takeyi ganin yadda yake kalamai masu daɗi akan cikin a hankali tace. "Yah Sheykh bafa jinka yakeba". Murmushi yayi tare da kissing cikin kana a hankali yace. "Ita Kekkyawar mgn tana tasiri akan shuke-shuken fulawima hakama akan yaron ciki, musamman da mahaifinshi ko mahaifiyarshi, bakyajin duk sanda nake masa mgn yakanyi ta jujjuyawa". Ya ƙarashe mgnar yana lakace hancinta. Daga nan dai yaje yayi wonka haka itama. Ummi kam sosai mura yayi mata rubdugu. Washe gari ranar jumma'a kuwa, gaba ɗaya Shatu gani take lokacin baya gudu ta gama shirinta. Bayan an idar da sallan Jumma'a. Sheykh ya nufo Side ɗinsa, su Jamil na biye dashi a baya. Yana shiga ya samu Shatu a falo tana zaune gaban Ummi dake kwance bisa kujera ɓare mgni takeyi tana bata. Sara kuma nacan kitchen tanayi musu girki. Cikin sauri ya wuce falonsa jim kaɗan kuma ya fito. Da sauri ya kalli Ummi tare da cewa. "La! Ummi bar mgnin nan yanzu zamu tafi Valli dake in duba miki wani mgnin". Da sauri Shatu ta kalleshi jin yadda yake mgn kamar hankalinsa a tashe, Shi kuwa Jamil ya kalla tare da cewa. "Yi maza kaje ka kira min Baba Ado direba". Da sauri Jamil yace to kana ya juya ya fita. Jalal kuwa Dinning area ya nufa riƙe da waya a kunne yana mgn da Hibba. Ummi kuwa, to kawai tace. Shi kuwa Sheykh cikin kula da alamun sauri da gaggawa yace. "Aish zo". Da sauri ta miƙe tabi bayanshi. Suna shiga falonshi ya juyo ya ruggumeta gam-gam a jikinshi cikin sanyi yace. "I'm so sorry afwan Mar'atussaliha. Wani aikin gaggawa ya sameni a Valli Hospital, wasune sukayi hatsari. To biyu daga cikinsu sunada ciki, sun jikkata sosai dole sai anyi musu CS. Dole yanzu zan tafi can. Nasan ke kuma kin matsu mu tafi Rugar Bani, shiyasa na kira Baba Ado zai kaiki. In Kuma zakiyi hakuri sai gobe muje tare to?". Cikin sanyi da tausayawa matan tace. "A a Hamma Jabeer babu komai Baba Ado ya kaini, kaje ka taimakesu. Sabida sun fini buƙatar ka a yanzu, tunda su ransu da lfyarsu zaka taimaka da abinda ke cikinsu." Ta ƙarashe mgnar da bashi ƙarfin guiwar yin aikinshi cikin nitsuwa". Lip ɗin ta na ƙasa ya sumbata tare da cewa. "Masha Allah Mar'atussaliha, ngd Matuƙa da kekyawar fahimta. Allah ya miki al'barka in sha Allah nima zanzo". Ya ƙarashe mgnar yana zaro wasu sabbin kudin rafa-rafa ɗaurin dubu hamtsin-hamtsin guda biyu ya bata. Kana a hankali ya sunkuyo ya durƙusa ya kife guiwowinsa a ƙasa. Hannu yasa ya ture rigar jikinta sama. Dai-dai kan hudar cibijiyarta ya mannawa kiss kana ya fara kissing ɗin cikin tako ina. Ita kuwa Shatu ido kawai ta lumshe tare dasa tafin hannunta bisa kanshi. Ya daɗe yana kissing cikin da sauri-sauri, kana ya manna kunnenshi bisa cikin tare dasa hannun ya zagaye ƙugunta. A hankali ya fara karanto Ayatulkursi'u yana tofawa yana idarwa ya sake saida yakaranceta ƙafa bakwai kana yayi falaƙi 3 nasi 3 ƙulhuwa 3 ya ƙara da azubikalmatillahi har ƙarshe. Ya tofe a cikin sannan ya taso. Ya ruggumeta tare da cewa. "Allah ya kaiku lfy yasa ku samesu lfy ki gaida min Ummey da Bappa da kyau. Akwai tsarabar Junainah tana cikin motar kice ina gaisheta". Cikin sanyi tace. "Zasuji Ngd matuƙa Allah ya ƙara buɗi ya rufe asiri". Fuskarta ya shafa tare da cewa. "Amin My dear bey'. Yana faɗin haka ya juya ya fita. Itama ta binshi a baya. Da sauri Ummi ta miƙa jin yana ce mata. "Toh Ummi mu tafi". Da sauri Ummi tace. "Toh Shatu sai mun dawo". A hankali tace. "Ummi nina yanzu zan tafi Baba Ado zai kaini". Dai-dai lokacin Baba Ado da Jamil suka shigo da sallama. Ita kuwa Ummi cikin ƙarfin hali dason zuwa gidansu Shatu ta ƙiddigi zarginsu tace. "A a Sheykh ba tare zamu jeba". Kanshi ya ɗan juyo kana a hankali yace. "No Ummi kada ki damu zamuje ɗaukota yanzu dai Baba Ado zai kaita". Sai kuma ya juyo ya kalli Baba Ado a hankali yace. "Baba Ado na yarda da tuƙinka amman a ƙara kulawa kuje a hankali, tafiyar kuma ta zama ta siiri kada kowa yasan da ita kuka fita kaji ko". Cikin mutunta juna Baba Ado yace. "In sha Allah ba matsala". Daga nan yace. "Jamil fito mata da kayanta, mu mun tafi". Nan suka fita shida Ummi. Ita kuwa Jamil ya kai mata kayanta cikin motar da Baba Ado ya kawo har bakin Part ɗin su. Tana fita Jalal na binta a baya, ya rage Sarace kadai ke musu aikin abincin dare. Tana shiga motar Baba Ado yaja a bakin Part ɗin Lamiɗo suka tsaya nan ta shiga tai musu sallama kana suka fito suka tafi. Ƙarfe uku dai-dai suka isa Rugar Bani. Motar nayin parking tayi sauri ta fito. Junaidu dake fitowa gidan ne, yayi maza ya nufi inda take fuska cike da murmushi yace. "Oyoyo Adda Shatu masha". Cikin tsananin jin daɗi tace. "Oyoyo Junaidu. Yauwa isa ka shigo min da kayana". Da sauri yace to, kana ya nufi. Wurin motar inda Baba Ado ya fito mata da jakarta da kuma ɗaya jakar wacce Sheykh yayiwa Junainah tsaraba. Amsar jakukkunan yayi ya ajiye a bakin zauren kana ya dawo kusa da Baba Ado ya bashi hannun suka gaisa tare da cewa. "Ka iso mana Baba". Cikin nitsuwa Baba Ado yace. "A a ba komai yaro sauri nake zan juya so nake kafin a kira la'asar na isa gida." "Bazaka tsaya ku gaisa da Bappanmu Baba". Junaidu ya Kuma faɗa. A a ba matsala sai in munzo ɗaukarta. Dole Junaidu ya barshi yaja mota ya tafi. Shatu kuwa cikin wani irin masifeffen jin daɗi da begensu ta kutsa kanta cikin gidan tare da cewa. "Assalamu alaikum Ummey ina kike Junanaih Ina Inna Amarya". Wani irin zabura Ummey dake cikin ɗaukita tayi tare da miƙewa ta nufi waje da sauri. Junainah kuwa da fitowarta daga ban ɗaki kenan. Wani irin ihu mai cike da tsalle da jin daɗi tayi ta cilla butar hannunta can gefe. Tare da nufo Shatu a guje tana cewa. "Wayyoooooooo Allah na Adda Shatu na Ummey ga Adda Shatu na Oyoyo". Ta ƙare zancen cikin tsananin jin daɗi tare da nufo Shatu haiƙan ƙadaran. Zaro ido Ummey tayi tare da cewa. "A a fa a a Junainah kada ki faɗa jikinta zakiji mata ciwo". Sai kuma tayi shiru tare da zuba musu ido ganin itama Shatu gudun takeyi cikin ƴar sassarfa kamar ba mai cikiba. ta nufo Junainah. Wani irin ruggume juna sukayi da ƙarfi tare da cewa. "Alhamdulillah". Sai kuma ta ɗago Junainah data makaleta tafara jujjuyawa da ita. Da sauri Ummey ta nufosu tana cewa. "Na shiga uku Shatu ki sauƙeta zakiji ciwofa. Inna Amarya ma da sauri ta nufosu tana. "La hailahalillah Shatu zaku faɗifa". Junaidun da shima yanzu ya shigo da jakukkunan sai kallonsu yake yana murmushi. Ita kuwa Shatu Ummey na isosu ta sauƙe Junainah kana ta faɗa jikin Ummey ta ruggume ta gam-gam tana maida numfashi da haki take cewa. "Oyoyo Ummey na yau kam daɗi zai kasheni". Itama Ummey wani irin ruggume ta tayi cikin tsantsar jin daɗi da tsananin so. Tace. "Oyoyo Shatuna Boɗɗona mangana yar al'barka." Sai kuma tayi saurin janye jikinta jin yadda ɗan cikin yake wutsul-wutsul da sauri ta kamo hannun ta. Ita kuwa Shatu hawayen farin ciki take zubdawa. Inna Amarya kuwa taburma ta shimfiɗa musu a tsakiyar gidan. A ƙarƙashin inuwar bishiyar mango da bishiyoyin ayaba suka zagayeshi hakan ya bada daddaɗan inuwa mai sanyi. Da sauri Ummey ta ajiyeta. Ruwan sanyin da Inna Amarya ke miƙa mata ta amsa ta bata. Ba musu ta amsa ta kafa kai dan hakin da takeyi yasata jin ƙishi. Gefenta Junainah ta zauna. Ummey kuwa gabanta ta zauna Inna Amarya kuma gefenta. Junaidu kuma shigar da kayanta ɗakin Ummey yayi kana ya fito ya gaisheta sannan ya tafi. Ita kuwa Shatu a hankali ta zame ta kwanta ta ɗaura kanta bisa cinyar Ummeynta cikin sanyi tace. "Alhamdulillah yau gani ga Ummey na". Murmushi Ummey tayi kana ta shafa cikinta tare da cewa. "Shatu ki dena wasa da jikinkifa, kada kije ki tadawa kanki naƙuda lokacin ta baiba". Cikin jin ɗan kunya tace. "Toh Ummey itama ai yau tana farin cikin ganinki". Sai kuma tayi maza ta miƙa zaune. Jin muryar Bappa na cewa. "A a a masha ALLAH yau gani ga Shatu na". Cikin sauri ya iso inda suke gefenta ya zauna ita kuwa hijabinta ta gyara tana ɗan rufe cikinta alamun kunya tace. "Oyoyo Bappa na". Cike da jin daɗi yace. "Sannu Shatu na. Nanfa suka fara gaggaisawa da hirar yaushe gamo, ɗaya Bayan ɗaya haka take tambayar ahlinta wato ahlin Abboi. Su iro ma suna dawowa aka zauna ana hira. Inna Amarya kuwa da Ummey gidin murhu suka koma sunata haɗa miyar jumma'a. Junainah kuwa na liƙe da ita. Sai salla ne kawai yake ɗagasu a wurin. Sai bayan sallan isha'i kuma duk suka zauna bisa taburma suna hira suna cin abinci. Cikin nitsuwa Shatu ta juyo ta kalli Bappa dake gefe dashi dasu Iro yayinda farin wata ya haskasu ras, numfashin ta ɗan fesar tare da cewa. "Bappa na ya lbrin su Yah Giɗi na". Tayi mgnar hawaye na ciko mata ido". Cikin sanyi yace. "Wlh Shatu jikina na gaya min su Giɗi suna gab da baiyana. Dan wayewar asuban yau nayi mafarkinsu wai Mijinki ya dawo min dasu da hannunshi. In sha Allah kuwa suna kan hanya da izinin ubangiji tabbas suna hanya, muci gaba da Addu'o'in da muka sabayi". Cikin gamsuwa da jin sanyi tace. "In sha Allah kuwa." Nan sukayi ta hira maƙota nata zuwa Binto budurwar Ya Gaini tazo haka Hari. Sune basu shiga sai kusan ƙarfe sha biyu na dare. Yau ko Junainah batayi bacci ba. Suna shiga suka kwanta, Ummey na kan ɗaya gadon ita kuwa Shatu ita da Junainah suna kan ɗaya gadon. Cikin sanyi Ummey tace. "Uhumm Shatu ya mai gidan naki da mutanen gidan naku?". Dogon numfashi ta sauƙe tare da cewa. "Uhumm Alhamdulillah Ummey yana lfy yace in gaidaki shima zaizo da tarema zamuzo to sai aka kai wasu asibitinsa sunyi hatsiri". Cikin sanyi tace. "Ayyah Allah ya basu lfy". Amin tace kana a hankali ta gyara kwanciyarta tare da jawo hand bang ɗin ta hannun tasa ta fito da cakuleti masu daɗi ta miƙa Junainah da sauri ta amsa ta ɓare tasa a baki. Ita kuwa Ummey ta kalla tare da cewa. "Uhmmm mutanen gidansu kuwa masu cike da sarƙaƙiya da mugunta suna can sunata fama da muguntarsu. Kai Ummey gidajen sarauta akwai wuyan zama". Kai ta jinjina tare da cewa. "Ke dai ki dage da addu'a in sha Allah babu abinda zai sameki". Cikin gamsuwa tace. "In sha Allah kuwa, shima Yah Sheykh yana yawan mana addu'o'in". Kai Ummey ta jinjina cikin gamsuwa. Dai-dai lokacin kuma. Sheykh ne tsaye tsakiyar falonshi gaba ɗaya ya rasa me ke mishi daɗi. Tsaki ya ɗan ja, tare da cewa. "Gidan ba daɗi". Sai kuma ya zauna bisa kujera, a karo na biyar ya kuma kiranta stiil bata ɗagaba. Sabida wayar na sailent kuma tana cikin hand bang ɗin ta. Allah ya sani ta mance da batun wani suyi waya dashi. Dogon tsaki ya ɗan ja tare da cewa. "Yayi kyau Aish wato kin samu su Ummeynki ni kin mance da nima". Haka dai ya kwanta yanata jan tsaki a haka yayi bacci. Ita kuwa da Ummey kusan kwanan zaune sukayi ranar. Koda asuba sukayi salla wani hirar suka kuma buɗe wa. Harda Bappa daya shigo. Nan ta jawo jakar da Sheykh yace tsarabar Junainah ne. Tana buɗe wa daga sama ta samu wata leda cike da kayayyakin kwalam na makwaɗaita irin Junainah. Sai kuma wasu irin tsala-tsalan turame atamfa da Shadda da lashi da hijabai guda biyar-biyar iri ɗaya alamun na Ummey da Inna Amarya. Sai kuma wasu dogayen riguna masu kyau guda biyar irin na larabawa da alamun na Junainah ne sai dai zasu ɗan mata tsawo kaɗan. kana sai takalma na manya da kamar na Junainah. Sai kuma wasu irin yadin Getzner masu kyau kala biyar sai manyan al'kyabba guda biyu da alamun na Bappa ne. Sai kuma kuɗi a cikin ko wanne kaso alamun kuɗin ɗinkin ne, sai can ƙasar jakar kuma turaruka ne masu tsadar gaske da sabulai da mayukan shafawa. Ido kawai suke zuba mata. Ita kuwa cikin jin daɗi tace. "Gashi inji Yah Sheykh". Cikin jin daɗi Junainah ta fara tsalle da ribibi kan kayan zaƙin sam batama kula kayan suturun ba. Bappa da Ummey da Inna Amarya data shigo musu da karin kumallo kuwa cikin fulaku da kawaicin fulanin kwarai sukace. "Kai Shatu ya zakiyi ki barshi yayi mana irin wannan hidimar haka". Cikin sanyi tace. "Ayyah Ummey kawai kusa mana al'baka". Cikin sanyi suka haɗa bakin cewa. "Allah ya muku al'baka ya sauƙeki lfy". Amin Amin tace tana jawon akoshin ɗumamen gashesshen naman. Nan Bappa ya fita su kuma suka zauna suka fara cin abinci. Ranar ma dai haka suka wuni hira, sam ko ta kan wayarta bata biba. Yauma kamar daren jiya haka sunata hira. A ɗaki duk da kusan sha ɗaya ne. Sheykh kuwa a hankali ya fito falo inda Ummi da Juwairiyya suke zaune dan Juwairiyya ta shigo dubata Ummi da jiki a haka nan a hankali yace. "Ummi gidan shiru ba daɗi". Da sauri Juwairiyya ta kalleshi tare da son gimtse dariyarta. Kana a hankali tace. "Ai fa kam gidan ba daɗi fa Sheykh". Kanshi ya ɗan jinjina kana yace. "Ummi ki shirya gobe zamuje Rugar Bani". Cikin jin daɗi Ummi tace. "To Allah ya kaimu". Amin Amin yace yana mai juyawa ya koma falonshi yana maici gaba da kiran Shatu. Dai-dai lokacin kuwa Shatu kwance take gefen Ummey cikin kula Ummey ta kalli cikin nata tare da cewa. "Ya kai wata nawa Shatu?". Ido ta ɗan lumshe tare da cewa. "Bakwai". Kai ta gyaɗa cikin gamsuwa tare da cewa. "Masha Allah, zan haɗa miki mgnin zaƙi ki fara sha yana sauƙaƙa naƙuda". Cikin gamsuwa tace. "Toh Ummey na". Sai kuma tasa hannunta ta jawo hand bang ɗin ta ganin haske da sauri ta fito da wayarta. Cikin juya ƙwayar idanunta ta amsa kiran tare da karawa a kunne a hankali tace. "Assalamu alaikum". Wani irin sassanyan numfashi ya fesar tare da cewa. "Wa alaikassalam yah Aishhhhhhhh". A hankali ta ɗan juya ta kalli Ummey tare da yin ƙasa da murya tace. "Ina wuni". Cikin narke fuska yace. "Aish nayi fushi dake". Da sauri tace. "Na tuba". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Wato kin samu su Junainah kin mance dani ko? Kin barni da kewa gaba ɗaya gidan ba daɗi". "Murmushi tayi tare da cewa. "Junainah ce take shagaltar dani". Da sauri yace. "Okay to ki shirya gobe da wuri zamu zo ɗaukari". A hankali tace. "A a dai kam Hamma". Kauda zancen yayi da cewa. "Ya Baby na tana Lfy ko". "Alhamdulillah tana lfy". "Masha Allah". Yace kana sukaci gaba da hira Daga bisani sukayi sallama. Ita harda Allah gani take zai barta tayi koda mako ɗaya ne. Koda ta juyo taga tuni Ummey da Junainah sunyi bacci. Shi kuwa Sheykh a hankali ya miƙe ya nufi Bedroom yana mmkin tsawon lokacin da sukayi suna hira. Allah ya sani bai taɓa zato da tunanin shaƙuwarsu ta kai hakaba saida bata kusa dashi. Washe gari bayan anyi sallan la'asar. Suna fitowa suka nufi Part ɗin Sheykhhhh. Suna shiga abincin rana sukaci kana suka fito cikin shiri suka shiga mota. Jalal ke tuƙi Sheykh na gefensa. Jamil kuwa na baya kusa dasu. Ummey kuwa tana can baya sit ɗin ƙarshe. Waya takeyi da Umaymah tana sanarmata cewa gasu nan kan hanya. Ƙarfe huɗu da kwata dai-dai suna bakin ƙofar gidan Bappa. A hankali sukayi parking cikin nitsuwa Sheykh ya buɗe marfin gefensa kana ya zira ƙafarsa ta dama ya fito. Da sauri Bappa ya miƙe tsaye ganin Sheykh. Hakama Junaidu. Shima Sheykh da sauri ya nufi Bappa Jamil da Jalal na biye dashi a baya. Ummi kuwa yanzu ta buɗe marfin motar ta fito. Ciken girmamawa Sheykh ya miƙawa Bappa hannu tare da ɗan rusunawa. Cike da mutumtaka Bappa ya bashi hannun fuska cike da fara yace. "A a a a masha ALLAH maraba lale marhabin da baƙin kirki kai sannunku da zuwa". Sai kuma ya kalli Jamil da Jalal da suke gasheshi yayinda Junaidu kuwa ya rusuna yana gaida Sheykh. Cikin tsananin karramawa Bappa ya juya yace. "Maraba lale kushi go ku shigo daga ciki." Cikin sanyi Sheykh yace. "Bappa nanma yayi ai". Da sauri ya jujjuya kai tare da cewa. "A a Muhammadu kada muyi haka da kai maza ku shigo ciki, ai nanma gidane". Yana faɗin haka ya juya yayi cikin gida. Dole tasa Sheykh ya bisa a baya. Kana Jalal da Jamil na biye dashi. Ummi kuwa na biye da bayansu. Haka nan sukeji suna mararin shiga cikin gida. Yayinda gaba ɗaya zuciyarsu ke bugawa da sauri-sauri. A hankali Sheykh ya sako ƙafarsa ta dama cikin gidan dai-dai lokacin kuma ya yayi ido biyu da....! By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Ya hango Shatu tsaye a gaban randunansu. Tana cikin shigar asalin fulani, riga da zanin, rigar guntuwa sai dai tasa wata a cikin red color mai dogon hannun yayinda yadin rigar da zanin kuma fari ne an ƙawatasu da kolliyar zanen ɗawosu, da zaren ulu red, blue and yellow, sosai cikinta ya baiyana. Ya fito ras Cikin da mamaki take kallonshi. Shi kuwa Sheykh ido ya lumshe tare da sauƙe sassayan numfashi, sabida tayi masifar mishi kyau Especially kitson kumbo bobini da akayi mata asalin kitsonmu na Fulani kenen. Murmushi tayi ganin wani irin mayataccen kallo mai cike da bege, shauƙi, kewa, so, kauna, tare da zallan fileeng mai kashe sasasan jiki. Ita kuwa kai ta ɗan ɗago ta kalli bayanshi hango Jalal da Jamil ne yasata. Faɗaɗa murmushin ta tare da cewa. "Lale marhaɓin da Hassan da Hussaini." Bappa kuwa bai kula da ita bama sai yanzu da tayi mgn, Dan sauri ya nufi ƙogar ɗakinshi yana ce musu. "Kai kunsha hanya kam, masha ALLAH ku iso ku iso." Haka yasa suke biye dashi a baya. Ita kuwa Shatu da sauri ta nufo bakin ƙofar zauren nasu sabida hango Ummi da tayi cikin tsanani jin daɗi tace. "Lah oyoyo Ummina," Ta ƙarashe mgnar cikin jin daɗi da isowa gaban Ummi ta ruggume ta. Shi kuwa Sheykh juyowa yayi ya ɗan kalleta tare da kwaɓe fuskarsa ya tura baki ya mata alamun. "Wato ni baki ganni bako". Harshenta ta ɗan zaro mishi ta gefe. Kanshi ya juyo da sauri ya kalli gabanshi jin ya ɗan bugi kanshi jikin rumfar Bappa. Cikin kula Bappa ya shimfiɗa musu babbar taburma, kana ya ware wani ɗan carpet a kam taburmar cike da kulawa yace. "Bismillah ku zauna". To sukace kana duk suka zauna. Ita kuwa Ummi cikin jin daɗi tace. "Oyoyo Shatu na, munyi kewarki". Cikin dariya ta ɗan janye jikinta, kana tace. "Ummi mu isa ciki". Sai kuma ta juyo da sauri tana cewa. "Inna Amarya! Inna Amarya gasu Ummi na sun zo". Da sauri Inna Amarya dake Kitchen tana gasa musu yan shilan tattabarun. Ta fito tare da cewa. "A maraba lale marhabin". Sai kuma tayi maza ta nufi ɗakin Ummi inda suma Shatu nan suka nufa. Cikin sakin fuska tace "Ummi shigo ɗakin Ummeyna". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh Shatun Ummey da Ummi". Dariya Inna Amarya tayi tare da cewa. "A lallai kam Shatun Ummey da Ummi fa". "Sannu da zuwa Ummi". Inna Amarya ta faɗa tare da juyawa har taje bakin ƙofar kuma sai ta juyo tace. "Shatu taho ki kai musu ruwa". Da sauri itama Shatu ta miƙa tabi bayanta. Shiru Ummi tayi bayan sun fita, tana mai bin ɗakin da kallo komai a kimtse yake ras. Babu hargitsi ko ƙura duk da jeren kayan dake da yawa. Ajiyan zuciya ta sauƙe mai ƙarfi tare da cewa. "Toh ina Ummeynta ɗin, naji wannan dai Inna Amarya ta kirata". Su kuwa Shatu kai tsaye kitchin ɗin suka koma, Da sauri Inna Amarya ta jawo kwaryan kindar tare dasa maburgi a ciki, ta fara burgashi tana cewa. "Yauwa Shatu miƙo min ƙwaryar zumar nan". Da sauri tace to, kana ta miƙa mata. Tsulala zumar tayi a ciki, ta burgeshi da kyau. Kana ta rabashi biyu, sannan ta jawo akoshin data saka furar data gama kirɓawa yanzu. Ta ɗauki ludayin damu ta fara damawa da sauri. Sai kuma ta kalli Shatu data jera ƴan ƙananan ƙore guda huɗu bisa tray'n fefeyin saƙa, damun ta fara zubawa cikin ƙoren kana tace. "Yauwa Shatu dauki akoshin nan ki haɗa musu da gashin tattabarun naki. To tace kana ta jawo ƙaramin akoshin tasa na Ummi kana nasun kuma ta barshi a ciki, ta rufe da fefeyin sai tururin da ƙamshin gashin tukunyar ƙasa yake da ƙamshin man shanu. Bayan sun gama kimtsa komai ne. Inna Amarya ta ɗauki na Ummi ƙaramar kwarya da damun kidar dai mai binshi zallan nonon da zuma, kana sai akoshin mai ɗauke da gasassun tattabarun. Ita kuwa Shatu akan fefeyin ta jera ƙoro Ukun ta rufe da fefeyin ɗaya babba kama ta jera kananan ƙoren uku masu zallar nono da zuma suma ta rufesu da fefeyi ɗaya, Kana ta ɗauka akoshin gashin a sama ta rufe sannan ta jera ludayeyin suma masu kyau da kwalli a saman fefeyin. Ta ɗauka ta nufi bakin ƙofar ɗakin Bappa inda suke gaisawa. A hankali tace. "Assalamu alaikum". Da sauri Sheykh ya juyo ya kalleta, ido ya zuba mata cike da bege. Bappa da Jamil ne suka amsa mata. A hankali ta zare takalmanta kana ta hau bisa taburmar, gefenshi ta ɗan tsuguna ta ajiye tray'n. Tare da kallon Jalal daketa kallon tsakiyar gidan yana murmushi da yanayin tsarin gidajen gargajin suna burgeshi. Jamil ne ya ɗan gyara zamanshi tare da cewa. "Ina wuni Adda Shatu". Cikin kula tace. "Lfy lau Alhamdulillah Jamil ya gida ya Gimbiya Aminatu da Abba da Lamiɗo da Galadima da Aunty Juwairiyya suna lfy ko". Jalal ne ya ɗan juyi cikin ɗan sakin fuska yace. "Alhamdulillah suna lfy, Lamiɗo yace mu gaidaka". Ya ƙarashe mgnar yana kallon Bappa. "Ina amsawa kuwa ngd matuƙa". Bappa ya bashi amsa. Ita kuwa juyawa tayi ta ɗan kalli Yah Sheykh a hankali tace. "Barka da yamma". Cikin sassauƙar murya yace. "Barka dai ya gida, ina Junainah?". Cikin jin daɗin kular da yake kan Junainah tace. "Yanzu nan ba jimawa suka fita unguwa ita da Ummey na". Fuska ya ɗan tsuke tare da cewa. "To amma meyasa baki cewa Junainah ina zuwaba nasan da zata bar zuwa unguwar". Cikin tura baki tace. "Toh ai ni banyi zaton zakuzo ɗinba". Bappa ne ya amshi zancen da cewa. "Ai kuwa itama Ummmeynkun da ta sani bazata fitaba". A hankali Shatu tace. "Ai magani taje amso min a Rugar Gebi, shine ita kuma Junainah tace sai ta bita. Amman bazasu daɗe ba". Jamil ne ya ɗan gyara zamanshi tare da cewa. "Toh ai sai mu ɗan jirasu ko?". Da sauri Shatu tace. "Yauwa ku jirasun". Ta ƙare zancen tana turo tray'n tsakiyarsu kana ta kalli Jalal tare da cewa. "Ga Kidar da gashi mai ɗumi". Kai Jalal ya jinjina dan ya gamsu da tsabtan mutanen gidan". Ganin hakane yasa Bappa ya miƙa ya basu wuri, yana mai cewa. "Sheykh kusha tsala". Kai Sheykh ya jinjina bayan Bappa ya fita ya ɗan kalli Jalal da Jamil da tuni suka jawo ƙoren bayan sun sauƙe akoshen gashin. Ido ya zuwa Jamil ganin yadda ya lumshe idonshi lokacin da ya kai damun nan bakinshi, sai kuma ya kalli Jalal da ya matso gaban akoshin tare dasa hannunshi ya jawo ƴar ƙaramar butar Bappa dake wurin ya wonke hannunshi kana ya yago naman mai haɗe da robon man shanu, yasa a baki ido ya lumshe tare da taunawa kana ya haɗiye. Cikin sauƙe dogon numfashi yace. "Yah Sheykh kaci wlh yayi daɗi sosai. Murmushi Sheykh yayi tare da cewa. "Aish dubo waiji kisa musu kada su faɗi". Dariya mai ɗan sauti tayi kana tace. "Kaima in kaci sai kayi santi". Idonshi ya ɗan zuba mata kana a hankali yace. "A a aini abinci ɗaya nakeci inyi santi, kuma ba banishi zakiyi ba dan rowa". Ya ƙarashe mgnar yana mata nuni da idonshi cewa. "Kece". Da sauri ta kauda kanta tare da cewa. "To kaci dai". Ƙoryar zallan nonon da zumar ya jawo kana yace. "Toh kije ki shirya kafin mu gama sha ko". Da sauri tace. "Wai tare zamu tafine?". Juyowa yayi ya fuskanceta da kyau kana yace. "Ai babu wai, in sha Allah yau a masarautar Joɗa zaki kwana". Cikin sanyi tace. "Ayyah dan Al...". Da sauri yace. "Please dan Allah kada ki haɗani da Allah ki cuceni ki sani yin abinda bana so, Please je kiyi shiri kinji ko Aish dan Allah". Cikin sanyi tace. "Toh zamu jira Ummey ta dawo ko". Kanshi ya ɗan sunkuyar tare da cewa. "Zuwa ƙarfe biyar da rabi zamu jira". Cikin sanyi tace. "In sha Allah ma kafin nan ma, zata dawo". Kai ya gyaɗa mata kawai ta juya ta tafi. Inna Amarya ta samu zaune da Ummi suna ɗan taɓa hira Ummi na shan nono. Gefensu ta zauna, kana ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi kunzo Ummey na bata nan". Cikin kula tace. "Eh yanzu Inna Amarya ke gaya min, ai zamu ɗan jirata". Da sauri tace yauwa. Nan sukaci gaba da hira. Bappa kuwa suna gama cin abinci yazo ya musu jagora cikin gida suka gaisa da Inna Amarya kana ya musu jagora har ƙofar gidan Arɗo Bani. Nan suka zauna anata gaisawa. Cikin kula Arɗo Bani yace. "Mun gode sosai da ɗawainiya Sheykh Allah ya ƙara rufa asiri". Amin Amin yace. Kana Alhaji Haro da Umaru suma sukayi godiyar, dan Bappa dasu ya raba yadukan Getzner da Shatu ta kawo mishi, al'kyabbar kuwa ya barwa kansa. Nan sukayi ta hira har biyar da minti ashirin. Kana Bappa yace. "Muje gida ko wata ƙil sun dawo". To sukace kana suka miƙe sukabi bayanshi. A gida kuwa, Ummi ce ta ɗan kalli Shatu tare da cewa. "Shatu da kin kimtsa kayanki ai kinga magriba tana ƙara towa, kuma nasan bazamuyi salla a nanba". Cikin yanayin sanyi tace. "Ɗazu da safe Ummey tamin wonkin kayana duk suna cikin jaka ma." Kai ta gyaɗa tare da cewa Inna Amarya. "Anya kuwa ba kwana zasuyi a canba". Da sauri tace. "A a wlh da wuya su kwana sai dai garin da nisane." Dai-dai lokacin Bappa ya shigo tare da cewa. "Shatu fito ku tafi dare yanayi". Jiki a mace tace. "Bappa bazamu jira Ummeyna ba". Kai ya jujjuya kana a hankali yace. "A a kuje kawai ba komai Shatu nida kaina zan kawo miki mgnin naga kamar Sheykh ɗin hankalinsa yayi gida". Kai Ummi ta gyaɗa cikin takaicin rashin ganin Ummey tace. "Eh dole hankalinshi zai koma can da yake shike limancin masallacin. Kuma ina sha Allah ni da kaina zanzo amsar mata mgnin". Da haka dai suka bawa Shatu ƙarfin guiwa suka taho. Ita da Ummi a baya, Sheykh da Jamil a gaba Jalal a tsakiya. Ana kiran sallan magriba suna isa bakin Part ɗin su. Da sauri Sheykh ya fito ya buɗe gidan ya shiga, dan yin al'wala. Kana suma suka shigo. Jalal da Jamil kuwa sukayi side ɗin su. Ummi na idar da salla ta miƙe da niyar shiga kitchen kenan Sara ta shigo da Foodflaks wanda Gimbiya Aminatu tasa aka shirya musu abinci. Suna dawowa sallan isha'i sukaci kowa ya nufi makoncinsa. Shi kuwa Sheykh yana shiga wonka yayi kana yayi shirin bacci. Shiru-shiru baiga Shatu ta shigoba, haka yasa ya miƙe ya fito falo, a hankali ya tsaya bayanta. Ganin ta zaune da alamun waya takeyi da Ummeynta, cikin sanyi tace. "Ayyah Ummey na, baki dawoba har muka tafi hankalina ya tashi gashi dare yayi kuma baku dawo ba." Murmushi mai kwantar da hankali Ummey tayi kana tace. "Wlh kuwa Shatu na kuna fita, ina isowa, nama hango bayan motarku". Sosai shima yaji abinda Ummeynta ta faɗa sabida kanshi da ya sunkuyar ya manna da wuyanta. Cikin sanyi tace. "Ayyah UMMEY NA ina Junainah". "Gata nan tayi bacci, tun ɗazu wai yau gidan shiru ba daɗi tunda bakya nan". Ummey ta bata amsa. Da sauri tace. "Ayyah ƴar uwata. To Ummey ya batun mgnin nawa kuma?". "Bappanki yace zai kawo miki". Ta bata amsa tana konciya. Daga nan dai sukayi saida safe. Hannunshi yasa ya juyota ya ruggumeta tsam a jikinshi a hankali yace. "I miss u so much my dear". Cikin yin ƙasa da murya tace. "Miss u to". Wuyanta ya ɗan sunsuna tare da jawota sukayi cikin bedroom. A hankali ya kwanta kana ya jawota jikinshi, hannunshi yasa ya zuge igiyoyin dake ƙasar gaban rigarta murya can ƙasa yace. "Wai maganin menene Ummey ta haɗa mana". Cikin fidda numfashi jin yadda ya kife tafin hannunshi kan Caɓɓulenta tace. "Wai maganin zaƙine zan zubdashi". Da sauri ya zaro ido tare da cewa. "Na shiga aljanna da izinin ubangiji. maganin zubda zaƙi kuma Boɗɗona bama na ƙara mana zaƙiba". Cikin jujjuya ido tare da dariyar kalmar shi ta na Shiga aljanna da izinin ubangiji tace. "A a zaƙifa na naƙuda, wai zai sauƙaƙawa mutun wahalar naƙuda". Ajiyan zuciya yayi tare da jawota jikinshi, ya haɗe bakinsu wuri ɗaya, wani irin hott kiss mai cike da bege yake mata. Daga nan suka narkewa juna. Washe gari da safe Gimbiya Aminatu da kanta tazo har Side ɗinsu tai mata sannu da dawowa da tambayar mutanen gida. Hakama Aunty Juwairiyya da Mom. Yau kwananta uku da dawowa. Junaidu da kanshi ya kawo maganin nata sai dai kai tsaye Valli Hospital ya kai mgnin ya bawa Sheykh. Inda kuma nan ya bashi takardunshi ma na neman ci gaban karatun jami'a. Sosai suke shan hira da Junaidun. Shida kanshi ya ɗauke shi a motarsa zuwa tasha, inda zai shiga motar Shikan. A cikin motar ne ya ɗan kalli Junaidun tare da cewa. "Junaidu ai da kazo mana da Junainah". Murmushi Junaidun yayi tare da cewa. "Malam ai bata sanma zan zoba, sabida in ta sani zatace muzo tare, kuma yanzu nafi son ta meda hankali kan karatunta, kaga dama ta rasa shekara ɗaya tafiyarsu Cameroon". Kai ya ɗan jinjina kana yace. "Zan roƙi Bappa ya bamu ita ai, sai in sauya mata makaranta". Cikin kwaɓe fuska Junaidu yace. "Uhumm Yah Sheykh ai kuwa ni ina tsoro". Da sauri yace. "Tsoron me?". Kai ya ɗan kauda ganin sun iso tashan, a hankali yace. "Kada ka dawo da ita birni tai nesa dani ta manceni wani ɗan sarakuna yayi wuf da ita". Murmushi mai yalwa Sheykh yayi kana a hankali yace. "Astagafirullaha". Sai kuma yace. "A a in sha Allah zan ajiye maka ita, kuma ai kaima yanzu zaka dawo nan cikin birnin". Murmushi yayi kana ya buɗe motar ya fita. Kiranshi yayi ya zagayo ta inda yake, sannan ya bashi kuɗi. Godiya yayi kana ya tafi, shima yaja mota ya tafi yana mai jin son Junaidun a ransa. Dan shine ya sanar dashi komai kan Ba'ana da ɓatansu Yah Gaini. Da wulaƙancin da Ɓachamawa ke musu, sai dai iya abin ya sani kawai ya sanar masa. Daga nan gidan Malam Abubakar ya wuce. Bayan sun gaisa ne, yake ce mishi. "Alhamdulillah Malam batun Sulaiman komai zaiyi sauƙi dan yanzu ina neman zama na musamman ne da shugaban SS da kuma shugabsn hukumar ƴan sanda na ƙasa. In sha Allah gsky zatayi aikinta". Cikin jin daɗi, Malam Abubakar yace. "Kai Alhamdulillah Sheykh Allah yayi maka al'barka ya rufa maka asiri duniya da ƙiyama". Amin Amin yace kana sukayi sallama da juna. Shine bai shigo gidaba sai bayan sallan isha'i. hannunshi riƙe da ledan magungunan da aka haɗawa Shatu wanda na zaƙine kuma yana sauƙaƙa naguɗa da izinin ubangiji. (Ganyen bishiyar Ceɗiya, Dirim, Ganyen Barma Gada ban san sunanshi da Hausa ba, sai kuma zobo. Sai cikinki ya kai wata bakwai zaki tafa sasu sai ki rinƙa shan ruwan, da zaran cikinki ya shiga wata takwas sai ki bari. Sai randa duk kikaga alamun naƙuda sai kiyi maza ki tafa kiyi ta shansa da ɗuminsa, da izinin ubangiji wlh wani kafin ma mgnin ya tafasa da yardar ubangijin sammai da ƙassai zaki haihu lfy. Yana sauƙaƙa nakuɗa sosai. Ki haifo ɗanki lfy ƙato kuma jazir kamar ɗan larabawa da izinin ubangiji) A hankali ya shigo cikin falon inda take zaune Ummi na gefenta. Gefenta ya zauna tare da miƙa mata ledar. Hannu tasa ta amsa tare da cewa. "Ngd matuƙa Allah ya rufa asiri". Cikin jin daɗi yawan addu'ar da take masa in ya bata abu koda bata san komai bane yace. "Amin Amin". "Na menene?." Ta tambayeshi a taƙaice. cikinta ya ɗan kalla tare da cewa. "Magungunan da Ummey ta amso miki ne". Cikin sauri tace. "Bappa yazo ne". Kai ya jujjuya mata alamar a a. "To kaine kaje". Cikin wasa ya gyaɗa mata kai alamar eh. Baki ta ɗan turo gaba tare da cewa. "Shine ko kaje dani Hamma Jabeer". Murmushi yayi yana miƙewa tsaye yace. "To banine najeba Junaidu ne ya kawo minshi har Valli". Cikin fidda numfashi Ummi tace. "Niko da har ina cewa gobe Jamil zai kaini mu amso". Yana mai nufar ɗakinsa yace. "Ato Junaidu ya hutasshe mu". Daga nan ya tafi, ita kuwa Ummi amsar mgnanin tayi taje kitchin rabashi biyu tayi ta tafasa mata rabi ta tace mata shi, ta tasa mata a ɗan madaidaicin bokatin roba mai marfi ta rufe, ta kawo mata. Kana ta ƙulle saura kuma. Daga ranar ta fara sha. Alhamdulillah komai na tafiya dai-dai yanzu cikin Shatu yayi watanni takwas cib, duk bayan sati biyu zai ɗauketa suje Valli Hospital ayimata awu su dawo gida. A hankali komai ke tafiya yanzu cikin ya shiga wata na tara. Yau asabar ne ba aiki shiyasa yake hutu in banda zuwa Masallaci ba abinda ke fiddashi. A hankali ta shigo riƙe da tray'n abincinsa. Da sauri ya tashi tsaye, maƙale da waya a kunnenshi bisa alamu da Umaymah yake mgn. Ajiye tray'n yayi tare da jawo hannunta bisa kujera 3 str suka zauna. Matsawa can ƙarshen kujerar yayi, kana ya sunkuyo ƙasa hannunshi yasa ya ɗago sawunta da yanzu sun fara ɗan kumbura, kan cinyarsa ya ɗora sawun nata. A hankali yasa kafaɗarshi ya maƙale wayar da yakeyi kana a hankali yasa yatsunshi ya ɗan fara mammatse mata sawun. Cikin nitsuwa ya ɗan kalleta kana a hankali yace. "Uhum gata nan ma. Umaymah gashi naga yanzu ƙafafun nata sun kumbura sosai mafa, bataji saitayi ta zama bisa kuje ƙafar a ƙasa." Cikin kula Umaymah tace. "Amman dai ba wata matsalar ko?". Da sauri yace. "A a ba komai tana lfy baby ma na lfy". hannunshi yasa ya gyara mata konciyarta, ganin ta mirgina ta konta. "Yaushe ne EDD'nta?". Umaymah ta tsmbayeshi Cikin nitsuwa yace. "Saura mako uku". murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Alhamdulillah kaga kuwa su Mamma da Aunty Rahma ma suna gab da zuwa dan jikin Jadda dake yawan tashin masa yace, yana buƙatar ganinmu baki ɗayanmu to zasu zo nanda sati ukun, amman banda yaransu". Cikin nitsuwa yace. "Uhumm tsohonan da tsoroba so yake ya ruɗar mana daku yana komai kamar mai barin wasiyya, ni tun zuwanmu auren Haroon sai wani cewa yake ko bayan ransa kaza da kaza zaiyi kaza, to ni dai fatana Allah yasa Mamey na ta ƙara haɗa ido dashi kafin ya tafi". Ya ƙarashe mgnar cike da rauni da kuma ƴar raha. Cikin rauni Umaymah tace. "Kaci gidanku ai kaima Abbanka zai tafi". Numfashin ya ɗan sauƙe still ysnayiwa sawunta tausa. Saida suka gama waya da Umaymah ya yunƙura zai ajiye wayar kenan. Wani kiran ya shigo wayarshi yana ɗaga yaga DSS. da sauri ya amsa tare da cewa. "Hello sir barka da dare". Yaƙi in sallama sabida sanin kafurune bisa lfyn. "Barka dai Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa." Murmushi yayi jin oganshi a fagen aiki ya kirasa da cikekken sunansa. A hankali yace. "Sir barka da dare". Cikin hausar arnataku yace. "Kai Sheykh, kai da yan uwan Sulaiman kun hanamu bacci da yawan Addu'o'in kuna gigitamu da addu'a dole mu fito da shiko". Cikin dariya da kekyawar mu'amala yace. "Sir ba dole muyi ta Addu'o'in ba, tunda bamu da kowa sai Allah da Manzonsa bamu da mai bi mana bayan gskyr masu gskyar da ake tozartawa. Ya zamuyi sai mu haɗaka da Allah". Cikin dariya shugaban hukumar binciken ƙasa na sirri yace. "Gsky to ku barni inyi bacci, kuzo ayi mgnar belinshi, nayi mgn da wanda case ɗin yake hannunsa. Yace shima duk sanda zai bacci sai yaga Sulaiman da wasu yara sunata kuka, suna salla da addu'a kuma da zai sa a duba hakan za'a samesu. Ni kuwa kwarjin Sulaiman na min yawa ko naje da niyar bincikarsa sai inji ban gamsu cewa shi mai sayan kayan sata bane". Wani irin sassanyan numfashi ya sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah to yanzu wacce rana zamuzo ayi mgnar belin". Cikin sauri yace. "Next to weeks". Da sauri yace. "Allah ya kaimu". Daga nan sukayi sallama. Addu'a'u saifulmumini kenan Gashi suda kansu sun nemesu. Nan take ya kira malam Abubakar ya sanar mishi komai. Bayan sati ɗaya, wanda ya kama saura kwanaki ne cikin Shatu ya cika wata tara. Kuma Alhamdulillah komai na tafiya dai-dai. A hankali suke tafiya lokacin da suka fito wurin awun. A nitse suka miƙe ɗan corridor'n har cikin Office ɗin shi. Bisa tattausar kujerar dake gefe ta zauna tare da sauƙe numfashi tace. "Gsky Yah Sheykh yanzu kam fa na fara jin nauyin cikin nan, in zan ɗaga kafata sai inji ya tokareni". Goron ruwan faro mara sanyin daya ɗauko ya miƙa mata, tare da cewa. "Eh dole kiji haka yanzu tunda cikin yayi ƙasa. Alamun haihuwa yau ko gobe ake cewa ko?". Rufe goran tayi bayan tasha mai yawa kana a hankali tace. "Uhummm ni naƙuda kawai nake tsoro in badon shiba ni Ko yauma in haihu mana kawai in huta". Sunkuyowa ya ɗanyi yayi kissing goshinta a hankali yace. "La, la, la kada ki damu ke kam Aish na ƙudarma ni zan miki kinji" Yayi mgnar cikin wasa da kwantar mata da hankali. Da sauri tace. "Allah yasa haka". Amin Amin yace cikin murmushin. Sai kuma ya fara tattare ƴan abubuwa shi dan zasu wuce gida. Yana gamawa suka fita suka tafi. Yau asabar Sheykh ne zaune gaban Malam Abubakar da Lamiɗo da Galadima dan Malam Abubakar ɗin ne yazo har gida a nitse Sheykh yace. "Toh Alhamdulillah Malam in Allah ya kaimu gobe. Ƙannen maman Sulaiman Ya Adam da Ashiru su shirya suje. Abuja su kai kuɗin beli kamar yadda suka faɗa. Naso inje to kuma abubuwa sun min yawa." Cikin gamsuwa ya gyaɗa kai kana a hankali yace. "Sai dai kuɗin belin ne wuyar 3 million da sukace". Kai Sheykh ya ɗan ɗago tare da cewa. "Eh ba damuwa na turawa Ashiru kuɗin a accutan ɗinsa in suje su cire suje musu da kash". Cikin jin daɗi Malam Abubakar yace. "Kai Alhamdulillah Muhammad Allah yayi maka al'barka Ngd matuƙa". Amin Amin sukace kana sukaci gaba da wata hirarsun. Alhamdulillah kuwa su Ashirun sunje lfya ranar Monday sun bada belin Sulaiman sun dawo lfy yan uwan shi mata kamar zasu mutu dan farin ciki. Cikin Shatu kuwa gaba ɗaya ya sauƙo yayi ƙasa a hasashen likitoci sauran kwana takwas ta haihu. Yau ta kasance ranar jumma'a ne. Tunda safe Sheykh yayi shirin jumma'a'arsa. Da sauri ya fito falonshi sai baza ƙamshi yakeyi. Wani tattausan yadine a jikinsa lemon green mai masifar kyau yasha aiki da farin surfani. Gariyar tayi cas da jikinsa. farin hula mai ratsin lemon green ya kafa bisa tattausan gashin kansa. sai takalminsa sau ciki shima lemon green. Da sauri ya ɗan ja da baya ganin ya kusa yayi karo da Aish ɗinsa da cikinta da ya fito sosai yayi kuma ƙasa sosai in ka ganta har kamar ta ɗan rame. Cikin kula tace. "Hamma Jabeer fita zakayi ne?". Motsota yayi a hankali ya ɗan ruggumota kana yasa hannunshi ya ɗan shafi cikin a hankali yace. "Eh fita zanyi Aish ina son inje gidan Malam Abubakar dan mu gana da Sulaiman tunda ya dawo shekaran jiya ban samu mun naje na masa jajeba". Cikin fidda sassanyan numfashi tace. "To zaka dawone kafin azahar". Kai ya jujjuya alamar a a. Manna kanta tayi da ƙirjinsa kana a hankali tace. "Toh kuma zanje makaranta fa, zan shiga aji daga ƙarfe sha ɗaya zuwa ƙarfe ɗaya zamu gama takardun da suka rage mana". Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa. "Wannan makaranta ni dai tana cimin rai". Cikin sanyi tace. "Toh ai ma mun kusa samun hutu yau last page ɗin ezam ɗin zamuyi". Kai ya ɗan sunkuyar ya manna hancinsa a wuyanta a hankali yace. "Toh yanzu muje in kaiki da kaina in na sauƙeki sai in wuce gidan malam kuna tashi inzo in ɗaukiki in dawo dake, nasan kafin nan kuma lokacin salla yayi." To tace kana taje ta shirya. Ta zurma ƙaton hijabi. Haka kuwa akayi yana sauƙeta saida ya tabbatar ta shiga aji lfy kana, ya juya ya nufi gidan. Malam Abubakar. A falonshi ya sameshi zaune shida Sulaiman. Da sauri Sulaiman ya tasa ya nufi inda yake. Cikin yanayi sabo da shaƙuwa suka ruggume juna. Murya na rawa Sulaiman yace. "Sheykh ngd ngd Ngd matuƙa Allah ya saka da al'khairi ya rufa asiri duniya da ƙiyama ya ceceka da wahalar siraɗi kamar yadda ka zama sanadin cetoni daga azabar hukumar ƴan sanda da na faɗa ciki". Amin Amin yace cike da tausayin ganin yadda Sulaiman ya rame yayi duhu farin shin nan duk ya tafi. Ga alamun tashin hankali da firgicin da basu gama sakeshi ba. A hankali suka zauna gaban Malam Abubakar da yaketa sanya musu al'baka a duniya bai taɓayin ɗaliban da yake so da ƙauna sama dasu ba. Cikin kula Sheykh ya ɗan rusunar da kai tare da cewa. "Barka da hantsi malam". "Barka dai Muhammad, ya iyalin taka da ƴan tagwaye da Jafar". "Alhamdulillah duk suna lfy sai dai Yah Jafar yanzu kusan wata uku kenan, yake yawan yin bacci dare da rana safe da yamma, salla da cin abinci kaɗai ke tada shi. Ni kaina wasu lokutan sai inyi kusan kwana biyar ban ganshi ba, sai in nine naje Side ɗinsa". Murmushi mai sanyi Malam Abubakar yayi tare da cewa. "Uhummm Alhamdulillah waraka na bisa hanya, ai bacci ga irin mai larurarsa alamun sauƙi ne". Cikin jin daɗi yace "Allah yasa haka". Amin Amin sukace. Kana ya kalli Sulaiman cikin kula yace. "Sannu Sulaiman Allah ya kiyaye gaba ya taƙaita, ya sauƙaƙa mana ƙadda rorinmu, dani da kai dama sauran al'ummar musulmi baki ɗaya." Cikin rauni murya na rawa hawaye na kwaranya, Sulaiman ya ɗago kanshi tare da son danne shessheƙan kukan da yake taso masa yace. "Tabbas wannan yana ɗaya daga cikin manyan ƙaddarorina masu zafi a rayuwata, na kuma samu tsira da kuɓuta cikin sauƙi, kasan cewar inda masu damar yin mgn aji. Amman tunda na dawo Jabeer ban bar yin kukan bayin Allah'n da na bari a tsare a can magarƙamar. Ina kuka har inji numfarfashi na yana fizga, tunda na fito na barsu ban sake samun nayi bacciba. Inajin tausayin kaina, inji tausayinsu, nayi ta kuka dana dawo da naga halin ƙunci da iyayena da yan uwana suka shiga. Ina tuno su kuma wanne hali iyayensu da ƴan uwansu suke ciki." Sosai kukansa ya tsananta cikin tsananin kukan da yasa. Malam Abubakar zubda hawaye Sheykh kuwa sai taune lip ɗinsa na ƙasa yayi cikin tausayin waɗanda Sulaiman yake mgn a kansu koda bai sansuba. Shi kuwa Sulaiman murya na rawa yace. "Yara ƙanana sun sadaukar da rayuwarsu domin tawa sun amsa laifin da ba nasuba domin ni in tsira. Ko wani hali iyayensu ke ciki, kuma dukansu uwarsu ɗaya ubansu ɗaya". Cikin rauni Sheykh yace. "Me sukayi ne Sulaiman?". Cikin wani irin shessheƙan kuka mai ciwo da rauni da tausayawa yace. "Wanna itace tambayar da kullum sukeyiwa haukumar dake tsare damu kullum in sun shigo suna dukansu suna azabtar dasu tammaya ɗaya sukeyi mushi nee. "Wai me mukayi ne aka kawowu nan kuke ta dukanmu ku gaya mana laifinmu". Zuwa yanzu hawaye sosai Malam Abubakar yake zubdawa. Sheykh kuwa tausayi da rauni sun adaddabi zuciyarshi hawaye musu masifar zafi ke tsastsafo mishi. Cikin rauni yace. "To Sulaiman sun gaya maka ya kayi aka kaisu can ne?". Kai ya fara jujjuyawa yana kuka murya a disashe kamar mace yace. "Sunce suma basu san me sukayi ba, kawai suna kiwo sun shiga suyi al'wala akazo akayi ta kamasu ɗaya bayan ɗaya, daga nan aka rufe musu ido, su dai sunji an kwana tafiya dasu a wannan ranar da asuba aka iso dasu wannan magarƙamar. Ƙaramin cikinsu kullum yakanyi ta kuka yana kiran iyayensu". Da sauri Sheykh yace. "To amman meyasa aka tsaresu kuma su kansu basu san laifinsu ba anya ba karya sukeyi ba ko dai criminals ne, kasan suna da taurin zuciya". Da sauri Sulaiman yace. "Wlh wlh su ba criminals bane, tunda na gani a gaban idona akayi musu sharri kuma akasa suka yarda dashi dole, amman sun yarda dashi ne dan su tseretar dani". Da sauri Sheykh yace. "Kamar yaya akayi musu sharri?". Hannu yasa ya share hawayensa murya na rawa yaci gaba da cewa. "Tun randa aka kaini wannan magarƙamar nayi matuƙar mamkin ganin waɗannan yaran, yarane ƴaƴan Fulani masu tarin kyau da farin fata, saidai yanayin wahalar da ake gana musu kullum tasa sun rame sunyi baƙi. Mafi akasarin kwanaki sai an daukesu hotuna ana tirsasu amsa laifinsu. Ni da yake ko muntsilina ba'ayi wlh ana dukan yaran nan ina kuka, da fari na fahimci ko isasshiyar Hausa basaji tabbacin fulanine kamar dai yadda duniya takewa Fulani kuɗin goro ga duk wanda aka ji ya iya fillanci ko yana kiwo to ya zama ba fulatani, so nima kai tsaye nai zaton fulanine kuma sai akayi dace hakan ne. Kullum ana dukansu ina kuka. Idan an tafi sai manya biyun su taru kan karamin cikinsu, suyita mishi tofi dan shi irin mutanen nan ne da basa jurar wahala lokuta da dama yana sumewa in an dakeshi sai daga baya ya farfaɗo, sukanyi ta kuka ina tayasu. Daga nan muka fara sabawa, ina mamakin rauninsu kan iyaye da yar uwarsu mace da kullum suke tunota nakan ruggume karamin inyi ta kuka dan yana tuna min yarana. A haka dai har ranar wata jumma'a nace musu dan Allah zan tambayesu me sukayi aka kawosu nan. To anane sukayi ta rantse min da Allah suna cewa wlh tallahi su basu san me sukayi ba, kawai an kamosu daga wurin kiwone aka kawosu nan, Babban cikinsu ya ƙara da cemin. "Yanzu shekararmu ɗaya a nan harda watanni, kullum in an zo an dakemu da dare akan dawo ace mana mu amsa cewa mu yan kinnafin ne, sukance mu yarda kawai cewa mu yan kinnafin ne za'a dena dukanmu, mu kuwa bamu ma san menene hakan ba sai daga baya muka fahimci masu sace mutane suce a basu kuɗine ƴan kinnafin ɗin. Yace min wlh tallahi summa tallahi mu ko gyadar gonon wani bamu taɓa sacewa mu bawa dabbobin bama, bare mu sace mutane ta yaya zamu yarda da laifin da bamuyi ba. Har ace muyi bayani a saka a gidajen tv da Radio, to nima a ranar na basu lbrin abinda ya kawoni nan ga mamakina sai sukayi ta kuka wai sun tausaya min gwara su basa da yara sai iyaye." Cikin rauni Sulaiman ya ɗan tsagaita kana ya ɗago kanshi ya kalli Sheykh da sai yanzu hawayenshi suka samu zubowa. Cikin kukan yaci gaba da cewa. "Inda na tabbatar da cewa, sharri akeyi musu basu san komaiba. Saida aka fara batun belina. Randa aka kai kuɗin sukazo sukace an kawo belina amman ba kuɗinane zai fiddani ba. Dole sai an samu wanda za'a liƙa sharrin sune suke kawo min kayan satan ina saya ta hakane za'a nunawa duniya an kama ainihin masu satan shiyasa ni za'a sakeni. Hankalina ya tashi ina zan samo wasu ayi musu sharri a banza tunda asalin waɗanda suka saida min saraƙunan can dai sun gudu su kansu hukuma sun kasa kamosu. Cikin tashin hankali nace. "Musu ni kam babu wanda zan nuna ince shike kawo min kayan sata ina saya. Sai suka cemin to asheko zanci gaba da tabbata a cikin magarƙamar babu belin. Ga mamaki na, sai yaran nan sukace. To su sun amince in nunasu su, da dai ace su masu satan mutanene gwara satan sarƙa kuma zasu samu a dena dukansu dan haka gwara su yarda su ɓarayin sarƙane, sabida su dai basu san darajar gold ba, basu kuma san saraƙunan matar gwamna bane. Haka yasa nace musu a a ni kam bazan iyaba bazan bari a ɓata musu sunanba." Hawayensa ya share tare da cewa. "Sai babban cikinsu ya matsoni cikin rauni yace. Kada mu zauna damu da kai duk mu ƙare rayuwarmu a nan. Mu dai bamu da gatan kowa a duniya sai Allah da iyayenmu, kuma mu yanzu iyayenmu su sadakar dan zasuyi tunanin kashemu akayi. Kuma mu bamu da yara, kai kuma kana da mata da yara da ƙanne da yayu waɗanda kaine gatansu. Mun amince zamuce duk abinda sukeso a fidda kai. In ka fita in ka samu dama ka nunawa duniya halin da muke ciki, kasa makusantanka su samu a Addu'o'insu tabbas munsan watan wata rana gsky zatayi aikinta, mu mun ɗaukeka matsayin ɗan uwanmu." Sai kuma ya kife kansa a jikin kujera yaci gaba da kuka yana mai cewa. "Yana gaya min haka ƙanne shi ma suka matsoni sukace su sun san tasu ta ƙare a ciki amma zasu tsaretar dani. A haka a gabana inaji ina gani aka fitar dasu woje, aka jera bindigogi da makamai da kuɗaɗen a gabansu, kana aka dasa musu camera bayan an gaya musu abinda zasuce. Anan ake tambayarsu ku su wayene. Cikin bushewar zuciya ganin sharrin da akeyi musu ido na ganin ido sukace. "Mu ƴan kinnafin ne". Kana aka sake cewa. "Ku wanne yarene?". Sukace. "Mu fulanine". Wlh sai gashi wanda suke ciki kusa dani suna dariya suna cewa. "Shegu fulanin dole sai mun koreku a kasar nan mun hanaku jin daɗi mun ɓata muku sunan ƙabilar shugaban ƙasar namu hegen bafullatani". Hankalina ya tashi dana gane wai ashe duk anayin hakane dan a ɓata sunan fulanin a dozarta ƙabilar shugaban ƙasar to amma. Alhamdulillah tun daga ranar aka dena dukansu da wahal dusu". Wani nannauyan numfashi suka sauƙe gaba ɗayansu suna masu zubda hawaye. Cikin rauni Sulaiman yace. "To tashin hankali na yaune za'a haska video da kayiwa yaran a nuna duniya cewa sune ɓarayin mutane". Tofa wannan al'amari yayi masifar tada hankalin Sheykh yayi kukan da shi kanshi bai san yaushe rabonsa da yinsa ba. Ganin ƙarfe ɗaya ta wuce ne yasa ya sharce hawayensa, murya a disashe yace. "Zan tafi Malam, amman in sha Allah zan meda hankali na kan batun yaran nan, in Allah ya yarda zan sasu cikin addu'o'i na. Zan kuma roƙi duk limamen masallacin jumma'a su sasu a addu'a." Cikin tsananin jin daɗi Sulaiman da Malam sukace. "Allah ya yarda ya bamu sa'a, ya tsaresu al'farmar Annabi da al'ƙur'ani ya fito dasu lfy". Amin Amin yace kana ya sallamesu ya tafi. Daga nan kai tsaye makarantar su Shatu ya wuce ya ɗaukota. Ta lura yana cikin tashin hankali kuma duk jikinsa a mace. To amma ganin lokacin salla yayi ne yasa batayi mishi mgn ba. Suna dawowa ta shiga ɗakin ta, shi kuwa al'wala yayi ya fita. Bayan an idar da salla kuma wurin Lamiɗo ya shiga ya mishi duk bayanin da Sulaiman yayi mishi. Wannan ne yasa baiyi baccin tsakanin azahar da la'asar ba. Kiran salla ne ya medasu masallaci. Ita kuwa Shatu koda ta shiga wonka tayi kana tayi salla, akan sallayar ta miƙe, dan ta gaji. Ummi kuwa jin motsinta ne yasa taje ta kai mata abinci. To nanma da kyar taci kaɗan kana ta koma ta konta. Itama Ummi ta koma ɗakinta. Saida tayi sallan la'asar ne ta fito ta nufi kitchen ita da Sara. Ita kuwa Shatu cikin ɗan jin sauƙin gajiyar ta miƙe doguwar riga ta zura kana ta fito, falonta. Har kamar zata wuce babban falonsu kuma sai taji ƙafarta ta riƙe wanda yafi wata da fara mata hakan. A hankali ta ja ƙafar ta isa gaban kayan kallon, hannu tasa ta kunna TV inda ta samu tashar BTV a kunne anayin zabi sonka. A hankali ta koma baya ta zauna bisa kujera 3 str, tana fuskantar tv murmushi tayi tare da cewa. "Oh ikon Allah ashe har yanzu anayin zaɓi sonka". Zama tayi tanajin ana gaishe-gaishe bayan minti biyar asa waƙa tayi minti biyar a cireta. Ƙarfe biyar dai-dai aka gama shirin. Shi kuwa Sheykh ana idar da sallan la'asar ya nufi gida, tafiya yakeyi cikin yanayin tsantsar dauriya da danne tsananin halin da yake ciki. Sabida wani irin masifeffen sarawa da ƙugunsa yake har sai yaji ƙahon zuciyarshi ya bada sautin ras-ras wata iriyar fitinenneyar zuface mai azabar zafi ce ta keto mishi tana tsastsafo mishi tako wani hudan gashin jikinsa. Da sauri ya tura ƙofar falon ya shiga. Ba kowa sai wulgawar Ummi daya hango ta shiga kitchen. Yah Jafar kuwa gidanshi ya nufa. Jalal kuwa yau kwana ukuma kenan baya gida. Jamil kuwa tun safe daya tafi wurin aiki bai dawoba. Wani irin azabebben karkarwa jikin shi ya farayi da tsuma sabida azabar ciwon da bai taɓa jin makamancinsa ba. "La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama". Haka yake maimaita kalmar shahadar sabida jin tamkar ciwon zai ɗauke ransa. So yake ya zaro wayarshi ya kira, Shatu ko Umaymah ko Abbanshi ko Lamiɗo ya gaza wani irin raunine ya rufeshi wanda yasa hawaye fara kwaranyo mishi, cikin zuciyarsa yake tunanin shike nan zai rasu ba tare da burinshi ya cikaba zai tafi matarsa bata haifuba zai bar ɗansa maraya. Zai bar su Jalal cikin makirin masarauta. Wani irin rumtse idanunshi yayi da azaban ƙarfi tare da taune lip ɗinsa na ƙasa. Kar-kar haka jikinsa ke karkarwar. Babu abinda yake cewa sai maimaita kalmar shahada, wani irin jujjuya kai yayi ya tafi luuu ya...! Ita kuwa Shatu, a hankali ta sunkuyar da kanta ta ɗaura hannunta bisa cikinta. Tana jin yadda ɗan cikin ke jujjuyawa. Da sauri ta ɗago kanta ta zubawa tv Ido, jin ɗan jaridar na cewa. To masu kallo barkanmu da war haka yau dai gamu tare da SP Daniel tare da rahoton ƴan kinnafin ƴan bindiga daɗi, daga babbar het kotansu na babban birnin tarayya, zaku kalli video ƴan kinnafin ɗin kana muji ƙarin bayani daga SP Daniel Ido ta zubawa allon tv lokacin da aka fara haske makaman dake jere gabansu Yah Giɗi Seyo Gaini da wasu matasan fulani waɗanda aka kamo kamar yadda aka kamosu. Ana cikin nuna makaman, ana jefa musu tambaya. "Wato wannan shine makaman da kuke amfani dasu a matsayin ku na masu GARKUWA da mutane?". Dai-dai lokacin kuma ake haska camerar kan fuskar Yah Gaini wanda duk sauyin da zai samu a duniya bazata gaza ganeshi ba. Ana ƙarasa haska fuskarshi da fuskar Yah Seyo da Giɗi. Tayi wani irin yunƙura da azaban ƙarfi zuciyarta kuwa tayi wani irin azabebben tsinkewa da masifan karfi. Wani irin azabebben juyi ɗan cikinta, yayi gaba ɗaya jikinta karkarwa ya farayi kamar wacce aka jonawa wutar lantarki. Wani irin rumtse idanunta tayi da ƙarfi tare damke cikinta, ta buɗe bakinta da azabar firgita da karfi ta kurma wani irin azabebben kuka mai haɗe da ihu da kiran sunan. "Yah Giɗi Seyo Gaini wlh ƙaryane. Sherri akeyi maku innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil wayyoooooooo Bappa wayyoooooooo Ummey na Yah Sheykhhhhhhhhhhhhh...! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 zaku tura ta Account 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na Debit alert ɗin ki turo shaidar biyanki ta whatsApp 09097853276 ƴan 300 ku in baki da damar biya ta Account ku sayi katin Mtn na ɗari uku kacal ku copy numbers ɗin ku turo min ta whatsApp 09097853276. Banbancin special Group da Normal group q yawan posting ne. Special Group su yanzu muna gab da ƙare littafin da izinin ubangiji. By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Ina masoya na 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ina masoyan littafin GARKUWA ? To ku marmatso kusa don ina da babban albishir a gare ku. Hazikar marubuciyar nan Mai suna RUKAIYA IBRAHIM GAWATA marubuciyar littafin " *Cikar buri na* " ta zo muku da wani littafin mai suna "ZURI'A BIYU". Zuri'a biyu ya zo da sabon salo mai ban mamaki da daukan hankalin Mai karatu, littafi ne da yake kunshe da fadakarwa, tunatarwa ilmantarwa, tare da nishadantarwa. "ZURI'A BIYU" sunan littafin na GAWATAN GARKUWA Kada Ku bari a baku labari....🤝🏻🥰😘 "Yah Sheykhhhh". Ta ƙira sunansa da ƙarfi da kuma karaji. Wani irin juyowa Ummi dake kitchin tayi da sauri cike da tsaro ta nufi falon nasu cikin ruɗani da gudu. Shi kuwa Sheykh jin muryarta da yadda ta zurma ihu da rakaji, yayi dai-dai da lokacin da yaji wani irin masifeffen azaban sarawa da ƙugunsa yayi, tare da harabar jijiyar bayanshi. Dai-dai lokacin Ummi kuma ta isa falon Shatu, da gudu ta ƙara sa gabanta, ita kuwa Shatu dai-dai lokacin ta kuma yin wani irin ƙara tare da sa hannunta duka biyu ta dafe bayanta, "La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam". Ta faɗa cikin wani irin masifeffen azaban sarawar da gugunta ya fara da ƙarfi naƙudar ta baro jikin Sheykh ta dawo gareta gadan-gadan. Cikin tsananin tashin hankali Ummi ta iso gareta, Ruggume ta tayi a jikinta ganin yadda take karkarwa, wani irin masifeffen zufa mai tsananin zafi ya keto mata tako wani hudan gashin jikinta. Cikin tsananin kiɗima Ummi ta fara kiciniyar zaunar da ita, jin yadda ta ƙaƙƙandare ne, yasa Ummi cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun. Sheykh! Sheykh!! Sheykh!!!". Ta ƙarashe kiran sunansa murya a hargitse. Shi kuwa Sheykh wani irin ajiyan zuciya mai azaɓan ƙarfin da nauyi ya sake. "Bismillah". Ya furta da ƙarfi tare da yunƙura ya miƙe tsaye jin lokacin ɗaya gaba ɗaya ciwon da yakeji ya sakeshi, tamkar a zare zirin gashi cikin man shanu. Cikin tsananin tsuma da tashin hankali ya nufi, falon sabida jin yadda Ummi ke auna mishi kira babu ƙaƙƙautawa. Yana shiga falon. Kuma dai-dai lokacin faya ta fashe a jikin Shatu. "Fushhhi". Cikin gigita Ummi tace. "Sheykh kayi sauri haihuwace. Wani irin saurin isowa garesu yayi. Yana isa yasa hannunshi ya tallabo ya mannata da jikinshi. Cikin tsananin tausayawa yanayin da take cike yace. "Aish! Aishhhhhhhh". Ina bata amsa mishi sai karkarwar da jikin ta, keyi kana hannunta na dama tasa tana nuna musu tv da har yanzu ake nuna fuskokin yayun nata, cikin tsananin wahala da azabar naƙuda da gigi da kiɗimar ganin ƴan uwanta tace. "Yah Sheykh kalli wlh ƙarya akeyi musu, wlh yan uwana ba ƴan ta'adda bane, su kam ba ƴan kinnafin bane, wlh ƙarya akeyi musu ƙazafine". Ta ƙarashe mgnar da ƙarfi tare da fara wani irin gigitaccen nishi wanda yasa jikin Ummi karkarwa ta kasa koda motsa ƙafarta, bata taɓa haihuwa bata san cewa azabar haihuwa ta kai hakaba. Shi kuwa Sheykh idonshi ya zubawa, tv inda take nuna mishi. Yanayi yana zaunar da ita kan kujerar yana cewa. "Aishhhhhhhh ki zauna ki nitsu". Cikin ƙarfi ta cakumo wuyan rigarshi sabida azabar da taji ta tsargun mata, cikin gigin wahala tace. "Ina nuna maka su Yah Giɗi Seyo Gaini kana cemin in zauna wlh ƙarya akeyi musu". Da sauri yace. "Eh A'ish na sani ƙarya akeyi musu, ki kwantar da hankalinki zan fito dasu, ki nitsu kinga haihuwa zakiyi." Da sauri ta rumtse idanunta wasu hawaye masu ɗumi suka kwaranyo mata ga cutar naƙuda ga fargar abinda ta gani murya na rawa tace. "Kayi min al'ƙawarin zaka taimakawa ƴan uwana Yah Sheykh wlh basu da laifi". Cikin tashin hankali ganin yadda idonta suke juyewa yace. "Nayi miki al'kawari Aysha zanyi duk iya iyawata zan fito dasu, kotu zata wonkesu fiye da yadda gurɓatattun jami'an tsaron kasar nan suka ɓatasu. Ido ta lumshe a hankali, kana ta sake wuyanshi. Sai kuma ta kamo hannun Ummi dake gifenta. Cikin rawan jiki ta zamo ƙasa bisa carpet, kanta ta jingina jikin Ummi ta riƙe ta gam-gam tare da karkarwa murya a fizge tace. "Yah ilahi ya mujibadda'awati Yah Sheykh riƙe min ƙafata". Da sauri ya zamo yayi ƙasa, hannunshi yasa yayi sama da rigarta, robar ƙugun gajeren wondon jikinta, ya kamo, da sauri yayi ƙasa dashi, ya zare shi. Kana ya gyara mata zamanta sannan ya meda doguwar rigar tata ya rufe mata jikinta. Hannunshi ɗaya yasa ya share mata zufar dake tsastsafo mata bisa goshinta tare da hura mata sassanyan iskan bakinshi a wuyanta. Cikin zubda hawaye tausaya mata yace. "Kiyi nishi Aish kiyi nishi". Cikin tattaro sauran kuzarinta tayi nishi mai karfi. Ai kuwa cikin ikon Allah da sahalewarsa sai ga yarinya mace fara ƙal ta faɗo kan hannunshi da yasa ya tare. Ita kuwa Shatu wani irin numfarfashi masifeffen wahala ta sauƙe tare da komawa ta jingina da jikin kujera. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin murmushi mai tafe da hawaye da rawan jiki yakeyi tare da kallon agogon Daimond dake ɗaure a hannunshi murya na rawa cike da rauni da tsananin farin ciki yake cewa. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Ummi ta haihu". Ita kuma Ummi wani irin zamewa tayi ta zauna bisa kujerar kana tasa hannun tana shafa kan Shatu tare da cewa. "Allahu Akbar duniya Allah mai iko". Shi kuwa Sheykh cikin rawan jiki ya fito da yarinyar, zama yayi dirsham a gaban Shatu, tan kwashe sawunshi yayi ya buɗa gariyar jikinsa da kyau, yasa yarinyar da ita kuma taketa cillara kuka. "Yaray, yaray, inyararray inyararray". Wani irin Murmushin mai cike da zubda hawaye itama Shatun tayi tare da kallon Sheykh ɗin yadda yasa yarinyar cikin jikinshi, murya na rawa tace. "Malam Dactor Hamma Yan Sheykh me Allah ya bamu?". Wani irin matsowa gareta yayi jin yadda ta jero mishi sunayen dake da cikekkiyar ma'ana a gareta gareshi, jawota jikinshi yayi ya ruggumeta gam-gam cikin tsananin jin daɗi yace. "Aysha Aish Mar'atussaliha my dear sweetheart my everything ɗiya mace Allah ya azurtamu da ita yau jumma'a ɗaya ga watan ɗaya da ƙarfe shida na yamma dai-dai". Cikin sanyi tace. "Alhamdulillah Yah Sheykh Allah ya raya mana ita bisa imani ya al'barkaci rayuwar ta, yasa ta kasance mana Jabbo a ahlinmu Allah yasa ta marabci su Yah Giɗi". Da sauri yace. "Amin Amin Ameeeeeeen ya rabbil izzati Allah yasa tare da Mamey na, ya Kuma amsa addu'ar da kikayi mata a matsayin mahaifiyarta". Amin Amin tace tana kallon fuskarshi data yarinyar, cikin sanyi ta koma ta jingina da kujera a hankali tace. "Alhamdulillah Yah Sheykh da Junainah take kama". Tayi mgnar tana mai sakin kuka mai cike da raunin ganin an sake hasko fuskokin su Giɗi. Da sauri ya ɗan ɗago yarinyar ya manna mata ita kan cikinta, kana cikin rauni yace. "In sha Allah hawayenki zasu dena zuba, Aish da izinin ubangiji zan zame miki GARKUWA keda ƴan uwanki, naji daɗin da ɗiyarmu tai kama da tsatsonki jininki koda ban san Junainah a fuskaba ina zaton dake take kama". Ina zuwa yanzu bazata iya mgna ba, sabida kukan da take son dannewa. Shi kuwa Sheykh cikin murmushin hawaye yace. "Ummi a kawo mana kayan amsar haihuwar masarautar Joɗa zan yanke mabiyar dan ta faɗo". Cikin tsananin sauri Ummi ta miƙe, kai tsaye wonje tayi. Shi kuwa Sheykh ronƙo fowa yayi kanta a hankali yasa tafin hannunshi ya share mata hawayenta, kana ya manna mata kiss kan goshinta cikin jin daɗi yace. "Alhamdulillah Noor Hayat komai naki mai tsabta kalli haihuwarki ma mai tsabta babu jini ko ɗigo, tsabtar zuciyarki ta wadaci komai, ga Babynmu tas da ita ba datti". A hankali ta buɗe idonta, sosai take jin abubuwa biyu a zuciyarta a lokaci ɗaya tsananin farin ciki da kuma tsananin baƙin ciki da tashin hankali, sai dai farin cikin yana gab da danne baƙin cikin. Hannunshi yasa ya ɗan ja ƙafarta, ya jawota kusa dashi ta matsa daga jikin mabiyar, cikin sanyi yace. "Bari a kawo abun karɓar haihuwar masarautar Joɗa, in na yanke cibiyar sai muje Bathroom dan masu irin haihuwarki haihuwar kulle inji hausawa, sukan haihu babu jini, amman bayan kamar mintuna talatin zuwa arba'in jinin zai taho sai dai bai musu zuba da yawa yakanyi dai-dai misali ne". Cikin nitsuwa tace. "To Doctor Hamma Sheykh Jabeer". Ummi kuwa tana fita kai tsaye Part ɗin Lamiɗo ta nufa. A can babban falon su ta zube gaban Lamiɗo da Galadima da Abba da Gimbiya Aminatu dake dama musu fura. Cikin kula Lamiɗo yace. "Bisa alamu dai yau da babban Al'bishir kike tafe". Cikin zaƙuwa tace. "Allah rene, Allah hokke sabbugo, Alhamdulillah Aysha matar Muhammad Jabeer ta haihu yanzun nan". Wani irin miƙewa tsaye Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "Alhamdulillah." Shima Lamiɗon da Galadima, kusan a tare suka cewa. "Alhamdulillah masha Allah. Me muka samu?". Da sauri tace. "Ɗiya mace". Murmushi sosai Lamiɗo yayi tare da cewa. "Allah ya raya mana ita bisa imani ya bawa mahaifiyarta lfyar shayarwa". Amin Amin sukace. Gimbiya Aminatu kuwa da sauri tace. "Taso muje da kayan amsar haihuwa". Da sauri Ummi tace to kana tabi bayanta, ɗakin ta suka shiga ta dauko wani babban ƙorya ta miƙawa Ummi kana suka juyo suka nufi gidan Shatun. Murmushi mai yelwa Gimbiya Aminatu tayi ganin yadda Sheykh ke ruggume da matarsa da yartsu a tsakiyarsu wace taketa wawure-wawuren hannunta. Kusa dasu ta zauna daɓas, kana tasa hannun ta amshi yarinyar tana cewa Shatu. "Sannu Gimbiya Aysha surkar Gimbiya Aisha mai sunan Maman Lamiɗo, uwa kuma ga AYSHA masha Allah." Shi dai Sheykh sai murmushi yakeyi Ita kuwa Gimbiya Aminatu amsar yarinyar tayi, Kana ta ɗan kamo zariyar cibiyar, ta saita da ƴar ƙaramar yatsarta ƴar ƙuri, wanda hakan yayi dai-dai da kan mahaɗan da alamun kamar ƙari a wurin wanda dai-dai kan ƙarin ta ƙasa tasa zaren ɗinki ta zagaye ta ɗaure cibiyar kana tasa reza ta yanke. Miƙa Ummi yar tayi tare da cewa. "Kin amshi haihuwar Babanta tsawon shekaru talatin da lokacin tun kina ƙaramar ki, yau kuma kin amshi haihuwarta, kiyiwa babanta jakadanci itama kiyi mata". Da sauri Sheykh yace. "A a kam shiyasa ban bari ƴar ta faɗo a hannuntaba, dan Ummi na ayntacciyace nima bazata min jakadanciba bare ɗiyata, jika ta samu wannan shine tukuicin forko da zanwa Ummi a masarautar Joɗa daga yau wannan sunan Jakadiya ya bar kanta". Ruggume ƴar Ummi tayi tare da sakin wani irin murmushi mai haɗe da hawaye tana sa yar cikin mayafin nan tana cewa. "Masha Allah, zuwanki ya iso mana da al'khairai". Shi kuwa Sheykh cikin sanyi yace. "Ummi ni wannan al'adarfa ba sonta nakeba, kada asa min ƴa a kwarya". Da sauri Gimbiya Aminatu tace. "Jakadiya fita harkar shi ɗauki ƴar ki kaiwa Lamiɗo gashi tafi da mabiyiyar kije ki benneta inda ake binne na ƴaƴan ɗakinsu". Da sauri tace. To. Shi kuwa Sheykh a hankali yace. "Ummi a bari in mata wonka". Bata kulashi ba ta fita. Ganin haka ya miƙe ya kamo hannun Shatu. Bedroom ɗinta Suka shiga, kai tsaye Bathroom Suka wuce, suna shiga ya ajiyeta kan toilet, ai kuwa sai ga jinin yana zubowa. Ita kuwa Gimbiya Aminatu tattare wurin tayi kana da sauri tabi bayansu. Tana zuwa bakin ƙofar tace. "Kai buɗe ƙofar ka fito". Cikin nitsuwa yace. "Wonka zatayi." Tura ƙofar tayi ta shiga tare da cewa. "Bani wuri". Shiru yayi ya koma gefe, ita kuwa Gimbiya Aminatu a nitse ta juyo ta kalli Shatu dake zaune. "Yanzu taso kizo kiyi wonka". Cikin sanyi tace. "Toh a haɗa min ruwan zafi". Da sauri Gimbiya Aminatu ta girgiza mata kai tare da cewa. "A a ai mu al'adar masarautar Joɗa mace in ta haihu bata wonka da ruwan zafi bazataci abinci mai zafiba bazatasha abin sha mai zafiba. Komai da abu mai sanyi zatayi amfani. Jaririnma muddin na mijine to da ruwan sanyi za'ayi mishi wonka in macece muke ɗan tarfa na ɗumi kaɗan sabida bamu sai ita ina rabo zai kaitaba". "Ikon Allah sai kallo waito wasu tsarabe-tsaraben sai yaushe za'a barsune a saki al'ada a kama gsky". Ya hafaɗa yana taimakawa Shatu ta shiga wurin wonkan. Kana yayi gefe. Ita kuwa Shatu kasan cewar ta gaji yasa bata ce komaiba. Wonka tayi kana ta fito. Suna fitowa Gimbiya Aminatu ta koma falo, shi kuwa a hankali ya jawo hannunta, bakin gado ya akiyeta, kana a hankali yace. "Ɗan gyara inga ko baby ta ƙaraki". A hankali ta ɗan kwaɓe fuska, kanshi ya jujjuya alamun kiyi haƙuri. A hankali ta ɗan zame ta konta, towel ɗin ya ɗan ja, kana ya sunkuyo, da sauri yace. "Akwai ƙarin amman ɗan ƙanƙanine ɗan kaɗan yanzu kici abinci mu tafi Valli muyi ɗinki". Ya ƙare mgnar yana gyara mata towel ɗin. Da sauri Ummi dake bakin ƙofar tace. "A a ba'a buƙatar ɗinki zai haɗe da kanshi". Shiru yayi yana kallon Ummi sai kuma ya miƙo hannunsa ya amshi Babyn. Wacce anyi mata wonka an naɗeta cikin rawanin Lamiɗo. Murmushi yayi, tare da matsowa gefe ya zauna a bakin gadon. Ita kuwa Ummi taya Shatu kimtsawa tayi. Kana tace. "To zauna bari in kawo miki abinci". Da sauri ta kwanta tare da lumshe ido kana tace. "A a Ummi barshi wlh bacci nakeji sai nayi in na tashi zanci". Jin haka yasa tace. "Toh." Har zata fita sai kuma ta tsaye jin yana cewa. "Uhummm Ayyah Ummi a bani zam-zam da dabino mana". Da sauri tace. "Toh". Ba kowa a falon haka yasa taje ta ɗauko danino da zam-zam ta kawo mishi kana ta juya ta fita. Shi kuwa Sheykh a hankali ya ɗan malle marfin zam-zam ɗin yasa a bakinshi yasha da kyau. Kana ya buɗe kwalin dabinon. "Bismillah". Yace kana yasa dabinon a baki, ya tattaunashi da kyau. Ya haɗe da damshin zam-zam da yawunshi ya tsastsafo da ruwan zaƙi da ɗan-ɗanon da binon. A hankali ya sunkuyo ya kawo bakinshi kusa dana yarinyar, ita kuwa Shatu ido kawai ta zuba musu. Da sauri ta kalleshi jin an fara kiran sallan magriba. Shi kuwa bakinshi ya manna kan na yarinyar ya rinƙa tura mata ruwan dabinon, ai kuwa sai gashi tana laluma tana haɗiyewa, murmushi yayi tare da juyowa ya kalli Shatu a hankali yace. "Uhumm Bubbuga Rumbun Abboi ta haifo bubbuga Rumbun Sheykh dan ke ta gado da ciye-ciye". Murmushi mai cike da jin daɗi tayi tare da cewa. "Allah Junainah ce uwar kwaɗayi da kuma Jamil to ta gaji ƙanin ka da ƙanwata". Murmushi ya kumayi yanaji a ransa yanzu dai sun gama zama abu ɗaya. Haka yayi ta taunar dabino yana bata ruwan saida ya tauni tabino bakwai. Amfanin fara bawo yaro dabino a matsayin abinci na forko da zai fara ci a duniya yana da yawa. Ɗaya daga cikin wanda manyan likitocin duniya sunyi ittifaƙi a kai kuma sun gamsu dashi shine. Sun gano duk wani abinci da na sha a duniya kab in ɗan adam yaci, sai sun fara zama a ciki uwar hanji ta bambance ta fidda mai kyau da mara kyau kana ya sarrafu ya zama jini kafin nan zuciya kuma ta harba ta rabashi ko wani sashi da saƙo na jikin ɗan adam. Sai dabino ne abinci ɗaya da likitocin suka tabbatar da cewa. Shi muddin ka cishi kai tsaye ƙoƙolwar ɗan adam yake wuce, ya wonketa ya in ƙantata. So bada ruwan dabino ga jariri yana sa yaro ya tashi mai kaifin basira da ilimi da kwarin ƙoƙolwa. Yayinda mutane kuwa ke cewa. Yaro zaiji mgnar wanda ya shayar dashi ruwan dabinon da yawunsa fiye data kowa. Wannan shine bayanin da Sheykh yakewa Shatu yana mai kontar mata da jaririyar kusa da ita. Murmushi tayi tare da cewa. "Masha Allah". A hankali ya ɗan shafa kanta kana yace. "Bari in tafi masallaci". Ya ƙare mgnar yana fita. Ita kuwa ido ta zuwaba ƴar tasu. Shi kuwa tv ya kashe kana ya nufi falonshi. Ummi kuwa tana kitchen zabbi take gasawa waya na saƙale a kunneta Umaymah taketa kira tun ɗazu amman bata ɗagawa. Katse kiran tayi ta kira Juwairiyya tana ɗagawa tace. "Juwairiyya Shatu fa ta haihu". Cikin tsananin jin daɗi Juwairiyya dake bisa sallaya tace. "Kai Ummi Alhamdulillah masha Allah me muka samu?". "Ɗiya mace". "Masha Allah bari inyi salla inzo". Galadima kuwa yana komawa Side ɗinsa ya gayawa matarsa. Ita kuwa Ummi Umaymah ta kuma kira, bugu ɗaya ta ɗaza da sauri tace. "Assalamu alaikum al'bishirinki Umaymah". Cikin dariya mai cike da zallar jin daɗi da farin ciki tace. "Goro Ummin Jabeer amman Lamiɗo ya rigaki, yanzu yake gayawa Jaddanmu kinsan su Mamma da Aunty Rahma sun zo shekaran jiya, nima tun jiya ina Katsina. To yanzufa Jadda ya shigo yake gaya mana kai Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!." Cikin dariyar jin daɗi Ummi tace. "Eh lallai Lamiɗo yamin shigar saurin". Sitti ce ta amshi wayar tare da cewa. "A a kada ki damu goron Al'bishir ɗinki na musamman ne". Aunty Rahma dake gefene tace. "Ummi yar da waye take kama". Da sauri Ummi tace. "Wlh da Ishma take kama". Mamma ce ta amshi zancen da cewa. "Allah sarki yadda take son Ishma haka Allah ya bata mai kama da ita". Dariyar jin daɗi sukayi dukansu da yake wayar a amsakuwa take". Daga nan Ummi ta ƙatse kiran ta nufi falon. Ɗakin Shatu ta fara shiga murmushi tayi ganin Shatun na konce tanata kallon yarinyar tana mata tofi. Fita tayi ganin bata gantaba. Ana idar da sallan isha'i suna fitowa Sheykh yayi sauri yabi bayan Abbanshi. Kana ya bar Jalal Jamil Yah Jafar, Yah Hashim Affan Laminu Sulaiman a bayanshi. Da sauri yace. "Assalamu alaikum, Abba". Da sauri Abban ya juyo wanda Dr Aliyu da Baba Basiru Baba Kamal Baba Nasiru da sauran ƙannen Abban nasu suka tsaya da sauri jin yana cewa. "Alhamdulillah Aysha ta sauƙa lfy". Yayi mgnar a hankali ne cike da nitsuwa da zallan farin cikinsa daya kasa ɓoyuwa. Cikin sauri Dr Aliyu ya juyo tare da cewa. "A a masha Allah, Masha Allah". Baba Kamal ma kalmar yake faɗi. Baba Nasiru kuwa cikin wani irin masifeffen tashin hankali da tsana yace. "Me aka haifa maka?". Da sauri Baba Basiru yayi wani irin murmushi tare da cewa. "Sa ranka a inuwa ƴan macece ba mai gadan mulki aka haifa mishi ba". Karo na forko a lokaci na forko Abbansu yasa hannunshi ya jawoshi jikinshi ya ruggume shi, gam a jikinshi tare da cewa. "Alhamdulillah Muhammad Allah ya raya mana ita bisa imani ya bawa mahaifiyarta lfyar shayarwa da bata kekyawar tarbiya, nayi farin ciki mai tarin yawan da jin wannan Magauta zasuyi rabkanuwar aiyukansu". Ya ƙare mgnar tare da sakeshi. Tabbas shi kam haihuwar nan tazo mishi da wasu abubuwa manya, wai yau shine har Abbansu ya ruggume shi. Su kuwa gaba ɗaya tafiya sukayi. Shima binsu a baya yayi. Su Jalal kuwa da Yah Jafar da Jamil da Affan da sauri sukabi Yah Sheykh ɗin nasu a baya. Sabida suna cike da mamakin yadda suka hango Abbansu ya ruggume shi. Kusan a tare suka kutsa kai cikin falon. Ummi dake riƙe da babban kular da tasa gasassun zabbin ne ta juyo da sauri, ta kalli Juwairiyya dake bayanta tana cewa. "Iye gafa Daddyn Baby da Uncles ɗinta". Da sauri Jamil ya shigo cikin falon yana cewa. "Kai haba dai My Adda Shatu ne ta haihu?". Yayi mgnar cikin zumuɗi suma sauran gaba ɗaya ido suka zuma mata jiran amsarta. Shi kuwa Sheykh murmushi mai cike da yelwa yake, tare da zaro wayarshi a aljihu. Ummi ce tayi dariyar jin daɗi tare da cewa. "Wlh kuwa Alhamdulillah Shatu ta haifo mana Kekkyawar ɗiyar fulani fara ƙal". Kusan a tare Jamil da Affan sukace. "Yesssss masha Allah Alhamdulillah". Jalal kuwa wani irin murmushi yayi mai baiyana farin cikinsa a hankali yace. " A a kai Alhamdulillah Allah mun gode maka, Allah ka raya mana ita bisa imani". Yah Jafar kuwa da sauri ya juyo ya kalli Sheykh ga mamakinsu babu zato babu tsammani sukaji yace. "La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam. Alhamdulillah Allah na gode maka, daka c nuna min wannan ranar Alhamdulillah ni Muhammad Jafar Allah na gode maka". Wani irin juyowa da ƙarfi Sheykh da zai shige falonsa yayi cikin tsananin kaɗuwa da tarin al'ajabi da mamaki da rantsar kokonton shin muryar Yah Jafar ce kuwa da tsawon shekaru 13 baiyi mgnaba yake mgn?. Jalal kuwa da sauri ya koma da baya ya faɗa kan kujera sabida rawan da jikinsa keyi. Jamil da Affan da sauri suka matso kusa dashi. Ummi kuwa da sauri ta saki kular dake hannunta. Ita kuwa Juwairiyya cikin tsananin kaɗuwa da tsoro ta matso gabanshi bakinshi take kallo tamkar zata cire idonta ta mannasu jikin lips ɗinsa gaba ɗaya sun kasa mgn. Shi kuwa Sheykh da sauri ya iso gabansa hannunshi ya kamo ya riko gam gam tare da cewa. "Yah Jafar mai-maita abinda kace Yah Jafar sake mgn inji maimata". Yayi mgnar da ƙarfi cike da kaɗuwa. Ga mamkinsu sai ga Yah Jafar ɗin yayi shiru yana kallonsu Tamkar kurma. Cikin wani irin tsuma da kaɗuwa duk suka zagayeshi. Cikin tsananin farin ciki Sheykh ya ruggume shi gam-gam a jikinshi murya cike da al'hini da hamdala yake cewa. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!. Yah Jafar kayi mgna ka sake yin mgn dan Allah kayi mgn". Ya ƙarashe mgnar yana mai janye jikinshi daga jikin Yah Jafar ɗin tare dasa hannunsa bisa kafaɗunsa duka biyu yana jijjigawa. Itama Juwairiyya cikin rauni murya na rawa cike da kukan hamdala tace. "Yah ilahi ya mujibadda'awati ya Allah idan mafarki nakeyi ka tabbatar min dashi". Cikin sauri Jalal dake zaune yace. "Ba mafarki bane Aunty Juwairiyya". Affan ne ya matsosu tare da haɗe su duka ya ruggume sai kawai ya saki kuka. Ummi kuwa cikin shassheƙan kuka tace. "Sheykh ku barshi mu bishi a hankali tabbas mgn yayi kuma in sha Allah zai kumayin mgn". Jamil kuwa gaba ɗaya jikinshi kerma yakeyi wayarshi ya zaro Umaymah ya kira tana ɗagawa ya fashe da sassayan kuka tare da cewa. "Umaymah! Umaymah!!". Cikin tsananin ruɗani da kiɗima tace. "Innalillahi Jamil mene! Jamil gaya min meyasa ka kuka". Da ƙarfi yace. "Umaymah kukan farin cikine. Yau Yah Jafar yayi mgna kuma ya maimaita Umaymah farin cikine ya samu kuka". Cikin wani irin farin ciki mara misaltuwa Umaymah ta saki wayar tare da juyowa ta kalli Sitti da Jaddansu da sauran ƙannenta da babban yayansu baban Aunty Juwairiyya da Ibrahim kenan. Cikin wani irin murmushi mai haɗe da hawaye tace. "Sitti Jadda Jafar ya fara mgn". Gaba ɗaya salati suka ɗauka a tare, suka direshi da kalmar. "Alhamdulillah ala kulli halin, Alhamdulillah lallai tabbas dukkan tsanani yana tare da sauƙin." Kawai sai kuma duk suka matso gaban Jaddansu da ya saki kuka kamar ƙaramin yaro cikin rawan murya yace. "Ɗaya daga cikin burukana ya cika, kafin mutuwata ko yanzu na kwanta dama nasan bakin Jafar ya buɗu. Sai dai har yanzu ina da wani babban buri Yah Allah ka bani aron rai da lfy ka ka baiya na min ƴata Aisha ka tsare min ita a duk inda take ka dawo da ita kan ƴaƴan ta al'farmar Annabi da al'ƙur'ani". Cikin zubda hawaye suka amsa da Amin Amin gaba ɗayansu. A nan masarautar Joɗa kuwa, Cikin tsananin tarin farin ciki Sheykh ya kamo hannun Yah Jafar ya zaunar dashi bisa kujera kana da sauri ya juya ya nufi ɗakin Shatu. Konce ya sameta da alamun bacci takeyi. Hannunshi yasa ya ɗauki Jaririyar kana da sauri ya juyo ya fito. Yana fitowa kuma dai-dai lokacin Lamiɗo da Galadima da Abbanshi suka shigo falon. Cikin sauri ya matso gaban Yah Jafar miƙa mishi ƴar yayi ga mamakinsu sai sukaji yace. "Bismillahi". Cikin tsananin kaɗuwa da mamaki Lamiɗo Galadima da Abba suka zauna, Lamiɗo da Galadima da Yah Jafar bisa kan kujeru sauran kuma duk kowa na ƙasa harda Abbansu. Kallon kallo sukayiwa juna lokacin da suka ga yana shafa kan yarinyar tare da buɗe baki a hankali yace. "Masha Allah. Allah ya raya mana ke bisa imani yayi miki al'barka". Zuwa yanzu Lamiɗo da Galadima cikin kaɗuwa suke cewa. "Jafar". Da sauri Sheykh ya juyo ya kalli Abbansu da tuni hawaye suke tsastsafo mishi ya kasa cewa komai sai tallabe haɓarsa yayi da hannu bibbiyu yana kallonshi. A hankali Sheykh ya juyo kamar ƙaramin yaro haka ya iso da rarrafe. Ya zauna gaban mahaifin nasu ya fuskanceshi da kyau hannunshi yasa ya kamo hannun Abban nasu ya zare mishi tagumin da yayi, kana yasa tafin hannunshi ɗaya ya share mishi hawayen da yakega suna zubo mishi cikin ƙarfin zuciya da tsananin farin ciki kan farin ciki murya cike da girmamawa yace. "Abbanmu kace Alhamdulillah kada kayi kuka, Abba kaga ikon Allah ko Yah Jafar yayi mgn a yau yayi hamdala yace ya godewa Allah daya nuna masa wannan ranar muma muce mun godewa Allah mana sai ya ƙara mana wata ni'imar domin indan Allah yayi maka wata ni'imar ka gode mishi sai ya ƙara maka da wata, muce Alhamdulillah". Kusan a tare gaba ɗayansu sukace. "Alhamdulillah". Harda shi Yah Jafar ɗin. Ya ilahi wannan shine kyautar Allah. Juwairiyya kam hawayenta yaƙi barin zubowa. Lamiɗo kuwa a hankali ya dawo kusa dashi hakama Galadima, sai ya zama sun sashi a tsakiyarsu. Abban da Sheykh kuwa suna gabansu da sauran Juwairiyya da Ummi kuwa suna gefe". Cikin nitsuwa Abba yace. "Jafar! Jafar!! Jafar!!!". Shiru babu amsa. Da sauri Lamiɗo ya jujjuya mishi kai tare da cewa. "A a barshi, dole sai a hankali komai zaiyi dai-dai." Sai kuma ya gyara zamanshi ya kalli jikokin nashi ya juya dama da hauni kana cikin yin ƙasa da murya yace. "Toh wannan al'amari ya zama sirri tsakaninmu har zuwa ɗan wani lokaci kada ku gayawa kowa na cikin masarautar Joɗa". Da sauri sukace "To". Shi kuwa Sheykh a hankali yasa hannunshin ya ɗauki Jaririyar ya miƙa Lamiɗo ita. Addu'o'in yayi mata sosai kana ya miƙawa Galadima ita, sannan Sheykh ya ɗauƙeta ya miƙa Abba ita cikin murmushi yace. "Aisha ta tafi Aisha ta dawo". Murmushi Ummi tayi sabida tuno irin tarin son da Abba kewa Mamey wanda shiga goma zai zaka jishi yana kira Aisha! kaxa Aisha kaza da kaza yayi kaza ko?,". Shima addu'o'in yayi mata kana, suka ɗan tattauna kaɗan suka tafi. Su Jamil kuwa suma ɗaya bayan ɗaya suka amsheta. Cikin murmushi da tarin son yarinyar Jalal yace. "Masha Allah da Ishma take kama". Da sauri Jamil ya amsheta tare da cewa. "Kace da Mamey take kama tunda Ishma dai da Aunty Rahma take kama Aunty Rahma Kuma da Mameynmu take kama". Da sauri Affan ya amsheta tare da cewa. "Masha Allah wlh da Mamey take kama, Alhamdulillah Yusuf ƙarami yayi kamu". Ɗan shi kenan takwaran Hamma Yusuf ɗin Zahra dariya sukayi baki ɗayansu. Kana Aunty Juwairiyya ta amshi yarinyar ita da Ummi suka nufi ɗakin Shatu. Suna shiga suka sameta zaune bakin gado da alamun waya takeyi da Rafi'a. "A a bazan gaya miki ba sai kinzo kiga mai aka samu". Tayi mgnar tana amsar Babyn da Aunty Juwairiyya ke miƙo mata. Ita kuwa Rafi'a cikin tarin jin daɗi tace. "Ai kuwa gobe da sassafe zan muku sammako". Da sauri tace. "Rafi'a baza kizo mu kwana ba". Cikin dariyar jin daɗi ta e. "Zan dai zo gobe kam da wuri". Daga nan sukayi sallama. Ita kuwa Ummi abinci ta zuba mata mai rai da lfy cimar jegon gaske. Tuƙeƙƙen tuwon shinkafa da miyar ɗanyar kuɓewa tasha man shanu da yajin daddawa da nama. Sosai ta tasata gaba taci. Ita kuma Juwairiyya tana riƙe da Ƴar. Bayan taci tuwon ne kuma Ummi tasa mata gashin da yaketa tururi yaji yaji tana fifita matashi dan yayi sanyi. Kana ta haɗa mata kunu da zuma ta bata, tanaci tana ɗan korawa. A hankali ta ɗan jingina bayanta da gado a hankali tace. "Ummi na ƙoshi". Da sauri tace. "A a Shatu ƙara sashi kada kice zakiyi jegonku na yaran zamani jego da soyayyan Arish da tea". Cikin sanyi tace. "Allah Ummi cikina zai fashe". Jin hakane tace. "To sai anjima ki ƙara". Gyaɗa kai tayi kana ta gyara zamanta. A can falon kuwa su Jamil duk Dinning area Suka nufa, suka zauna suka fara cin abinci. Yah Sheykh kuwa falonshi ya wuce, wayarshi liƙe a kunne wanda Bappa yake kira. Shi kuwa Bappa a can Rugar Bani yana zaune a tsakar gida Junainah na gefenshi su Ummey na gefenta. Da sauri Junainah ta miƙo mishi wayar da dama Game takeyi da ita. Amsa yayi da sauri ya amsa kiran. Gyara zamanshi yayi jin muryar Sheykh na cewa. "Assalamu alaikum". Cikin kulawa yace. "Wa alaikassalam Muhammad". Da sauri ya zauna bisa kujera cikin tarin jin daɗi da son tsohon da tausayinsa yace. "Na'am Bappa na Ina wuni". Fuska ɗauke da murmushi yace. "Lfy lau Alhamdulillah Muhammad ya su Lamiɗo ya Abbanka dasu Jalal duk suna lfy koma?". "Alhamdulillah Bappa duk suna lfy cikin farin ciki". Ya bashi amsa yana murmushi. Shi kuwa Bappa cikin kula yace. "Yah Shatu na?". Murmushi Sosai yayi kana yace. "Alhamdulillah Bappa Shatunka ta girma yau ɗazu da yamma gabanin magriba ta zama uwa". Cike da tsananin farin ciki Bappa yace. "Masha Allah! Alhamdulillah yaushe ta haifu mata na samu ko aboki mai tayani kiwo?". Murmushi yayi tare da cewa. "A a Bappa wannan Gimbiya ce amrya ka samu". Cike da farin ciki Bappa yace. "Alhamdulillah Allah ya raya mana bisa imani". "Amin Amin". Yace yana mai jin muryar Junainah tana cewa. "Ayyah Bappa bani shi Adda Shatu ce ta haihu?". Cikin kula yace. "Bappa a bawa Junainah waya". To yace kana ya miƙa mata wayar, tare da juyowa ya kalli Ummey cikin murmushin yace. "Alhamdulillah Shatu ta sauƙa lfy an samu ƴa mace yanzu da yamman nan". Wani irin ajiyan zuciya mai sanyi Ummey ta sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah yau kam zanyi bacci hankali na konce Shatuna ta haihu lfy". Murmushi Inna Amarya tayi tare da cewa. "Wlh kuwa kai Alhamdulillah Metai fi haka daɗi kaji kawai ɗan ka ya haihu lfy". "Wlh kuwa fa". Cewar Bappa. Sai kuma suka juyo suna kallon Junainah dake tsalle tana cewa. "Alhamdulillah Hamma Jabeer kace dani takeyin kama?." Murmushi yayi tare da cewa. "Sosai ma kuwa Junainah". Cikin dariya tace. "Allah shi ƙara dama kullum Addana sai tace wai ta fini kyau wai inada dogon bakin kwaɗayi, ni kuma kullum ince Allah yasa ta haifi irina ai zata dena cemin mummunan". Dariya yayi sosai kana yace. "Toh gobe dai zaki zo mana ko?". Da sauri tace. "Eh zanzo Bappa na da Ummey ma zasu zo". Katse kiran tayi kana ta miƙawa Bappa wayar. Shi kuwa kiran Abboi yayi ya kara wayar a kunne tare da cewa. "Assalamu alaikum". "Wa alaikassalam". "Barka da dare Abboi". "Barka dai Bappa Shatu." Abboi yace yana murmushi tare da kallon Dedde dake gefensa. Cikin jin daɗi Bappa yace. "Alhamdulillah yau Shatu na ta hau matakin uwa ta sauƙa lfy mun samu ɗiya mace". Wani irin yalwataccen murmushi mai cike da jin daɗi Abboi yayi tare da cewa. "Alhamdulillah kai yau naji labari mai daɗi masha Allah. Kace lallai zuwa Nigeria ya kamani". Da sauri Bappa yace. "Sosai ma kuwa, yanzu dai su waye zasu fara zuwa". Da sauri yace. "Khadijah da Amina ƙanwar Deddena Shatun, dama nayi mgnar da mijinta tun kwanaki to yanzu kuwa zan kirashi in sanar mishi anfa yi haihuwar ba mamaki gobe ko jibi su taho da safe zuwa gidan naka. Kaga da azahar sai su wuce masarautar da iyalin taka". Cikin gamsuwa Bappa yace eh hakan yayi. Yana katse kiran yayiwa Ummey bayani cikin gamsuwa tace. "Eh hakan yayi amman in Amina da Khadijah sun zo suje da Junainah ni sai bayan suna sai inje ko". Cikin gamsuwa yace. "Eh amman bayan suna da kwana ɗaya zakije in anyi suna kamar yau sai gebe kije ko". "Eh hakanma yayi". Tace cikin jin daɗi. Shi kuwa Abboi a ya juyo ya kalli Dedde ya mata bayani. Sosai ta shiga cikin farin ciki a take ta miƙe ta nufi ɗakinta. Nan ta gaya Khadijah ta fara shiri Addanta ta haifu. A masarautar Joɗa kuwa gaba ɗaya a daren labarin haihuwar Shatu ya karaɗe ko ina lungu da saƙo na masarautar. Riskar wannan lbrin a kumnunwan Magauta yayi masifar tada musu hankali. Hajia Mama kuwa a dare cikin masifar tashin hankali ta wuce gidan bokanta. Tana shiga tace. "Meyasa ne wai ku bokaye babu wasu maƙaryata a duniya sama daku, ya mukayi da kai da shaiɗanun makaranka maƙaryata. Shin ba cewa sukayi randa aka haifi yarinyar a wurin yanke cibiya zasu kashe min itaba". Cikin wani irin masifeffen razana ta daka tsalle tayi baya, sabida wani irin razanenne tsawa da bokan ya daka mata da ƙarfi. Cikin ɗaga amo yace. "Ke tafi daga can waya isa ya cutar da wanda Allah ya kare, dama ai na gaya miki babu abinda da zai samu cikin nan sai al'khairi. Amma da yake ke tinkiyace ƙidahuma kikazo kina min ihu a kai in zaki iya cutar da itan ke kije ki gwada mana". Cikin tashin hankali gano tayi asarar kuɗaɗenta a banza ta juya ta fita tana cewa. "Tabbas sai na kashe yar nan babu shakka bazata rayuba". Shi dai boka tsaki yaja. Ita kuma ta juyo ta dawo hankali a masifar tashe. Shi kuwa Sheykh yana gama mgn da Bappa DSS ɗinsu ya kira. Cikin hikima da iya sarrafa harshe yace. "Sir naga wasu yaran da akayi nasarar kamasu da laifin kinnafin ko?". Jim kaɗan yayi tare da cewa. "Eh yaran fulani masu kiwo ko?". Da sauri yace. "Eh su waɗanda akasa suka amsa laifin da ba nasuba akan dole." Da sauri yace. "A a kamar yaya laifin da ba nasuba?". Cikin nutsawa ya gyara zamanshi kana yayi mishi duk bayanin da Sulaiman yayi mishi ɗazu. Cike da al'hini irin yanayin nan na ba'a mugun sarki sai mugun bafade ogan nashi yace. "Kai Malam ni bansan da zancen nanba, kawai nasan kotu ta bada beli babu batun a nemo wasu a basu laifin da ba nasuba". Da sauri Sheykh yace. "Ni nasan baka saniba dan na yarda da adalci ka yanzu me abun yi a kan lamarin yaran nan?". Cikin takaicin yadda wasu jami'an tsaron kasar nan suka zama azzalumai yace. "Dole zamu kai zancen kotu ayi bayani a gaban al'ƙali a kawo Sulaiman ya bada shaida, da kuma sauran ma zauna magarƙamar". Cikin wani irin jin daɗi sanin muddin mgnar taje kotu. Komai zai iya dai-dai yace. "To ka taimaka musu a meda case ɗin yaran zuwa kotu". Cikin nitsuwa yace. "Toh ba matsala". Suna gama wayar kuwa ya fara bincikan lmrin a afaren ya turawa wani al'ƙali rahoton. Shi kuwa Sheykh a hankali ya miƙe ya nufi ɗakin Shatu. Tuni tayi wani baccin gajiya. Ummi na kwance gefenta. A hankali yace. "Ummi bakuyi bacci bako?". Gyara konciyarta tayi tare da cewa. "To ita dai mai jego tayi sai nida ƙawar tawane muke hira". Murmushi yayi kana ya matso. Miƙawa mishi yar tayi, amsa yayi, ya zauna a bakin gado gefen Shatu. Addu'o'in ya farayi yana tofa mata. Kana a hankali ya kalli Shatu data buɗe ido a hankali tana kallonsu. fuskar yarinyar ya kalla yadda taketa wawure-wawuren hannunta. Cikin nitsuwa yace. "Ummi yunwa nefa ya hanata bacci". Ya ƙare mgnar yana kallon Shatu. Ita kuwa Ummi da sauri tace. "Yauwa tunda ta tashi ta bata maman ta tsotsa". Kai ya gyaɗa kana yasa hannunshi ya kamo na Shatu ta tashi zaune. Ɗaura mata yar yayi bisa cinyarta, kana yace. "Bata Baloon ɗin tasha". Cikin ɗan yamutsa fuska tace. "Daga yanzu?". Da sauri yace. "Eh". Ya ƙare mgnar yana tattaro rigarta yayi sama dashi, tare da ɗan ɗago kan Baby ya saita bakinta da nimple ɗin ya manna mata. Ai kuwa da ƙarfinta ta damƙi nimple ɗin. Wani irin zillo Shatu tai tare da yarfa hannun cikin sakin ƴar ƙara tace. "Wayyo Allah na Yah Sheykh zafi". Da sauri ya saki dariyar mugunta. Hakama Ummi dariyar suke mata. Ita kuwa cikin kunya ta ɗan sunkuyo tana kallon yadda ƴar taketa zuƙam nonon da har yanzu bai tsastsafo da ruwaba. Haka nan taji wani irin son yarinyar yana shiga ta. Tsawon 5 minute tana tsotsar bakin nimple ɗin ta, wanda saida yayi ja yayi tsami a hankali tace. "Zafi wlh zata cinye min nimple". Murmushi yayi tare da lakace hancinta kana ya janye kan yarinyar. Ya kwantar da ita, ai kuwa gajiya da tsotson yasa tayi bacci. Ita kuma Shatu meda breast ɗinta cikin riga tayi kana ta koma ta konta. Sunkuyowa yayi kansu yayi musu addu'a. Kana ya juya ya fita yana cewa Ummi. "Sai da safe". Allah ya bamu al'khairi tace. Amin yace yana fita. Yana komawa ɗauki shi yayi shirin bacci kana ya kira Haroon da ibrahima sukayi hira sosai cikin farin cikin. Daga nan ya kwanta. Washe gari da safe. Gimbiya Saudatu ce zaune a falon Shatu. A hankali ta fito ruggume da yar a hannunta sunyi kyau sosai cikin shigar tasu. Especially Babyn da aka shiryata cikin wasu kayan sanyi masu taushi red color and white masu masifar kyau da taushi, tayi lib a ciki. A hankali ta kalli Shatu dake miƙo mata ƴar amsa tayi tare da cewa. "Masha Allah, ƴarinya kam kekkyawan sai dai Allah yasa kada ta gaji Rashin kunyar uwarta da ubanta". Sheykh dake shigowa ne yace. "Ai kuwa zata gada dan kyan ɗan ya gaji iyayensa". Cikin watsa mishi harara tace. "Kai matarka ta haihu ka girmama bazaka bar yiwa manya rashin kunya bane wai?". Da sauri ta juyo ta kalli Shatu dake cewa. "Toh ai kema baki bar rashin kunyarba bare mu". Cikin ta kaici tace. "To uwar fitsara ke kiji da jegon ma mana tukun". Murmushi tayi tare dasa hannun ta amshi babyn da take miƙo mata tare da cewa. "Allah ya raya". Karo na forko a rayuwar Sheykh da yaji Gimbiya Saudatu ta mishi addu'a ko mgn mai kyau. Cikin jin daɗi yace. "Amin ngd". Tsaki taja tare da watsa musu harara ta fita. Murmushi yayi mai sauti ƙana ya iso gareta. Ya ruggumeta ita da Babyn cikin raɗa yace. "Ana Uhubbuk ya habibi Da'iman". Murmushi tayi dan bata gane da ita yakeba, a zatonta da yar tasu yakeyi. Shi kuwa ganin bata gane bane sai ya share tare da cewa. "Ɗazu nazo kuna bacci". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Ummi ta gaya min". Da sauri ya janye jikinsa gareta, jin Muryar Mom Maman Imran wacce itace matar Abbansu ta uku. A daƙile ya amsa sallamar tata, sai ya kuma saki fuskarsa ganin harda Abbanshi da cingam ɗinsa amaryarsa kenan. Bayan su zauna ne Shatu ta miƙa musu ƴar ɗaya bayan ɗaya, cikin murmushin Mom tace. "Masha Allah, tana kama da kakarta". Amaryar Abban ta miƙawa amsa tayi tare da cewa. "Kekkyawar Baby Allah ya raya amaryar Habibullah". Da sauri Abba yace. "Uwar gida dai, ai kece amarya kam". Kauda fuska Sheykh yayi kamar baya wurin. Haka dai sukayi musu Barka suka tafi. Haka kuma mata da maza bayi da hadimai keta yiwa Sheykh Barka a duk sanda ya gilma cikin masarautar. Rafi'a kuwa tazo wanda zuwanta yasa Shatu ƙara sakewa sosai gashi Khadija tace mata gobe zasuzo da sassafe, dan jirgin dare zasu biyo da yauma zasu isota. Alhamdulillah kuma bayan sallan isha'i suka iso. Salmanu ne ya ɗauke su ya kaisu Rugar Bani, shima zai kwana can saida safe zai taho dasu. A masarautar Joɗa kuwa abin mamaki kowa yazo barka yaga baby ammma. Banda Hajia Mama, Mami Matar Affan kuwa kusan nan Part ɗin Shatu ta wuni dan suna masifar ɗasawa. Washe gari da safe, Aunty Amina ƙanwar Dedde da Khadijah ƙanwar Shatu da Inna Amarya da Junainah suka shirya zuwa masarautar Joɗa. Inda Ummey ta haɗawa Shatu man shanu, kwan zabbi yajin daddawa dana borkono da zuma da madarar shanu, ko wanne mai yawa suka taho mata dashi. Ƙarfe tara da rabi dai-dai Salmanu yayi parking a asalin babban gate ɗin masarautar Joɗa. A hankali ya juyo ya kalli Khadija dake gefensa yace. "Kira ta ki gaya mata kun iso a turo masu shiga daku". To tace kana ta kira Shatu. Tana ɗagawa tace. "Assalamu alaikum ƴar uwa rabin jiki kun isone?". Da sauri tace. "Eh mun iso muna babban gate ki turo azo a shigo damu naga masu jajayen rigunar nan sai kallonmu suke tayi". Da sauri tace. "Toh ba matsala bari yanzu Jamil ko Jalal zaizo". Tana faɗin haka ta katse kiran, tana ruggume da Babyn ta nufo falon. Tana fitowa ta hangosu can bisa. Dinning table suna yin breakfast harda Yah Jafar. Da sauri Ummi ta nufi inda take tare da cewa. "Yah dai Shatu kina son wani abune?". Gyara riƙon da tayiwa Babyn tayi tare da cewa. "Eh Ummi dama su Junainah ne suka zo, suna can babban gate to inaso a shigo da sune". Da sauri Ummi tace to kana ta juyo tana ƙwalawa Sara dake kitchin kira. Da sauri ta fito tare da cewa. "Na'am". Cikin kula tace yauwa dan Allah jeki can bakin babban gate ki shigo da baƙi". Da sauri tace to kana ta fita. Tana isa tace su shigo da motar har Salmanu yace a a sai kuma yace to sabida tuno akwai kaya. A hankali tayi gaba motar na binta a baya suna kutsa hancin motar cikin masarautar Joɗa. Junainah ta sauƙe wani irin masifeffen ajiyan zuciya kamar dai irin ka dade kana neman abu baka samuba ka samu. Wani irin daɗi takeji na musamman yana ratsa mata jiki da zuciya. Haka nan taji tsikar jikinta yana tashi tsaye. Har bakin Part ɗin su. Sukayi parking. A hankali suka fito. Shi kuwa Salmanu kayan nasu ya fitar ya ajiye bisa barandar dake bakin ƙofar falon tare da cewa. "Toh ni zan juya in kin shiga Khadijah kiyi mata barka". Da sauri Khadijah tace to. Kana ta sunkuya ta ɗauki jarkan man Shanu Junainah kuwa galam ɗin zuma ita kuwa Sara ta ɗauki kwaryan ƙoyayen. Inna Amarya kuwa jarkan madarar shanu. Sara ce a gaba Junainah na biye da ita a baya sauran na biye dasu. A can cikin falon kuwa dai-dai lokacin Sheykh ya fito Falon gefen Shatu ya zauna. Jalal kuwa tsaye yake gefensu yana kallon Babyn dake hannun Sheykh su Jamil Affan Yah Jafar kuwa suna Dinning area. Haka nan sukeji zuƙatansu na harbawa da ƙarfi da ƙarfi. A hankali Sara ta buɗe ƙofar tare da turo kai tana mai sallama. A hankali Junainah ta sako ƙafarta cikin falon tare da buɗe muryarta sama tace. "Assalamu alaikum Adda Shatu". Wani irin ratsa amon sautin muryar ta kunnuwansu Jalal Jamil Jafar Sheykh sukayi tare da juyowa da sauri suka fuskanci bakin ƙofar ɗakin. Dai-dai lokacin Junainah ta shigo cikin falon. Cike da mamaki Sheykh Jabeer, Yah Jafar, Jamil, suka zuba mata ido tare da haɗa baki wurin cewa. "....! Littafin GARKUWA na kuɗine akwai Normal group 300, akwai Special Group 1k babbancinsu a wurin yawan posting ne ga ac no 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kuyi screenshort na Debit Alert ɗin sai ki turo shaidar biyanki ta whatsApp 09097853276 ƴan Normal group in baki da halin biya ta ac zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku kacal ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Cikin zuba mata ido tare da mamaki muryarta da kamanninta suka haɗa baki wurin cewa. "Wa alaikassalam". Shatu kuwa da sauri ta miƙe tsaye tare da nufosu cikin farin cike take cewa. "Oyoyo Allah sarki My Junnu". Da gudu Junainah ta ƙara sa inda take ruggume juna sukayi suna dariya. Da sauri Shatu ta ɗan ɗago kanta ta kalli Khadija date cewa. "Wato ma Junainah kawai kika gani ko Adda Shatu shekara biyu baki ganniba ko ki kulani". Da sauri ta saki Junainah ta ruggume Khadijah tana dariya tare da cewa. "Oh Dija ƙorafi". Ita kuwa Junainah dariya tayi tare da cewa. "Oh su Adda Dija kishi akeyi dani". Cike da mamaki da kuma farin cikin ganin Junainah Ummi ta kalli Aunty Amina da Inna Amarya tare da cewa. "Lalako jaɓɓama mon poi". Da sauri Shatu ta ture Dija cikin tarin so ta ruggume Aunty Amina da Inna Amarya tare da cewa. "Aunty Amina Inna Amarya marabanku." Da sauri suka ɗan juyo jin Sheykh yana cewa. "Sannunku da zuwa". Cike da kunyar sirkai sukace yauwa. Kana sukabi bayan Ummi dake cewa. "Ku iso mu shiga ciki." To sukace kana sukabi bayanta itama Shatu tabi bayansu. Sara kuma ta kwashi kayan duk ta kaisu kitchin. Ita kuwa Junainah jin muryar Sheykh ne yasa ta juyo da sauri. Ganinshi riƙe da jaririyar ne yasa ta juyo da sassarfa ta nufi inda yake tare da cewa. "Hamma Jabeer?". Tai mgnar tana zubawa Jalal da Jamil ido, da alamun so take taga wanda zai amsa a cikinsu ta gane waye shi. Cikin sauƙe wata iriyar nannauyan ajiyan zuciya yace. "Na'am Junainah". Da sauri ta ƙara so inda yake, tana isa ta ɗan sunkuyo tana kallon Babyn murmushi mai yalwa tayi tare da cewa. "Ina kwana Hamma". Yana mai kallon yantsun hannunta data miƙo mishi alamun ya bata Babyn yace. "Lfya lau Alhamdulillah Junainah ya Bappa". Da sauri tace. "Yana lfy yace in gaidaku duka, harda Yah Jafar Yah Jalal da Yah Jamil". Da sauri ta ɗan juyo jin Affan na cewa. "Banda ni kenan". Kai ta jujjuya tare da cewa. "A a harda kai mana". Sai kuma ta juyo tana kallon Sheykh tare da yin ƙasa da murya tace. "Hamma Jabeer me sunanshi". Murmushi yayi tare da yin ƙasa da murya kamar yadda tayi yace. "Affan". Cikin gyaɗa kai, ta ƙara matsowa zama tayi gabanshi tare da miƙa sawunta cikin zaƙuwa tace. "Hamma Jabeer bani ita mana". Da sauri yace. "Junainah zaki iya kuwa inafa tsoron kada ki kada ita". Da sauri tace. "Zan iya mana". To yace kana ya sunkuyo ya ɗaura mata yar bisa cinyarta, yasa hannunshi ya tallabe kan Babyn. A hankali Jalal yayi wani irin rumtse idonshi da ƙarfi. Jamil kuwa cikin sanyi ya taso ya taho kusa da ita, matsawar da yayine yasa Yah Jafar hangota. Miƙewa yayi da sauri ya nufo tsakiyar falon. Ido suka zuba mishi ganin yadda yazo ya tsuguna gaban Junainah da Babyn da Sheykh ɗin. Da sauri Junainah ta ɗago kanta ta kalleshi cikin zuba mishi ido cikin ido tace. "Ina kwana". Shiru yayi bai amsa ba, sai hannunshi da yasa kan sawunta yatsun ƙafarta ya ɗan kama tare da rumtse idonshi. Da sauri ta kuma cewa. "Ina kwana?". Shiru bai amsaba sai kuma ga hawaye na zubo mishi. Hakane yasa ta juyo da sauri ta kalli Sheykh cikin rauni ido cike da hawaye tace. "Hamma Jabeer baya mgn ne? Meyasa yake kuka." Ta ƙarashe mgnar hawaye na zubo mata. Da sauri Jalal ya tsuguna gabanta tabbas ta tuno mishi abu da yawa kam Mameynsu sabida masifar kamar da sukeyu. Haka nan yaji son yarinyar yana ratsa dukkan sasan jikinshi gaba ɗaya. So irin na ƴan uwataka so irin na wa da ƙanwa Cike da mamaki Sheykh yake kallon Jalal da yasa tafin hannunshi yana share mata hawayenta. Wanda ita kuma haka ya ƙara tunzura zubowar hawayen nata. Cikin rawan murya tace. "Hamma Jabeer meyasa yake kuka?". Cikin wani irin yanayi Jamil ya tsuguna shima ya zama sun zagayeta sun sata a tsakiya. Shi kuwa Sheykh a hankali yasa hannunshin bisa kanta cikin rauni yace. "Nima ban saniba Junainah wata ƙil yana tsoron kada ki kada Baby ne ko kuma muryarki ce tayi iri ɗaya da muryar Mamanshi". Cikin shessheƙan kukan da haka nan taji ya kubce mata tausayin mutumin ya rufeta cikin rauni tace. "A a bazan kada itaba, Ummey na ta koya min yadda ake riƙe yara ai lokacin da mukaje gidan Abboi da yarinyar Maman Idris to Ina Maman nashi". Sai kuma ta ɗan musukuta ta gyara zamanta tare da gyara riƙon yarinyar. Cikin sanyi Jamil yace. "Mamanshi bata nan". Cikin zubda hawaye tace. "Ina take?". Tai mgnar da alamun tausayawa. Sheykh ne ya ɗan sunkuyo ya kalli ƙwayar idonta a hankali yace. "Mugayanen magauta sun sabauta rayuwarta sun ɓadda ita". Kanta ta jingina jikin Jalal dake gefenta cikin sanyi da rauni tace. "Ayyah Allah ya isan mata, Allah zai saka mana". Sai ta kuma kalli Yah Jafar ɗin da tsananin kamanninta da Mameynsu ne da kamar murya ya sashi zubda hawaye a hankali tace. "Kayi haƙuri Yaya zamuyi ta mata addu'o'in, kuna Ummey na zata zama mamanku, kuna so ko?". Da sauri Sheykh ya gyaɗa mata kai ganin yadda ta ƙarashe mgnar da zuba musu ido". Affan kuwa gefen Sheykh ya zauna yana mai kallonsu cike da al'ajabin yanayin da suke ciki Especially Jalal da ba kula yara yakeyi ba. Ummi kuwa a can cikin ɗakin Shatu, tayiwa su Aunty Amina iso. Bayan sun zauna ne, Sara data kai kaya kitchen ta kawo musu ruwan. Kana ta fito ta koma Kitchen taci gaba da aikinta Ummi na biye da ita a baya. A falon ta tsaya tare da zubawa ikon Allah ido. Muryar Junainah dake iri ɗaya sak da muryar da bazasu taɓa mancewa da itaba a duniya. Ita kuwa Junainah a hankali ta kalli Ummi data iso gabansu. Tare da kallon yadda suke a hankali tace. "Uhm autar Mamey kawo ɗiyar taki in kaiwa su Inna Amarya ita". Da sauri tace. "Toh". Ta ƙare zancen tana miƙa mata ƴar. Jalal kuwa ido ya zubawa Ummi. Sheykh kuwa juya kanshi yayi yana kallonta yana nazartan kalmarta, itama taga kamar kenan." Ya faɗi a ransa. A fili kuwa murmushi suka ga Jafar yayi tare da miƙewa tsaye murya can ƙasa yace. "Autar Mamey nima haka idona ke sanarwa zuciyata Ummi". Da sauri suka kalleshi. To daga jiya zuwa yau dai sun saba da yayi mgn a fizge sai dai bai kuma ƙarayin wata duk mgnar sa za'ayi mishi. Yana faɗin haka shi kuma ya juya ya tafi. Da sauri Jalal yabi bayanshi. Affan kuwa a hankali ya miƙe ya fita ya nufi falon Hajia Mama. Jamil kuwa sashin Gimbiya Aminatu ya nufa. Shi kuwa Sheykh a hankali ya yunƙura ya gyara zamanshi ya koma bisa kujera, kana ya kalli Junainah dake tsaye tana gyara tarhan da tayiwa ɗan kwalin hijab din jikinta. Cikin yin ƙasa da murya yace. "Wannan ɗayar itace Ummey?". Da sauri ta matso kusa dashi a hankali tace. "A a Ummeynmu tana gida bata zoba. Wannan Aunty Amina ce ƙanwar Dedde, ɗayar kuma Inna Amarya ɗayar kuma Adda Khadija ƙanwar Adda Shatu ne. Na fita kyau ko?". Murmushi yayi tare da cewa. "Sosai ma kuwa, ke mai zubin larabawa". Wani irin murmushi tayi tare da cewa. "Yessss my Hamma ka iya gayan gsky". Sai kuma ta juya ta nufi falon Shatu tana cewa. "Bari inje inga Adda na da kyau". Da ido ya rakata. Jamil kuwa yana shiga ya gayawa Gimbiya Aminatu cewa wasu baƙi sunzo wurin Shatu da wata yarinya mai kama da Mameynsu. Tofa wannan al'amari yasa Gimbiya Aminatu sanarwa Lamiɗo haka, da kanshi yace taje tai musu sannu da zuwa. Yah Jafar kuwa yana shiga, falon shi ya samu Juwairiyya na tsaye. A hankali yaja hannunta suka wuce bedroom ɗinsa. Haka nan yaita maimaita kiran sunanta tana amsawa. Shi kuwa Jalal juyawa yayi ya fita. Affan kuwa a hankali ya kalli Hajia Mama cikin sanyi yace. "Mama ƴan uwan Shatu sun zo, sai kinga wata yarinya mai kama da Mameynmu, ko muryarsu iri ɗaya, anjima kije ki ganta". Cikin tsuke fuska tace. "Toh uban marasa zuciya, kullum kai ke cemin in jene". Da sauri ya kuma juyo ya kalli Rumaisa yayarshi. Dake jan dogon tsaki tare da cewa. "Shi bai san damuwar mutane ba, da kishin uwarsa, kana da rashin kunyar da yarinyar nan kewa Mama kake wani cewa taje taga ƴan uwanta." Idonshi ya kuma juyowa kan Maman tasu jin tana cewa. "Barshi sakarai ni ko ƴar da aka haifanma banje na ganiba bare wata can baƙuwar ba hillatanar daji, mitssssss". Cikin sanyin jiki yace. "Uhumm". Daga nan bai kuma cewa komaiba, baisan komai kan makirci mahaifiyar tashi ba, iya saninsshi tana son su Yah Sheykh fiye da yadda take sonshi sai dai wasu lokutan yana zargin tana da wani manufa a kansu. A hankali ya miƙe ya fita ya nufi Part ɗinsa. Ita kuwa Hajia Mama cikin fidda numfashi ta kalli Rumaisa tare da cewa. "Sai gobe zanje duba jaririyar, kuma zanje da garin batur, tabbas zan zuba matashi a baki. Tana haɗiyewa zai tsistsinka ƴaƴan hanjita ta mutu kowa ya futa, shegu masu yawan haihuwa". Cikin cin daɗin haka Rumaisa tace. "Dai-dai kenan". Gimbiya Aminatu kuwa anayi sallan la'asar taje,. Tabbas itama tayi mmkin kamannin. Koda ta dawo ta sanarwa Lamiɗo da Abba da Gimbiya, cikin al'ajabi Lamiɗo yace. "Yarinyar zata kai shekara nawa?". Da sauri Gimbiya Aminatu tace. "To gsky bana ceba dan irin yaran nanne masu jiki ɗan cafal ba wawan girma ku ba ƙaramin ruwa da wuya ka iya ƙiyasce shekarunta kai tsaye". Wani irin dogon numfashi Abba ya sauƙe tare da cewa. "Shi Muhammad ɗin zai tambayi yayar tata". Galadima kuwa cikin nitsuwa yace. "Uhummm babu shakka akwai abinda ke shirin tabbata daga zantu kan Malam Musa, yace ƴa mace mai kama da ita zata fara zuwa kafin ita. Amman bai saniba ƴartace ko ba tataba, ya kuma ce mana a haihuwar matar Muhammad ne zai sanadin zuwanta. Tabbas bawai munyi imani da abubuwan daya faɗa bane. Wasu ma mun mancesu. Sai dai gashi bayan shekaru goma sha biyu abubuwan daya faɗa sun fara baiyana na aure ba fullatar daji. Sai kuma batun haihuwarta da zuwan yarinyar koda banga ƴarba inaji a jikina itace ƴarinyar dayake nufin". Cikin nitsuwa Abba ya gyara zamanshi a hankali yace. "Ni dai yanzu inga yarinya ce damuwa ta, inji shekarunta. Domin na sani tabbas kafin Aisha ta haɗu da ibtila'in juyewar halinta wlh tanada shigar juna biyu wanda ita kanta bata saniba, saida na gaya mata. dan lokacin baifi kwanaki ba. Kuma har bayan ta juye naci gaba da jin abubuwan da nakeji muddin tanada juna". Cikin rauni ya ƙarashe mgnar. Daga nan sukaci gaba da tattaunawa kan batun. Washe gari yau kwanan Baby uku da zuwa duniya. Ƴan uwa da abokan arziƙi duk sun zo, kab Masarautar Joɗa hatta matar Galadima da take tsohuwa sosai tazo, sai Hajia Mama ce kaɗai bata zoba. Zaune suke a falon Shatu. Lokacin suka dawo daga yiwa Inna Amarya rakiya dan Salmanu yazo ya ɗauke ta ya meda ita gida. Ya rage Khadijah Aunty Amina da Junainah. Zaune suke a falon Shatu, Ummi ce zaune gaban Shatu ta zuba mata abinci a plate ta bazashi yayi sanyi. Kana tana jujjuya zumar data saka mata cikin kunun tsamiyar data dama mata mai citta. Cikin sauƙe numfashi Aunty Amina tace. "Oh ikon Allah ko ina da al'adarsu mu ai mai jego in dai abinci yayi sanyi to bazata cishi ba". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Uhum kinga mu kuma nan sai abincin yayi sanyi ƙalau ma kafin mai jego taci, tai wonka da ruwan sanyi, tasha mai sanyi taci mai sanyi kuma babu abinda ke damunsu". Hannu Shatu tasa ta amshi ɗan ƙwaryar da kunun yake ciki ludeyin dumar tasa ta ɗan ɗebi kunun ta kurɓa, ido ta ɗan lumshe dan tana jin daɗin shi a bakinta. Ita kuwa Aunty Amina riƙon da tayiwa Babyn ta gyara tare da cewa. "Gari banban Allah ɗaya kenan". Junainah ce ta miƙe tsaye alamun zata fita. Shatu ce ta ɗan kalleta tare da cewa. "Ina zakije Junnu?". Ba tare da ta juyo ba tace. "Zanje kitchen wurin Adda Khadijah da Sara in tayasu girki". Sai kuma tayi sauri ta ɗan ja da baya, ganin Sheykh da sauri tace. "Hamma Jabeer ina kwana". Murmushi ya ɗan yi tare da cewa. "Lfy lau Alhamdulillah". Sai kuma ya ɗan juya tare da cewa. "Yauwa Junainah jeki kira Adda Shatu kice tazo da Baby". To tace kana ta koma ciki shi kuma ya nufi ɗauki sa. Bayan ta gayawa Shatu saƙon nashinne ta juya zata fita kuma tayi kiciɓis da Hajia Mama da hadimanta. Cikin zuba mata ido Hajia Mama ta ɗan kauda kai ta wuce. Ummi ce ta ɗan miƙe tare da cewa. "Sannu da zuwa". Cikin sakin fuska tace. "Yauwa Ummin Jabeer ina kishiyar tawa kishiya ban haushi". Ta ƙare mgnar tana zama bisa kujerar dake gefen Ummi ya zama suna fuskantar juna da Shatu. Cikin sakin fuska Aunty Amina tace. "Ina kwana?". "Lfy lau Alhamdulillah ya yar jikallena?". Hajia Mama ta faɗa. "Gata lfy lau". Aunty Amina ta faɗa tana yunƙurin tashi zata miƙa mata ƴar. Da sauri Shatu tace. "A a Aunty Amina kada ki bata ita dan Allah". Da sauri tace. "Sabida me?". Ajiye kwaryar hannunta tayi tare da cewa. "Haka kawai". Ta ƙare mgnar tana miƙo hannun ta amshi ƴar. Tare da jan dogon tsaki kana a hankali tace. "Aniyar kura tabi daji aniyar moɗa tabi randa, wannan dai nan gani nan bari da izinin ubangiji". Ta ƙare mgnar tana juyawa ta fita ta nufi falon Sheykh. Hajia Mama kuwa gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi da masifar takaici da tsanar Shatu da abinda ta haifa dama wanda ya bada cikin dan sune gagararrunta. Cikin takaici ta miƙe ta fita. Hadiman ta na biye da ita a baya. Wani irin murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ɗan Adam kenan mugun icce kai dai kaga mutun baka san me accikin zuciya nai ba". Cikin mamaki Aunty Amina tace. "Ikon Allah kai wannan gida naku yana cike da sarƙaƙiya". Da sauri Ummi tace. "Sosai ma kuwa". Har bedroom ta wuce. Zaune ta sameshi bisa bakin gado. Da sauri ya buɗa mata hannunshi, ba musu ta raɓa jikinshi. Ruggume ta yayi tare da sauƙe numfashi a hankali yace. "I miss you so much". Ƙamshin jikinshi ta shaƙa tare da cewa. "I miss U to". Gyara rungumar da yayi mata yayi, tare da amsar Baby cikin manna mata kiss a goshi yace. "Baki tambayi sunan ta ba". A hankali tace. "Kayi mata huɗuba ne?". Da sauri yace. "Tuntini ma tun randa nace miki ko kinada sunan da kike son saka mats, kikace insa sunan Mamey duk da ban gaya miki wacece itaba". A hankali ta manna kanta da ƙirjinshi tare da cewa. "Toh ai nasan itace mafi ƙololuwar soyuwa da daraja a wurinmu, tunda koda ban santaba baka gaya min komai a kanta ba. Na fahimci tafi ko wacce mace daraja a garemu, tunda in kaji wuya ita kake kira kana raki in kaji daɗi ma ita kake fara tunowa. Nasan tanada matsayi na musamman a rayuwarmu". Murmushi yayi tare da cewa. "Aish sarkin falsafa, to nasa mata sunan Mamey kamar yadda kikace". A hankali tace. "Me sunan?". Murmushi mai sanyi yayi tare da yin ƙasa da murya yace. "Aisha shine sunan Mamey na, kuma sunan matata sunan ƴata ta fari kuma". Cikin murmushi tace. "Masha Allah sunan Ummey nama Aisha ne". Ruggume ta yayi tare da cewa. "Iye zuriyar Aysha's kenan". Da sauri ya zaro ƙaramar wayarshi. Murmushi yayi ganin 3bala'i. Da sauri ya ɗan janye jikinshi gareta. Amsa kiran yayi tare da karawa a kunne tare da cewa. "Uhumm ya akayi ne". Cikin huci Hajia Mama tace. "Jahan wlh zan kashe mutanen nan baki ɗaya in huta". Da sauri ya miƙa ya nufi cikin Bathroom yana juyowa yana kallon Shatu cikin yin ƙasa da murya yace. "Dame zaki kashesu?". A hankali Shatu ta bishi da ido, fahimtar kamar yana buƙatar sirrine baison tasan abunda zai tattauna a wayar ne yasa ta miƙe a hankali ta nufi side ɗin ta. Bayan ta gyarawa jaririyar kwanciya bisa gadonshi. Shi kuwa Sheykh a hankali ya sauƙe ajiyan zuciya jin Hajia Mama na cewa. "Wallahi nayiwa kaina al'ƙawarin tabbas ranar suna zan kashe ƴarinyar nan cikin buzun al'ada da za'a naɗeta, tabbas da ita zan fara kafin inbi ta kan uwar da uban su ƙannen dama a tafin hannuna suke, yayan kuwa majanunine". Cikin danne tashin hankalinsa yace. "To wai meya hatsalaki hakane?." A fusace tace. "Yanzu na baro ƙofar Sheykh wlh naje da garin batur a hannuna zan turawa ƴar shi a baki, wannan fitsarerriyar ƙauyen matar tasa ido cikin ido tace. Kar a bani ƴarta ita bata so. A gabana ta amshi ƴar ta fita inaga ɗakin shegen ustazun ta tafi". Cikin danne dariyarsa yace. "To bari yanzu ina cikin uzuri anjima zanzo muyi mgnar dake". To tace kana ta katse kiran". Shi kuwa Sheykh a hankali ya fito. Ganin bata ɗakin ne ya sashi sauƙe ajiyan zuciya. Yana murmushin wautar Hajia Mama Ya fito falo. Dai-dai lokacin kuma Junainah data shigo da tray'n breakfast ɗinshi ta ajiye bisa Dinning table. Shiru tayi tana jin kukan tsuntsayen dake cikin Garden ɗin, a hankali ta juyo ta sauƙa kan steps ɗin. Ganin tsaye ne yana kallonta yasa ta ɗan matsoshi. A hankali tace. "Hamma Jabeer wannan kukan tsuntsayen fa a ina suke?". "Cikin Garden suke nan baya". Da sauri tace. "Ayyah dan Allah ta ina hanyar zuwa wurin yake". Cikin tsareta da ido yace. "Zaki jene?". Kai ta gyaɗa alamar eh. "Toh me zakiyi a can?". Ya kuma tambayarta "Zanje inga tsuntsayen ne ina son kukansu daɗin ji". Kai ya jinjina tare da cewa. "Gacan hanyar muje in rakaki". Yayi mgnar yana yin gaba tana biye dashi a baya. Dai-dai lokacin kuma Lamiɗo da Galadima da Abbanshi suna ciki can bakin ruwan waya sukeyi da Jadda. A hankali ya tura ƙofar forko kana ya turo ta biyun. Cikin sauri ta biyo bayanshi tare da cewa. "Wow masha Allah". Sai kuma ta lumshe idonta tare da buɗa hannayenta, tana binshi a baya. Juyowa yayi ya kalleta bisa alamu duk tana jin daɗin iskar dake kaɗawan. A hankali ta fara juyi tana gaba. Da sauri yace. "Ke Junainah tsaya a nan". Ya faɗa lokacin data nufi inda ɗawisun su yake, da sauri ya nufota, sanin muddin bawai ya gabatar da ita gareshi bane zaiyi ta yagusheta sai in jinin masararutar Joɗa ce ita to nan babu abinda zasuyi mata. Ita kuwa Junainah hango ɗawisun a gefenta ne, yasa tayi sauri ta nufi inda yake. Shima ɗawisun kanta ya nufo gadan-gadan. Da sauri Lamiɗo da Abba da Galadima suka zuba mata ido. Shi kuwa Sheykh da sassarfa ya biyota yana cewa. "Junainah! Junainah!! Dawo nan zai ji miki ciwo". Da ƙarfi ya rumtse idonshi lokacin daya hango ɗawisun ya iso gab da ita ya buɗe fikafikansa a zatonshi ya guneta zai farayi. Ita kuwa Junainah wani irin murmushi tayi tare dasa hannun kan ƙunɗun ɗawisun ta fara shafawa, shi kuma fiffigensa ya fara kaɗawa yana jujjuyashi. Da sauri Sheykh ya buɗe idonshi jin shiru sai dariyar ta da yake juyowa. Lamiɗo kuwa da Galadima da Abbanshi da sauri suka miƙe tsaye suka nufosu cike da al'ajabin ganin ɗawisun ya fara zagayata kamar yadda yakeyiwa dukkan jinin masararutar Joɗa. Zagayeta sukayi gaba ɗayansu suna kallon tsananin kamarta da Mameyn Sheykh. Shi kuwa Sheykh cike da mamaki ya zuba mata. Ita kuwa idonta a lumshe tana jin yadda Ɗawisun ke goga mata fikafikansa a fuskarta. Cikin gamsuwa Lamiɗo yace. "Tsuntsuwa tana shunshunar jinina". Da sauri ta buɗe idonta jin muryar mutun. Shi kuwa Sheykh Jabeer hannunshi yasa ya kamo nata, da sauri ta matsoshi tare da cewa. "Sannunku ina kwana". A hankali Abba ya ɗan matsota hannunshi yasa ya dafa tsakiyar kanta. da sauri tasa hannunta kan nashi ta dafe hannun nashi a kanta. Murmushi mai faɗi Abba yayi tare da cewa. "Allah yayi miki al'barka". Cikin jin daɗi tace. "Amin Amin Baba ngd". Shi kuwa Sheykh murmushi yayi fahimtar tarbiyyar su Shatu da Junainah ɗaya ne suna masifar jin daɗi in akayi musu addu'a da sanya musu al'baka". Da sauri Galadima yace. "Me sunanki?". Buɗe idonta tayi tare da cewa. "Sunana Junainah Aliyu Garkuwa". Da sauri Lamiɗo yace. "Shekarun ki nawa ne?". Murmushi tayi tare da cewa. "Kaka shekaruna fa da yawa". Murmushi Abba da har yanzu hannunshi ke bisa kanta yayi tare da cewa. "Gaya mana mana". Cikin nitsuwa tace. "13". Wani irin dogon numfashi mai nauyi Abba ya sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah". Sai kuma ta janye hannunshi daga kanta cikin sanyi yace. "Uhumm yanzu abu biyu ya rage, muga ko tanada tambarin jinin masarautar Joɗa a tsakiyar kanta kana muga mahaifiyarta". Da sauri tace. "Ummey na tana gida, bata zoba". Cikin son fahimtar manufar Abba Sheykh yace. "Kuma kuna irin zaton da nakeyi ne?". Da sauri Lamiɗo yace. "Aimu namu ma yafi naka ƙarfi". A hankali yace. "Toko dole mubi komai a hankali". Kai suka jinjina kana Sheykh ya nuna mata hanya tare da cewa. "Koma ciki ina zuwa". To tace kana ta juya ta tafi. Su kuwa zama sukayi. A nan Sheykh yake basu lbrin batun ƙarar da ya shigar kan case ɗinsu Gaini. Tuni Affan kuwa ya tattara dukkan hujjoji da shaida a matsayinsa na lawyer mai cikar ƙwarewa. So yama tafi shida Sulaiman da Malam Abubakar. Gobe za'a zauna a kotun. Alhamdulillah yau kwana biyar da haihuwar Shatu. Anata shirye-shirye bikin suna. Su Umaymah ma yau tunda safe suka iso, ita da Hibba da Aunty Rahma da Mamma da Ishma. Sai Haroon da Jannart ɗinsa. Gaba ɗaya gidan ya cika da ɓakin. Junainah kuwa tun kafin su iso take Part ɗin Mami matar Affan da yaransu Zahra'n Hamma Yusuf ce da tazo take zana musu lalle. Gaba ɗayansu cike suke a falon. Sai hadimai dake can kitchen sunata faman aiki. Umaymah ce riƙe da jaririyar cikin jin daɗi tace. "Alhamdulillah yau gani riƙe da Yar Jazlaan. Alhamdulillah ƴarinya kuwa sak Mamey. Cikin sauri Aunty Rahma ta ajiye cup ɗin da take shan ruwan da shi tare da leƙo fuskar ƴar tace. "Alhamdulillah kuce dani take kama". Murmushi Sheykh yayi tare da cewa. "Sosai ma kuwa". Jamil ne ya ɗan jujjuya kanshi tare da cewa. "Yoh ai ke masu kama dake sunada yawa Adda Shatu ina Junainah ne". Khadija ce ta ɗan kalleshi tare da cewa. "Uhumm Junainah kuwa Sarkin yawo tun da sassafe ta tafi gidan Affan har yanzu bata dawoba". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Tanada saurin sabone ba ruwanta kowa natane". Kai Sheykh ya jingina jikin kujera yana kallon Shatu dake lumshe idonta alamun bacci takeji. A hankali Jalal ke tafiya tana riƙe da yatsarsa manuniya tana ɗigirgire da sawunta. Wanda takalmanta ke hannun Jalal ɗaya cikin yawan surutunta tace. "Yah Jalal lallena zai ɓaci fa. Ni mu zauna a nan sai ya bushe mu tafi". Sunkuyowa yayi ya ɗan kalleta fuska ɗauke da murmushi yace. "Mun isofa Junnu saura kaɗan". Tura baki tayi dai-dai lokacin da yasa hannunshi ya tura ƙofar tare da sallama a bakinshi. "Ni dai bana son Junnu Hamma Jabeer yace ba kyau ace Junainah yafi daɗi". Tayi mgnar tana ƙara riƙo hannunshi. Da sauri Umaymah ta kalleta ta kuma juyo ta kalli Ishma dake lafe jikin Shatu. Ita kuwa Junainah da sauri ta saki hannun Jalal tare da rugowa a guje tare da cewa. "Lah oyoyo Ummey na". Tayi mgnar tana nufo gaban Aunty Rahma data hango tamkar Ummey'nta. Da sauri ta tsaya tare da cewa. "Laah". Sai kuma ta juyo ta kalli Ishma kana ta kalli Aunty Rahma. A hankali ta ɗan matsa kusa da Shatu cikin yanayin jin kunya tace. "Ina kwana". Ta ƙare mgnar tana kallon Aunty Rahma da suma duk ita suke kallo. Da sauri Mamma tasa hannunta ta kamo hannun ta jawota kusa da ita kusan a tare sukace. "Ikon Allah kenan dan Allah kalli kama". Murmushi Shatu tayi tare da cewa. "Ai natama dana Ishma wasane na Ummey na da Aunty Rahma shine gaske". Cikin sauri Jalal yace. "Dan Allah yaushe Ummeynki zata zo mana ne kam". Murmushi Aunty Amina tayi tare da cewa. "Ai kam zata zo wata rana amman ba yanzuba". Da sauri Aunty Rahma tace. "Ai kuwa in sha Allah mu kam zamuje mu ganta". Junainah ce ta ɗan lafe jikin Mamma tana kallon Umaymah a hankali tace. "Itama ai zata zo taga Baby". Murmushi Umaymah tayi tare da shafa fuskarta. Hibba kuwa Jawo Ishma tayi ta ajiyeta kusa da Junainah hota ta fara ɗaukansu tana cewa. "Masha Allah tagwayen kamanni". Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa. "Wlh kuwa". Ranar dai haka suka wuni. Anata hira da raha. Ranar suna bayan sallan asuba, aka raba goro da dabino. Kana akayi yanka yarinya taci sunan Ummey kuma Mamey Aisha. Jamil na shigowa ya faɗawa Umaymah dasu Mamma dake cike a falon. Da sauri Hibba tace. "To da wanne sunan za'a kirata?." Shiru Shatu dake cikin shiga ta al'farma tayi tana kallonsu. Khadija ce ta ɗan gyara zama tare da cewa. "Afreen yayi". Da sauri Jamil yace. "Sosai ma kuwa kin iya zaɓi mai kyau kamar yadda kike mai kyau". Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa cikin kunya, sai kuma ta tashi da sauri tayi falon Shatu jin Jamil ɗin na cewa. "Umaymah tayi ko surkaki ce". Ya ƙare mgnar yana kallon Shatu. Murmushi sukayi tare da cewa. "A tayi sosai ma kuwa". Sai kuma yace. "Ko dai baza'a bani ita bane Adda Shatu?". Da sauri tace. "A a ni kam banceba ba ruwana, ai ina ganinku bini-bini kuna tare". Sheykh da yanzu shigowarsa ne yace. "In ka nitsu mu baka ita in Kuma baka bar ƙelle-ƙellen idoba da kallon mata mu habaka its". Ƙeyarshi ya sosa tare da cewa. "A ai yanzu na girma na bari ko Yah Haroon." Ya ƙarashe mgnar yana kallon Haroon dake bayan Sheykh. Dariya sukayi baki ɗayansu. Shi kuwa Haroon zama yayi gefen Mamma tare da cewa. "Ai kam yanzu ka girma". Ummi ce ta fito daga kitchen da akoshin cike da hanta gashin tukunyar da akayiwa Shatu. Sai Jannart kuma riƙe da gashin da tayi musu nasu daban. Sara da Larai kuwa da sauran duk riƙe da manyan Foodflaks suka shigo dasu a hannunsu. Kana suka koma suka dauko plates da cups da spoons. A tsakiyar falon suka ajiyesu. Nan suka taru gaba ɗayansu suka zauna a falon. Harda Junainah. Aunty Amina kuma da Khadijah da Shatu falonta suka tafi. Shi kanshi Sheykh a nan kusa da Umaymah ya zauna a plate ɗaya sukeci shida Haroon. Ishma da Junainah. Jannart da Hibba da Aunty Juwairiyya. Rahma Kuma ita da Mamma Umaymah kuwa ita da Ummi. Jalal da Jamil. Affan kuwa yana can Abuja bai dawoba shida Sulaiman da Malam Abubakar sai dai Alhamdulillah shariya tayi kyau babu jeka ka dawo kasan cewar akwai manyan shaidu kuma ga yawan Addu'o'in iyaye da yan uwa kan su Gaini da Addu'o'in masallatan jumma'a kana ga taimakon gskya. Da samun ƙwararren lawyer da kuma sa bakin babban mutum Lamiɗo da Jadda da kuma shi kansa Sheykh. A ranar kotu ta wonkesu tsab. Kana akayi ram da Dineal dama sauran ɓata garin jami'an tsaron kasar da suke da hannu cikin irin wannan kitimurmurar. Shi kuwa Sheykh Affan ya gaya mishi komai amman yaƙi ya yardama suyi mgnar da Shatu da zaran ta fara mishi mgnar sai ya zille yafi son yayi mata ba zata. Bayan duk sun gama cin abinci ne, kowa wacce ta fesa wonka da kolliya Sosai sukayi kyau cikin shiga ta al'farma, Hajia Kubra ma tazo. Dama sauran abokan arziki. A hankali Sheykh ya meda ƙofar ɗakinshi ya rufe, tare da amsa kiran Hajia Mama. Dariya mai sauti tayi tare da cewa. "Hahaha shegu zanyi mgninsu yau. Tuni fatar ragon sunan ya shiga hannuna na gama yin shirina har na meyar musu da ita. Da sauri cikin tsoro yace. "Toh me kikasa a cikinta". Dai-dai lokacin kuma sairkin al'adun Sunan masarautar Joɗa ya shigo falon wurinsu Umaymah tare da Gimbiya Aminatu da Yana riƙe da fatar ragon sunan. Bayan sun zauna ne ya sun gaisa ya shimfiɗa fatar ragon sunan. Tare da miƙowa Ummi dake riƙe da Afreen yace. "Masha Allah kawo Aisha ƴar Aysha jikar Aisha mu cika mata masakinta". Da sauri Ummi ta miƙa mishi Afreen dake naɗe cikin shawul fari ƙal mai taushi da ɗaukan, ido. Hannunshi yasa ya fara zare Shawul ɗin yayi kana ya fara cire mata kayan jikinta ya rage daga ita sai Pampers. Aunty Rahma ce ta ɗanyi ajiyar zuciya tare da cewa. "Kai wannan masarautar Joɗa taku tanada tsarabe-,tsaraben al'adu masu masifar tsauri. Allah ya baku cikekken ahlul sunna ya mulki masarautar shine kaɗai zai kauda al'adun ya wanzar da sunna, ina dalili a ninke yarinya cikin ɗanyen fata ayi ta garata a tsakiyar ɗakin mahaifiyarta ai ko ba'ayi hakaba dole zata san ɗakin uwartace". Umaymah ce ta ɗan gyara zamanta tare da cewa. "Toh ya zamuyi tunda abu nasune". Gimbiya Aminatu ce tayi murmushi tare da cewa. "Watan wata rana dai tabbas al'adun zasu kau sunna ta wanzu in wanda muke zaton ya yarda ya amshi masarautar". Allah ya sa haka. Umaymah tace. Amin Amin sukace baki ɗayansu. Suna masu kauda kansu kan fatar dan wani irin warin da basu gane kamsaba da fatar keyi wanda dole in kaji zakayi zaton ƙarnin ɗanyar fatarne. Wanda fiyafiyen ya gauraye dashi sai dai shi kanshi sarkin al'adun sunan kauda kanshi yakeyi dan azabar warin fiyafiyar da Hajia Mama ta turbuɗa cikin fatar. Kansu suka ɗan kakkauda tare da cewa. "Dan Allah kayi maza ka gama ka fito da baiwar Allah". Cewar Umaymah da Mamma. Shi kuwa Sarkin al'adun suna murmushi yayi tare da naɗa Afreen cikin fatar ragon sunan, da Hajia Mama ta gama zazzaga mata madarar fiyafiya mai masifar ƙarfi. Sai dai da yake fatar a ninke take yana kuma warewa ya naɗe da sauri to sai ya zama kamar a rufe yake, shiyasa basu ji wari sosai ba. Dan duk wari shi ai in a rufe yake bakajin warin sosai. Cikin murmushi mugunta ya haɗe yarinyar ya ninke ciki ya matse da ƙarfi kana ya ɗagata ya nufi Bedroom ɗin Shatu. Zaune ya sameta bisa bakin gado. Tayi masifar kyau cikin wata dakekkiyar Getzner Orange color mai masifar kyau da sheƙi. Khadija na tsaye gefenta tana ninke ɗan kwalin zatayi mata ɗauri. Da sauri ta ɗago kanta ta kalli Sairkin al'adun Suna cikin mamaki tace. "A bawan Allah ya da kawo fatan rago kuma har cikin ɗaki". Cikin yin ƙasa da kai yace. "Al'adar ranar suna zamuyi". Hannunta tasa ta dafe kanta kana ɗaya hannun ta ɗaurashi kan ƙirjinta dake harbawa da azaban ƙarfi da sauri-sauri kuma. Aunty Amina ce tace. "Kai gsky yana wani irin wari fa". Ummi dake biye dashi a baya da ita da Umaymah da Gimbiya Aminatu ne suka haɗa baki wurin cewa. "Toh ka fara mana". Juyowa Khadijah kam tayi ta zauna tana kallon ikon Allah. Itama Aunty Amina hannu tasa ta dafe haɓarta tana kallon ikon Allah. Dan dagasu har Shatu basuma gane cewa. Afreen ce a naɗe a cikiba. Shi kuwa a hankali yake komai yana mai jin yadda yarinyar take mutsu-mutsun neman ceton rai sai ƙara danneta yakeyi. Ƙarshen ginin ɗakin yaje kana ya sunkuya ya ajiyeta tare da garata ta gangaro har gaban gadon. Tuni zuwa yanzu numfashin yariyar in ya fita baya komawa. Gaba ɗaya fatan jikinta yayi jazir idanunta sun ƙaƙƙafe. A can ɗakin Sheykh kuwa cikin tsananin hatsala da gajiya da dariyar muguntar da Hajia Mama ke kerketa mishi cikin kunnensa tsawon lokaci a tsale yaja tsaki tare da cewa. "In kin san bazaki gaya minba meyasa kika kirani ina tambayarki me kikasa cikin fatar ragon sunan kina tamin dariya". Cikin dariyar mugunta tace. "Hahahahahhh madarar fiyafiyar mai surke da garin sukudaye na turbuɗa cikin fatar da nasan yanzu ana can an naɗe musu ƴar tasu a ciki, kafin miti biyar da za'ayi ana garata ta zama gaw..." Cikin wani irin tashin hankali ruɗani da firgici da gigita ya cilla wayar ya liƙata da jikin gini a take ta buɗe batir ɗin ya rabu da wayar. ba tare daya bari ya ida jin me zata ceba. Cikin tsananin tashin hankali ya fito da gudu. Gaba ɗaya jikinsa tsuma da karkarwa yakeyi tamkar mazari namfashinsa tamkar zai bar gangar jikinsa. Daga falonshi yake rabkawa Shatu da Umaymah kira da ƙarfi yana cewa. "Aysha! Aysha!! Umaymah! Umaymah!!! Ummi! Kada ku bari asa Ƴarinyar nan cikin fatar nan". Da sauri Aunty Rahma da Aunty Juwairiyya da Haroon da Jannart suka miƙe tsaye. Da sauri Haroon ya nufi falonshi su Jamil ma kan tashi tsaye sukayi jin yadda yake mgn da azaban ƙarfi. Kiciɓis sukayi da harun. Da ƙarfi yace. "Haroon ina Aysha ina Baby Ina Umaymah?". Cikin tsoro Aunty Rahma tace. "Suna ɗakin Shatu ana al'adar fata". Da ƙarfi ya ture Haroon dake gabanshi. Cikin tsananin masifar tashin hankali da ruɗani ya nufi Bedroom ɗin Shatu. Wanda haka yasa suka kab suka bishi a baya. Da sauri Shatu ta miƙe tsaye tare da cewa. "Na'am Yah Sheykh". Sabida jin yadda yake abka mata kira tare da cewa. "Aysha Aish Ina kike ina ƴata?". Kiciɓis sukayi a bakin ƙofar shigowa ita zata fita shi zai shiga. Da sauri tasa hannun shi ya tureta har saida ta faɗa jikin Umaymah sabida hango Sarkin Al'adun suna yana gara Afreen dake cikin fatar a ƙasa a tsakiyar ɗakin. Cikin wani irin masifeffen tashin hankali yasa hannunshin da ƙarfi ya ture sarkin al'adun sunan Ya faɗi ƙasa tib. Cikin rawan jiki da tashin hankali Umaymah da Ummi sukayi kanshi. Aunty Amina da Khadijah kuwa cikin mamaki suka zuba mishi idanu. Su Aunty Juwairiyya kusa duk shigowa sukayi cike da mamaki. Ita kuwa Shatu da sauri ta gyara tsayuwarta tare da nufoshi. Ganin yadda gaba ɗaya jikinshi ke karkarwar tamkar mazari. A gigice ya sunkuyo ya zaro Afreen dake naɗe cikin fatar da sauri ya fara worwore fatar. Gani yakeyi ma tamkar baya sauri murya na rawa hankali a tashe yake cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil Aish zasu kashe mana ita." Dai-dai lokacin kuma ya gama woreta. Cikin wani irin tashin hankali Ya juyo a gigice yace. "Innalillahi Umaymah sun kashe min ita". Jiki na rawa hankali a tashe Umaymah ta iso gabanshi da sauri tasa hannunta ta amshi yarinyar ganin yadda jikinsa ke karkarwar. Da Sauri ta juyo gaban Gimbiya Aminatu tare da cewa. "La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam. Ta rasu." Da ƙarfi Shatu tace. "Innalillahi Umaymah me kikace kada kice haka dan Allah ku duba da kyau". Cikin tsananin tashin hankali Gimbiya Aminatu ta amshi Afreen jujjuya yaya tayi da sauri tace. "Ta...! By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: "Ta Suma ne!". Da sauri Sheykh ɗin ya taso, tare da sa hannunshi ya amsheta, da sauri ya juya. Itama Umaymah da sauri tabi bayanshi. Side ɗinsa ya koma da sauri key ɗin motarsa ya ɗauka Umaymah na biye dashi a baya kana Haroon ma na biye dasu a baya. Shatu kuwa cikin wani irin kuka mai rauni daya kubce mata ta koma bakin gado ta zauna gaba ɗaya jikinta kerma yakeyi. Shi kuwa Sarkin al'adun suna, da rarrafe ya fita ya bar ɗakin yana fita falon ya miƙe a guje ya bar Part ɗin da sauri Jalal ya mara mishi baya, kafinma ya bar Part ɗin ya damƙeshi Part ɗinsu ya wuce dashi. Mamma kuwa da Gimbiya Aminatu gefen Shatu suka zauna. Hannunta tasa bisa kafaɗarta a hankali tace. "Kiyi haƙuri Aysha in sha Allah babu abinda zai samu ƴarki da izinin ubangiji, zata samu lfy". Cikin rauni murya na rawa ta juyo ta kalli Mamma ido cike da hawaye tace. "Mamma me tayi musu, da zasu cutar da ita ba tare da haƙƙinta ba, shike nan yanzu duk magautan Yah Sheykh sai su dawo kanta, kawai dan ta kasance ƴarsa, Mamma ya zamuyi". Da sauri Gimbiya Aminatu tace. "Babu komai Shatu da izin Ubangiji baza suci nasara a kankuba". Aunty Rahma da Aunty Juwairiyya da Jannart kuwa jiki a mace suka koma falon Shatu suka zauna. Gaba ɗaya jikin kowa yayi sanyi. Khadija da Aunty Amin kuwa tsoron al'amarin masarautar Joɗa ne ya rufesu. Da sauri Mamma ta miƙa ganin Shatu ta zabura ta miƙe tsaye da sauri tare da tallabe breast ɗinta. "Aysha zauna". Murya na rawa tace. "Mamma maman Afreen na tsastsafo da ruwa, Ina Yah Sheykh ya tafi da ita? Ni kam zanje inga halin da take ciki". Ajiyan zuciya mai nauyi Hajia Kubra dake tsaye gefen Mamma tace. "Asibiti suka tafi, kuma insha Allah zataji sauƙi". Kai Gimbiya Aminatu ta gyaɗa tare da cewa. "Sosai ma kuwa tunda har kikaji haka to ta farfaɗo ne". Dai-dai lokacin kuma Umaymah dake tsaye bakin ƙofar ɗakin da Sheykh da wasu manyan likitocin su na Valli Hospital Suka shiga da Afreen a sume. Ta sauƙe wata ƙaƙkarfan ajiyan zuciya jin kukan da Afreen ta cillara da ƙarfi. A cikin ɗakin kuwa. Kusan a tare sauran likitocin suka sauƙe ajiyan zuciya tare da ɗagowa suna kallon Sheykh daya ruggumeta jikinshi tare da cewa. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!". Sai kuma ya juyo da sauri ya kalli Dr Lukman Ibrahim babban likitan yara kenan na asibitin na cewa. "Ina Maman baby a yi maza a bata mama tasha shi zai taimaka wurin ƙara ƙarya ƙarfin gubar". Da sauri Sheykh yace. "To". Kana ya juya. Yana fitowa Umaymah tabi bayanshi. Tana tambayarshi. "Ta farfaɗo ko?". Cikin ƙara saurin tafiyarsa yace. "Eh Umaymah". Suna shiga motar yaja da sauri ya nufi masarautar Joɗa a guje. A can part ɗinsu Jalal kuwa. Wani irin gigitaccen mari Jalal ya yarfawa Sarkin al'adun suna. Wanda yasa shi jin fitsari ya kubce mishi. Ba tare daya gama dawowa hayyacisa ba ya kuma jin saukan wasu tagwayen maruka a gigice ya kurma ihu tare da cewa. "Wayyoooooooo Allah na na shiga uku ni ilu Jalaluddin kayi haƙuri". A fusace Jalal yasa ƙafarshi ya taɗe sawunshi har saida ya faɗi tib! A ƙasa hannunshi yasa ya tallabe ƙeyarsa tare da sakin wani gigitaccen ihu. Da sauri Jalal yasa ƙafarshi ya taƙa yatsun hannunshi tare da cewa. "Sheeeyyt rufe min baki, uban me kuka sa a cikin fatar ragon sunan?". Cikin kerma da zare ido yace. "Wlh bani ne na sakaba". Ƙara taka yatsun yayi tare da murjesu da ƙarfi yace. "Me akasa a cikin fatar ragon? kuma waya saka? Nawa kuma aka biyaka?". Cikin sakin fitsarin azaba yace. "Madarar fiyafiya ce aka saka cikin fatar. Hajia Mama ce ta saka! Dubu ɗari bakwai ta biyani". Wani irin murza yasun yayi da ƙarfi tare da cewa. "Okay bari in daddage yatsun hannun da zaiyi kisan kai da amsar kuɗin yin kisan kai ɗin". Zuwa yanzu ya gigice ihu kawai yakeyi, shi kuwa Jalal rufe Windows ɗinsa yayi ya mishi ɗan karen duka. Kana ya kira ɗaya daga cikin ma'akatansu na jami'an sirri na soja yazo ya tafi dashi. A nan falon Shatu kuwa, a hankali Jamil da Yah Jafar Suka koma suka zauna. Yana gaba Umaymah na binshi a baya a haka suka shigo. "Aish Aish Aysha!". Ya ɗan ƙare kiran da ƙarfi. Da sauri Shatu ta miƙe da sauri ta nufo falon. Ummi da sauran na biye da ita a baya. Aunty Amina da Khadijah kuma suna zaune. Da sauri ya kamo hannunta bisa kujera ya ajiyeta gefen Aunty Rahma da sauri yace. "Bata nono yi sauri". Da sauri tace to tare da fara kiciniyar ɗago rigarta. Ina gani yake bata sauri shiyasa cikin sauri ya ɗaura mata ita kan cinyarta. Kana yasa hannunshi ta baya ya zuge zip ɗin rigar yayi ƙasa da ita. Hannunshi yasa ya fito da breast ɗinta na dama. Tare da ɗago kan Afreen daketa fidda wani irin numfarfashi alamun har yanzu numfashin bai dai-dai taba. Da sauri kuwa ta damƙi nonon tare da fara zuƙa. Wani irin dogon ajiyan zuciya mai nauyi suka sauƙe a tare shi da ita. Lokaci ɗaya kuma hawayensu ya kwaranyo bisa fuskokinsu. Cikin sanyin murya yace. "Alhamdulillah Aish kada kiyi kuka kiyi mata addu'o'in samun lfy ke wuce addu'aki gareta bata da hijabi". Hannunta tasa tana ƙara tallaɓe kan Babyn murya na rawa tace. "Yah Allah ka bawa wannan baiwa taka lfy ka yaye mata wahalar shaƙar numfashi ka sauƙaƙa mata shi al'farmar Annabi da al'ƙur'ani." "Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati my Dear". Ya faɗa yana share mata hawayen fuskarta da hannunshi na hagu. Su kuwa saura kab ajiyan zuciya sukayi tare da cewa. "Alhamdulillah".. Sai lokacin ya ɗan kalli Aunty Rahma dake gefen Shatu tana zubda hawaye a hankali yace. "So sorry my Aunty in Sha Allah babu komai likita yace, da shayar da ita shi akayi zaifi mata illa yanzu kuma shaƙane an mata duk wani taimakon gaggawa daya kamata". Cikin gamsuwa ta gyada kai. Sai kuma ya ɗan taso tsaye sai lokacin yaga yawansu. A hankali ya ɗan sunkuyar da kanshi cikin sanyi yace. "Gimbiya Aminatu in sha Allah daga yau wannan al'adar zata kau a masarautar Joɗa dama duk wasu tarkacen al'adun daba addiniba ki gayawa Lamiɗo". Cikin jin daɗi tace. "Ai ba ita kaɗai ba in dai ka yarda ka mulki masarautar Joɗa duk wata al'ada na masarautun gargajiya kana da damar datsesu ka wanzar da Sunnah". Wani irin dogon ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe. Tabbas masarautar Joɗa tana buƙatar sabon Sarki sabon tsari sabon zubi bisa koyarwar musulunci da sunnar manzon Allah a kauda bidi'a a kawo sunna. To amman shi baida ra'ayin mulki. Cikin sanyi yace. "Gyaran ba lallai sai ni ɗaya zan yi shi ba ai, kuma ko bani ke mulkiba zan iya bada shawara in an yarda a amsa". Cikin sauri Umaymah tace. "Idan dai har kana son kauda al'adun a wanzar da sunna to dole ka mulki masarautar Joɗa da kanka". Kanshi kawai ya jingina jikin kujerar kana a hankali ya sunkuyo yana kallon Shatu dake cewa. "Baiyi mulki Bama Umaymah ana neman ransa da na ahlinsa". Lamiɗo da Galadima dake shigowa ne dan jin lbrin abinda ya faru a bakin Jalal ne. Suka haɗa baki wurin cewa. "Ƙi gudu sa gudu, Shatu ke muke zaton zaki bashi ƙarfin guiwa kuma sai ki karaya da wuri haka." Da sauri su Umaymah kab suka ja da baya suka basu wurin zama. Suna zama dai-dai lokacin kuma Shatu ta zare mamanta daga bakin Afreen ɗin cikin tsoron ganin yadda ta ke ɗan yunƙuri tana kwaro amai. Da sauri Sheykh ya matso tare da cewa. "Innalillahi". Ita kuwa Shatu ɗagota tayi da sauri ganin yadda taketa yunƙirin kakarin amai ba ƙaƙƙautawa. Da sauri Gimbiya Aminatu ta matso tana cewa. "Subahanallahi" Shi kuwa Sheykh wayarshi dake cikin al'jihun rigarsa ya zaro da sauri ya kira Dr Lukman Ibrahim yana ɗagawa yace. "Dr Baby fa sai amai takeyi ba tsayawa". Da sauri Dr Lukman Ibrahim yace. "Alhamdulillah tasha Mamanta ko?". "Eh tasha, tana shane ma ta fara aman". Ya bashi amsa. "Yauwa haka akeso Sheykh ba komai yanzu duk kaifin gubar ya karye ta harar dashi yanzu zatayi bacci kuyi mata wonka da ruwan sanyi. Tana farkawa kuyi mata wonka da ruwan sanyi kuma zata dawo dai-dai da izin Ubangiji". Da sauri ya katse kiran bayan yace. "Ok thanks Dr". Ita kuwa Shatu ajiyan zuciya ta sauƙe tare da meda kanta ta jingina da kujera ganin ta bar aman. Shi kuwa Umaymah ya kalla tare dayi mata bayanin da Dr yayi mishi. Da sauri ta iso garesu ta amshi ƴar kana ta wuce Bathroom. Wonka tai mata da ruwan sanyi ɗan kwalinta ta wore ta naɗeta a ciki. Tuni tayi bacci kafinma ta fito da ita. A hankali ta zauna bakin gadon Shatu gefen Aunty Amina da Khadijah dake waya da Abboi Appansu kenan tanai mishi bayanin duk abinda ya faru. Cikin tashin hankali da mamaki Abboi yace. "Subahanallahi, kai wannan gida nasu akwai sarƙaƙiya. yanzu ina Parvina?". A hankali tace. "Tana falo can naji kamar harda Lamiɗo ma yazo da kanshi, amman yanzu yarinyar gata nan ta farfaɗo harma tayi bacci". Cikin kula da son ahlinshi especially Parvina a hankali yace. "In sha Allah nida Dedden ku da Al'ameen zumu zo gobe gobe da izinin ubangiji, dama tun tuni ma shiryawa hakan, in Parvina ta shigo kice ta kirani". Da sauri tace. "Toh Appa". Guntun murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Babanku kika gayawa ne?". Cikin alamun karaya da lamarin gidajen sarauta tace. "Eh Umaymah". Kai kawai ta gyaɗa tare da gyarawa jaririyar kwanciya. Aunty Amina kuwa sunkuyowa tayi tana kallon fuskar Babyn. A falon Shatu kuwa sosai Lamiɗo ya kwantar mata da hankali kana suka tafi Gimbiya Aminatu na biye dasu a baya. Bayan ta shiga ta ƙara duba Babyn. Umaymah kuwa fitowa falon tayi suka zauna a nan. Ita kuwa Shatu bedroom ta koma ta konta tasa yarta a gaba tofi takeyi mata tana kallon fuskarta Allah ya sani ji takeyi kamar bata tsiraba shiyasa har yanzu hanjin cikinta ke kaɗawa. A hankali ta jawo wayarta. Abboi ta kira, bayan sun gama gaisa ya alhinta abinda ya faru ya ɗaura da cewa. "Dama can gobe zamu zo ko ba komai zanzo inga amryata, inga mummunace ko kekyawa". Ya ƙare mgnar da ƴar raha da son kontar mata sa hankali. Murmushi tayi tare da cewa. "Allah ya kawomku lfy Appa na, da Ummey na da Junainah take kamafa". Tayi mgnar cikin jin kunya duk da yawan shaƙuwa dake tsakaninsu. Murmushi yayi tare da kallon Dedde dake jin duk tattaunawar da sukeyi yace. "Ato kekkyawace sadaki ta garken shanun Bappa zai bata". Dariya sukayi baki ɗayansu kana sukayi sallama da juna. Daga nan kuma Bappa ta kira, wanda tun ɗazu Abboi ya shaida masa abinda ya faru yana ɗagawa yace. "Shatu na ya jikin Aisha ƙaramar dai?". A hankali ta ɗan shafa kan Afreen tare da cewa. "Alhamdulillah Bappa na ba komai ta samu lfy gatama tana bacci". Cikin jin daɗi yace. "Alhamdulillah ga Ummeynki tun ɗazu hankalinta a tashe yake". Amsa Ummey tayi cikin kula tace. "Boɗɗo na me sukayi miki?". Cikin yin ƙasa da murya tace. "Ummey na so sukayi su kashe miki jikarki tun baki ganta ba, dan Allah da Manzonsa Ummey na kizo gobe". Cikin kaɗuwa da begen son ganin Shatu da ƴar tata tace. "In Sha Allah Gobe za muzo tare da Abboi da izin Ubangiji". Cikin jin daɗi tace. "Alhamdulillah naji daɗi na, Gobe ina cikin gatana". Su kuma ta kalli Umaymah da ta shigo yanzu tare da cewa. "Alhamdulillah Umaymah na Gobe Ummey na zatazo da Bappa na da Deddena da Abboi". Cikin wani irin masha'hurin farin cikin alamun son tabbatuwar wani abu Umaymah tace. "Alhamdulillah Allah ya kawo mana su lfy". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Haka dai akayi wunin sunan jiki a mace da abinda ya faru. Sai can da yamma ne da Afreen ɗin ta farka daga baccin suka ganta lfy lau kafin hankalin kowa ya kwanta. Nan Umaymah suka fito da kayan suna na gani na burgewa, da aka haɗawa mai jego da Ɗiyarta. Kayan da Sheykh yayi musu kuwa abin sai dai ace son barka. Gaba ɗaya wunin yau shima ya kasa fita ko nan da can tunda akayi sallan Jumma'a ya shigo ya wuce Side ɗinsa. Bini-bini ya kira Shatu ko Umaymah ya tambayi jikin yarinya. Bayan sun dawo sallan la'asar ne. Jalal ya biyoshi har cikin falonshi, gefen Haroon ya zauna kana a hankali yace. "Shima sarkin al'adun sunan harda shi a sahun Magauta sai dai biya shi Hajia Mama tayi da dubu ɗari bakwai daga baya yace min tace in ƴar ta rasu zata cikata mishi dubu ɗari uku ya zama one million". Cikin mamaki Haroon yace. "Ikon Allah ikon gaske, wai ita wannan shegiyar matar meyasa bazamu fito mata a fili bane mu nuna mata mun san komai mu kuma juyo kanta". Cikin taune lips Sheykh yace. "Uhumm bazaku gane bane,". Da sauri Umaymah dake shigowa tace. "Ni na gaji bazamu gane me ɗin ba kuma". Cikin wani irin yanayi mai rauni cikin sanyi murya na rawa yace. "Affan ina ɗagawa Hajia Mama kafane sabida Affan ina jin takaici in na tuno a cikinta Affan ya fito, ku kun san waye Affan kun kuma san asalin zahirin gskyar so da ƙaunar da yake mana, kunsan yadda yake faman faɗa da yaƙin sauya mahaifiyarshi daga mummunan ɗabi'a eh zuwa kekkyawan ɗabi'a. Ta yaya zanci zarafin ta al'halin Affan ya ɗaukeni matsayin Uba ya ɗaukeni ciki ɗaya muka fito,kada ku manta son da Affan kewa Mameynmu Jalal ka duba tarin son da Affan yakeyi muku kaida Jamil. Ko a lahira wani kanci al'barkacin wani. Ina barine sabida ko Affan zai samu nasarar juya halinta". Ya ƙarashe mgnar hawaye na zubo mishi. Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi tabbas sun san waye Affan ko su Jalal basa so da shaƙuwa dashi kamar Affan. A hankali yace. "Duk abinda nasa Affan zaiyi minshi babu musu koda baya son abin duk inda na aikeshi zaije min duk abinda na bashi zaɓi zaɓina yake bi, Affan da kanshi ya fara nuna min baya son inci abincin Hajia Mama wacce take uwace a garesa, yayi hakane sabida zargin tana samin abu a cikin abinci. Yasha yin kuka yana mgiya in ya tareta tana wani abun me zanyiwa Affan in nuna mishi halaccin ɗan uwantaka banda in rufawa mahaifiyarshi asiri". Shiru yayi ganin kiran Affan daya shigo wayarshi. Jiki a mace itama Umaymah ta zauna. A hankali ya kara wayar a kunne bayan a amsa kiran. "Assalamu alaikum Hamma Jabeer". Affan ya faɗa cikin tsananin so da ladabi ga ɗan uwan nasa. "Wa alaikassalam Affan kana lfy". Sheykh yayi mgn yana mai jin wasu zafafan hawaye na tsastsafo mishi. Murmushi Affan yayi cikin yanayin shi na Happy mood yace. "Alhamdulillah Hamma Dr Akarmakallu Yah Sheykh, mun sauƙo lfy". Jingina bayan sa yayi da kujera tare da cewa. "Alhamdulillah Affan Allah yayi ma al'baka". Da sauri yace. "Amin Hammana". Sai kuma yace. "Jamil ne yazo ya daukomu a airport to yanzu mun biya mun sauƙe Yah Sulaiman da Malam Abubakar. To gani tare dasu Giɗi ɗin yanzu su ina zamu kaisu, umarni nake jira Hamma?". Cikin sanyi yace. "Alhamdulillah Affan ku dawo dasu masarautar Joɗa ku wuce dasu Part ɗinsu Jalal a sauƙesu a can. Bawa Jamil wayar". Da sauri yace. "An gama sir yadda kace haka za'ayi ga Jamil ɗin". Ya kare mgnar yana miƙawa Jamil wayar. Saƙale wayar yayi da kafaɗarsa tare da cewa. "Assalamu alaikum Yah Sheykh". Gyaɗa al'kyabbar jikinshi yayi tare da cewa. "Wa alaikassalam Jamil ka kaisu part ɗinku ɗakinka ka nuna musu Bathroom suyi wonka. Aunty Rahma zata kawo musu abinci ka tabbatar sunci sun ƙoshi. Sannan Jalal zai ɗauki Dr Kabir zaizo ya dubasu in sunada matsalar lfy zai kula da komai". Cikin gamsuwa Jamil yace to yana kallon kekyawar fuskar Giɗi ta madubin motar. Shi kuwa Sheykh a hankali yace. "Toh Umaymah a hakan ta yaya zan tozarta mahaifiyar Affan wanda duk munin halinta uwa dai uwace." Cikin rauni Umaymah tace. "Wannan hakane Jazlaan amman Hajia Mama tanayi mana illa a rayuwa". Sosai jikin Haroon yayi sanyi. Shi kuwa Sheykh Jalal ya kalla tare da cewa. "Kaje Valli ka taho da Dr Kabir". Jiki a mace Jalal yace to kana ya miƙe ya fita. Umaymah na biye dashi a baya, har taje bakin ƙofar fita a hankali yace. "Ayyah Umaymah Ɗiyar taki ta kawo min ɗiyar tawa mana in ganta". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh". Shi kuwa Haroon da sauri yace. "To bari in baka wuri dan nasan dai uwar ɗiya za'a gani ba ɗiyaba". A hankali yace. "Mutun da abinsa". Dariya Haroon yayi kana ya nufi ƙofar da zata sadashi da Garden. A hankali ta turo ƙofar Bedroom ɗinsa. Tare da cewa. "Assalamu alaikum". Cikin wani irin happy yace. "Wa alaikissalam". sai kuma ya juyo ya fuskanceta tare da buɗe mata hannunshi. Cikin sauri ta faɗa jikinshi ruggume da Afreen haɗe su yayi ya ruggume tare da cewa. "Alhamdulillah ya Allah ka tsare min ahlinna ka cika mana farin cikinmu". "Amin ya Allah". Ta faɗa a hankali sai kuma ya jawo hannunta suka zauna a bakin gadon. Cikin narke fuska yace. "Nayi fushi Aish tun ɗazufa na aika kizo baki zoba sai yanzu". Cikin sanyi tace. "Ayyah Malam sallan la'asar nakeyi". Cikin sauri ya kalleta tare da cewa. "Kai haba dai Aish da gaske shine baki gaya minba yaushe kika fara salla". Murmushi tayi tare da cewa. "Yoh ai dama ina salla". Lakace hancinta yayi tare da cewa. "Batun gsky dai my dear yaushe kika samu tsarki?". Cikin nitsuwa tace. "Yau da safe, nai wonka naci gaba da salla tunda naga jinin biƙin ya ɗauke na samu tsarki". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Masha Allah, jego yayi kyau kenan Boɗɗo na, dama wasu matan kafin satin sunama sun samu tsarki sun fara salla, kinga kema kina ɗaya daga cikinsu wasu kuma sai anyi arba'in ma, wasu har hamsin suna likin. Koda yake ke dama al'adarma kwana uku kikeyi ko". Kai ta gyaɗa mishi. Hannunshi ya cusa ƙasan pillow'nshi tare da zaro key ɗin sabuwar mota dal a leda. Kamo hannun ta yayi ya danƙa mata key ɗin tare da cewa. "Al'ada kwana uku baƙi kwana bakwai kai naji daɗi na, na more". Da sauri ta buɗe tafin hannunta tare da kallon key ɗin sai kuma ta lumshe idonta jin ya manna mata tattausan lips ɗinsa a goshi ya sake mata sassayan kiss. Tare da cewa. "Taki ce motar sai dai bani son kiyi tuƙi nafi son a jamin ke, sai daifa bana miji zai jamin keba. Sara taki zata zama yar rakiyarki mai jan mota da tayaki kula da Babynmu, duk inda kuke in bana kusa daku. Gimbiya Aminatu zata bamu wata mai girki". Cikin wani irin farin cikin ta ruggumeshi gam-gam a jikinta. Da sauri yace. "Wayyo Aish zaki danne Mimi na". Da sauri ta kwantar da Afreen gefe, kana ta faɗa jikinshi ta rungume shi. Murmushi yayi mai cike da farin ciki cikin wasa yace. "Zaki bani abin daɗi?". Da sauri tace. "Ban workeba". Dariya mai ɗan sauti yayi tare da haɗe bakinsu wuri guda. A part ɗinsu Jalal kuwa. Yah Giɗi Seyo Gaini ne zaune bayan duk sunyi wonka, sun saka sabbin kayan da Jamil ya zaro musu cikin durowarsa. Cikin wani irin yanayin jin daɗin duniya da kuma bege da kewar iyaye da ƴan uwa wanda da sun cire tsammani. A hankali Yah Giɗi ya kalli Jamil dake miƙo mishi turare yana cewa. "Kai masha Allah sai kunga yadda kukayi kyau, farinku ya ƙara fitowa". Cikin rauni Giɗi yace. "Dan Allah bawan Allah, nan ina muke ne? Kuma ina wanda muka dawo dashi? Sannan ina za'a kaimu? Wayasa aka fito damu?". Da sauri Jamil ya zauna gabanshi kamo hannun shi yayi a hankali yace. "Nan kuna cikin Ɓadamaya ne, cikin masarautar Joɗa, wanda kuka dawo dashi kuma Yayana ne Affan ya tafi ƙofar matarshi. Wanda ya taimake ku yasa aka fitar daku kuma babban Yayanane Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa. Yana nan matarsa ta haihu yau akeyin suna. Sai in ya nitsu zaizo wurinku shi zai gaya muku ina za'a kaiku". Wasu irin hawaye ne suka tsunkowa Gaini murya na rawa yace. "Alhamdulillah kowa yace yaya zaiyi ya manta da Allahu wahidun ƙahharar sarki buwayi gagara misali mai badawa mai hanawa mai raya mai kashewa mai kawo sauƙi cikin tsanani mai yaye tsananin duhu ya wanzar da haske". Ido Jamil ya zuba musu cike da so da ƙaunar su, sai kuma ya kalli Seyo da yake zubda hawaye cikin sanyi yace. "Ko wanne hali ahlinmu ke ciki". Da sauri Jamil yace. "Yanzu muje falo kuci abinci kunji dan Allah ku bar kukan". Kasan cewar ya haɗa su da Allah yasa ba musu suka tashi. Amman badon hakaba farin cikin da suke ciki ya kori yunwa bare ƙishi. A tsakiyar falon suka zauna. Jamil da kanshi ya zuba musu abincin da Aunty Rahma ta kawo musu. Sukaci suka sha. Dai-dai lokacin kuma aka kira sallan magriba. Nan sukayi al'wala kana Jamil ya jasu sukayi jam'i. Shatu kuwa bata bar ɗakin Sheykh ba saida ya tafi masallaci. Ta fito cike da farin ciki. Aunty Amina da Khadijah da Umaymah da Hibba ta samu a falonta Umaymah ta miƙa wa key ɗin tare da cewa. "Umaymah Yah Sheykh ya saya min mota". Cikin jin daɗi Umaymah tace. "Masha Allah. Allah ya sanya al'khairi". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Kana duk sukayi al'wala haramar salla. Ƙarfe goma da rabi. Duk baƙi sun watse. Sai su Umaymah da su Aunty Amina. A falon Shatu suke suna hirarsu cikin salama Ummi na ruggumi da Afreen. Umaymah kuwa na haɗawa Shatu tea da fifitashi da kyau. Aunty Rahma kuwa kitso Khadija keyi mata. Junainah da Ishma kuwa suna can babban falon da Hibba da Jalal. Sara da Larai da indo hadimar Aunty Juwairiyya kuwa tattare kitchin sukeyi da kimtsa ko ina na gidan. Sheykh kuwa a hankali ya jawo wayarshi daya tattare wacce yake waya da Hajia Mama da ita. Kiranta yayi. Tana amsawa yace. "Ƴar ta mutu ko?". Wani irin gigitaccen tsaki taja tare da cewa. "Inafa ta mutu na dai ji ta suma amman wannan Shegen yaron duk abinda nayi a kanshi ko matarsa yanzu dama yar tashi abun baya tasiri. Sannan babban tashin hankali na, shima Sarkin al'adun suna bai dawoba. Kuma wayarshi na shiga baya ɗagawa, tsorona kada dai sun ganeshi". Cikin sauya muryarsa ih zuwa muryar Jahan yace. "A a ba dai kamashi ba kam, sai dai ko in yana jin tsoron amsa kiran nakine sabida kada kiyi mishi faɗa tunda ƴar bata rasuba kada kice bai iya aikinsa bane a ganina fa shine yasa baya amsa kiran naki". Cikin tashin hankali tace. "Ni babbar matsala ma yau tunda gari ya waye hankalina yake a tashi zuciyata na tsinkewa gaba ɗaya tsoro ya rufeni ji nakeyi wani mugun abu yana tunkaro rayuwata, naje gidan boka kuma ya koroni shima sai tsalle yakeyi yana kaɗe jikinsa Wai komai na gab da dawo mana". Murmushi mai cike da jin daɗi yayi a ransa yake zaton ko shiryace zata zo mata, haka yasa yace. "Sai gobe zanzo muyi mgn in kaiki gidan wani sabon boka". Da sauri tace. "To". Daga nan ya katse kiran. Kana ya miƙe ya fito falo, a hankali ya kalli Jalal da Hibba tare da cewa. "Jamil fa". "Yana Part ɗin mu". Jalal ya bashi amsa". To yace kana ya juyo ya kalli Yah Jafar da yanzu ya shigo kenan. A hankali ya tsaya gaban Sheykh. A hankali suka lumshe idonsu a tare, da sauri Sheykh da Jalal da Hibba suka matso kusa dashi sosai jin yana cewa. "Jabeer zuciyata na tsinkewa tun jiya sai inji kamar wani abu zai faru". Cike da mamaki Jalal yace. "Wlh nima tun jiya zuciyata ke tsinke kirjina yaita bugawa". Wani irin rumtse ido Sheykh yayi tare da cewa. "Nima abinda naketa fama dashi kenan tun jiya, to da Aisha ta suma sai nai zaton ko abinne ke samin tsinkewar zuciya. To kuwa still abin bai bariba saima ƙaruwar da yakeyi yana tsananta". Cikin sanyi Hibba tace. "To kuyi ta addu'a hakama Umaymah da Mamma da Aunty Rahma sukace suna ji". Kai suka gyaɗa gaba ɗaya. Hannun Yah Jafar ɗin Sheykh yaja suka nufi Part ɗin su Jamil. Su kuwa su Jalal zama sukayi suna kallon Ishma da Junainah daketa sabgoginsu. A hankali Sheykh ya zauna tare da kallon Jamil dake zaune tsakiyarsu Giɗi a hankali yace. "Ka barsu su huta mana". Cikin sanyi Jamil yace. "Allah ko Hamma Jabeer ina so in tafi wurin Khadijah ma sai inji zuciyata na tsinkewa kamar dai zan samu wani abu". Cikin kula Sheykh yace. "Uhmm duk haka mukeyi kaita mai-maita innalillahi wa innailaihi rajiun". To yace. Shi kuwa Sheykh nitse ya kalli Gaini da zai kai sa'an Affan. Cikin kula yace. "Sannunku da hanya". A tare sukace sannu. Jamil ne ya ɗan kallesu tare da cewa. "Shine babban yayanmu Sheykh da yasa aka fito daku". Da sauri suka ɗan gyara zama suka matsoshi tare da cewa. "Allah sarki bawan Allah mun gode Matuƙa Allah ya saka da al'khairi ya kula da ahlinka fiye da yadda ka kula damu". Cikin jin daɗi yace. "Amin ya rabbil izzati, amman kuma duk haka ya farune sanadin Sulaiman da aka rufeshi tare daku". Cikin gamsuwa sakace. "Ayyah". Sai kuma Giɗi ya ɗan share hawayen da suka zubo mishi tare da cewa. "Ayyah bawan Allah yaushe zamu koma Rugar Bani muga Bappa da Inna da Ummey da Shatu da Junnu". Cikin gamsuwa da tausayinsu Sheykh yace. "In sha Allah nan kusa amman nafi son sai naga kunyi aski kun ƙara hutawa, gobe zuwa jibi da kaina zan medaku". Cikin wani irin masifeffen jin daɗi sukace. "Allah ya kaimu". "Amin Amin". Yace kana ya musu sai da safe. Daga nan wurin Abbanshi da Lamiɗo da Galadima yaje suka ɗan yi wata mgnar kana ya dawo. Ranar dai haka suka kwana gaba dayansu babu wanda yayi isasshen bacci sabida masifar bugawa da ƙirazansu keyi. A can Rugar Bani kuwa. Ko abincin dare Ummey bata iya ciba. Haka nan sai taji zuciyarta na tsinkewa yana bugawa. Tun abun bai damunta har ta gayawa Bappa, so ya bata ƙarfin guiwa da yin addu'a. *Ba'ana* Zaune yake gaban yaransa cikin rauni da yanayin damuwa yace. "Nanda wata uku masu zuwa zan koma ƙasar Nigeria zanyi yaƙin neman Shatu koda zan rasa rainane, zan koma gareta. Zan gaya mata ko mutuwa nayi sonta ne ajali na". Cikin bashi ƙarfin guiwa ɗaya daga cikinsu yace. "Zama kayi nasara". A hankali yace. "Babu tabbas, domin tunda na rasa Shatu nakega nayi rashin babbar nasara". Sai kuma ya miƙe ya shiga cikin ƴar ƙaramar bukkarsa. Murmushi Baron yayi tare da katse kiran da yayi Sheykh yana jin duk bayanan Ba'ana. Dan shi Baroon yanzu ya zama ɗan aikin Sheykh dan tun zuwansa lokacin ciwon hannun Shatu. Da fari har yasa a kirasa daga baya yasa aka dawo dashi. Ya biyashi kuɗi masu tarin yawa, yayi mishi duk bayanin ɗaya nema, kana yasashi ya koma wurin Ba'ana kuma ya naɗo mishi rahoto da duk wani motsin Ba'ana yana turo mishi. Alhamdulillah kuma yanzu duk shirin kama Ba'ana yakeyi. Washe gari ranar asabar yau babu aiki. Da misalin ƙarfe goma na safe jirginsu Abboi ya sauƙa cikin birnin Ɓadamaya. Kai tsaye Salmanu yayi musu jagora zuwa Rugar Bani dan a take suna sauƙa wasu tsala-tsalan motoci guda biyar suka iso wanda dama su tun jiya suka iso. A ƙasan plate number motocin akwai tambarin hatimin kan shanu a ƙasa ansa Abboi, irin tambarin dake jikin jiragen Abboi kenan. Suna zuwa kuwa babu ɓata lokacin suka isa har cikin gida. Inda nan Arɗo Bani da kanshi da sauran dattawan sukazo. Bayan sun gaggaisane Abboi ya ɗan yi gyaran murya tare da cewa. "Toh Alhamdulillah lallai komai yayi forko to tabbas yana da ƙarshe, to bayan bincike da bin diddigi dai mun gama fahimtar inane asalin wannan baiwar Allah'n kuma munada yaƙinin daga masararutar Joɗa ta fito. To yau dai kam ranar data kamata mu shiga da ita ciki da yardar ubangiji tazo. Kamar yadda muka tsara, yanzu zamu tafi". Cikin tsananin jin daɗi da kuma fargabar ko ya al'amarin zai kasance Bappa yace. "Alhamdulillah mu duk a shirye muke, fatanmu Allah yasa ina munje ta tuna baya, ta tuno ita wacece". Da sauri Arɗo Bani yace. "In Sha Allah ma zata tuna Malam Babayo". "Allah yasa haka". Al'ameen ya faɗa. Amin Amin sukace kana duk suka miƙe suka fito. Kana Bappa yazo yacewa Ummey da Dedde su fito. Nan suka mara musu baya. Mota ɗaya Bappa da Abboi da Arɗo Bani suka shiga. Ummey da Dadde da Al'ameen kuwa suma mota ɗaya suka shiga. Sauran kuma ƴan tsaronsu ne a ciki sai motar Yah Salmanu da Hafsi ƙanwar Shatu a haka suka fito daga Rugar Bani suka nufi Masarautar Joɗa. A hankali Ummey ta jingine kanta da jikin kujera tare da dafe ƙahon zuciyarta a hankali ta furta innalillahi wa innailaihi rajiun". Sabida tsananin tsinkewar da zuciyarta keyi Dedde kuwa hankalinta naga makiyayan dake zirya. A nan cikin birnin Ɓadamaya a tsakiyar Masarautar Joɗa kuwa. Gaba ɗaya su Umaymah suna falon Shatu. Aunty Rahma ce da su Sara a kitchin, Aunty Juwairiyya tana part ɗinta da Hibba. Junainah da Ishma kuwa suna kitchen tare da Aunty Rahma. Kowa sabgar gabansa keyi. A hankali Shatu ta miƙe ta nufi ƙofar falon Sheykh da sallama a bakinta. Shiru ba kowa a falon tray'n breakfast ɗinshi shida Haroon ta ajiye bisa Dinning table. Ganin ba kowane yasa ta turo kanta cikin bedroom ɗin. Shiru ba kowa a hankali ta ƙara so ciki tana cewa. "Salam Yah Sheykh". Ƙofar bathroom ta matso a hankali ta tura ba kowa a ciki komai yana kimtse tsab-tsab. "Toh ina yaje kuma yau Lahadi kuma ai babu inda zaije". Shiru tayi tare da juyowa ta matso tsakiyar ɗakin jujjuya kanta tayi ba mutun ba alaman mutun a ɗaki. Har ta juya zata fita, sai kuma tayi sauri ta juyo tazo bakin gadonshi, abun data hanƙo ƙasan pillow'nshi ne yasa ta sunkuyowa da sauri hannunta tasa ta zaronshi. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Ta faɗa jiki na rawa tare da sakin fuskar robar da Sheykh ake amfani da ita a matsayin Jahan. Da sauri ta juyo da nufin zata fita, sabida tsoron daya rufeta. Sai kuma tayi sauri taja da baya tare da zare idanunta dai-dai lokacin da ta iso jikin marfin wodurob ɗin sa Wanda yayi dai-dai da lokacin da Sheykh ya turo marfi ya fito. A gigice take jujjuya kai tare da zaro ido. Sai kuma ta juya da sauri ta kalli fuskarnar da ƙarfi ta buɗe baki tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Yah Sheykh". Da sauri yasa hannunshi ya kamo nata ya fizgota jikinshi cikin haɗe fuskarsu wuri ɗaya yace. "Na'am Aysha please kada kiyi ihu tsaya nitsu nine Muhammad Jabeer Yah Sheykh mijinki Abu Afreen". Cikin yanayi kaɗuwa tace. "Yah Sheykh kai mutum ne ko al'jan". Da sauri ya kamo hannunta suka iso gaba durowar. Buɗe ƙofar yayi, kana a hankali yasa hannunshin ya ture, al'kyabbas ɗin shi dake jere a hanga a saƙale, sai ga wani ƙofa mai kamar glass. A hankali yace. "Aysha nitsu ki jini kinji ko". Cikin sauƙe numfashi tace. "Toh". Kanshi ya gyaɗa kana a hankali yace. "Kinga wannan wurin ko?". Da sauri tace. "Eh naga kamar ƙofa ne". Jawota yayi suka ɗan matso hannunshi yasa ya tura ƙofar da sauri tace. "Lahh". Sabida ganin wata ƴar siririyar hanya mai tsawo. A hankali yace. "Ni mutum ne Aish yanayin tsarin masararutar Joɗa ne yasa dole nake amfani da wasu ababen. Kinga wanan hanyar har cikin bedroom ɗin Lamiɗo da Abba na duk akwai su. Muna haɗuwa dasu a ɗakin Lamiɗo lokuta da dama. In kina so anjima zan nuna miki, dan yanzu Lamiɗo ya rufe ƙofarsa ne da yanzu zamuje". Da sauri tace. "Me kukeyi a ɓoyen". Jawo ƙofar yayi ya rufe kana a hankali yace. "Ina wani aikine Aish Kuma aikin sirrine, tsawon shekaru inayi babu wanda ya sani sai Lamiɗo da Abba na da Umaymah sai yau kuma da kika zama ta uku". Ya ƙarashe mgnar yana jawota suka zauna bakin gado. A hankali ta sauƙe numfashi ido ta zuba mishi a hankali tace. "Kai SS ne ko Yah Sheykh?". Murmushi yayi tare da cewa. "Ba'a faɗa kiyi shiru kada wani yaji kinji ko sirri ne Boɗɗo na". Murmushi mai cike da jijjina tayi mishi. Shi kuwa ruggume ta yayi ya koma baya ya kwanta. Dai-dai lokacin kuwa motar Salmanu dake gaban motocin su Abboi ta kusa kai cikin matsarautar Joɗa bayan an wangale musu gate. Wani irin rumtse ido da ƙarfi Ummey tayi tare dasa kanta bisa guiwowinta sabida wani irin masifeffen tsarawa da kanta yayi da azaban ƙarfi. Kai tsaye bakin part ɗin su Sheykh Salmanu ya nufa dasu sai dai Motar Abboi da sauran duk a can baya bakin fada suka tsaya inda Bappa ya nuna musu. Yadda suke ƙara kusanto Part ɗin su haka sarawa da bugun zuciyar da Ummey keyi yake ƙaruwa. A can cikin falon Shatu ma, da sauri Umaymah da Mamma Suka kalli juna sabida masifar bugawa da ƙirazansu sukayi. Sheykh kuwa da ƙarfi ya ruggume Shatu sabida ji yayi tamkar zuciyarsa zata faso ƙirjinsa ta fito woje. Jalal da ke Part ɗin Yah Jafar da sauri ya rumtse idanunshi shida Yah Jafar ɗin. Hakama Jamil dake tare dasu Gaini. A hankali motocin sukayi parking. Ummey kuwa wani irin ƙara rumtse idanunta tayi da masifan karfi. Dedde kuwa a hankali ta buɗe ƙofar. Ta sako ƙafarsa cikin shigarta ta al'farma. Shi kuwa Al'ameen da sauri ya zagayo ya buɗe wa Ummey kofar tare da cewa. "Ummey mun iso bismillah". Cikin tsananin danne sarawar da kanta keyi ta ɗago jajayen idanunta a hankali ta zuro ƙafafuwan woje. Ras ras Din dab din dab haka zuciyarta ta bada wasu tagwayen bugu. Da sauri tasa hannunta ta dafe ƙirjinta. Dedde kuwa a hankali ta zagayo inda take. Shi kuwa Al'ameen a hankali yace. "Bismillah ku shiga ga ƙofar". A hankali Dedde tace to kana ta nufi ƙofar. Ita kuwa Ummey cikin rawan jiki ta ɗaga ƙafarta ta dama ta ɗaura kan barandar tare da ƙara dafe ƙirjinta da rumtse idanunta sabida jujjuyawan da kanta ya fara. Shi kuwa Al'ameeen bayansu yabi. Shi kuwa Salmanu a hankali ya kalli Hafsi ƙanwar Shatu dake bin Khadijah. Cikin yin ƙasa da murya yace. "Ko in ɗagaki ne in kaiki". Cikin jin kunya tace. "A a Yah Salmanu zan shiga da ƙafata". Su Bappa kuwa Sarkin ƙofa ne yayi musu iso zuwa cikin fada. A hankali Dedde ta kai hannunta ta kama handil ɗin ƙofar falon ta murɗa tare da turawa kana tasa ƙafarta ta dama ciki bakinta ɗauke da sallama. Aunty Rahma dake fitowa daga kitchen Junainah na biye da ita da sauri ta ɗan juyo ta kalli Dedde tare da cewa. "Wa alaikassalam". Ta ƙarashe amsa sallamar tana matsowa dan ganin wani irin fitinenne kama da Dedde keyi da Shatu. Da sauri ta juyo bayanta jin Junainah na cewa. "Lah Oyoyo Dedde". Dai-dai lokacin kuma Ummey ta ƙarasa shigowa ciki wanda hakan yayi dai-dai da bugawar da kanta yayi wanda saida tayi sauri sa hannunta duka y ta damƙe kanta da masifan karfi tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Da ƙarfi wanda haka yasa Dedde juyowa ta fuskanceta sanadin juyawar da Dedde tayi kuma ya bawa Aunty Rahma da Junainah damar ganin fuskar Ummey da kyau. Wani irin sauri Junainah tayi ta nufi inda suke ganin yadda gaba ɗaya jikin Ummeynta yake karkarwa da tsuma. Aunty Rahma kuwa cikin wani irin tsananin firgita da kaɗuwa ta zazzaro idanunta waje har kamar zasu faɗo. Wani irin taku mai cike da firgici tayi tana matsowa gaban Ummey dake jujjuyawa tana mai-mai-ta. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil". Wani irin matsowa kusa da ita Aunty Rahma tayi tare da buɗe baki da ƙarfi tace. "La ha ila ha illahu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallama. Aunty Mamey!." Ta ƙarashe kiran da azaban ƙarfi da rakaɗi. Ummey kuwa. Kiranta da Aunty Rahma tayi yasata ƙara gigicewa. Karkar haka jikinta ke rawa. Cikin wani irin gigitaccen murya Aunty Rahma ta fara rabkawa ahlinta kira. "Umaymah! Mamma Jazlaan ga Aunty Mamey ta dawo da izinin ubangiji Jazlaan, Jafar, Jalal, Jamil, Umaymah. Kuzo ga Aunty Mamey...". Wani irin azabebben zabura...! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k ne kacal zaki turo ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Normal group Kuma 300 zaki turo ta asusuna ɗin sai kuyi screenshort na Debit Alert din ku turo min ta whatsApp 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: "Aranar wata jumma da da wanna Zazzafar ƙaddara ta rufta damu shekaru goma sha uku baya." Sai kuma ya ɗan tsakaita tare da jan sassayan numfashi ya gyara zamansa tare dasa tafin hannunshi ya share hawayensa. Yayin da gaba ɗayansu kacokam suka mai da hankalin su kansa, Duk sun ƙagu suji yadda a kayi a wannan ranar da basu manceba. Shi kuwa Yah Jafar wani numfashin yakuma. Saukewa kana yaci gaba da cewa. "Ranar da dare bayan anyi sallan isha'i duk muna falon Mamey dani dasu Jalal Jamil Affan da Ummi da Imran yana ɗan sheksru takwas lokacin. Anan mukaci abinci kana muka zauna muna hira. Kasan cewar akwai shaƙuwa mai tarin yawa tsakanin Mamey da Affan da yake tana da son yara. Amman son Affan da banne a wurinta har su Jamil kance wa Affan na hannun daman Mamey. Takanyi Dariya tace. "Eh ɗin ai ya fiku nitsuwa". Muna zaune sai hamma Mamey keyi tare da miƙa da lumshe idonta hakane yasa tace mana. Duk ta sallamemu saida safe tanajin bacci. Ummi tace. To. Still Kuma sai mukaci gaba da hira. Da ido muka bita ganin ta miƙa cikin sanyi tace. "Kai zanje inyi bacci wlh wani irin bacci mai nauyi nakeji yana fuzgata tamkar zan faɗi. Ni na shiga saida safenku". Allah ya bamu al'khairi mukace dukanmu kana ta shiga. Tana shiga kwanta ko second uku batayi da kwanciya ba tayi bacci. Mu kuwa muna gama hira muka watse. To su Jalal ne ƙarshen fita ashe basu tasheta ta rufe ƙofarta ba a famintata kenan fa?". Ya ƙare mgnar yana kallon su Jamil. Da sauri Jamil yace. Eh. Cikin sanyi ya kalli su Lamiɗo kana yaci gaba da cewa. "Ina komawa ɗaki na kira Juwairiyya muka fara hira a waya kamar kullum. To bayan mun gama waya da Juwairiyya har na kwanta sai na mike na nufi ɗakin Mamey dan inaso nayi mata magana a kan Juwairiyya fa tasanar wa mahaifin su maganar auren mu da ita, tun da lokacin takammala karatun ta dan haka itama ta gayawa Abba na ayi batun aurenmu dan nima tuni lokacin na gama karatuna har na fara aiki. Kuma a kwanakin ne aka bani sarautar Galadima wanda da mijin Gimbiya Saudatu ce mai matsayin to daya rasune Lamiɗo ya maida mulkin kaina. A zatonshi ta hakane zaisa yaranshi bazasuyi faɗa da junaba tunda bazasuce ya baiwa wane ya hana waneba. Ni a lokacin dagani har Mamey da Jabeer da baya ƙasar ma ba son wannan mulkin mukayiba bisa dole aka bani ita. Sai kuma ya jingina bayanshi da kujera kana yaci gaba da cewa. Ina isa bakin kofar Mamey natura kofar da sallama nashiga ɗakinta. Da sauri naja natsaya nan bakin kofar. Can na hangi Mamey na kwance. Bisa gado tana bacci da alamun baccin mai nauyi ne. Hajiya mama kuwa na tsaye a kanta da wata iriyar shiga da tafi kama data bokaye ko ince matsafa. Da mamaki nake kallon Hajia Mama dake tsaye bakin gadon sanye da wasu irin jajayen kaya tun daga samanta har ƙasa, kanta babu ko ɗan kwali hannunta rike da wani ƙwarya. Tana yayyafawa Mamey wani ruwa dake cikin ƙwaryar tare da yin wasu surutai da sukafi kama da surkullen matsafa. "Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un, nafurta da karfi. Da sauri nanufo in da Hajia Mama'n ke tsaye cikin ruɗani da kiɗima ina faɗin. Meye hakan Hajia Mama? me kike mata? me kike zuba mata a jiki haka?. Dasauri tajuyo kaina tasaka hannunta cikin ƙwaryar taɗibo ruwan tashiga watsamin tana ƙara matsoni, kaucewa nashiga yi ina matsowa in da Mamey take kwance kamar gawa ko matsi batayi, itako Hajia Mama masoni tarikayi tana watsamin ruwan, Baki na buɗe da karfi sabida wani irin masifeffen suka da naji duk inda ruwan ya taɓa a jikina yanayi. Ƙara watsomin tayi wanda yasa na ƙara kaucewa da sauri tare da buɗe baki da nufin yin ihun zafin da nakeji da kuma fargabar halin da Mamey na ke ciki. Sai kawai naji harshena yafurta Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un,wannan kalmar narika nanawata da karfi madadin inyi ihu." Ita kuwa Hajia Mama da sauri tajuya cikin alamun tsoron tonuwar asirinta. dan lokacin dare baiyi nisa sosai ba misalin ƙarfe goma ne, da gudu tafita a ɗaki dan jin yadda na kara sautin salatin da nake. Ita kuwa Hajia Mama tana fita part ɗinta ta nufa direct bathroom ɗinta ta shiga gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi number'n bokan ta takira yana ɗagawa cikin haki da fargabar a bin da zaije ya da wo tace. "Boka yanzu nafito daga ɗakin matarnan na samu tayi bacci kamar yadda kace, kuma na watsa mata ruwan bata farka a sai daifa wani yaganni lokacin danake yayyafa mata ruwan maganin nan babban ɗanta Galadiman Masarautar Joɗa kenan ya ganni". Wani irin dariya irin nasu na hatsabibai bokan yayi kana yace. "Toh daya ganki me yakeyi? me kuma yake cewa?". cikin rawar baki da soron da ya ziyarce ta gudun kada ai kin ya ɓaci tace. "Sunan Allah yaketa ambata salati yaketayi babu ko kakkautawa da wasu addu'o'i". Cikin ɗan tsagaita dariyar mugayen bokan yace "To aiki kam zaici amma dai akwai nakasu aciki, amma kada kidamu yanzu shi yaron zamu rufemasa baki zai dauwama kurma ba mgna a bakinsa bazai iya yin maganaba bazai iya furta komai ba haka zai dauwama ba mgn saidai yayi ta mai-mai-ta abinda yake cewa. Sannan daga nan tagwayen kuma zamu haɗa ɗaya da bin mata ɗaya shaye-shaye shi kuma babban kinga zai zama kamar Mahaukaci, shi kuma wancan Jabeer ɗin na gaya miki tun yana ƙaramin akwai sihirin da wani yayi mishi kada ki damu dashi bazai taɓa yin aureba har gaban abadan ko an mishi bazai zauna da matarba, kinga kenan duk sun zama suna da matsalar da dole baza'a basu mulkiba sai dai a bawa ɗanki Affan tunda kinga shi Imran ɗan ɗaya kishiyar taki shine ƙarami kan Affan." Cikin sauƙe numfashi tace. "Yauwa boka na gode ni dama fatana ɗana yayi mulki dan bana son mulkin ya bar ɗakina tunda dai kace min tabbas cikin yaran Habibullah ne mijin wani zai gaji kakansa sarauta. Dariya yayi tare da cewa. "Kada ki damu mulki na gareki da ɗanki". Wa iyazubillah kaɗan kenan daga sharrin tsinannun shaiɗanu maƙiya Allah da Manzonsa bokaye taɓaɓɓu masu sa mai binsu ya taɓe ya gaza sauri a ranar da muminai ke sauri a bisa siraɗi. Acan cikin ɗakin Mamey kuwa. Sosai sautin addu'a da karatun da Jafar keyi yatsanan ta yana kankame da Mamey, wacce ke ƙwance ida nunta a rufe, har lokacin bata farka daga. Baccin sihirin da akasa takeyi ba saboda nauyin. Baccin da suka je fata ciki. Sheko bakinsa baya iya furta komai sai addu'o'in sai kuma hawaye da keta tsatstsafowa daga cikin ida nunsa sabida fargarba da kuma zafin da yakeji, Abba kuwa dake can part ɗinsa da yake Part ɗin shi na natsakanin na matan nashi ne. Yana cikin ɗakinsa dake sama. Haka yasa yarinƙa jiyo muryar Jafar da irin addu'o'in dayake cikin kiɗima, da kajin addu'ar kasan acikin tsananin firgici da tashin hankali yake yinsa, Wuf yamike yanufo part in Mamey kasan cewar babu wata tazara sakaninsu. Gudu-gudu sauri-sauri ya isa. Cikin hanzari yatura kofar bedroom ɗin Mamey cikin sananin tashin hankali da kaɗuwa ganin yadda Yah Jafar ke rungume da Mamey sai innalillahi yake da karfi hawaye yagama wanke fuskarsa idanunsa sun yi jazir saboda kuka da zafin da yakeji da fargabar ganin tamkar Mamey a mace take a kiɗime yanufo in da suke yana faɗin. "Subahanallahi kai Jafar meya farune me ya sameta?". Yayi tambayar hankali a tashe, tare da miƙa hannu ya ɗago kan Mamey dake kan kafar Ya Jafar yashiga girgizata yana kiran sunan ta. "Aisha! Aisha!! Ummu Jabeer!. Gani shiru bata ko matsi sai dai tana numfashi ya tsananta firgicinsa. Hankali a tashe yakuma kallon ya Jafar wanda keta addu'o'in babu ko kakkautawa. Mai da kan Mamey'n yayi ya kwantar kan cinyar kafar Jafar. Kana ya juya a kiɗime ya fita a ɗakin da sauri ya nufi sashin mahaifinsa Lamiɗo. Shi ko ya Jafar cigaba da maimata innalillahi yakeyi yana zubda hawayen. A can ɓangaren Hajia Mama kuwa. fitowar ta daga ɗakinta kenan cike da jin daɗin yadda bokan ya karfafa mata guiwa tanajin daɗi a ranta yanzu komai zai tafi mata yadda take bukata zata rabu da zugar yayan Mamey da ita duk kowa ya huta, tana fita ta hangi Abba ta window yafita daga cikin part ɗinsa hankali a tashe. Fuska ta ɗan yamusa tazauna saman ɗaya daga cikin kujerun parlour'n, can kuma tamike kamar an tsikareta tabi bayansa da sauri. Acan shashin Lamiɗo kuwa. Da sauri Lamiɗo da Galadima suka mike, bayan Abba yagama sanar musu abin da ke faruwa. A tare suka fito suka nufi part ɗin Mamey'n. Lamiɗo na gaba Galadima da Abba na biye dashi suka shiga ɗakin, in da Abba yabar Yah Jafar a haka suka iske shi yana ganinsu ya miƙe da sauri Mamey yashiga nuna wasu Lamiɗo da hannu yana kuka yana nuna musu ita da kwatanta musu yadda Hajia Mama tayi mata. Da sauri Hajia Mama ta turo kofar dan taga shigowar su Lamiɗo'n. Jafar kuwa yana ganinta yashiga nunata da hannu sai kuma ya nuna Mamey'n yana cigaba da ƙwatanta yadda tayi matan shidai baki kam babu shi sai dai addu'o'in da kuma kukan dayake tayi. Gaba ɗaya su suka maida kallonsu kan Hajia Mama nan take Lamiɗo da Galadima da Abba suka ɗiga ayar tambaya a kanta. itako ganin bawai magana Jafar ɗin keyiba sai bata damuba bata kuma fahimci cewa sun zargi meyafaru ba kuma basu gane me. Jafar ɗin yake cewa ba da hakan ba. Hajia mama kuwa cikeda da karfin hali irin nata na makiran mugaye mata tafara tafa hannu tana masar kwalla tana faɗin "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un Jafar me nake gani haka me yasami Mamey'n ku? kayi magana mana". Sai kuma tasaki kuka mai haɗe da salati. Lamiɗo ne yaɗanyi gyaran murya ganin Mamey'n tafara motsawa alamar tafarka daga nannauyan Baccin da take mikewa tayi zaune tare da zuba musu ido. Da sauri suka ɗan matso gareta kana duk suka mai da hankalin su kanta. Suna ce mata sannu Aisha, Amman shiru ba amsa. Cikin tsananin sauri da tsoro Abba ya matso kusa da ita tare da zubawa yatsun kafarta ido mamaki cike da kiɗima yake kallon yatsun kafarta da suka fara sauya kamannin halitta suka koma kamar na tsuntsu. Cike da alhini suma su Lamiɗo suke kallon yatsun kafar nata, hankali a tashe. Cikin gigita Abba ya kamo hannunta tare da nunawa Lamiɗo murya a daburce yace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Lamiɗo kalli yatsunta". wani matsanancin tashin hankalin ne yakuma dabaibayesu lokacin da suka ga yatsun hannunta yafara komawa irinna fiffiken tsuntsu. Gaba ki ɗaya su haɗa baki sukayi wajan furta "innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un hasbullahu wani'imalwakin". Sabida tsananin firgici da tashin hankali gaba ɗaya jikinsu rawa yakeyi. Cikin matsanan cin tashin hankali Lamiɗo da cushewar tunani Lamiɗo ya juyo ya kalli Galadima murya a hargitse yace. "Subahanallahi maza a kira Malam Musa yanzu nan". Cikin hanzari Galadima ya amsa da. "To". Kana yajuya da sauri yafita. Kan kace me labari yabaza masarautar Joɗo, Batare da bata lokaci ba sakon kiran da Lamiɗo yayiwa Malam Musa ya isa gareshi. Cikin ƴan daƙiƙu malam Musa ya iso cikin masarautar Joɗa Lamiɗo yabada umurnin a shigo dashi har cikin ɗakin Mamey. Yana shiga kallonta malam Musa yayi cikin tashin hankali ya girgizata kai kana yakallesu Lamiɗo yace. "Sihirine a kamata mai haɗe da tsafi kuma daga yanzu zuwa ko yaushe ko wanne lokacin zata iya juyewa daga mutun ta dawo tsunsuwa". Salati suka ɗauka baki ɗayansu nan kuma ɗakin yakacame da koke-koke su Jamil da Jalal Affan Ummi Jafar yayin da duk muryar Hajia Mama yafi amo wajen kuka da shiga tashin hankali ziraran miraran. (uhum makircin mugu kenan.) (Sai daifa akwai kishiyoyi na gari da matsalar kishiya kan sasu kukan gaske wlh.) Ranar kuwa wannan masarautar taga tashin hankali mara misaltuwa, Jiƙe-jiƙe da hayaƙi da shafe-shafen magungun gargajiya babu wanda malam Musa baiba, kiɗima yasa sun mance da suyi amfanin da ayatul shifa. Ganin anyi duk abinda za'ayi na gargaji abin yaci tura ne yasa hankalin. Dr Aliyu yakasa ƙwanciya gani yake ko wata cutarce ta da ban haka yasa ya fitadaga ɗakin yatafi part ɗin sa, kiran wasu manyan likitoci a bokansa. Yasanar musu koda wani shawarin da zasu basu bayan sun gama wayar kuwa. Kayan ai kinsa ya ɗauko yakomo ɗakin Mamey'n yayi iya gwaje-gwajen sa babu abinda ya gane na wani cuta ko wani abu. Cikin takaici Malam Musa yace. "Kama bar gwada ta babu wani cuta face sihiri". Daga karshe dai dole ya hakura. Ranar babu wanda ya rumtsa kusan a tsaye suka kwana nan cikin ɗakin Mamey'n ganin yadda gaba ɗaya kamannin halittarta ke juyewa, Gimbiya Aminatu tayi kuka iya kuka. Lamiɗo ya kira Jadda ya sanar mishi halin da ake ciki tashin hankali iya tashin hankali Jadda da Sitti sun shigeshi nan suka fara shirin tahowa. Can gabanin kiran sallar asuba lamari ya ƙara munana dan a lokacin suffar Mamey ta gama juyewa izuwa na tsunsuwar Boleru a gabana a gabansu Lamiɗo a gaban mafiya yawan al'ummar Masarautar Joɗa. nan take kuwa Abba ya yanke jiki yafaɗi yasuma. Cikin kiɗima Dr Aliyu yayi kansa yafara bashi taimakon gaggawa. Mamey kuwa da yanzu takoma tsuntsuwa fara kaɗa fiffikenta tayi alamun son tashi take. Ai kuwa tamkar al'mara sai gashi ta tashi firr ta fire tabi ta window dake a buɗe tayi tacikin Garden tashige cikin tawagarsa tsuntsayen dake wurin. Innalillahi Jamil Jalal kuwa suma sumewa sukayi. Cikin hanzari da kiɗima Lamiɗo da Galadima suka zo jikin window nan suka hango ta ta sauka cikin tsuntsayen kawai sai suka fashe da kukan tsoron al'amarin duniya. Wani irin kuka Hajia Mama tasaka tana faɗin "wayyo Allah na waishin meke faruwa damune kam". sai kawai ta yanke jiki tafaɗi ta kakkafe idanunta kamar wacce ta suma. Ranar Hajia Mama haka tawuni tana kuka ta rungume Jamil da Jalal dasuke keta kuka kamar ransu zai fita. Jadda da Sitti da Umaymah da Aunty Juwairiyya da babanta duk a ranar sukazo. An kamo tsuntsuwar Boleru suna killaceta, yayinda aketa tururuwan zuwa ganin tsuntsuwar. Ido da ido da Gimbiya Saudatu tazo da yake sokuwace. Sai cewa tayi. "Allah sarki wato al'haƙi kuikuyo ko sharrinta ya dawo kanta, ohoho larabawa an zama tsuntsuwar Boleru". Toh fa daga nanne Magautan su Sheykh duk suka samu suka fake suka laɓe a bayanta. Su kuwa haka sukaci gaba da kukan Hajia Mama ko uwartace ta mutu sai haka, duk wanda yaganta sai ta bashi tausayi akasin Lamiɗo da Galadima da suka sa zargi a kanta duk abin da take shirine da zallar iya tuggu munafurci da makirci. Tun daga lokacin tsuntsuwar nan ko ince Mamey ko yaushe sai ana kamata ita kuwa tana firewa tana komawa cikin tsuntsaye ƴan uwanta. Al'amarin ya magaga ya tada hankalin kowa. Ana kamata zata zille ta fire ta koma cikin Garden ta zauna cikin tsuntsayen cikin masarautar Joɗa. Duk wannan tashin hankali da ake ciki Sheykh Jabeer bashida labari dan lokacin yana karatu a jami'ar Madina sai dai kwata-kwata a lokacin hankalinsa yakasa ƙwanciya idan yakira wayar Mamey'n sai asa Aunty Rahma ta ɗauka tayi mishi mgn wanda ita kuma dama lokacin sun zo suna nan da Mamma. Yadda Hajia Mama ke nuna tashin hankali tane yasa suka yarda da ita. Wannan juyewar Mamey shine. Sanadin da Jadda ya samu hawan jini kenan. A ranar da dare Umaymah Mamma Aunty Rahma Aunty Juwairiyya Sitti duk sun gaza bacci, sun sa tsuntsuwar Boleru a gaba Magauta na musu dariya. Sai da asubane sun kabbarta yin salla asuba, tsuntsuwar ta tashi ta fire, Bata tsaya cikin masararutar Joɗa bama ta fuskanci ƙasar Cameroon ta nausa tayi can yankin Yahunde. Ɓacewar tsuntsuwar nan shi yafi tada musu hankali. Anyi neman duniya har an gaji. Ba ita ba dalilinta har dai aka ruggumi ƙaddara. Sai dai Lamiɗo da Galadima da Jadda da Umaymah sunci gaba da bincikawa da neman mafita. Lokacin da Sheykh ya kammala digirin sa na farko yazo. Nigeria nan ne ake faɗa masa abin da ya faru a lokacin tashin hankalin da kiɗimar rayuwar daya faɗa ciki baya misaltuwa wani babban tashin hankalin kuwa shine daya iske ya Jafar baya magana sai addu'o'in da yin karatun al'ƙur'ani mai girma da kuka, dakuma ya buƙaci yaje yaga Mamey'n shi a yadda take ɗin a tsuntsuwar ta ɗin, nan ake faɗa masa ai tun lokacin da abun yafaru da kwana ɗaya rak ta fire tabar cikin masarautar Joɗa. Ranar Sheykh kuka kamar karamin yaro ya rungume Jamil Jalal Yah Jafar da tun isowarsa Jafar ɗin ke ƙanƙame da hannun sa yana karatun yana kuka haka sukayi ta kuka Hajia Mama na tayasu. Ranar tazamo musu tamkar sabuwa. Tun daga wannan lokacin kuma sai yazamo kamar an cire hankalin Abba'n su a kansu madadin a lokacin ya janyosu jikinshi yazame musu Garkuwa dan suɗan sami sassaucin kunar dake cikin zuciyarsu sai yariƙa nisanta kanshi dasu. Shi kansa bai san dalilin hakan ba, duk wannan kuma acikin shirin Hajia Mama ce, kwana ɗayan da tsuntsuwar tayi tafire ma ita takoma gun bokanta tace tanaso tsuntsuwar tabar cikin masarautar gaba ɗaya dan taga sun dage da magungunan. Dariya bokan nata yayi tare da cewa. "Ke shar-shar banza da kika samu ma ba Addu'o'inku na musulmai sukeyiba ai da tuni sun karya sihirin". Cikin jin daɗi tace. "Aini gaba ta kaini da hankalin su baije ga canba". Lamiɗo kuwa lokacin ya ƙara jan Sheykh a jiki sosai. Sabida bayanin da Malam Musa yayi musu na cewar a sanadin aurensa da ba fulatanar daji mahaifiyarsu zata dawo. Haka yasa part in da a ka bashi kusa da Garden inda tsuntsayen suke. aka buɗe mishi wata kofa taciki in da daga cikin part ɗin direct zai sadashi da cikin Garden ɗin. Bai wani jima sosai a Nigeria ba yakoma Madina sabida jin yakeyi ya tsani ƙasar Nigeria Especially Masarautar Joɗa. Koda ya koma sosai ƴan uwan Sitti suka ga canji a rayuwarsa saida aka dage da addu'a kafin ya dawo hayyacinsa. Daga nan suka ƙara kula ta musamman a kanshi suka zame mishi uwa uba ƙanne yayu sukeyi mishi komai. Yakanyi shekara uku huɗu bai zoba. Sai dai yana yawan sawa Jadda yazo mishi da Jamil Jalal Yah Jafar da Affan yawanci duk shekara zasu zo sau biyu hajji da umra wani shekaranma sau uku. Ya maida hankali sa kan karatunsa da addu'a Allah ya baiya mishi Mameynshi a duk inda take ko a tsuntsuwar Boleru shi zaici gaba da rainonta da kula da ita iya rai da mutuwa. Daga nan yayi master's madadin ya dawo ya haɗe. PHD ɗinsa. daga nan yadawo Nigeria'n bisa tirsasawar Lamiɗo da Jadda da Galadima da Umaymah dake matsayin Uwa. Dole ya yarda ya dawo ya sanyawa ƙannensa ido wajen kula da su dakuma tarbiyyan su dakuma neman hamaifiyar su da kula da yayansa yakuma zame musu Garkuwa Da kuma bincikar Magautansu wanda dalilin haka ya samu matakin SS wanda dama shine burinsa to kuma Alhamdulillah ya gane komai Especially da ya samu damar aikin SS wanda dama burinshi kenan a dole Lamiɗo ya sashi karantan likitancin. A kwai sabo ƙauna tausayi da shaƙuwa da tsama tsakaninshi da kakanun nashi sosai. Hajia Mama kuwa da gayya ya barta da wayonta ita tanayi mishi kallon biri shi yana mata kallon ayaba. Dama kuma malam Musa. Ya faɗa musu cewa sanadin Sheykh ɗin ne Mamey'n zata dawo yabasu lbrin iya abinda Allah ya sanar mishi cewa bata rasuba tana raye kuma tajuye daga tsuntsuwar dasuke tunani tadawo mutum tuntuni tun bayan tafiyarta da watanni. (Rayuwa kenan takan iya sauyawa a duk san da Allah yaso domin shi yake juya daƙuƙu i zuwa sa'a wuni zuwa dare kwana zuwa shekara ya fidda matacce a cikin rayayye ko ya fidda rayayye a cikin matacciya) Ajiyan zuciya mai nauyi suka sauƙe baki ɗayansu da suke cikin falon. Bayan ya Jafar yagama basu labarin yadda akayi da abinda ya sani har Mamey'n su ta juye ta zama tsuntsuwa da kuma yadda akayi shima yakoma baya magana sai kuka da karatu. Gabaki ɗaya parlour'n ya kaure da ambaton sunan Allah da yiwa uban giji tasbihi. Ita kam Mamey sai murmushi takeyi tare da maimata. "Alhamdulillah! Alhamdulillah alakulli halin". Affan kuwa kuka yakeyi tamkar ransa zai bar gangar jikinsa. Cike da rauni Sheykh ya jawoshi jikinshi ya ruggumeshi suna masu zubda hawaye baki ɗayansu. Cikin rauni da tausayin irin kukan ƙuncin da Affan keyi Lamiɗo ya gyara zama tare da yin gyaran murya kana ya juyo ya kalli Bappa tare da cewa. "Ka bamu labarin yadda akayi. Aishatu tashigo hannun ku". Ai kuwa kaf hankalin jamar parlour'n yadawo kan Bappa dan kowa nason jin yadda akayi Mamey'n tashigo hannunsa gaba ɗaya shi suka zuba ido. A hankali yayi Bappa gyaran murya tare da gyara zamanshi kana ya ɗago hannunshi ya nuna Shatu da yatsarsa manuniya kana yace. "Shatu itace sanadin. Dan a lokacin da tashigo hannun mu mu muna mata kallon tsuntsuwar Boleru ne tsawon kusan wata bakwai muna tare da ita muna ganinta Giɗi yarona shike kula da ita saida ya zama tare suke cin abinci. To Shatu itace ta fara ce mana ba tsuntsuwar Boleru bace mutunce ita a ranar wata jumma'a da tazo tare da mahaifin ta Alhaji Abboi wanda ni makiyayinsa ne. Nan taga tsuntsuwar yara na son kamata su yaran damu manyan duk muna cewa tsuntsuwa ce. Ita kuma tana cewa mutum ce. Wanda haka yasa dole basu koma cikin birnin Yahunde a ranarba ita da mahaifinta suka kwana a gidana a Rugar Arɗo Babayo wanda nanne asalin mahaifata. haka ta kwana tana gaɗin tsuntsuwar har dai Allah yanuna mana ikon sa da asuba tajuya ta dawo mutum a gaban idonmu, Sai dai tana cikin larurar naƙuda. Cikin ikon Allah ta haifu ta sauƙa lfy ta haifi ɗiyarta mace. To lokacine mukaga sarƙar dake wuyanta. Mai ɗauke da tambarin masarautar Joɗa kasan cewar masarautar fulɓe ce kuma mahaifin Alhaji Abboi abo kine ga Lamiɗo akan ɗan ziyarci juna kaɗan kaɗan to sanadin hakane Alhaji Abboi ya gane tambarin dake jin sarƙar na masarautar Joɗa ce. Tofa anan muka gane cewa duk yadda akayi ita ahalin masarautar Joɗa ce. Kuma Sarkin bakanmu ya tabbatar mana ita mutunce aikin sihirine to sai dai babu yadda za'ayi mu fuskanceku da mgnar kai tsaye tunda bamu san komai nakuba." Ɗan tsakaita maganar yayi yaɗan ja numfashi kana yaci gaba da faɗin. "Ni banine mahaifin Shatu ba Alh Abboi shine mahaifinta ga kuma mahaifiyarta. Ni makiyayin mahaifinta ne. inayi masa kiwone yana biyan. Mafi akasari duk karshen wata suna zuwa tare da ita nan Rugar Arɗo Babayo. To ita Shatu tanason yanayin daji rugarmu shiyasa duk sanda zaizo da ita zai zo, in zai koma kuma wasu lokutan yakan koma yabarta anan Rugarmu da yake ranar Jumma'a yake zuwa, to sai ranar lahadi da yamma Al'ameen ko wani daga cikin yayunta yazo ya ɗauke ta su koma. Yawan zuwasu shi yasa tasaba da da yarana sosai da mai ɗakina. To amman zuwansu da Allah ya ƙaddara lamarin Ummey ta juye a gabanta fir babu yadda ba'ayi da ita ta komaba taƙi bin mahaifinta fir taƙi tace ita zata zauna da Ummey ita ta zaɓa Junainah suna. Wannan yasa dole mahaifinta ya koma ya barta. To lokacin da Ummey'n Shatu'n ta faɗo hannunmu muka kuma ga wannan sarkar dake wuyanta na masarautar Joɗa shine Alh Abboi yace mu ƙaura mu dawo nan. Nigeria kusa da masarautar Joɗa cikin Rugar Bani dan tasami kusan ci da masarautar. to nan fa muka dawo Nigeria har da ita Shatu'n dan taƙi yar da a raba su da Ummey'n ta ashe rabo ke jawota nan. dole iyayenta suka haƙura suka barta tare dani. Muna dawowa nan muka sata a makarantar cikin Shikan". Nan yaci gaba da basu labarin duk wani bayanin gwa-gwar mayar da Shatu tayi a ka Ummey duk sai da ya basu labari. Ya ƙara da cewa. "Lokacin da muka zo Nigeria da Ummey wato (Mamey) Ba'ana naɗan shekaru sha takwas a duniya, lokacin (Parvina) wato Shatu kenan ita kuma du-du shekarun ta takwas ne, to kafin mu dawo ma Mamey bata dawo daga haiyacin taba bata fara magana ba, lokacin da mukazo. Nigeria Rugar Bani sai Ba'ana yace zai bata mgnin zata fara mgn kuma zata zama dai-dai sai dai zaiyi wuya ta tuna baya, Amman zata dawo tayi mgn amman da sharadi. kasan cewar fatanmu ta tuna baya mu maidata ga ahlinta yasa mukace mun amince da sharaɗinsa wanda bamu san menene sharaɗin ba. Shi saida ya fara bata mgnin kuma yace sai da sharaɗin in Ummey ta worke ta fara mgn muyi al'ƙawarin aura mishi Shatu. To lokacin mu baƙine bamu san halinsa na ɓoyeba kuma burinmu da fatanmu ta worke mu maidata hannun ƴan uwanta sai muka amince mukayi mishi wannan al'ƙawarin bisa rashin sanin halin daga ranar Mata yake kiran Shatu. Kullum Shatu ita ke zuwa gidansu Ba'ana da safe tana karɓawa Ummey magani a gunsa, dan shi tun tashin sa yake wannan cacube-cacuben nasa, so kullum. Shike bawa Shatu magani ta kawo wa Ummey tana sha har Ummey tadawo tafara magana sai dai bata iya tuna baya ba nan. Ba'ana'n ke ce mana duk randa taga wasu nata ko ƴan uwan ta ko wani abu nata zai yiwu tunanin ta yadawo ta iya tuna baya." Sai kuma ya ɗan tsagaita tare da sauƙe numfashi kana a hankali yaci gaba da cewa. "Toh tun daga ranar ne muka fara neman hanya da dalilin da zai haɗamu daku mutanen masarautar Joɗa. Sabida munsan aikin sihirine dole akwai Magauta sannan a gefen Ba'ana kuwa ya addabemu ya hana Shatu salama duk mai sonta sai yaga bayanshi. To sai marigayi Cuɓaɗo ya bamu tabbacin bulalin Shaɗin masarautar Joɗa ne kawai zai karya duk wani sihirin jikin Ba'ana to kasan cewar yana sonta so na gsky bai cutar da ita in hankalinmu ya tashi kan muna tsoron ya aureta takan ce mana. "Abinda in na gama karatuna zamu koma Yahunde sabida ita bamu sanar mata mun gano asalin Ummey ƴar ina bane gudun ita yarinyace kada tai ta gayawa wasu. To munata son yadda alaƙa zata haɗamu sai kuma ga ƙabilar ɓachama su tasomu gaba. Ran da muka zo nan na forko da muka ga Jamil sosai muka ƙara ƙarfafa guiwar ita ahlin masarautar Joɗa ce dan akwai kamar jini tare dashi da ita. To da akayi faɗa kukaje mana jaje da gayya Arɗo Bani ya gaggayawa mai martaba Lamiɗo mgn dan ya tunzurashi ayi Shaɗi mu jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya kenan. Mun dawo da ita, mu kuma samu mgnin Ba'ana to kuma Alhamdulillah duk abin neman ya samu. Sai kuma yayi ƙasa da kanshi murya na rawa yace. "Sai dai sanadin faɗan ni na rasa kowa nawa". Bappa ya ƙarashe mgnar cikin rauni da zubda hawayen tuno matarsa da zaratan yaranshi. Cikin raunin tuno ahlinshi kuka mai rauni ya rufeshi yayinda Shatuma kuka mai ƙarfi ya kubce mata hakama Ummey sabida ita dai gata ta dawo ahlinta shi kuma garin dawo da ita cikin ƴaƴanta ya rasa nashi yaran. Cikin tsananin jin daɗi Sheykh ya ɗan muskuta cikin tsananin farin ciki da jin daɗin da godewa Allah daya bashi damar kuɓutar dasu ƴaƴan Bappa su Gaini shima zaisa Bappa farin ciki kwatankwacin yadda ya sashi. Cikin sauri da bada umarni ya kalli Jamil tare da cewa. "Jamil tashi maza kaje kazo dasu". "To". Jamil yace kana ya miƙe da sauri yafita batare da ɓata lokaciba sabida ya gano su waye Gaini. Yana zuwa yace. "Yah Gaini taso taso kuzo ga Bappanku da Shatu da Junainah". Ai kafinma ya rufe baki duk sun muƙe cikin tsananin zaƙuwa suka biyo bayanshi. Shi kuwa Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro da Alhaji Umaru rauninsu ya rigada ya dawo tuno irin kisan gillar da ƙabilar ɓachama sukayi musu. Shi kuwa Sheykh dasu Lamiɗo shiru sukayi sabida son yi musu ba zata. Da sauri Jamil yasa hannunshi ya tura ƙofar suka shigo tare da cewa. "Assalamu alaikum Bappa share hawayenka gasu Yah Gaini Seyo da Giɗi". Duk sauran mutanen falon duk suka ɗago kansu. Ido cikin ido Shatu tayi da Yah Giɗi'nta abokin tsamarta. Wani irin yunƙura tayi ta miƙe tsaye tare da cewa. "La'ilahaillaha Muhammadu rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam Alhamdulillah Bappa gasu Yah Gaini". Jin kalaman Shatu ne yasa Bappa dayake sunkuye ya ɗago kanshi yana kalli bakin ƙofar shigowa ya sauƙe kwayar idanunshi kan.....! Kuyi haƙuri da typing errors ina cikin ciwon kai nayi typing ɗin a daddafe. Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300. A yawan posting ne babban cinsu 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa in kin tura sai kiyi screenshort na Debit Alert ki turo min ta whatsApp 09097853276 ƴan 3oo in naki da halin biya ta Account zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ku turo min ta whatsApp ɗin 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: "Aranar wata jumma da da wanna Zazzafar ƙaddara ta rufta damu shekaru goma sha uku baya." Sai kuma ya ɗan tsakaita tare da jan sassayan numfashi ya gyara zamansa tare dasa tafin hannunshi ya share hawayensa. Yayin da gaba ɗayansu kacokam suka mai da hankalin su kansa, Duk sun ƙagu suji yadda a kayi a wannan ranar da basu manceba. Shi kuwa Yah Jafar wani numfashin yakuma. Saukewa kana yaci gaba da cewa. "Ranar da dare bayan anyi sallan isha'i duk muna falon Mamey dani dasu Jalal Jamil Affan da Ummi da Imran yana ɗan sheksru takwas lokacin. Anan mukaci abinci kana muka zauna muna hira. Kasan cewar akwai shaƙuwa mai tarin yawa tsakanin Mamey da Affan da yake tana da son yara. Amman son Affan da banne a wurinta har su Jamil kance wa Affan na hannun daman Mamey. Takanyi Dariya tace. "Eh ɗin ai ya fiku nitsuwa". Muna zaune sai hamma Mamey keyi tare da miƙa da lumshe idonta hakane yasa tace mana. Duk ta sallamemu saida safe tanajin bacci. Ummi tace. To. Still Kuma sai mukaci gaba da hira. Da ido muka bita ganin ta miƙa cikin sanyi tace. "Kai zanje inyi bacci wlh wani irin bacci mai nauyi nakeji yana fuzgata tamkar zan faɗi. Ni na shiga saida safenku". Allah ya bamu al'khairi mukace dukanmu kana ta shiga. Tana shiga kwanta ko second uku batayi da kwanciya ba tayi bacci. Mu kuwa muna gama hira muka watse. To su Jalal ne ƙarshen fita ashe basu tasheta ta rufe ƙofarta ba a famintata kenan fa?". Ya ƙare mgnar yana kallon su Jamil. Da sauri Jamil yace. Eh. Cikin sanyi ya kalli su Lamiɗo kana yaci gaba da cewa. "Ina komawa ɗaki na kira Juwairiyya muka fara hira a waya kamar kullum. To bayan mun gama waya da Juwairiyya har na kwanta sai na mike na nufi ɗakin Mamey dan inaso nayi mata magana a kan Juwairiyya fa tasanar wa mahaifin su maganar auren mu da ita, tun da lokacin takammala karatun ta dan haka itama ta gayawa Abba na ayi batun aurenmu dan nima tuni lokacin na gama karatuna har na fara aiki. Kuma a kwanakin ne aka bani sarautar Galadima wanda da mijin Gimbiya Saudatu ce mai matsayin to daya rasune Lamiɗo ya maida mulkin kaina. A zatonshi ta hakane zaisa yaranshi bazasuyi faɗa da junaba tunda bazasuce ya baiwa wane ya hana waneba. Ni a lokacin dagani har Mamey da Jabeer da baya ƙasar ma ba son wannan mulkin mukayiba bisa dole aka bani ita. Sai kuma ya jingina bayanshi da kujera kana yaci gaba da cewa. Ina isa bakin kofar Mamey natura kofar da sallama nashiga ɗakinta. Da sauri naja natsaya nan bakin kofar. Can na hangi Mamey na kwance. Bisa gado tana bacci da alamun baccin mai nauyi ne. Hajiya mama kuwa na tsaye a kanta da wata iriyar shiga da tafi kama data bokaye ko ince matsafa. Da mamaki nake kallon Hajia Mama dake tsaye bakin gadon sanye da wasu irin jajayen kaya tun daga samanta har ƙasa, kanta babu ko ɗan kwali hannunta rike da wani ƙwarya. Tana yayyafawa Mamey wani ruwa dake cikin ƙwaryar tare da yin wasu surutai da sukafi kama da surkullen matsafa. "Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un, nafurta da karfi. Da sauri nanufo in da Hajia Mama'n ke tsaye cikin ruɗani da kiɗima ina faɗin. Meye hakan Hajia Mama? me kike mata? me kike zuba mata a jiki haka?. Dasauri tajuyo kaina tasaka hannunta cikin ƙwaryar taɗibo ruwan tashiga watsamin tana ƙara matsoni, kaucewa nashiga yi ina matsowa in da Mamey take kwance kamar gawa ko matsi batayi, itako Hajia Mama masoni tarikayi tana watsamin ruwan, Baki na buɗe da karfi sabida wani irin masifeffen suka da naji duk inda ruwan ya taɓa a jikina yanayi. Ƙara watsomin tayi wanda yasa na ƙara kaucewa da sauri tare da buɗe baki da nufin yin ihun zafin da nakeji da kuma fargabar halin da Mamey na ke ciki. Sai kawai naji harshena yafurta Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un,wannan kalmar narika nanawata da karfi madadin inyi ihu." Ita kuwa Hajia Mama da sauri tajuya cikin alamun tsoron tonuwar asirinta. dan lokacin dare baiyi nisa sosai ba misalin ƙarfe goma ne, da gudu tafita a ɗaki dan jin yadda na kara sautin salatin da nake. Ita kuwa Hajia Mama tana fita part ɗinta ta nufa direct bathroom ɗinta ta shiga gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi number'n bokan ta takira yana ɗagawa cikin haki da fargabar a bin da zaije ya da wo tace. "Boka yanzu nafito daga ɗakin matarnan na samu tayi bacci kamar yadda kace, kuma na watsa mata ruwan bata farka a sai daifa wani yaganni lokacin danake yayyafa mata ruwan maganin nan babban ɗanta Galadiman Masarautar Joɗa kenan ya ganni". Wani irin dariya irin nasu na hatsabibai bokan yayi kana yace. "Toh daya ganki me yakeyi? me kuma yake cewa?". cikin rawar baki da soron da ya ziyarce ta gudun kada ai kin ya ɓaci tace. "Sunan Allah yaketa ambata salati yaketayi babu ko kakkautawa da wasu addu'o'i". Cikin ɗan tsagaita dariyar mugayen bokan yace "To aiki kam zaici amma dai akwai nakasu aciki, amma kada kidamu yanzu shi yaron zamu rufemasa baki zai dauwama kurma ba mgna a bakinsa bazai iya yin maganaba bazai iya furta komai ba haka zai dauwama ba mgn saidai yayi ta mai-mai-ta abinda yake cewa. Sannan daga nan tagwayen kuma zamu haɗa ɗaya da bin mata ɗaya shaye-shaye shi kuma babban kinga zai zama kamar Mahaukaci, shi kuma wancan Jabeer ɗin na gaya miki tun yana ƙaramin akwai sihirin da wani yayi mishi kada ki damu dashi bazai taɓa yin aureba har gaban abadan ko an mishi bazai zauna da matarba, kinga kenan duk sun zama suna da matsalar da dole baza'a basu mulkiba sai dai a bawa ɗanki Affan tunda kinga shi Imran ɗan ɗaya kishiyar taki shine ƙarami kan Affan." Cikin sauƙe numfashi tace. "Yauwa boka na gode ni dama fatana ɗana yayi mulki dan bana son mulkin ya bar ɗakina tunda dai kace min tabbas cikin yaran Habibullah ne mijin wani zai gaji kakansa sarauta. Dariya yayi tare da cewa. "Kada ki damu mulki na gareki da ɗanki". Wa iyazubillah kaɗan kenan daga sharrin tsinannun shaiɗanu maƙiya Allah da Manzonsa bokaye taɓaɓɓu masu sa mai binsu ya taɓe ya gaza sauri a ranar da muminai ke sauri a bisa siraɗi. Acan cikin ɗakin Mamey kuwa. Sosai sautin addu'a da karatun da Jafar keyi yatsanan ta yana kankame da Mamey, wacce ke ƙwance ida nunta a rufe, har lokacin bata farka daga. Baccin sihirin da akasa takeyi ba saboda nauyin. Baccin da suka je fata ciki. Sheko bakinsa baya iya furta komai sai addu'o'in sai kuma hawaye da keta tsatstsafowa daga cikin ida nunsa sabida fargarba da kuma zafin da yakeji, Abba kuwa dake can part ɗinsa da yake Part ɗin shi na natsakanin na matan nashi ne. Yana cikin ɗakinsa dake sama. Haka yasa yarinƙa jiyo muryar Jafar da irin addu'o'in dayake cikin kiɗima, da kajin addu'ar kasan acikin tsananin firgici da tashin hankali yake yinsa, Wuf yamike yanufo part in Mamey kasan cewar babu wata tazara sakaninsu. Gudu-gudu sauri-sauri ya isa. Cikin hanzari yatura kofar bedroom ɗin Mamey cikin sananin tashin hankali da kaɗuwa ganin yadda Yah Jafar ke rungume da Mamey sai innalillahi yake da karfi hawaye yagama wanke fuskarsa idanunsa sun yi jazir saboda kuka da zafin da yakeji da fargabar ganin tamkar Mamey a mace take a kiɗime yanufo in da suke yana faɗin. "Subahanallahi kai Jafar meya farune me ya sameta?". Yayi tambayar hankali a tashe, tare da miƙa hannu ya ɗago kan Mamey dake kan kafar Ya Jafar yashiga girgizata yana kiran sunan ta. "Aisha! Aisha!! Ummu Jabeer!. Gani shiru bata ko matsi sai dai tana numfashi ya tsananta firgicinsa. Hankali a tashe yakuma kallon ya Jafar wanda keta addu'o'in babu ko kakkautawa. Mai da kan Mamey'n yayi ya kwantar kan cinyar kafar Jafar. Kana ya juya a kiɗime ya fita a ɗakin da sauri ya nufi sashin mahaifinsa Lamiɗo. Shi ko ya Jafar cigaba da maimata innalillahi yakeyi yana zubda hawayen. A can ɓangaren Hajia Mama kuwa. fitowar ta daga ɗakinta kenan cike da jin daɗin yadda bokan ya karfafa mata guiwa tanajin daɗi a ranta yanzu komai zai tafi mata yadda take bukata zata rabu da zugar yayan Mamey da ita duk kowa ya huta, tana fita ta hangi Abba ta window yafita daga cikin part ɗinsa hankali a tashe. Fuska ta ɗan yamusa tazauna saman ɗaya daga cikin kujerun parlour'n, can kuma tamike kamar an tsikareta tabi bayansa da sauri. Acan shashin Lamiɗo kuwa. Da sauri Lamiɗo da Galadima suka mike, bayan Abba yagama sanar musu abin da ke faruwa. A tare suka fito suka nufi part ɗin Mamey'n. Lamiɗo na gaba Galadima da Abba na biye dashi suka shiga ɗakin, in da Abba yabar Yah Jafar a haka suka iske shi yana ganinsu ya miƙe da sauri Mamey yashiga nuna wasu Lamiɗo da hannu yana kuka yana nuna musu ita da kwatanta musu yadda Hajia Mama tayi mata. Da sauri Hajia Mama ta turo kofar dan taga shigowar su Lamiɗo'n. Jafar kuwa yana ganinta yashiga nunata da hannu sai kuma ya nuna Mamey'n yana cigaba da ƙwatanta yadda tayi matan shidai baki kam babu shi sai dai addu'o'in da kuma kukan dayake tayi. Gaba ɗaya su suka maida kallonsu kan Hajia Mama nan take Lamiɗo da Galadima da Abba suka ɗiga ayar tambaya a kanta. itako ganin bawai magana Jafar ɗin keyiba sai bata damuba bata kuma fahimci cewa sun zargi meyafaru ba kuma basu gane me. Jafar ɗin yake cewa ba da hakan ba. Hajia mama kuwa cikeda da karfin hali irin nata na makiran mugaye mata tafara tafa hannu tana masar kwalla tana faɗin "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un Jafar me nake gani haka me yasami Mamey'n ku? kayi magana mana". Sai kuma tasaki kuka mai haɗe da salati. Lamiɗo ne yaɗanyi gyaran murya ganin Mamey'n tafara motsawa alamar tafarka daga nannauyan Baccin da take mikewa tayi zaune tare da zuba musu ido. Da sauri suka ɗan matso gareta kana duk suka mai da hankalin su kanta. Suna ce mata sannu Aisha, Amman shiru ba amsa. Cikin tsananin sauri da tsoro Abba ya matso kusa da ita tare da zubawa yatsun kafarta ido mamaki cike da kiɗima yake kallon yatsun kafarta da suka fara sauya kamannin halitta suka koma kamar na tsuntsu. Cike da alhini suma su Lamiɗo suke kallon yatsun kafar nata, hankali a tashe. Cikin gigita Abba ya kamo hannunta tare da nunawa Lamiɗo murya a daburce yace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Lamiɗo kalli yatsunta". wani matsanancin tashin hankalin ne yakuma dabaibayesu lokacin da suka ga yatsun hannunta yafara komawa irinna fiffiken tsuntsu. Gaba ki ɗaya su haɗa baki sukayi wajan furta "innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un hasbullahu wani'imalwakin". Sabida tsananin firgici da tashin hankali gaba ɗaya jikinsu rawa yakeyi. Cikin matsanan cin tashin hankali Lamiɗo da cushewar tunani Lamiɗo ya juyo ya kalli Galadima murya a hargitse yace. "Subahanallahi maza a kira Malam Musa yanzu nan". Cikin hanzari Galadima ya amsa da. "To". Kana yajuya da sauri yafita. Kan kace me labari yabaza masarautar Joɗo, Batare da bata lokaci ba sakon kiran da Lamiɗo yayiwa Malam Musa ya isa gareshi. Cikin ƴan daƙiƙu malam Musa ya iso cikin masarautar Joɗa Lamiɗo yabada umurnin a shigo dashi har cikin ɗakin Mamey. Yana shiga kallonta malam Musa yayi cikin tashin hankali ya girgizata kai kana yakallesu Lamiɗo yace. "Sihirine a kamata mai haɗe da tsafi kuma daga yanzu zuwa ko yaushe ko wanne lokacin zata iya juyewa daga mutun ta dawo tsunsuwa". Salati suka ɗauka baki ɗayansu nan kuma ɗakin yakacame da koke-koke su Jamil da Jalal Affan Ummi Jafar yayin da duk muryar Hajia Mama yafi amo wajen kuka da shiga tashin hankali ziraran miraran. (uhum makircin mugu kenan.) (Sai daifa akwai kishiyoyi na gari da matsalar kishiya kan sasu kukan gaske wlh.) Ranar kuwa wannan masarautar taga tashin hankali mara misaltuwa, Jiƙe-jiƙe da hayaƙi da shafe-shafen magungun gargajiya babu wanda malam Musa baiba, kiɗima yasa sun mance da suyi amfanin da ayatul shifa. Ganin anyi duk abinda za'ayi na gargaji abin yaci tura ne yasa hankalin. Dr Aliyu yakasa ƙwanciya gani yake ko wata cutarce ta da ban haka yasa ya fitadaga ɗakin yatafi part ɗin sa, kiran wasu manyan likitoci a bokansa. Yasanar musu koda wani shawarin da zasu basu bayan sun gama wayar kuwa. Kayan ai kinsa ya ɗauko yakomo ɗakin Mamey'n yayi iya gwaje-gwajen sa babu abinda ya gane na wani cuta ko wani abu. Cikin takaici Malam Musa yace. "Kama bar gwada ta babu wani cuta face sihiri". Daga karshe dai dole ya hakura. Ranar babu wanda ya rumtsa kusan a tsaye suka kwana nan cikin ɗakin Mamey'n ganin yadda gaba ɗaya kamannin halittarta ke juyewa, Gimbiya Aminatu tayi kuka iya kuka. Lamiɗo ya kira Jadda ya sanar mishi halin da ake ciki tashin hankali iya tashin hankali Jadda da Sitti sun shigeshi nan suka fara shirin tahowa. Can gabanin kiran sallar asuba lamari ya ƙara munana dan a lokacin suffar Mamey ta gama juyewa izuwa na tsunsuwar Boleru a gabana a gabansu Lamiɗo a gaban mafiya yawan al'ummar Masarautar Joɗa. nan take kuwa Abba ya yanke jiki yafaɗi yasuma. Cikin kiɗima Dr Aliyu yayi kansa yafara bashi taimakon gaggawa. Mamey kuwa da yanzu takoma tsuntsuwa fara kaɗa fiffikenta tayi alamun son tashi take. Ai kuwa tamkar al'mara sai gashi ta tashi firr ta fire tabi ta window dake a buɗe tayi tacikin Garden tashige cikin tawagarsa tsuntsayen dake wurin. Innalillahi Jamil Jalal kuwa suma sumewa sukayi. Cikin hanzari da kiɗima Lamiɗo da Galadima suka zo jikin window nan suka hango ta ta sauka cikin tsuntsayen kawai sai suka fashe da kukan tsoron al'amarin duniya. Wani irin kuka Hajia Mama tasaka tana faɗin "wayyo Allah na waishin meke faruwa damune kam". sai kawai ta yanke jiki tafaɗi ta kakkafe idanunta kamar wacce ta suma. Ranar Hajia Mama haka tawuni tana kuka ta rungume Jamil da Jalal dasuke keta kuka kamar ransu zai fita. Jadda da Sitti da Umaymah da Aunty Juwairiyya da babanta duk a ranar sukazo. An kamo tsuntsuwar Boleru suna killaceta, yayinda aketa tururuwan zuwa ganin tsuntsuwar. Ido da ido da Gimbiya Saudatu tazo da yake sokuwace. Sai cewa tayi. "Allah sarki wato al'haƙi kuikuyo ko sharrinta ya dawo kanta, ohoho larabawa an zama tsuntsuwar Boleru". Toh fa daga nanne Magautan su Sheykh duk suka samu suka fake suka laɓe a bayanta. Su kuwa haka sukaci gaba da kukan Hajia Mama ko uwartace ta mutu sai haka, duk wanda yaganta sai ta bashi tausayi akasin Lamiɗo da Galadima da suka sa zargi a kanta duk abin da take shirine da zallar iya tuggu munafurci da makirci. Tun daga lokacin tsuntsuwar nan ko ince Mamey ko yaushe sai ana kamata ita kuwa tana firewa tana komawa cikin tsuntsaye ƴan uwanta. Al'amarin ya magaga ya tada hankalin kowa. Ana kamata zata zille ta fire ta koma cikin Garden ta zauna cikin tsuntsayen cikin masarautar Joɗa. Duk wannan tashin hankali da ake ciki Sheykh Jabeer bashida labari dan lokacin yana karatu a jami'ar Madina sai dai kwata-kwata a lokacin hankalinsa yakasa ƙwanciya idan yakira wayar Mamey'n sai asa Aunty Rahma ta ɗauka tayi mishi mgn wanda ita kuma dama lokacin sun zo suna nan da Mamma. Yadda Hajia Mama ke nuna tashin hankali tane yasa suka yarda da ita. Wannan juyewar Mamey shine. Sanadin da Jadda ya samu hawan jini kenan. A ranar da dare Umaymah Mamma Aunty Rahma Aunty Juwairiyya Sitti duk sun gaza bacci, sun sa tsuntsuwar Boleru a gaba Magauta na musu dariya. Sai da asubane sun kabbarta yin salla asuba, tsuntsuwar ta tashi ta fire, Bata tsaya cikin masararutar Joɗa bama ta fuskanci ƙasar Cameroon ta nausa tayi can yankin Yahunde. Ɓacewar tsuntsuwar nan shi yafi tada musu hankali. Anyi neman duniya har an gaji. Ba ita ba dalilinta har dai aka ruggumi ƙaddara. Sai dai Lamiɗo da Galadima da Jadda da Umaymah sunci gaba da bincikawa da neman mafita. Lokacin da Sheykh ya kammala digirin sa na farko yazo. Nigeria nan ne ake faɗa masa abin da ya faru a lokacin tashin hankalin da kiɗimar rayuwar daya faɗa ciki baya misaltuwa wani babban tashin hankalin kuwa shine daya iske ya Jafar baya magana sai addu'o'in da yin karatun al'ƙur'ani mai girma da kuka, dakuma ya buƙaci yaje yaga Mamey'n shi a yadda take ɗin a tsuntsuwar ta ɗin, nan ake faɗa masa ai tun lokacin da abun yafaru da kwana ɗaya rak ta fire tabar cikin masarautar Joɗa. Ranar Sheykh kuka kamar karamin yaro ya rungume Jamil Jalal Yah Jafar da tun isowarsa Jafar ɗin ke ƙanƙame da hannun sa yana karatun yana kuka haka sukayi ta kuka Hajia Mama na tayasu. Ranar tazamo musu tamkar sabuwa. Tun daga wannan lokacin kuma sai yazamo kamar an cire hankalin Abba'n su a kansu madadin a lokacin ya janyosu jikinshi yazame musu Garkuwa dan suɗan sami sassaucin kunar dake cikin zuciyarsu sai yariƙa nisanta kanshi dasu. Shi kansa bai san dalilin hakan ba, duk wannan kuma acikin shirin Hajia Mama ce, kwana ɗayan da tsuntsuwar tayi tafire ma ita takoma gun bokanta tace tanaso tsuntsuwar tabar cikin masarautar gaba ɗaya dan taga sun dage da magungunan. Dariya bokan nata yayi tare da cewa. "Ke shar-shar banza da kika samu ma ba Addu'o'inku na musulmai sukeyiba ai da tuni sun karya sihirin". Cikin jin daɗi tace. "Aini gaba ta kaini da hankalin su baije ga canba". Lamiɗo kuwa lokacin ya ƙara jan Sheykh a jiki sosai. Sabida bayanin da Malam Musa yayi musu na cewar a sanadin aurensa da ba fulatanar daji mahaifiyarsu zata dawo. Haka yasa part in da a ka bashi kusa da Garden inda tsuntsayen suke. aka buɗe mishi wata kofa taciki in da daga cikin part ɗin direct zai sadashi da cikin Garden ɗin. Bai wani jima sosai a Nigeria ba yakoma Madina sabida jin yakeyi ya tsani ƙasar Nigeria Especially Masarautar Joɗa. Koda ya koma sosai ƴan uwan Sitti suka ga canji a rayuwarsa saida aka dage da addu'a kafin ya dawo hayyacinsa. Daga nan suka ƙara kula ta musamman a kanshi suka zame mishi uwa uba ƙanne yayu sukeyi mishi komai. Yakanyi shekara uku huɗu bai zoba. Sai dai yana yawan sawa Jadda yazo mishi da Jamil Jalal Yah Jafar da Affan yawanci duk shekara zasu zo sau biyu hajji da umra wani shekaranma sau uku. Ya maida hankali sa kan karatunsa da addu'a Allah ya baiya mishi Mameynshi a duk inda take ko a tsuntsuwar Boleru shi zaici gaba da rainonta da kula da ita iya rai da mutuwa. Daga nan yayi master's madadin ya dawo ya haɗe. PHD ɗinsa. daga nan yadawo Nigeria'n bisa tirsasawar Lamiɗo da Jadda da Galadima da Umaymah dake matsayin Uwa. Dole ya yarda ya dawo ya sanyawa ƙannensa ido wajen kula da su dakuma tarbiyyan su dakuma neman hamaifiyar su da kula da yayansa yakuma zame musu Garkuwa Da kuma bincikar Magautansu wanda dalilin haka ya samu matakin SS wanda dama shine burinsa to kuma Alhamdulillah ya gane komai Especially da ya samu damar aikin SS wanda dama burinshi kenan a dole Lamiɗo ya sashi karantan likitancin. A kwai sabo ƙauna tausayi da shaƙuwa da tsama tsakaninshi da kakanun nashi sosai. Hajia Mama kuwa da gayya ya barta da wayonta ita tanayi mishi kallon biri shi yana mata kallon ayaba. Dama kuma malam Musa. Ya faɗa musu cewa sanadin Sheykh ɗin ne Mamey'n zata dawo yabasu lbrin iya abinda Allah ya sanar mishi cewa bata rasuba tana raye kuma tajuye daga tsuntsuwar dasuke tunani tadawo mutum tuntuni tun bayan tafiyarta da watanni. (Rayuwa kenan takan iya sauyawa a duk san da Allah yaso domin shi yake juya daƙuƙu i zuwa sa'a wuni zuwa dare kwana zuwa shekara ya fidda matacce a cikin rayayye ko ya fidda rayayye a cikin matacciya) Ajiyan zuciya mai nauyi suka sauƙe baki ɗayansu da suke cikin falon. Bayan ya Jafar yagama basu labarin yadda akayi da abinda ya sani har Mamey'n su ta juye ta zama tsuntsuwa da kuma yadda akayi shima yakoma baya magana sai kuka da karatu. Gabaki ɗaya parlour'n ya kaure da ambaton sunan Allah da yiwa uban giji tasbihi. Ita kam Mamey sai murmushi takeyi tare da maimata. "Alhamdulillah! Alhamdulillah alakulli halin". Affan kuwa kuka yakeyi tamkar ransa zai bar gangar jikinsa. Cike da rauni Sheykh ya jawoshi jikinshi ya ruggumeshi suna masu zubda hawaye baki ɗayansu. Cikin rauni da tausayin irin kukan ƙuncin da Affan keyi Lamiɗo ya gyara zama tare da yin gyaran murya kana ya juyo ya kalli Bappa tare da cewa. "Ka bamu labarin yadda akayi. Aishatu tashigo hannun ku". Ai kuwa kaf hankalin jamar parlour'n yadawo kan Bappa dan kowa nason jin yadda akayi Mamey'n tashigo hannunsa gaba ɗaya shi suka zuba ido. A hankali yayi Bappa gyaran murya tare da gyara zamanshi kana ya ɗago hannunshi ya nuna Shatu da yatsarsa manuniya kana yace. "Shatu itace sanadin. Dan a lokacin da tashigo hannun mu mu muna mata kallon tsuntsuwar Boleru ne tsawon kusan wata bakwai muna tare da ita muna ganinta Giɗi yarona shike kula da ita saida ya zama tare suke cin abinci. To Shatu itace ta fara ce mana ba tsuntsuwar Boleru bace mutunce ita a ranar wata jumma'a da tazo tare da mahaifin ta Alhaji Abboi wanda ni makiyayinsa ne. Nan taga tsuntsuwar yara na son kamata su yaran damu manyan duk muna cewa tsuntsuwa ce. Ita kuma tana cewa mutum ce. Wanda haka yasa dole basu koma cikin birnin Yahunde a ranarba ita da mahaifinta suka kwana a gidana a Rugar Arɗo Babayo wanda nanne asalin mahaifata. haka ta kwana tana gaɗin tsuntsuwar har dai Allah yanuna mana ikon sa da asuba tajuya ta dawo mutum a gaban idonmu, Sai dai tana cikin larurar naƙuda. Cikin ikon Allah ta haifu ta sauƙa lfy ta haifi ɗiyarta mace. To lokacine mukaga sarƙar dake wuyanta. Mai ɗauke da tambarin masarautar Joɗa kasan cewar masarautar fulɓe ce kuma mahaifin Alhaji Abboi abo kine ga Lamiɗo akan ɗan ziyarci juna kaɗan kaɗan to sanadin hakane Alhaji Abboi ya gane tambarin dake jin sarƙar na masarautar Joɗa ce. Tofa anan muka gane cewa duk yadda akayi ita ahalin masarautar Joɗa ce. Kuma Sarkin bakanmu ya tabbatar mana ita mutunce aikin sihirine to sai dai babu yadda za'ayi mu fuskanceku da mgnar kai tsaye tunda bamu san komai nakuba." Ɗan tsakaita maganar yayi yaɗan ja numfashi kana yaci gaba da faɗin. "Ni banine mahaifin Shatu ba Alh Abboi shine mahaifinta ga kuma mahaifiyarta. Ni makiyayin mahaifinta ne. inayi masa kiwone yana biyan. Mafi akasari duk karshen wata suna zuwa tare da ita nan Rugar Arɗo Babayo. To ita Shatu tanason yanayin daji rugarmu shiyasa duk sanda zaizo da ita zai zo, in zai koma kuma wasu lokutan yakan koma yabarta anan Rugarmu da yake ranar Jumma'a yake zuwa, to sai ranar lahadi da yamma Al'ameen ko wani daga cikin yayunta yazo ya ɗauke ta su koma. Yawan zuwasu shi yasa tasaba da da yarana sosai da mai ɗakina. To amman zuwansu da Allah ya ƙaddara lamarin Ummey ta juye a gabanta fir babu yadda ba'ayi da ita ta komaba taƙi bin mahaifinta fir taƙi tace ita zata zauna da Ummey ita ta zaɓa Junainah suna. Wannan yasa dole mahaifinta ya koma ya barta. To lokacin da Ummey'n Shatu'n ta faɗo hannunmu muka kuma ga wannan sarkar dake wuyanta na masarautar Joɗa shine Alh Abboi yace mu ƙaura mu dawo nan. Nigeria kusa da masarautar Joɗa cikin Rugar Bani dan tasami kusan ci da masarautar. to nan fa muka dawo Nigeria har da ita Shatu'n dan taƙi yar da a raba su da Ummey'n ta ashe rabo ke jawota nan. dole iyayenta suka haƙura suka barta tare dani. Muna dawowa nan muka sata a makarantar cikin Shikan". Nan yaci gaba da basu labarin duk wani bayanin gwa-gwar mayar da Shatu tayi a ka Ummey duk sai da ya basu labari. Ya ƙara da cewa. "Lokacin da muka zo Nigeria da Ummey wato (Mamey) Ba'ana naɗan shekaru sha takwas a duniya, lokacin (Parvina) wato Shatu kenan ita kuma du-du shekarun ta takwas ne, to kafin mu dawo ma Mamey bata dawo daga haiyacin taba bata fara magana ba, lokacin da mukazo. Nigeria Rugar Bani sai Ba'ana yace zai bata mgnin zata fara mgn kuma zata zama dai-dai sai dai zaiyi wuya ta tuna baya, Amman zata dawo tayi mgn amman da sharadi. kasan cewar fatanmu ta tuna baya mu maidata ga ahlinta yasa mukace mun amince da sharaɗinsa wanda bamu san menene sharaɗin ba. Shi saida ya fara bata mgnin kuma yace sai da sharaɗin in Ummey ta worke ta fara mgn muyi al'ƙawarin aura mishi Shatu. To lokacin mu baƙine bamu san halinsa na ɓoyeba kuma burinmu da fatanmu ta worke mu maidata hannun ƴan uwanta sai muka amince mukayi mishi wannan al'ƙawarin bisa rashin sanin halin daga ranar Mata yake kiran Shatu. Kullum Shatu ita ke zuwa gidansu Ba'ana da safe tana karɓawa Ummey magani a gunsa, dan shi tun tashin sa yake wannan cacube-cacuben nasa, so kullum. Shike bawa Shatu magani ta kawo wa Ummey tana sha har Ummey tadawo tafara magana sai dai bata iya tuna baya ba nan. Ba'ana'n ke ce mana duk randa taga wasu nata ko ƴan uwan ta ko wani abu nata zai yiwu tunanin ta yadawo ta iya tuna baya." Sai kuma ya ɗan tsagaita tare da sauƙe numfashi kana a hankali yaci gaba da cewa. "Toh tun daga ranar ne muka fara neman hanya da dalilin da zai haɗamu daku mutanen masarautar Joɗa. Sabida munsan aikin sihirine dole akwai Magauta sannan a gefen Ba'ana kuwa ya addabemu ya hana Shatu salama duk mai sonta sai yaga bayanshi. To sai marigayi Cuɓaɗo ya bamu tabbacin bulalin Shaɗin masarautar Joɗa ne kawai zai karya duk wani sihirin jikin Ba'ana to kasan cewar yana sonta so na gsky bai cutar da ita in hankalinmu ya tashi kan muna tsoron ya aureta takan ce mana. "Abinda in na gama karatuna zamu koma Yahunde sabida ita bamu sanar mata mun gano asalin Ummey ƴar ina bane gudun ita yarinyace kada tai ta gayawa wasu. To munata son yadda alaƙa zata haɗamu sai kuma ga ƙabilar ɓachama su tasomu gaba. Ran da muka zo nan na forko da muka ga Jamil sosai muka ƙara ƙarfafa guiwar ita ahlin masarautar Joɗa ce dan akwai kamar jini tare dashi da ita. To da akayi faɗa kukaje mana jaje da gayya Arɗo Bani ya gaggayawa mai martaba Lamiɗo mgn dan ya tunzurashi ayi Shaɗi mu jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya kenan. Mun dawo da ita, mu kuma samu mgnin Ba'ana to kuma Alhamdulillah duk abin neman ya samu. Sai kuma yayi ƙasa da kanshi murya na rawa yace. "Sai dai sanadin faɗan ni na rasa kowa nawa". Bappa ya ƙarashe mgnar cikin rauni da zubda hawayen tuno matarsa da zaratan yaranshi. Cikin raunin tuno ahlinshi kuka mai rauni ya rufeshi yayinda Shatuma kuka mai ƙarfi ya kubce mata hakama Ummey sabida ita dai gata ta dawo ahlinta shi kuma garin dawo da ita cikin ƴaƴanta ya rasa nashi yaran. Cikin tsananin jin daɗi Sheykh ya ɗan muskuta cikin tsananin farin ciki da jin daɗin da godewa Allah daya bashi damar kuɓutar dasu ƴaƴan Bappa su Gaini shima zaisa Bappa farin ciki kwatankwacin yadda ya sashi. Cikin sauri da bada umarni ya kalli Jamil tare da cewa. "Jamil tashi maza kaje kazo dasu". "To". Jamil yace kana ya miƙe da sauri yafita batare da ɓata lokaciba sabida ya gano su waye Gaini. Yana zuwa yace. "Yah Gaini taso taso kuzo ga Bappanku da Shatu da Junainah". Ai kafinma ya rufe baki duk sun muƙe cikin tsananin zaƙuwa suka biyo bayanshi. Shi kuwa Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro da Alhaji Umaru rauninsu ya rigada ya dawo tuno irin kisan gillar da ƙabilar ɓachama sukayi musu. Shi kuwa Sheykh dasu Lamiɗo shiru sukayi sabida son yi musu ba zata. Da sauri Jamil yasa hannunshi ya tura ƙofar suka shigo tare da cewa. "Assalamu alaikum Bappa share hawayenka gasu Yah Gaini Seyo da Giɗi". Duk sauran mutanen falon duk suka ɗago kansu. Ido cikin ido Shatu tayi da Yah Giɗi'nta abokin tsamarta. Wani irin yunƙura tayi ta miƙe tsaye tare da cewa. "La'ilahaillaha Muhammadu rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam Alhamdulillah Bappa gasu Yah Gaini". Jin kalaman Shatu ne yasa Bappa dayake sunkuye ya ɗago kanshi yana kalli bakin ƙofar shigowa ya sauƙe kwayar idanunshi kan.....! Kuyi haƙuri da typing errors ina cikin ciwon kai nayi typing ɗin a daddafe. Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300. A yawan posting ne babban cinsu 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa in kin tura sai kiyi screenshort na Debit Alert ki turo min ta whatsApp 09097853276 ƴan 3oo in naki da halin biya ta Account zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ku turo min ta whatsApp ɗin 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Ya sauƙe idanunshi kan Giɗi Seyo Gaini. Cikin wani irin yanayin tarin farin ciki mai sanya rauni. Wasu zafafan hawaye suka kwaranyo mishi. Da sauri ya yunƙura ya juyo ya fuskanci al'ƙibila. Sujjadar godiyar Allah yayi kana ya ɗago yana mai zubda hawaye. Ita kuwa Shatu da sauri ta ƙarasa garesu, kawai sai ta faɗa jikinsu baki ɗayansu, tare da sakin raunataccen kuka. Cikin rauni da yanayin kula Seyo wa mai tausayi kamar uwa yace. "Shatu dena kuka, mu godewa Allah". Sai kuma ta kalli Yah Giɗi cikin sanyi ta ruggume shi tare da cewa. "Tunda na rasaka kusa dani na rasa abokin faɗa da tsama, shiyasa lokuta da dama ina jin daɗin inyi taƙaddama da Gimbiya Saudatu dan sai yana tunamin ta ƙaddamar mu, da Yah Giɗi na abokin faɗana". Cikin zubda hawaye shima Giɗi yayi murmushi tare da janyeta jikinshi kana yace. "Nayi kuka a lokuta ma banbantan da bazan iya ƙididdiga ba sabida tunoki da rayuwarmu". Hannun tasa ta share hawayenta kana ta kalli Yah Gaini wa mai matsayin Uba cikin kulawa da yanayin rayuwarta yace. "Shatu ina Ba'ana ko mun samu nasarar rabuwarki dashi". Da sauri tace. "Yah Gaini Allah ya rabamu da Yah Ba'ana". Cikin tarin jin daɗi yace. "Alhamdulillah". Dai-dai lokacin suka isa gaban Bappa daketa zubda hawaye. Zama sukayi a gabanshi gaba dayansu huɗu. A hankali Giɗi ya sunkuyo ya kwantar da kanshi bisa cinyar Bappa tare da sakin sassayan kuka a hankali yace. "Bappa mun ganka kaida Shatu ina Innarmu ina Ummey ina Junainah ina Yah Lado?". Da sauri Ummey tasa hannunta ta rufe bakinta jin kuka zai kubce mata. Sai dai tuni sautin kukan ya fito. Da sauri Giɗi ya rarrafo gabanta murmushi yayi still Ido na zubda hawaye a hankali yace. "Alhamdulillah Ummey Junainah ina Innarmu da Yah Lado". Cikin kuka Junainah ta faɗa jikinshi tare da cewa. "Arnan Ɓacama sun kashe Innarmu sun kashe Yah Lado sun kashe mutane da yawa na rugarmu". Da sauri Giɗi ya juyo ya kalli Ummey cikin tashin hankali da kubcewar kuka. Gaini da Seyo suma kuka mai rauni suka sake ganin Bappansu yana jinjina musu kai alamun zancen Junainah hakane". Shiru falon sukayi baki ɗayansu sai sutin kukan Giɗi, Shatu, Junainah, Ummey, Seyo, Gaini. Raunin da kukansu ya sauƙar a zuciyar Bappa ne yasa shima sakin kuka dan yau sai sukaji gaba ɗaya rasuwar Yah Lado da Inna ta dawo musu sabuwa. Sosai Shatu keyin kuka tana durƙushe ta tanƙwashe sawunta, hakama Ummey. Gaba ɗaya kab falon saida idon kawa ya ciko da ƙwalla. Cikin Rauni Sheykh ya matso inda Shatu ke durƙushe gaban yayun nata, cikin sanyi ya kalli Bappa Ummey murya a raunace yace. "Tabbas bansan irin ƙunar da kakaji a cikin ranka ba Bappa amman nasan kwatankwacin kamannin ƙunan rashin ɗa, a suman da Afreen tayi naji ciwo da ƙuna a zuciyata tamkar ban taɓa farin cikiba, nasan zafin rashin uwa, amman ban san zafin rashin mataba dan kamin gatan bani Mar'atussaliha ta zame min GARKUWA tana sani farin ciki a duk lokacin da nake cikin baƙin ciki." Shiru yayi sai kuma ga hawaye shar-shar a idanunsa cikin rauni yace. "Na samu komai da nake nema a rayuwata daga gareka ka bani mata ta gari, Allah ya azurtamu da samun ƙaruwar arzin haihuwa sanadinka Ummey na ta dawo. Inama! inama! ace Inna da Lado ɓata sukayi ba rasuwa ba, da tabbas zanyi iyakar iyawata in dawo maka dasu da izinin ubangiji. To amman wannan hurumin ubangijin sammai da ƙassaine. Kayi haƙuri Bappa Allah ne ya baka Inna matsayin mata ya ɗauketa ya sauyama da ƴar uwarta kuma Allah shi ya baka Lado ya ɗauke shi kuma ya killace maka Seyo Gaini Giɗi, wanda wata ƙil da suna Rugar ba'a sacesu ba da an kashesu. Gashi yanzu Allah ya dawo maka dasu. Bappa kace Alhamdulillah ka godewa Allah da ni'imar da yayi maka sai ya ƙara maka wata a kai. Kayi haƙuri ka bar kuka kaga kukanka na ƙara ingiza nasu". Ya ƙare mgnar yana sa hannunshi cikin tafin hannun Shatu yana murza a hankali. Cikin gamsuwa da jin sanyi a ransa Bappa yace. "Alhamdulillah". Da sauri Su Giɗi suma sukace. "Alhamdulillah". Hakama su Lamiɗo kab falon sai suka fara mai-mai-ta hamdala. Ai kuwa cikin ikon Allah duk ƙuna da ƙuncin da zuƙatansu keyi a take Allah ya sauƙaƙa musu shi. Cikin gyaran murya Lamiɗo yace. "Alhamdulillah komai yayi forko zaiyi ƙarshe duk abinda yayi tsananin tabbas zaiyi sauƙi Allah mun gode maka daka ara mana rai da lfy". Ya ƙarashe mgnar yana kallon Sheykh dake kallon agogon hannunshi sabida jin anyi kiran sallan azahar. Cikin tarin jin daɗi Abbansu Sheykh ya matso kusa da Bappa da Abboi murya cike da tarin jin daɗi yace. "Bappa Abboi dama duk al'ummar Rugar Bani da Rugar Arɗo Babayo ngd matuƙa Ubangiji yayi muka sakayya da gidan al'ljanna mafi ƙololuwa girma. Shatu Allah ya dafa miki ya tsareki dake da ahlinka". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Shi kuwa Bappa Sheykh ya kalla tare da cewa. "Muhammad Ngd matuƙa Allah ya saka da al'khairi da kulawarka Alhamdulillah ga mahaifiyarku da ƙanwarku Allah ya bamu aron rai da lfy da ikon dawo muku dasu lfy". Cikin jin daɗi Ummey tace. "Bappa dani dasu ya kamata muyi godiya ba kuba kun gama min komai a duniya musamman Alhaji Abboi da matarsa Dedde sun min karar bani yar su duk da tarin son da sukeyi mata, suka amince muka dawo da ita nan, kana suka bawa Jabeer na aurenta." Sai kuma ta juyo ta kalli Shatu tare da cewa. "Kin min komai kin juya min Jabeer daga bauɗeɗɗen mutun zuwa dai-daice gashi yanzu har fara'a yakeyi ga Jalal na shima ya zama mai fara'a Jamil kuma ya nitsu. Sai dai yanayin Affan nane ke min ciwo a rai, Affan ka dena kuka kajiko Shalelen Mamey". Cikin rauni Affan ya matsota ɗaura kanshi bisa cinyarta yayi tare da sakin kuka. Gaba ɗaya kowa yasan takaicin abinda mahaifiyarsa tayine yake sashi kukan. A hankali Lamiɗo yace. "Kayi shiru Affan ita rayuwa kowa abinda ya shuka zai girba". Daga nan dai kuma akayi gaishe-gaishe. Kana mazan duk suka tafi masallaci. Matan masarautar Joɗa kuwa irinsu Gimbiya Saudatu da Gimbiya Aminatu dasu Mom da Samira duk ko wacce ta koma part ɗin ta cike da al'hinin sharrin ɗan Adam. Matan kuma duk kowa tai al'wala sukayi salla, kana suka sake fitowa falo suka zauna suna cin abinci. Affan kuwa Part ɗin shi ya koma ganin tashin hankali da yake cikine yasa Mami meda hankalinta gareshi. Shi kuwa Rumaisa yayarshi ya kira tana ɗagawa yace. "Uhummm tunda kullum kece kike zuga Hajia Mama kuna cutar waɗanda basu damu da kuba sai ki shirya kizo kiga halin da Mama ke ciki na girbar aiyukanta data shuka". Cikin tashin hankali Rumaisa tace. "Affan m.." Bai bari ta ida zancenta ba ya katse kiran. Su Sheykh kuwa dasu Haroon falon Sheykh Suka wuce. Bayan anyi sallan la'asar ne, Dedde ta kalli Ummey cikin kula tace. "Toh Ummeyn Shatu mu zamu koma Rugar Bani, sai jibi zamu koma Cameroon da izinin ubangiji Allah ya kiyaye gaba ya tsaremu". Cikin sauri Umaymah tace. "Yanzu-yanzu zaku tafine?". Cikin nitsuwa Dedde tace. "Eh ai su tuni ma sun shiga mota nida su Khadijah suke jira". Da sauri Umaymah tace. "Ayyah ni kuwa ina son ku gaisa da Sittinmu da Jadda kafin ku tafi". Da sauri Mamma tace. "Ai sun iso suna Part ɗin Lamiɗo. Amman yanzu zasu iso". Da sauri Shatu tace. "Toh Dedde am ki ɗan jira ku gaisa mana". Suna cikin mgnar Sitti da Jadda suka shigo. Allah sarki iyaye sai gashi Ummey a tsakiyarsu suna kuka gaba ɗayansu an rasa mai rarrashin wani. A hankali Sheykh da Haroon suka shigo falon cikin tsiya Sheykh yace. "Toh Alhamdulillah Jadda ni dai burina ya cika ko yau in kana son tafi ka gaida na gaba tunda kaga Mamey na ta dawo ta sameku cikar farin cikinta kusa mata al'barka". Dariya sukayi baki ɗayansu kana su Dedde suka matso aka gaggaisa. Sannan Jadda ya fita ya koma wurin su Lamiɗo. Cikin sanyi Shatu ta kalli Deddenta Aunty Amina Hafsi Khadijah waɗanda duk suke cikin shirin tafiya. A hankali tace. "Allah sarki da mu ƙara kwana mana, yanzu kuma in kun tafi shikenan sai yaushe ni na zama a nan ina gefe duk ƴan uwa suna Cameroon". Da sauri Ummi tace. "Kema kina tare da yan uwanki ga Ummeynki ta dawo kusa dake ga kuma Junainah gani ga Hibba". Da sauri suka kalli Jamil da ke cewa. "Kuma zan auro mana Khadijah ma ta dawo nan zaku bani ita ai ko Dedde". Ya ƙare mgnar cikin yanayinsa na wasa da dariya da kowa. Murmushi Dedde tayi tare da cewa. "Ai an baka ma Jamilu". Dariya mai sauti yayi tare da cewa. "Alhamdulillah". Junainah kuwa a hankali ta matso kusa da Ya Giɗi tare da cewa. "Ummey ni dai zan tafi tare dasu Yah Giɗi ban gaji da ganinsu ba". Cikin jin kewar juna Ummey tace. "Kije Junainah nima in Sitti na da Jadda sun tafi zamuzo tasu Mamma". Da sauri tace to. Kana ta kalli Shatu da tai shiru tana kallonta tare da cewa. "Kada ki damu Addana nima zanke zuwa masarautar Joɗa". Da sauri Jalal yace. "Zaki dawo dai Junnu gamu ga Abbanmu ga Adda Shatunki ga Ummey". Da sauri ta kalli Sheykh tare da cewa. "Toh Yan Junaidun fa". Dariya mai sauti Sheykh ya ɗan yi tare da cewa. "Shima zai dawo nan". Nan dai suka fito gaba dayansu dan yiwa su Dedde rakiya. Jadda kuwa harda kuka yayi yana yiwa su Abboi da Bappa godiya. A hankali Salmanu wanda yazo wurin ɗan Hafsi ne ya ɗan matso kusa da Ummey ƙasa yayi da murya tare da cewa. "Ummey ki roƙa min su Abboi a bar mana Hafsi mana". Dariya Ummey tayi tare da cewa. "Alhamdulillah kuce duk ma zamu kwasosu mu dawo nan dasu". Da sauri Salmanu ya shiga mota. Shi kuwa Yah Al'ameen gefen Shatu ya ɗan kalla tare da yafitota. Bayan Sheykh suna ɗan ratsa a hankali yace. "Wannan ƙawar taki Rafi'a fa, da batunta yasa su Abboi zuwa gobe zasuje su zanta da manyanta sai jibi zamu koma". Cike da mamaki tace. "Lahh Yah Al'ameen ashe mgnar taku har ta kankama". Da sauri yace. "Ke da Allah ni kada kimin shele". Baki ta ɗan tura tare da cewa. "Toh sai na gaya ma kowa yaji". Da sauri ya biyota ita kuwa cikin dariya tace. "Ummey ashe Yah Al'ameen da Rafi'a munahikai ne soyayyar sirri sukeyi". Dariya Sheykh yayi tare da juya mata ido alamun ai kema soyayyar sirri kikayi. Haka dai suka shiga motocin suka tafi cikin farin ciki da kewar juna. Cike da farin ciki suka koma cikin falon. Da sauri Umaymah ta amshi wayarta da Ishma ke miƙa mata. Amsa kiran tai da sauri ganin Abbansu Sheykh ne. "Assalamu alaikum Abban Jazlaan". Da sauri Abba dake part ɗin shi ya ɗan gyara zamanshi tare da cewa. "Toh wai Umaymah ni sai yaushe zan samu in gaisa da Yayar takune kun taru kun riƙe min ita da hira". Dariya mai sauti Umaymah tayi tare da cewa. "A a sai mun koma mana". Da sauri yace. "A a dan Allah kada muyi haka dake, kinga yara na cike nan ki kirata gefe kice mata ina kiranta". Murmushi tai tare da cewa. "Nawa zaka biya". Dariyar jin daɗi yayi tare da cewa. "Kujerar hajji tayi miki". Da sauri tace. "Sosai ma kuwa yanzu kuwa zan cika aiki". Tana gama wayar ta yafito Mamey suka tafi ɗakin Ummi ta gaya mata. Cikin jin kunya Mamey tace. "A'a kinga dama ke tsiyarki yawane da ita Khadijah ya da girmana kuma ana cike yarana da jikoki ku wani kawo min batun inje gareshi". Dariya Umaymah tayi tare da cewa. "Toh shike nan ni dai yar aikece. Cikin yanayin tarin shaƙuwarsu ta ya da ƙanwa Mamey tace. "To ai dai ya bari sai dare ko". Da sauri Umaymah tace. "Ohoh anaso ana kaiwa kasuwa". Hararan wasa tayi mata kana ta fito. Nanfa sukaci gaba da hira. Ana gab da kiran sallan magriba. Suka juyo ehu da kururuwar Hajia Mama da faɗe-faɗen da takeyi. Da sauri Sheykh ya nufi ɗakin daya rufeta, yana buɗeta. Ta fito tanata yayyarfa hannunta tare da cewa. "Wayyoooooooo zan zama tsuntsuwar Boleru". Da sauri yabi bayanta tuni ta iso falo. Tana kaɗan yatsun hannunta da sun fara komawa na tsuntsuwar Boleru. Cikin tsoro da mamaki da tausayi Mamey tace. "Innalillahi Jabeer kamanninta fa na sauyawa". Da sauri ya iso, yana mai kara wayarshi a kunne sabida kiran da yayiwa Affan. Yana ɗagawa yace. "Affan kazo kayi maza kazo". Cikin tashin hankali da tsoro Affan yace. "Toh". Yana fitowa yayi kiciɓis da Rumaisa a tare suka nufi. Part ɗin Sheykhhhh. Umaymah kuwa Abba da Lamiɗo ta kira ta gayawa. Kusan duk a tare suka iso. A tsakiyar falon suka sameta. Tana yayyarfa hannunta tare da cewa. "Na ji daɗi zan zama tsuntsuwar Boleru zanyi ta firewa kamar jirgi". Sai kuma ta kalli Sheykh da yake ta karanto Ayatul shifa yana tofa mata. Dariya tayi tare da cewa. "Kai bar ɓata lokacin ka a kaina ai al'haƙine kuikuyo ya dawo kaina wayyo ni Halima naga ta kaina". Da sauri Rumaisa ta iso gareta ihu tasa tare da kururuwar ganin yadda kafafunta duk suka zama cingil-cingil kamar na tsuntsuwar ladin kogii. Da sauri Rumaisa tace. "Dan Allah Affan mu kaita gidan bokan ya karya sihirin". Cikin tarin takaici da zubda hawaye Affan yace. "Banza mahaukaciya gafalelliya ni nan Affan babu gidan wani mushirkin mugun kafurin bokan da zanje. Anayi mata addu'o'in kina batun aje gidan boka". Cikin ihu tace. "Abba dan Allah mu kaita". Da sauri Abba yace. "In kika sake kirana kika haɗani da Allah dan inje inda zan tsaɓa mishi zan tsine miki shasha mara hankali". Sheykh ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace. "Aunty Rumaisa ki bari ki nitsu muyi mata addu'a in sha Allah zata samu lfy". Da sauri tace. "An ƙi ɗin sabida ba uwarka bace ai shiyasa zakace haka". Sai kuma ta zaro wayarta ta kira bokan bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga cikin kurma ihu da kururuwa yace. "Nima ƙonewa nakeyi, ita kuma a haka zataci gaba da rayuwa ita ba mutumba ita ba tsuntsuwar Boleru ba, zata zama aya ta yadda duk wanda ya ganta sai ya tambayi mai tayi. Domin dama shi mugunta ɗan aikene yakan iya dawowa wurin wanda ya aikeshi. Sai kuma ya kurma ihu da ƙarfi. A nan ya faɗi yana burburwa. Ya shiga gudu yana kwaɓe kayansa yana cewa wuta na ƙonashi ya zama mahaukaci tubran. Ita kuwa Rumaisa kamo Hannun Hajia Mama tayi suka tafi Part ɗin ta. Lamiɗo kuwa kai ya jinnina tare da cewa. "Ƙarshen mugu kena". Sheykh kuwa da Mamey da sauri suka zauna gefen Affan dayake kuka kamar ya haɗiyi zuciya cikin sanyi Sheykh yace. "Affan kayi haƙuri ka bar kuka in Sha Allah zamu dage da addu'a zata samu lfy". Cikin shassheƙan kuka. Ya tashi yabi bayansu. Sabida ita dai uwa duk yadda take uwace. Abba kam juyawa yayi ya fita ko a jikinsa. Domin shi tausayin Affan ne kawai ke cinsa a rai. Lamiɗo da Gimbiya Aminatu da Galadima ma kwaffa kawai sukayi suka fita. Umaymah kuwa cikin zafin zuciya tace. "Wlh Ni dai ko duk zaku yafe mata ni ba yafewa zanyi ba". Da sauri Sheykh ya kalleta idonshi cike da hawaye. Sai kuma ya kalli Mamma da Aunty Rahma dasu Yah Jafar da suma suke cewa basu yafe mata ba. Jin an kira sallan magriba ne yasa duk suka miƙe suka tafi masallaci. Ana idar da sallan Isha'i Sheykh ya nufi Part ɗin Hajia Mama kuka sosai ya sameta tanayi Affan na gefenta shima kukan yakeyi Addu'o'in ya rinƙa tofa mata. Har saida yaga tayi bacci kana ya fita. har yaje bakin ƙofar fita sai kuma ya juyo jin Affan ya ruggumeshi ta baya yana kuka tare da cewa. "Ngd matuƙa Hamma Jabeer Allah ya bar zumunci da ƙauna". Cikin rauni yace. "Amin Amin Affan". Daga nan suka fita kowa yayi Part ɗinsa. Hira sosai sukayi ranar hirar yaushe gamo kusan sai gab da kiran sallan forko kana duk suka tashi sukayo al'wala sukayi ta nafila suna godewa Allah. Washe gari da safe gaba ɗayansu suna falon Abba ya shigo. Suna gaisawa yana kallon Umaymah dake mishi dariya ƙasa-ƙasa. Hajia Mama kuwa da taimakon addu'o'in da Sheykh yake mata hankalinta ya ɗan dai-dai-ta yadda zata fi jin ciwo da zafin sauyawar halittarta, da gaba ɗaya yanzu kafafunta sun zama na tsuntsuwar ladin kogi, yatsun hannunta kuma sun zama fiffizgewa tsuntsuwar Boleru, idanunta kuwa kamar na tsuntsuwar Duji sunyi ƙuru-ƙuru tamkar an taka kwaɗo. Wannan al'amarin yasa Lugga da saƙo mutanen masarartar Joɗa shigowa sunayi mata kallon sabuwar halitta masu dariya nayi. Tsananin tsoron Allah ya wadaci zuƙatan mata da mazan Masarautar. Bayan Aunty Juwairiyya ta dawone take suffantawa su Mamma yadda Allah ya maida Hajia Mama. Sosai jikinsu yayi tsanyi. Umaymah ce ta ɗan kalli Shatu da yanzu ta fito wonka cikin shirin baccinta. "Naji kamar Jazlaan ke kiranki". Umaymah ta faɗa cikin kulawa. Da sauri tace to kana ta miƙe ta funi Side ɗinsa. A falo ta sameshi gaban steps ɗin hawa wurin Dinning area. Hannunshi na cikin zirin zirin igiyoyi dake sarƙafe da duwatsu masu daraja sheƙin Daimond. Wanda a ciki yake liƙe da CCTV camera ta sama wanda da wuya mutun ya iya ganeshi. Ruggume shi tayi ta baya tare da cewa. "I miss you so much Sheykh Malam akarmakallu Dr Hamma Jabeer". Murmushi mai cike da jin daɗi yayi kana ya juyo ya ruggumeta. A hankali tasa tafin sawunta saman rumfar sawunshi kana tasa hannun ta saƙalo wuyanshi. Ya zama tana lafe a jikinsa. A hankali ya fara taku a haka ya nufi Bedroom. Suna shiga ya maida ƙofar ya rufe. Da cikin tsokana tace. "Yah Sheykh Haroon". Baki ya ɗan taɓe tare da cewa. "Wannan jarabebben tun yaushe yaja Ƴar mutane suka shiga ɗakin nan suka rufe ko kunya babu". Murmushi tayi tare da cewa. "Mutun da matarsa". A hankali ya sunkuyo kan gadon ya kwantar da ita tare da yi mata rumfa da ƙirjinshi kana yace. "Okay to ai nima gani da matata". Da sauri tace. "Yah Sheykh jego nakeyi, kwana Afreen goma kacal fa". Hancinsa ya manna da wuyarta tare da cewa. "Eh mu samo mata ƙanwa ko ƙani mu samu irin tagwayen Nana Faɗima". Da sauri tace. "Uhum wuya". Kissing lips ɗin ta yayi tare da cewa. "Ke ai yar baiwa ce nine zanke mana laulayi da naƙuda". Murmushi tayi tare dasa tafin hannunta ta tallabe kanshi a hankali tace. "Harda naƙudar ma Yah Sheykh". Da sauri yace. "Sosai ma kuwa ai na Afreen ɗinma ni nayi naƙudar ke ba kallonki kikeyi hankali konceba..". Dariya mai sauti tayi sabida lbarta mata yadda yaji a lokacin da karayar da yayi ya ƙara da cewa. "Mata kuna jin azabar duniya akan hayhuwa bamu da abinda zamuyi muku kuji sanyi sai kyautata muku da nuna muku soyayya in kuna matsayin matanmu iyaye kuwa ayi musu biyayya da tausayawa da kulawa shine kaɗai tukuicin wahalarsu dan bazamu taɓa iya biyansu ba inaji kamar ko wuta Mamey tace in shiga zan shiga dan biyayya sabida azabar da naji wanda nasa irinshi koma fiye da haka taji. In matsayin yarane kuma mu jiƙansu mu sosu mu kula da amanarsu da Allah ya bamu". Cikin sauƙe numfashi tace. "Yauwa niko Yah Sheykh inada tambaya". Rigarta ya fara turawa sama yana shafa cikinta tare da cewa. "Allah yasa na sani Boɗɗona". Juyowa tayi ta ɗan kalleshi tare da yin murmushi kana tace. "In sha Allah ma ka sani". Murmushi yayi tare dasa yatsarshi cikin hudar jibiyarta tare da cewa. "Uhum ina jinki". Kai ta gyaɗa kana tace. "Yauwa Dr dama ina son kayi min ƙarin bayani ne kan batun laulayi cikin Afreen da kai tayi." Murmushi yayi tare da cewa. "To ina jinki tambayi in baki amsa in na sani". Muskutawa tayi ta fuskanceshi da kyau tare da cewa. "Bayanin sanadin faruwar haka. Nake son sani. Don yana da kyeu mugane dalilin hakan. Shin yawan shaƙuwace da soyayya tsakanin ma'aurata kawai ke sa hakan ya faru. Ko kuma wani biology ne na Ubangiji?. Yake sa miji yayiwa matarsa laulayin ciki a wasu lokuta?". Murmushi mai cike da shauƙi yayi tare da cewa. "Eh wato kina son kiji ba'asin miki laulayi ko irin kin huta ɗin nan". Kai ta gyaɗa mishi tare da cewa. "Eh mana kaga in zakayi ta mana laulayi da naƙuda to ko duk shekara zan haihu ba matsala." Lakace hancinta yayi tare da cewa. "Uhum". Kiss ta manna mishi a goshinsa tare da cewa. "Dan Allah gaya min". Zamanshi ya gyara kana yace. "Toh Aish ba yawan shuƙuwa ko soyayya ba ne ke sa miji yayiwa matarsa laulayi. Asali ma ai dangantakar ba tsakanin matar da mijin ba ne. Dangantakar tsakanin ɗan ne da ubansa." Sai kuma ya ɗan ƙara jawota jikinshi tare da cewa. "Samuwar ɗan, ana nufin kamar yadda ya shafi uwar kai tsaye, to haka kuma ya shafi uban. Don haka, irin yanayin da ta ji saboda zuwan yaron, shi ma yakan iya jin hakan. Sai dai kawai nasa bazai kai yawan na uwar ba, saboda ta fi shi kusance da ɗan, kasancewar yana jikinta kin gane ko?." Cikin gamsuwa ta gyaɗa kai tare da cewa. "Na gane na gamsu. To kuma batun naƙuda fa da kace kayi min. Shin dama na miji kan ji ciwon naƙudan matarsa kamar yadda wasu mazan ke jin ciwon laulayi ciki ne? Ko dai kwatakwata babu wannan!?". Kanshi ya ɗan cusa tsakanin wuyanta da kafaɗarta tare da shaƙar ƙamshin jikinta cikin fahimtarwa yace. "A dai iyakar abinda muka sani zuwa yanzu, wanda kuma bincike da gwaje-gwace likitocin duniya suka tabbatar shi ne, namiji ba ya iya jin ciwon naƙuda. Sai dai yakan jin tsananin damuwa da ciwon rai ne, maimakon ciwon jiki da raɗaɗi da mai naƙudar take ji. Sai dai bincike ya tabbbatar da cewa yana da tasiri sosai wurin sauƙaƙa wa matar ciwon naƙudar, idan zai kasance tare da ita har ta haihu". Da sauri tace. "Kamar yaya to dan yana kusa da ita zataji ciwon ya sauƙaƙa?". Kai ya ɗan ɗago ya kalleta tare da cewa. "Domin idan ya zauna a gunta, musamman in zai riƙe mata hannunta ko ya riƙa ɗan shafa goshinta yana yi mata sannu kamar dai yadda nai miki ta miki lokacin kina naƙudar gab da haihuwar. To tabbas zataji sauƙi da sassaucin naƙudar da samun haihuwa a sauƙaƙe da izinin ubangiji. Saboda yayin da suka kasance a haka, jikin matar yana samar da wani sinadari da ake cewa oxytocin , wanda yake sanadin tsattsafowar wannan ruwa mai tsantsi to zai sauƙaƙa fitar yaron daga jikinta. Da iznin Allah". Cikin gamsuwa ta sauƙe numfashi tare da cewa. "To kai kuma kace harda ciwon baya kaji ranar da zan haihu a lokacin ma meya kawo hakan?". Cikin sanyi ya jujjuya kanshi tare da cewa. "Allahu ahlamu, kawai abinda nasa a raina wannan wani ikone da ƙudurar ubangiji daya gwada a kanmu wanda tabbas na taɓa riskar makamancin lbrin miji yayiwa matarsa naƙuda, to amman dai a likitance bamu ganoba tukun, dan haka wannan fagene na ubangijin sammai bakwai da ƙassai bakwai, shiyasa nasan zafi da ciwon da mata kanji yayin haihuwa". Cikin gamsuwa tace. "Ayyah sannu Yah Sheykh". Murmushi yayi tare da cewa. "Ke kam ba cewa kikayi in dan zanci gaba dayi miki laulayin ciki da naƙuda ba, ko duk shekarama ki haihu ba matsala ko". Murmushi tayi tare da cewa. "Eh mana". Murmushi yayi tare da jawota jikinshi yana mai sa hannunshi ɗaya zai zare boxes ɗinsa. Fahimtar inda ya dosane yasa ta miƙe da sauri tare da cewa. "Bari inje wurin Ummey na naji alamun Afreen ta farka". Fuskarshi ya kwaɓe tare da cewa. "Kai Aish ni dai banjiba". Cikin son zille mishi tace. "Kaji can muryarta tana kuka". Komawa yayi ya kwanta Cikin jinjina ƙudurar ubangiji yace. "Toh ɗaukota kuzo". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh". Kana ta fita. Tana fita ya maida kanshi bisa pillow'nshi yana tasbihi da girman zatin Allah daya samar da cikekkiyar dangantaka tsakanin uwa da ɗanta ta yadda ko bata tare dashi in zaiyi kuka ko ya tashi bacci. Mamanta zai sanar mata. Ita kuwa Shatu tana zuwa ta wuce bedroom ɗin Ummi. Umaymah da Ummin kawai ta samu sunata hira da dariyar Abba daya shigo da kansa ya kira Mamey wai tazo su gaisa da abokanshi, daga nan yayi Part ɗin shi da ita wanda yake kusa da nata. Umaymah na kwance Afreen na gabanta Ummi kuwa zaune. A hankali ta zauna gefensu tare da cewa. "Umaymah Ina su Ummey". Kai Umaymah ta juya tana danne dariyarta tace. "Sun tafi Side ɗin ta". Da sauri tace. "Harda Mamma". Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa. "Bakiga tun da yamma Mamma da Rahma sukaje suka gyara komai na Part ɗinta ɗinba. Sabida Abban yasa an kawo mata sabbin kayan ɗaki sannan anyi duk abinda ya kamata". Jinjina kai tayi tare da cewa. "Ayyah". Sai kuma tace. "Bari inje in kwanta". Sai da safe tayi musu. Ta fita ta tafi. Ishma da Hibba ta samu kwance bisa gadonta tuni sunyi bacci da alamun Hibba wayama takeyi tayi baccin. Gefenta ta kwanta. Su kuwa su Umaymah sukaci gaba da hira. Sai kusan ƙarfe biyu ne da Afreen ta tashi Umaymah ta kaita ta bata mama tasha kana ta dawo da ita wai karta hana uwarta bacci. Alhamdulillah fa komai na tafiya yadda ya kamata rayuwa ta miƙa. Gsky tayi halinta. Jadda da Sitti da Babansu Aunty Juwairiyya sun koma. Haroon ma da Jannart sun da Hibba sun koma. Saura Umaymah da Mamma Aunty Rahma. Tuni Mamey ta koma Part ɗin ta. Hajia Mama kuwa ta tabbata mai suffa hudu kafar ladin kogi, hannun fiffigen tsuntsuwar Boleru idanu na Duji, sauran jiki na mutun. Ta zama abar kallo Abba kuwa ya danƙara mata saki. Affan kuwa yana nan lfy da ƴan uwanshi. Yanzu Shatu ta kusa wata ɗaya. Wanda ya kama satin su Umaymah uku da zuwa kenan. Abboi kuwa dasu Bappa sunje ga iyayen Rafi'a sun nemi aureta ga Al'ameen an basu kuma. Kana su Bappa kuwa sun nemawa Salmanu auren Hasfi an kuma basu. Zaune suke Umaymah Mamey Lamiɗo Galadima Abba A hankali Lamiɗo ya gyara zamanshi tare da cewa. "Toh Alhamdulillah komai ya wuce ya zama tarihi. Manufar taruwarmu anan a kan Masarautar Joɗa ne. Na gama zama da duk manyan fada mun gama tsaida zance duk kowa ya gamsu da batun Jabeer ya mulkin Masarautar Joɗa. Toh amman inda gizo ke saƙan kun san ɗan naku, na kira sarki Jalaluddin akan batun to shi mgn ɗaya yayi cewa yasan Jabeer mai biyayya ne ga Khadijah da take ƙanwar mahaifiyarshi ma bare ke Aisha da Habibullah da kuke iyayensa yace ya sani tabbas in kuka cewa Sheykh ya mulki masarautar Joɗa ku bashi umarnine ba shawaraba tabbas zai yarda". Cikin gamsuwa Galadima yace. "Haƙƙun wannan haka yake tabbas zai yarda bisa dole bisa umarnin iyayenshi". Cikin sanyi Mamey tace. "In kuna son in bashi umarni zan bashi kuma nasan zai min biyayya to amman meyasa baza'a bawa wani cikin ƙannen mahaifinshi ba sai shi". Shiru sukayi baki ɗayansu jin Lamiɗo na cewa. "Sabida ina son masararutar Joɗa ta tsarkaka ta rabu da duk wata al'ada daba addiniba. Na sani babu mai iya sarrafa Masarautar Joɗa ya juyata daga bahahuwa zuwa ba damiya ya kauda al'adar bidi'a ya wanzar da sunna sai shi. Zai gyara masararutar ta yadda za'a dena zalama da son cutar da juna bisa kujerar zai sauyata ta yadda sai mai cikekken ilimin addini ne zai iya mulkarta." Cikin gamsuwa Mamey tace. "In sha Allah zaku sameni mai biyayya bisa umarnin ku na in bashi umarni kuma na sani zai min biyayya". Cikin jin daɗi sukace to. "Allah ya shige mana gaba". Amin Amin sukace. Sai kuma suka nitsu jin Lamiɗo na cewa. "Alhamdulillah yanzu Ita matarshi ta kusa gama wonka tana gamawa zukjne Rugar Bani suyi kwana ɗaya daga nan su dawo su shirya suje Ƙasar Cameroon wurin iyayen Shatu kuma zasuje da Aliyu (Dr Aliyu) kenan da Basiru da Galadima domin su nemawa Jamilu auren Khadijah ƙanwar Shatu". Cikin jin daɗi Mamey tace. "Alhamdulillah to Allah ya kaimu". Amin Amin sukace. Sai kuma Abba yace. "Jalal kuwa mun gama mgna da Abban Haroon kan batun Jalal da Hibba". Cikin tsananin jin daɗi sukace. "Alhamdulillah daga nan suka watse taron. Washe gari su Umaymah suka koma. Alhamdulillah yau Shatu ta gama arba'in. Sosai Afreen tayi kuɓul-kuɓul da ita gwanin burgewa ta cika tayi kyau in ka ganta kamar yar wata biyu. Sosai kuwa Shatu tasha gyara na musamman daga wurin Ummi da Mameynta. A can ƙasar Cameroon kuwa. Ba'ana ya gama shirin dawowarsa kab. Wanda da azatonsa zai kaishi watanni uku sai gashi cikin wata biyu ya gama shirinsa. Kana ya kamo hanya. Yau Alhamis da misalin ƙarfe tara na dare yayiwa Rugar Bani diran miki...! Ban samu nayi editing ba By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Dirar mikiya tare da tawagar shi wanda Baroon na ciki. A bakin titi motar ta sauƙesu kana suka ƙaraso cikin Rugar tasu da ƙafa. Dai-dai bakin mashigar Rugar Bani ɗin suka tsaya, sabida ganin uban gayan tafiyar ya tsaya. A hankali ya lumshe idonshi, tare da shaƙan sassayan iskan garin dake kaɗawa yana ratsa jiki. Hannunshi ya buɗe ya waresu, ya tanƙwashe kansa bisa wuyanshi cikin muryar dake nuni da gskyar abin dake binne can ƙasan zuciyarsa yace. "Uhummmmmmm ko wani ɗan adam yanada yanki na musamman da yake cikin bugun zuciyarsa. Ni kuwa Rugar Bani ce bugun zuciya ta. RUGAR BANI itace mahaɗin soyayya da Mata. Allah ka sani kaine ma sannin sirrin zuciyata ina son Shatu son da ni kaina ban san adadinshi ba. Son da bana yiwa kaina shi. Mata itace cikon farin cikina ban taɓa son wani abu a duniya sama da Shatu ba ya Allah ka yafe min kura-kuraina na baya, ka bani ikon samun Shatu, ka tsare min imanina duk da nasan. Ban fiye aikata aiyukan gsky ba a rayuwata. Amman son Shatu gsky ne a cikin zuciyata kuma tuban da nayi gsky ne. Ya Allah ka jiƙaina ka tausaya min ka cika min burina ka ƙaddara Mata ta tabbata matar aure na, in rayu da ita inuwa ɗaya. Domin itace sanyin idaniyata in ka samar min ita rayuwata zata inƙanta." Ya ƙarashe mgnar cikin rauni da rawan muryar kana wasu irin tafasassun hawaye suna masu kwarya mishi. Sheykh kuwa dake jin duk abinda Ba'ana yake faɗa bisa kiran da Baroon yayi mishi. Da ƙarfi ya rumtse idanunshi, yana mai jin wani irin azabebben kishi mai masifar zafi da ƙuna yana caccakar zuciyarsa. So yake ya tashi yaje suyi hira da Mamey'nshi Amman gaba ɗaya yanayi shi ya hautsine kishi ajalin maza. Domin in mu mata kumallonmu ne tofa su maza yakan iya karsu. A can Rugar Bani kuwa, cikin rauni Ba'ana yaci gaba da magana cikin sanyin jiki da raunin da bai taɓa riskar shi ba yace. "Na sani na yarda akan komai ni bazan amsa sunan mai gsky ba ko mai tausayi amman akan tubana da Shatu ni mai gsky ne! Ya Allah ka mallaka min Shatu na yarda na gane babu wani sihiri ko tsafi ko boka ko dodon tsafin da zai mallaka min ita sai kai sarkin da bashi da tamka sarki buwayi gagara misali sarkin kowa na Annabi baban zara". Kawai sai ga hawaye shar-shar suna kwaranya daga idanunsa rusunawa yayi ya durƙusa bisa guiwowinsa ya kafa kanshi cikin sassayan yashin garin. Ya saki wani irin raunataccen kuka. Gaba ɗaya yaran nashi shiru sukayi cikin tarin mamaki da tsantsar gaskata soyayya ba ƙarya bace shirya kuma ta Allah ce dan tuni sun san yabar komai na tsafi saidai wasu abubuwan dake jikinsa basu karyeba kamar ɓacewa har yanzu yana iya ɓacewa. Saida yayi kuka mai tarin yawa kana suka miƙe suka nufi cikin gari. A tsakiyar wurin garken al'ummar Rugar Bani ɗin ya tsaya ya juya gabas da yamma kudu da arewa. Kana a hankali yace. "Duk da son hanaku ci gaba da nakeyi, ya rigada Allah ya lamunce muku kuna ci gaba da izininsa." Kai tsaye garken Bappa ya nufa bayan duk ya sallamesu sai Baroon kawai. A hankali yasa ƙafarshi ya ratsa tsakiyar garken cikin ɗan ɗaga murya yace. "Bappa". Cikin wani irin masifeffen tashin hankali da firgici Bappa ya miƙa tsaye. Tare da cewa. "Na'am Ba'ana". Giɗi da Seyo ne dake gefenshi suma suka miƙe da sauri cike da tsoron me zai faru. A hankali ya zame ya zauna gaban Bappa kana a hankali yace. "A nan a tsakiyar garken nan na rayu da ita tsawon shekaru goma sha biyu, na rayu da sonta kan gsky. Koda komai ƙaryane Bappa ka yarda ina son Shatu son da bana yiwa kaina". Cikin sauƙe ajiyan zuciya Bappa ya zauna jiki a mace hakama su Gidi da Baroon. Cikin nitsuwa yace. "Ba'ana yaushe ka dawo?". Murya na rawa yace. "Bappa yanzu na shigo Rugar Bani ko gidanmu ban jeba, ina so ka yarda cewa da gaske ina son Shatu". Yadda yayi mgnar yasa Bappa jin wani irin rauni da tausayinsa a hankali yace. "Na yarda Ba'ana na sani kana son Shatu". Da sauri yace. "Bappa ka tuna kun min al'ƙawarin aura min ita". Da sauri Bappa yace. "Na tuna Ba'ana ban manceba to amman al'ƙawarin Allah ya ture namu ya rigada Allah ya tsara Shatu ba matarka bace." Cikin sauri ya miƙe yana cewa. "A'a a'a bana son jin haka". Yana faɗin haka yana yarfa hannun a haka ya nufi cikin gari Baroon na biye dashi a baya. Shiru Bappa da su Giɗi sukayi cikin tarin rauni. Shi kuwa Ba'ana a tsakiyar gidansu ya zauna gaban Bukar da Bugulu mahaifiyarshi. Cike da mamaki suke kallonsa jin yadda yake kuka babu sassauci. Cikin tsananin tausayi da so irin na iyaye da yaransu. Sukayi kanshi cikin kula Bugulu tace. "Ba'ana yau ranar farin cikine a garemu ba ranar kuka ba. Kada kayi kuka muna cikin farin cikin ganin juna". Ba mgn sai kuka. Da sauri Bukar ya jawoshi jikinshi tare da cewa. "Gaya min me ya saka kuka haka?". Cike da rauni yace. "Karo na forko dai a rayuwata Baba zan roƙeku in kuna da hali ku aura min Shatu ku dawo da ita gareni". Ganin tsananin tashin hankali da yake cikine yasa sukace. "To kwantar da hankalinka ina shine kawai burinka zamu dawo maka da farin cikin ka". Da sauri yace. "Allah Baba?". Kai ya gyaɗa mishi cikin tausayinsa. Shi kuwa jin hakane ya zame ya kwanta ya ɗaura kansa bisa cinyar babanshi yana sauƙe numfashin kuka shima Baroon gefe ya zauna. Sheykh kuwa cikin tsananin tashin hankali na kishi ya rumtse idanunshi da ƙarfi. Kana ya taune lip ɗinsa na ƙasa. Shatu ce zaune ita da Mamey har cikin ɗakinta Afreen na hannun Ummi. A hankali Mamey tace. "Shatu". Da sauri ta ɗago kanta ta kalli Mamey tare da cewa. "Na'am Mamey na". Gyara zama tayi tare da cewa. "Shatu batun mijinki ne, nake son kisa baki a lamuransa". A hankali tace. "Mamey waɗannen lamuran ne?". "Shin kina son Mijinki ya mulki masarautar Joɗa?". Ta jefa mata tambayar kai tsaye. Da sauri Shatu ta zubawa Ummey nata ido ta karanci yanayinta na ƴan wasu daƙiƙu kana a hankali tace. "Mamey in dai kuna so ya mulka to nima zanso, hakan sai dai ina tsoro kada a sabautamu". Da sauri Abba dake shigowa yace. "A'a Shatu in sha Allah babu komai babu abinda zai faru sai al'khairi. Burinmu ya mulki masarautar Joɗa ne dan ya gyara ta zama Tsarkakkiyar masarauta mai wadatar sunna da ƙarancin al'adun bidi'a". A hankali ta gyaɗa kanta tare da cewa. "Shi kenan Abba Allah ya sanya al'khairi yasa hakan ya zama ci gaba ga Musulunci da musulmai". Amin Amin sukace. Kana ta ɗan yunƙura zata tashi. Ganin Abba ya shigo yana amsar Afreen tare da cewa. "Ƴar lukuta". Murmushi tayi kana ta kalli Mamey dake cewa. "Ki fara nuna mishi amfanin ya mulki masarautar bisa hikima ta yadda zaki sa mishi abin a ransa ba tare da yaji dole akayi mishi ba". Da sauri tace. "Toh Ummeyna". Har ta isa bakin ƙofar kuma sai ta tsaya jin Mameyn na cewa. "Umurnine fa Shatu ki fara daga yau". Ajiyan zuciya mai sauƙi ta sauƙe tare da cewa. "In sha Allah kuwa Mamey". Tana fita Ummi na biye da ita a baya. A bakin ƙofar shigowa suka haɗu da Sheykh shida Affan. Wuce sukayi kana su kuma suka fita. Kai tsaye har bedroom ɗin suka wuce. Suna hira ta tsakanin iyaye da yaransu. Da sauri Sheykh ya ɗan ɗago ya kalli Mameynshi tare da sakin murmushi jin tana cewa. "Jabeer wannan gemun haka ka ɗan rageshi mana ga saje ga gemu". A hankali yace. "Mamey bai min kyau bane?". Da sauri tace. "A'a wlh yayi maka kyau sosai ma fiye da zaton mai zato sai dai yasa kayi kwarjini da yawa ni kaina sai inji kana min kwarjini". Dariya mai sauti yayi tare da cewa. "Uwa mai daɗi Allah ya bar mana ke Mameynmu". Dariya Abba da Affan sukayi tare zubawa Sheykh ɗin ido jin yana cewa. "Toh gemu da saje ku kiyayi kanku da sa Mameyn Jabeer ganin kwarjini mai yawa". Jamil da Jalal da Yah Jafar Imran dake shigowa ne suka haɗa baki wurin cewa. "A to a haɗa harda mu dan muma kansu mana kwarjini yana mana yawa Hamma Jabeer". Murmushi yayi kana suka shigo suka zauna suna hira cikin jin daɗi. So a nanne yaji kaso 30 cikin 100 na azabebben kishin daya cakeshi ɗazu ya ragu. Ita kuwa Shatu suna shiga kai tsaye bedroom nashi ta wuce. Ta gyara komai ta killace komai ta ɗan ƙara gudun AC kana tasa turaren ɗaki Tuch me mai sassayan ƙamshi. Kana ta dawo ɗakinta, kamar kullum bayan tayi wonka ta fitone. Ummi ta shigo riƙe da kasko da rushi kaɗan a ciki. Gaban gadon ta ajiye kaskon tare da jawo kujerar ƴar tsuguno mai rami ta turaren gyara ta ɗaura kujerar kana ta jawo wani kolba dake kan mirror ta buɗe tasa hayaƙi mai ƙamshi ya fara tashi. "Zauna". Tace tana fita. Da sauri Shatu ta zauna bisa kujerar tana mai jin yadda ƙamshin yake game jikinta, Tabbas wannan turaren tana jin daɗin shi ita da kanta da kanta. Dan ko fitsari tayi sai taji yana ƙamashi sai dai tana ji yana tsuketa. Bayan kamar 30 minute Ummi ta kuma shigowa riƙe da cup da madarar gongoni a ciki mai sanyi da haɗin *Garin maɗi.* Motsashi tayi da cokali tare da cewa. "Yauwa amshi ki shanye". Ba musu ta amsa sabida tana masifar jin daɗin haɗin. Bayan ta shane ta ajiye cup ɗin kana ta matso gaban dreesing mirror'n humra mai sanyin ƙamshi ta murza a jikinta tare da zura wata tattausar rigar bacci royal blue mai ɗigo-ɗigon fari. Rigar iya karya guiwa. Turaren laylaytul sahrah ta fesa. Kana ta zura jibajinta har ƙasa. Su Sheykh kuwa bayan sun gama hirane. Yasa hannunshi ya amshi Afreen da Mamey ke miƙa mishi tare da cewa. "Kaita tasha mama". To yace. Tare da amsarta ruggume ta yayi a jikinshi tare da cewa. "Sai da safe". "Allah ya bamu al'khairi". Amin yace yana mai fita, sai kuma ya tsaya jin Abbanshi na cewa. "Kaje wurin Lamiɗo akwai takardun aiken masarautu da yakeso ya baka". Cikin bin umarni yace. "Toh". Yana fita Part ɗin Lamiɗo ya nufa. Gefenshi ya zauna ruggume da ƴarsa cikin kula Gimbiya Aminatu tace. "Kai ɗa da daɗi ko Sheykh". Murmushi yayi tare da kallon Afreen dake jujjuya ido tana lumshesu alamun bacci zatayi yace. "Uhumm sosai ma kuwa ɗa kam da daɗi Gimbiya Aminatu". Dariya sukayi baki ɗayansu. Shi kuwa kissing goshinta yayi tare da sa mata al'barka. Kana ya kalli Lamiɗo a fakaice yace. "Abba yace akwai takardun da zaka bani". Eh yace tare da miƙo mishi wasu takardu liƙe cikin wani, kekkyawan mazauni tare da tambarin hatimin masarautar Joɗa a jiki. Hannu yasa ya amsa tare da cewa. "Toh na menene?". Cikin tsareshi da ido Lamiɗo yace. "Aiken Masarautar Joɗa ce zuwa ga sauran masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria, zaka kai musu ɗaya baya ɗaya". Da sauri yace. "Yaushe kuma aiken menene?". A daƙile Lamiɗo yace. "Gobe sai kaje ka dawo zan gaya maka na menene. Waziri, Wambai, Galadima, Chiroma, Durbi, duk sun sa hannun". Taɓe baki yayi tare da cewa. "Sai dai kuma ai kai ba ubana bane da zaka wani tirsasani ka sani abu dole. Harda wani wai gobe". Ya ƙarashe zancen yana miƙewa tsaye riƙe da takardun. Shi kam Lamiɗo murmushi kawai yayi ya bishi da ido. Kai tsaye Part ɗin su ya nufa. Ba kowa a falon haka yasa ya rufe ko ina ya kashe duk kayan wuta. Kana ya wuce Side ɗinsa ruggume da Afreen. A hankali yaja sassayan numfashi tare da shaƙar ƙamshin ɗakin. Wutan ya kunna, ido ya lumshe ganin komai fes-fes. A can tsakiyar gado ya kwantar da Afreen tare da gyara mata kwanciyarta dan tuni tayi baccinta. Addu'o'in yayi ya tofa a tafin hannunsa ya shafa mata. Bathroom ya wuce. Wonka yayi mai rai da lfy kana ya kimtsa cikin wasu tattausan riga da wondo pink guava color da ratsin Royal blue masu ɗan karen taushi. OudKareem ɗinsa ya fesa kana ya fito. A hankali ya ɗan zauna bakin gadon ba tare daya kashe wutanba. Miƙe sawunshi yayi bisa gadon tare da ɗan zamewa ya kwanta rigingine. Ido ya rumtse a hankali tuno kalaman Ba'ana a kan Shatu. Ita kuwa Shatu a hankali taja ƙofar ɗakinta ta rufe Sannan ta nufi Side ɗinsa. A hankali ta tura ƙofar tare da cewa. "Assalamu alaikum". buɗe idonshi yayi tare da zuba mata su. Murya can ƙasa yadda bata jiba yace. "Wa alaikassalam". A zahiri kuma sai ya haɗe fuska tare da tsuke bakinshi. Motsowa ta inda yake tayi tare da cewa. "Yah Sheykh kayi bacci ne?". Bai kulata ba kuma bai ɗauke idonshi a kanta ba. Ƙara matsoshi tayi tare da zare hijabin ta ninkeshi tana cewa. "Hamma Jabeer yau ba mgna ne". Bakinshi ya taɓe mata. Wanda hakan ya tabbatar mata yana fushi da itane wanda tasan fushin bai rasa nasaba da yadda yake buƙace da ita take kauce mishi. Ajiye hijabin tayi a gefe. Sannan ta ɗan matso gaban shi. Yatsun ƙafarshi ta ɗan ja tare da cewa. "Nooryat". Idonshi ya cire a kanta, yana mai ji kamar ya ruggumeta. Fahimtar dafa gaskene fushin yasa ta ɗan hauro saman gadon. A hankali ta sunkuyo kanshi tabi tsawon shi. Hannunta ta cusa cikin rigar tashi, ta fara mishi tafiyar tsutsa ta gefe da gefen cikinsa. Kana ta haɗa fuskarshi da nata. A hankali ta kamo lip ɗinshi na ƙasa ta tsotsa tare da fidda sautin. "Shyyyyuuyyh Yan Sheykh na tuba". Miƙa mai tsawo yayi jin yadda takeyin ƙasa da hannunta. Kana ta haɗe bakinsu wuri guda. Wani irin lasa tayiwa harshensa wanda yasa yaji. Sheykh ɗin shi ya amsa amo ya miƙe cike da zalama. Da sauri yace. "Barni". Cikin raɗa tace. "Naƙi". Kanshi ya ɗan ɗago tare da tsareta da ido. "Sai kuma ya tashi zaune yana riƙo hannunta jin tana kwance mishi zariyar wondo. Da sauri yace. "Wai menene hakan?". Cikin tura baki tace. "Abuna zan nema". Bai san lokacin da dariya ta kubce mishi ba ganin yadda tayi mgnar cikin dariyar yace. "Abun naki kuma babu inda zaki nemo shi sai cikin wondona?". Ya ƙare mgnar tare da jawota jikinshi ya ruggumeta gam-gam yana kissing wuyanta. Cikin jin daɗin ya huce da kuma son fara shigar mishi da ra'ayin sarauta tace. "Mai martaba Lamiɗo Jabeer. Allah ya nuna min randa zaka mulki masarautar Joɗa ka rabamu da duk wasu al'adu marasa kan gado". Cikin yi mata kallon shauƙi yace. "Yoh al'adun gida nama ai kin nuna ban isa in hanasuba bare na masarautar Joɗa". Cikin cusa hannunta cikin ƙugunshi tace. "Al'adar gidanka kuma wacce ta isa tafi ƙarfin ka hanata". Hannunshi yasa yana kunce igiyoyin dake sarkafe gaban rigarta murya can ƙasa yace. "Al'adar wai in mace ta haihu sai ta kwana arba'in kafin ta bari mijinta ya kusanceta. Kullum a wahale nake kwana ke ko a jikinki kina sane dai al'adace ba addiniba amman kikayi tauye min haƙƙina". Da sauri tace. "Toh ai hakanma Al'adar masarautar Joɗa ne ni yamin ka sani ma". Ta ƙare mgnar cikin gimtse dariyarta na ƙaryar da tayi na wai Al'adar masarautar Joɗa sai bayan arba'in za'a koma turaka, tayi ƙaryar ne kuma sabida ta samu ta ƙara cusa mishi tsanar al'adun da son kaudasu. Ai kuwa cikin kwaffa yace. "Zancen banza, ai wannan aikin jahilci ne ya za'ayi nida matata kuma ace sai wata Al'adar masarautar Joɗa ta bani izini da damar kusantarta". Murmushi mai cike da ƙauna tayi tare da cewa. "Toh ai shine muke fatan ka mulkemu ka kauda ire-iren waɗannan abubuwan". Tayi mgn tana kai bakinta gareshi. Wani irin dogon numfashi yaja tare dasa hannun duka biyu ya tallabe kanta. Tare da fidda sautin. "Shiyyyyyy Ahhhh Aishh". Sosai ta gigitashi da salon da tasan yana masifar so. Saida taga ya gama narkewa ta ɗan janye kanta kana ta ruggume shi a hankali ta kai bakinta kusa da kunnenshi murya can ƙasa tace. "Yah Sheykh ka mulki masarautar Joɗa dan Allah da manzonsa dan son samar da gyara". Cikin yanayin da bai san hali da duniyar da yake cikiba yace. "Tohhhhh Aish". Da sauri tace. "Kayi al'khairi". Jikinshi da muryarsa kab na rawa yace. "Nayi al'ƙawarin". Ai kuwa sai ta mirgina ta jikinshi da kyau. Bayan ta cire rigarta. Wani ɗan raunataccen ƙara ta saki sabida. Zafin da taji yayin ziyartarsa wanda dole ta janye ta kwanta tare da cewa. "Bazan iyaba". Jikinshi na rawa yayi mata rumfa. Da ƙarfi ta ɗan saki ƙara sabida ji tayi kamar yau ta taɓa sanin namiji dan gyaran da Ummi da Mamey da Umaymah sukayi mata ya haɗawa. Hannunta ta ɗan yarfa cikin raki tace. "Wash Honey". Cikin yanayin shiga duniyar maji daɗi Yah Sheykh ya rinƙa sanya mata al'barka". Cikin nitsuwa cikin sararin samaniya murya a narke tace. "Yah Sheykh zaka mulki masarautar Joɗa ko". Da sauri yace. "Eh eh ehhhhhhhhhhhhhh Aishhhhh". Sabida yana gab da jin numfashin sa na shirin ɗaukewa in bai buɗe bakinshi ba... Bayan komai ya lafane sunyi wonka sun dawo suna konce. Ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe tare da shafa maransa kana a hankali yace. "Alhamdulillah naji sakayau". Sai kuma ya kai hannunshi bisa cikinta tare da cewa. "Allah yasa ƙanwa ko ƙanin Afreen ya kasantu". Cikin sauƙe numfashi tace. "Ai ni dai tunda ka yarda zaka mulki masarautar Joɗa ko duk shekara zan haihu ba matsala". Da sauri yace. "Toh yaushe kuma mukayi haka dake?". Cikin kwaɓe fuska tace. "Yanzu mana". Juya mata baya yayi yana gyarawa Afreen kwanciya yace. "Uhumm to ke waya ce miki al'ƙawarin a irin wannan lokaci yana aiki, ai ko al'ƙalai basa amsar shaida da al'ƙawarin mai fataucin kayan daɗi". Da sauri tace. "Yah Sheykh al'ƙawarin fa kayi". Jawota jikinshi yayi tare da cewa. "Kai sake wannan al'ƙawarin Aish, yoh ai sai ince miki na baki Makka da madina ma a cikin wannan yanayin ke baki san Y.M.D.G. bane". Dariyar da take dannewa ne ta kubce mata. Haka yasa ya lakace hancinta tare da cewa. "Ja'ira wato dariya ma zakiyi min". A haka dai sukayi bacci liƙe da juna. Washe gari da asuba suna dawowa masallacin. Abbanshi yake ce mishi. Wai yayi maza fa ya fito su tafi shi ɗaya ake jira. Sosai yayi mamakin ashe dama da gaske Lamiɗo yake yau zaiyi tafiyar. Bisa dole bisa umarnin iyayenshi ya fito suka tafi. Shatu nata bashi baki. Ta kaicinsa ɗaya da aka hanashi tafiya da ita. Alhamdulillah yayi tafiyar kai takardun murabus ɗin da Lamiɗo zaiyi ya bashi mulki ga masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria. Gaba ɗaya sunyi na'am da haka sun sa hannun. Duk da shi baima san takardun me bane dan bai buɗeba. Randa ya isa masarautar su Umaymah kuwa daɗi kamar zai kasheta. Kwanashi goma ya gama zagaye kab masarautun ya dawo dasa hannun da buga hatimin dukkan masarautun. Koda ya dawo da Lamiɗo ya gani saida yayi ƙwalla sabida zallan farin cikin ganin yadda ya samu haɗin kan kab masarautu har aka ƙara da yabawa sarki maijiran gadon. Shida Shatun kuwa a ranar suka tabbatarwa juna. Sunyi bege da kewar juna. Kasan cewar ranar Al'hamis ya dawo. Tun a daren Shatu ke ta masa batun. Zuwa Rugar Bani. Toh yace dai ba matsala ran asabar zai kaita. Mamey ma da Ummi dasu Jalal duk sunce zasu je. Ba'ana kuwa zuwa yanzu gaba ɗaya. Ya zama wani irin al'ummar Rugar Bani kuwa sun cika da mamakin ganin yadda ya sauya jami'in salla baya wuceshi yayi sanyi ya sauya kamar ba shiba abu kaɗan sai hawaye. Yauma kamar kullum yaje ya samu Bappa a garkensa bayan ya gama magiyar a bashi Shatunsa Bappa ya babbashi haƙuri. Sai kawai ya jingina kanshi da jikin itacen nim dake gefenshi. Murya na rawa yace. "Zan sake barin Nigeria'n kuma tabbas da Shatu da duk dabbobinmu Rugar Bani zanyi awon gaba dasu muddin baku dawo min da ita cikin lumana ba." Ya ƙarashe mgnar cikin alamun wai baraza zai mishi. Ganin yadda Bappa ya zuba mishi idone yasa yaci gaba da cewa. "Wlh Bappa mutuwa ce kaɗai zata rabani da Mata in haƙura, bayan mutuwa babu abinda zai rabani da ita na barshi. Tabbas zan saceta. Sabida itace cikon farin cikina Mata ce burin duniyata". Ya ƙare mgnar hawaye na zuba. Kai Sheykh ya jinjina tare da cewa. "Uhumm da kuma ita zanyi maka tarko ka shiga hannun hukuma ba taƙadiri". Shi kuwa Bappa da Baroon shiru sukayi suna jin yadda sautin kukansa ke tashi. Washe gari ranar asabar. Misalin ƙarfe goma na safe. Tsaye suke gaba ɗayansu cikin shiga ta al'farma. Jalal da abokanshi sojoji mutun huɗu su motarsu da ban. Yah Sheykh kuwa shi yake jan motar da kanshi Shatu na gefenshi Ummi da Mamey na baya. Saratu kuwa tana motar Aunty Juwairiyya da Yan Jafar da yaransu. Jamil da Affan kuwa motarsu ɗaya a haka suka nufi Rugar Bani. Ƙarfe sha ɗaya dai-dai na safe tayi musu cikin Rugar Bani. Cikin wani irin masifeffen zabura Ba'ana ya tashi zaune. By *GARKUWAR FULANI* 👆🏻 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 GARKUWA Page 11 Tare da kallon zoben azurfan dake yatsarsa wacce irinta ya sawa Shatu a yatsarta wanda in suna kusa da juna zasuyi ta yin haske. Wani irin dariya mai cike da jin daɗi yayi tare da cewa. "Mata". Ya faɗi yana mai miƙewa tsaye ya nufi ƙofar gida. Su Sheykh kuwa a hankali sukayi parking cikin nitsuwa suka fara fitowa. Ummi na Ruggume da Afreen yar wata biyu tayi kuɓul-kuɓul da ita gwanin burgewa da sha'awa gashin kanta yana kwance lib-lib kamar ɗiyar larabawa. Wasu irin tattausan kayane masu masifar kyau da taushi da tsada aka kimtsata a ciki rigar mai ɗan karen kyau. Yellow and Pink color masu taushi sai ɗan banɗanan nashi mai kyau da akasa mata a kanta yayi cib dashi. Sai Safar kafarta yellow sai takalmanta pink. Kana towel din da aka ninketa ciki shima pink color. Sai wani irin fitinenne ƙamshi mai daɗin shaƙa da takeyi. A hankali suka fito baki ɗayansu. Ajiyan zuciya Mamey da Shatu suka sauƙe tare da shaƙan daddaɗan iskan Rugar tasu. Kowa ya bar gida tabbas gida ya barshi. Da sauri Ummi da Aunty Juwairiyya da Sara suka matsosu. Mamey ce a gaba duk suna biye da ita a baya. Sheykh kuwa shine a gaba Yah Jafar da Affan dasu Jamil na biye dasu. A cikin gidan kuwa, Junainah ce riƙe da hannun Yah Giɗi tana ɗan tsalle-tsalle tare da cewa. "Yauwa Ya Giɗi muje lambu ka ciro min inabi mana". Gyara riƙon da yayiwa hannunta yayi tare da cewa. "Ba Junaidu ya kawo miki wani ba ɗazu". Da sauri tace. "A a ai na ajiyewa su Adda Shatu da Ummey na shi. In sun iso zan basu". Juyowa yayi ya ɗan kalleta tare da cewa. "Toh ai kije kawai kici abunki, su tun jiya da yamma bappa yasa na ciro musu komai". Dai-dai lokacin kuma suka iso ƙofar gida. Da sauri Junainah ta saki yatsarsa tare da cewa. "Oyoyo Ummey na Adda Shatu na". Tayi mgnar tana nufar inda suke a guje. Da sauri Shatu ta buɗe mata hannu ta faɗa jikinta. Ruggume juna sukayi suna dariya. Giɗi kuwa da sauri yace. "Kai maraba lale sannunku da zuwa". Ya ƙare mgnar yana isa gabansu Sheykh. Da sauri Bappa ya fito jin muryar Junainah na cewa. "Oyoyo Ummey na". Ai kuwa a cikin zauren yayi kiciɓis dasu Ummey cikin jin daɗi yace su isa. Kana ya wuce wurinsu Sheykh yayi musu jagora har barandar ƙofar ɗakin shi. Shatu kuwa kai tsaye ɗakin Ummey ta buɗe musu suka shiga. Inna Amarya kuwa daɗi kamar ta haɗiye haƙorinta Allah ya sani sun shaƙu da Ummey tayi kewarta ainun. Bayan sun zauna ne ta kalli Shatu tare da cewa. "Shatu taso kizo ki kaiwa su Sheykh ruwa". Da sauri tace. "Toh Inna Amarya". Kana tabi bayanta. Tiren saƙar kabar dake cike da fruits danginsu Ayaba, inabi, tupa, yazawa, goiba, mangoro, danino, masu masifar sanyi kasan cewar cikin tulu suka kwana. Sai kuma ƙwaryar damemmen fura da nono da zuma. Da fefeyin kayan ya'yan itatuwa ta rufe ƙwaryar kana ta ɗauki kananan ƙore da ludayayeyin suma masu kyau, ta riƙe, kana ta miƙe ta nufi ƙofar Bappa. Ita kuwa Inna Amarya ta ɗauki sauran ta nufi cikin ɗakin Ummey dashi. A hankali ta ratsa gefen Sheykh ta ajiye kwaryar a tsakiyar su. Kana a hankali tace. "Bismillah ga ruwa". Murmushi mai yelwa Sheykh yayi tare da cewa. "Mun gode". Jalal kuwa hannunshi yasa ya ɗan tsinko gefen nonon inabi kana ya fara kaiwa bakinshi yana tsinka. Ido ya lumshe tare da cewa. "Wai ni kam Adda Shatu kuna da Fridge ne a garin nan". Dariya sukayi baki ɗayansu. Bappa kuwa miƙewa yayi ya fita yana cewa. "Toh bari inje nan kusa kafin kusha ruwa". To sukace sanin bazai zauna ba. Ita kuwa Shatu ruwa ta koma ta kawo musu cikin kwanon sha na asalin gargajiya. Ajiyewa tayi tana kallon Affan da yake lumshe ido yana shan kindirmon. Jamil kuwa Ayaba yakeci. Yah Jafar ma nonon yake Sha. Shi kuwa Sheykh dabinon yake ci. A hankali ya kalleta tare da cewa. "Ni zan sha nonon amman zumar bata ji minba a ƙaro min". Da sauri tace to tare da miƙewa a nitse ta shiga cikin ɗakin Bappa. Ido ya ɗan zuba mata lokacin data fito riƙe da akoshi ta ajiye a gabanshi tana buɗe wa. Da sauri ya ɗan jawo akoshin ganin asalin farar zuma da sakarta, yatsarsa yasa ya laso yasa a baki. Girarshi ɗaya ya ɗan ɗaga mata tare da cewa. "Kefa baƙuwa ce, zaki shige musu har ɗaki". Da sauri tace. "Tab baƙuwa kuma ni da gidanmu". Yana mai lasan zumar yace. "Gidanku na can masarautar Joɗa". Murmushi tayi kana ta miƙa ta koma wurin su Ummey. Sosai suka sake anata hira da dariya ga sanyin safiya. Ga yanayin garin ga farin ciki. Junainah kuwa tana ruggume da Afreen tanata kiciniya da ita. Ganin Inna Amarya ta koma Kitchen yasa Shatu Binta a baya. "Inna Amarya me kike dafa mana ne?". Juyowa tayi tana kallonta bayan ta sauƙe tukunyar kana tace. "Tuwone miyar kase da man shanu. Sai Danderun Zabbi". Da sauri ta matso tare da cewa. "Kai Inna Amarya kin biyani dama na dade banci miyar Kase ba". Gefenta ta zauna tare da jawo akoshin dake gefenta babba da karami. Danderun ne a ciki sai tururi da ƙamshin yake zubawa. Da sauri ta rufe. Kana ta buɗe manyan da sukafi wannan tuwon ɗanyar shinkafane anyi mata asalin kwasan gargajiya an lailaye samanshi da man shanu. Rufewa tayi. Tana kallon Inna Amarya data buɗe tukunyar miyar data sauke. Murmushi tayi tare da cewa. "Wannan miyar harda ta gobena". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh Shatu yanzu dauki tuwon da Danderun ki kai musu sai kizo ki kai musu miyar. Da sauri tace to. Ta ɗauka ta kai musu. Ta dawo ta kai nasu Ummey kana tazo. Ta zauna tana kallon yadda take zuba miyar. Ƙwaryar dake gefenta ta buɗe. Nanma tuwon ne da alamun na su Yah Giɗi ne. Gefe kuma kwanukan Bappa ne. Motsowa tayi tana cewa. "Inna Amarya su Ummey duk basu wani damu da nama, Amman waɗan can kuraye ne. Irin Jalal da Yayanshi sunfi son duk loma su tsakura da nama". Dariya Inna Amarya tayi tare da cewa. "Yoh kice irin Giɗi ne su". Dariya tayi da sauri ta juyo jin Yah Giɗin nata dake Ruggume da Afreen yana cewa. "Toh in banda irin Shatu wa zaiƙi nama, ko sunanshi mafa yana da daɗin ji". Murmushi tayi tuno lokacin da ya dirka mata dundu a tsakiyar bayanta sabida ta hana a yanka tsuntsuwar Boleru wacce da Ummey aka yanka". Ita kam inna Amarya naman ta kara musu. Ita ta dauki nasu Ummey ta kai musu. Ita kuwa Shatu ta kaiwa su Sheykh. Murmushi tayi ganin tuni Jalal ya buɗe akoshin Danderun. Yana ganinta yace. "Yauwa Adda Shatu a kawo mana tray'n mana ko plate". To tace. Kana taje ta kawo musu tirurruka guda biyu. Ajiyan zuciya Sheykh ya sauke tare da cewa. "Wai anya kuwa kunci abincin safe?". Da sauri Affan yace. "Bamu ciba". Murmushi Yah Jafar yayi tare da cewa. "Koma dai munci ai yanzu hantsi ya duba ludeyi. Dan haka Affan sa mana". Allah sarki rayuwa mai daɗi ba girman kai. Shatu ta raya a ranta. Shi kuwa Sheykh dariya yayi. Shi kuwa Affan ludeyin duma yasa ya zuba musu tuƙeƙƙen tuwon nan. Kana ya zuba musu miyar kasen da yaji nama da kifi banda a saman tuwon. Jalal kuwa ƙara min tray'n ya jawo. Danderun ya juye a ciki fiye da rabi. Ita kam Shatu juyawa tayi ta tafi. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa Affan, Jamil, Yah Jafar. Sun haɗa hannu cikin kono ɗaya suna cin abinci cike da gamsuwa da shaƙuwa da ƙaunar juna. Haka nan yaji wani irin daɗi. Jalal ne ya ɗan matso gabanshi da tray'n tare da cewa. "Ni dai Allah ya sani ba cin tuwo zanyiba, Hamma Jabeer muci Danderun". Jamil ne ya ɗan kalleshi tare da cewa. "Manyan kuraye ba". Eh ɗin Jalal yace kana sukaci gaba da ci suna hira. Ita kuwa Shatu bakin kitchin ɗin ta koma. Gefen Yah Giɗi ta zauna. Tare da sa hannunta cikin akoshin abincin da yake cin. Kana ta kalli Junainah dake gefenshi riƙe da Afreen tace. "Junnu kaita wurin Ummi kizo muci mana". Kai ta jujjuya tare da cewa. "Ni na koshi naci da Ummey na a ɗaki". A hankali ta ɗan juyo ta kalli ƙofar ɗakin Bappa jin Sheykh yayi gyaran murya. Ido ya juya mata, alamun me takeyi. Cikin jin daɗin yanayin tace. "Ina cin abinci da Yah Giɗi na". Murmushi yayi tare da juya kai. Shi kuwa Yah Giɗi dama ya kaiwa abokan Jalal dake can ƙofar gida zaune kan taburma a gindin bishiya. Suma sunci. Haka dai sukaci suka sha sukayi haniƙan. Kana Shatu ta tattare komai ita da Junainah. Bayan sun gama ne Bappa ya dawo nan suka sake sabuwar gaisuwa kana suka ci gaba da hira. Sannan sukaje sukayi sallan azahar a masallacin ƙofar gidan Arɗo Bani. Kana suka dawo sukaci gaba da hira. Shi kuwa Ba'ana yana fita. Ya kalli Babanshi cikin zaƙuwa yace. "Baba Mata tana Rugar Bani tabbas tazo". Da sauri Bukar yace. "A a Ba'ana banji lbrin ba". Da sauri yace. "Ga nan zobe na yana gaya min kana cemin a a". Sai kuma kawai ya juya ya nufi. Bakin garin inda yasan zai samu Baroon yana zuwa yace. "Baroon taso muje gidan malam liman indan mun isa ni zan zagaya ta baya kai kuma ka shiga ta ƙofar gida. Ina da tabbacin yau Mata na nan kuma yau zan tafi da ita. Yanzu bari in kira su Droo baki ɗayansu." Da sauri Baroon yace to. Kana sukayi maza suka nufi cikin garin. Shi kuwa Ba'ana ya kira duk sauran yaranshi suka biyo bayanshi. Ta bayan gidan suka zagaya. Shi kuwa Baroon ya shiga cikin gidan kai tsaye sabida sanin Sheykh na ciki kuma zaije ya bashi bayani ne. Yana shiga kuwa Sheykh ya yafi toshi da hannu da sauri ya iso. Bappa kam ido ya zuba musu jin Baroon nayiwa Sheykh duk bayanin abinda Ba'ana yake shiryawa. Murmushi Sheykh yayi tare da cewa. "Yanzu yana bayan gidan nan kenan?". Da sauri yace. "Eh dashi da sauran yaran". Da sauri Sheykh ya kalli Jalal tare da cewa. "Ka gayawa su Khalid su kula da duk wani dake jikin gidan". To yace kana ya kira su ya sanar musu. Nan take kuwa suka miƙe suka fara ɗan zirya Ajiyan zuciya mai nauyi Bappa ya sauke lokacin da Sheykh yayi mishi duk bayanin abinda ke faruwa. Ya ƙara da cewa. "Idan ban kamashi ba bazai daina bibiyar rayuwar Shatu ba, kuma zai iya ci gaba da yiwa mutane illa in ya rasata". Cikin sanyin jiki Bappa yace. "Hakane". Dai-dai lokacin ita kuma Shatu ta fito cikin ɗakin. Randunansu ta nufa. Dai-dai lokacin kuma Ba'ana yana ta wurin ta bayan danga. Tasa hannu zata ɗebo ruwa kenan taga zoben yatsarta ya kawo wani haske. Da sauri ta miƙe tsaye. Jin muryar Ba'ana cikin raɗa da leƙota ta tsakankanin karan da akayiwa danga a madadin katanka. Da sauri ta dafe ƙahon zuciyarta jin muryarshi ras cikin kunneta murya cike da rauni yace. "Mata! Mata!! Mata!!!". Ta sani duk duniya mutum ɗaya rak ke kiranta da wannan sunan. Murya na rawa tace. "Yah Ba'ana". Cikin rauni yace. "Mata ina kika shiga kika mance dani. Mata kika barni cikin ƙunci da ciwon rai da zuciya na rashin ki Mata wlh zan iya jure komai amman bazan iya jure rashin kiba". Kar-kar haka jikinta ya fara rawa. Da sauri ta juya, da nufin zata koma ɗakin Ummey sai kuma ta tsaya tare da rumtse idanunta da ƙarfi. Ganinshi ya ɓace ɓat ya dawo gabanta. Cikin rauni yace. "Ina zakije? Tafiya zakiyi ki barni!". Ya ƙare mgnar da rauni yana kuma ƙoƙarin kai hannunshi zai kamo nata. Cikin tsananin ruɗani tace. "A a, Yah Ba'ana kada ka taɓani ni matar aurece". Sai kuma ta kauce. Da sauri shima ya kauce ya bita. Cikin tsoro tace. "Dan Allah Yah Ba'ana ka bar fito min". Da sauri Sheykh ya miƙe tsaye cikin tsananin tashin hankali jin furucin da Shatu keyi tare kuma da kakkaucewan da takeyi alamun ana binta. Su Jalal ma kab miƙewa tsaye sukayi. Shi kuwa Sheykh da sauri ya nufi inda take. Dai-dai lokacin su Ummey ma kab Suka fito sabida karan da Shatu tasa. Sabida riƙo hannunta da Ba'ana yayi ya fara ja. A zahiri ita kaɗai ake gani amman a badini shike janta. Cikin rawan jiki ta tashin hankali tace. "Bappa Yah Ba'ana ne yake jana wai zai tafi dani. Yah Sheykh zai tafi dani". Ta ƙare mgnar da ƙarfi da kuma sakin kuka. Shi kuwa Ba'ana shima kukan yakeyi cikin rauni da tsananin so yake cewa. "Mata yanzu wani kike cewa yazo ya ceceki ya rabaki dani. Shin bakya so nane?". Dai-dai lokacin kuma Jalal ya iso gab da ita. Da sauri duk suka buɗe baki tare kallon yadda Jalal yayi sama ya faɗi ƙasa tib sabida wani irin azabebben naushi da Ba'ana ya kima mishi. Wanda su ba ganinshi sukeyi ba. Cikin wani irin tafasan zuciya irin na sojojin Jalal ya miƙe tsaye tare da nufosu. Jin Shatu na cewa. "No Jalal kada ka iso zai illa taka". Ina bai kulaba sabida ranshi ya gama tafasa. Ai kuwa kamar da fari, suka sake ganin Jalal yayi sama-sama yayi ƙasa har saida Ummey tayi kansa da gudu hannu tasa ta dagoshi. Tare da juyowa tana kallon gaban Shatu cikin sanyi tace. "Ayyah Ba'ana kayi haƙuri kada ka cutar min da ahlina nasan kai mai al'khairi ne a gareni. Bappa ne ya matso shima a hankali hakama su Affan da Yah Jafar. Shi kuwa Sheykh jingina kanshi yayi da jikin bishiyar Ceɗiya dake gefenshi. Hannunshi na dama yasa ya tallabe haɓarshi yana mai bin inda Shatu take da wani irin kallo. Sabida da fari zatonshi ko makaranta ne suka dawo. So yanzu ya fahimci ba makaranta bane. Hatsabibancin Ba'ana ne, Nazari yakeyi yadda zai fito mishi ta sigar da dole ya karya lagonshi da takwabin addu'a. Da sauri su Ummi duk sukace. "Innalillahi". Sabida ganin Ba'ana ya baiyana kansa garesu. A take kuma ya ɓace. Sai ya kuma sake baiyana ya kuma bace, saida yayi haka sau uku kana ya ɓace sai muryarsa ke tashin cikin rauni yace. "Baroon kaci amanata ina sane na Barka. Nayi hakane dan ka jawo shi wannan mai jajayen kunnuwa ya kawo min ita har nan. Ku a zatonku tarkonku na faɗa baku san cewa nawa tarkon kuka faɗa ba sa'ansu ɗaya nayi tuba na gaske bazan sake kashe raiba." Sai ya kuma bayyana still hannunshi riƙe da hannun Shatu cikin rauni murya na rawa tace. "Ayyah Yah Ba'ana dan Allah ka sakeni kada ka rabani da ƴan uwana da ƴata". Wani irin jujjuya kai yayi tare da cewa. "Bappa kun kasa cika min al'ƙawarin da kukayi min ko. Kai kuma Baroon kaci amanata ka muna furceni. Shatu ke kuwa kin yiwa soyayya ta ta gsky riƙon sakainar kashi. Wani abu kuke tunanin zaifi min ciwo da zafi sama da rabuwa da Shatu". Sai kuma ya kalli Sheykh daya zuba mishi ido yana takaronto addu'o'i babu ƙaƙƙautawa ido cikin ido ya tsare Ba'ana da ido. Shi kuwa Ba'ana murya a mace yace. "Ko na bar barun a raye kaima watan wata rana zai ci amanarka tabbas zaici amanarka maci amana kuwa gubane". Cikin sauri suka juyo kan Baroon daya saki wata iriyar gigitaciyar ƙara tare da komawa bayan Sheykh. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa inda Shatu take tana nufoshi alamun Ba'ana na matsowa inda yake. Da sauri sojojin dake wojen suka shigo da gudu Lokaci ɗaya mutane suka fara tururuwan shigowa gidan sabida ihun da Baroon yakeyi yana kiran sunan Ba'ana yana bashi haƙuri. Jalal kuwa da sauri ya kuma nufo inda Shatu take wanda da ita suke gane inda Ba'ana yake. Cikin tsoron kada ya cutar da Sheykh ya nufosu. Gib ya kuma ture Jalal tare da cewa. "Ummey ki gayawa wannan yaron zan illatashi fa ya dena matsowa inda nake". Gaba ɗaya tsoro ya rufesu jin furucinsa. Jalal kuwa hatsala iya hatsala ya hatsalo allurar ta motso to amman kuma faɗa da Ba'ana tamkar faɗa da iska mai kaɗawa ne ko kuma duhu. Da sauri Ba'ana ya juyo kawai sai ya fara dukan sojojin nan baki ɗayansu. Ya bugi wannan ta nan ya bugu wan can ta can. Kana ya haɗa da shaƙo wuyan Baroon. Kurma ihu da kakarin mutuwa Baroon yakeyi da ƙarfi. Wanda yasa gaba ɗaya gidan ya cika da mutane. Harda su Arɗo Bani. Bukar da Bugulu kuwa gefen Bappa suka tsaya suna kekrketa dariyar mugunta. Junaidu kuwa gefen Junainah dake ta kuma ta tsaya yana bata baki. Gaba ɗaya hankalin mutane ya tashi. Su Bappa da Arɗo bani da sauran dattawan Rugar Bani duk sai haƙuri suke bawa Ba'ana sabida ganin yadda yaketa dukansu Jalal ba sauƙi. Ita kuwa Shatu da gudu ta faɗa jikin Sheykh sabida saketa da Ba'ana yayi. Ganin ta nufi wurin Sheykh ne ya sashi sakin wuyan Baroon tare da barin dukan su Jalal. Ya nufo kansu Sheykh da Shatu. Cikin tsananin ruɗani Shatun ke cewa. "Yah Sheykh mu gudu zai maka illa". Jamil kuwa tuni ya fara aikinshi. Affan kuwa da Yah Jafar Kara matsowa kusa da Sheykh suke gudun kada a cutar dashi. Aunty Juwairiyya da Ummi da Sara da inna Amarya kuwa gaba ɗaya jikinsu rawa yakeyi. Shi kuwa Sheykh murmushi yayi jin Shatu tace. "Wayyoooooooo Allah Yah Ba'ana ka sakeni". Hakane yasa ya fahimci Ba'ana na kusa dashi. Ido ya lumshe tare da ɗago hannunshi kana a hankali yace. "Bismillahi". Yana faɗin haka yaji hannunshi ya sauƙa kan hannun Ba'ana kuma ya baiyyana kowa na ganinshi. Cikin nitsuwa Sheykh ya fara karanto Ayatulkursi'u yana mai kallon Ba'ana ido cikin ido wanda a take ya karya duk wani sihirin da Ba'ana ke tutiya da tinkaho dashi da ayar Allah. (Haske ya kori duhu) Da sauri Shatu ta koma bayan Sheykh ɗin. Shi kuwa Sheykh juyowa yayi ya kalli su Jalal daketa haki cikin haki da tsananin tafasar zuciya suka nufosu. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa Ba'ana ganin yadda yaketa fiffizgewa da buga ƙafarshi ta dama da ƙasa amman ina ya kasa ɓacewa. Cikin sanyi yace. "Jalal ku kamashi da sunan Allah bazai sake ɓacewa ba har abadan da izinin ubangiji". Ai kuwa da sauri Jalal yasa hannunshi ya damƙo wuyan Ba'ana tare da cewa. "Bismillahi". Ai kuwa bai ɓace ɗinba. Cikin wani irin tafasan zuciya da zafin yadda Ba'ana yayi ta libgarsu kamar shine sojan sune masu laifi cikin takaicin. Yayi mishi wani irin azabebben shaƙa tare da kima mishi naushi a cikinsa tare da kalmar "Bismillahi". Wani irin azabebben ihu mai rakaɗi da baiyyana azabar da yaji yace. "Wayyoooooooo Allah na rana,". Cikin haki Jalal ya kuma haɗa mishi wani naushin tare da cewa. "Kasan Allah ne kafurin banza matsafi". Dai-dai lokacin kuma sauran abokanshi sojojin suka rufe Ba'ana da azabebben duka da ammaton sunan Allah wanda hakan ke ƙara kwance duk wani ɗaurin sihirin dake jikin Ba'ana. "Ya ilahi ya mujibadda'awati." Mamey da Ummi ke faɗi sabida wani irin dukan zaban da su Jalal keyiwa Ba'ana. Ita kuwa Shatu cikin tsananin tsoro da kerma ta ɗan leƙo. Dai-dai lokacin Khalid ya murɗe hannun Ba'ana ɓas ya bada sautin karyewa. Da sauri ta rumtse idanunta tare da sakin wani irin kuka mai ciwo a rai. Da sauri Sheykh ya juyo yana kallonta. Bappa kuwa dasu Arɗo Bani dasu Yah Jafar kab Bukar da Bugulu suke kallo wa ɗan da suke wani irin kuka mai cike da tashin hankali. Jamil da Affan kuwa sarawa su Jalal sukayi. Mutanen Rugar Bani kuwa kab suna tsaye wasu tuni hawaye na zubo musu. Da ƙarfi Ba'ana yayi wani irin azabebben ihu da kururuwa sabida taka hannunshi da Khalid ya karya. Wanda Umar yayi ɗaya sojan ya murza tare da buga mishi naushin da saida yayi birgiman kule ya iso har gaban Sheykh. Cikin rauni da azabar raɗaɗi murya na rawa yace. "Mata! Mata zasu kasheni!". Cikin wani irin rauni da tsananin tausayi wani irin masifeffen kuka mai ƙarfi yan kwacewa Shatu. Da sauri ta zame har ƙasa ta durƙusa. Sabida wani irin azabebben tokara da guiwa da Jalal yayi mishi bisa tsakiyar bayanshi. A take sai ga jini ta hancinsa da bakinsa. Murya na rawa cike da rauni Shatu ta ɗago kanta. Ta kalli Jalal dasu Khalid kana ta kalli jinin bakinshi daya ɗan tsallo ya taɓa farin gyalen jikinta. Wani irin kukane mai cike da tsananin tausayi rauni ta fashe dashi tare da cewa. "Ayyah Jalal dan Allah ku barshi kada ku kasheshi ku barshi dan Allah". A hankali Jalal ya ɗan tsaya yana maida wani irin azabebben numfashin haƙi. Sheykh kuwa wani irin kallo mai cike da azabebben kishi ya watsawa Shatu. Tare da sa tafin hannunshi ya tallabe haɓarshi. Kana ya jingina kanshi da jikin bishiyar yana mai kallonsu. Mamey kuwa itama zamewa tayi tanamai sakin kuka. Ummi, Inna Amarya, Aunty Juwairiyya, Sara, dama duk sauran matan dake wurin wasu irin hawaye ne masu zafi suka tsastsafo musu. Junainah kuwa zuwa tayi ta durƙushe gaban Ba'ana gefen Shatu cikin wani irin azabebben kuka mai cike da rauni tace. "Wayyo Yah Ba'ana Dan Allah Adda Shatu ki hanasu dukanshi." Da ƙarfi Junainah ta faɗa jikin Shatu lokacin da Jalal yayi wani irin juyi ya kifawa Ba'ana wani irin masifeffen mari da tafin ƙafarsa. Tare da cewa. "Wato kai gaka shege har zaka sa hannu ka daki jamin soja". Wani irin azabebben karkarwa jikin Ba'ana ya farayi tamkar mazari. Wani irin kuka mai azabar ciwo da cin rai Bukar da Bugulu suka saki sabida ganin yadda hukuma ke azabtar da Ba'ana tamkar zasu ɗauke ransa. Cikin rauni murya na rawa ido na zubda hawaye Mamey tace. "Jalaluddin ku bar dukanshi". A hankali Jalal ya koma baya ya zauna bisa dakalin ƙofar ɗakinsu Giɗi. Sabida yasan muddin Mamey ta kirashi da sunanshi kai tsaye to abu ya ta'azzara gareta. Domin Babana take kiranshi, sai gashi yau full name ɗinshi ta kira bama Jalal kawai ba. Sai kuma ta kalli su Khalid kana ta juyo ta kalli Sheykh murya na rawa tace. "Muhammad ka hanasu dukanshi". Cikin wani irin yanayi Sheykh ya ɗagawa su Khalid hannu. Haka yasa suma suka koma gefen Jalal suka zauna suna haki da maida numfashi. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa Shatu dake kuka tamkar ranta zai fita. Gaba ɗaya wurin babu wanda rauni bai darsu bisa zuciyarsa ba. Yah Jafar da Bappa kuwa tuni hawaye suke zubdawa. Bukar da Bugulu kuwa da rarrafe suka iso gareshi. Shi kuwa Ba'ana wani irin dogon numfashi mai cike da azaba rauni nadama ya fesar a wahalce kana a hankali ya fara yunƙurin tashi zaune. Amman Ina ya kasa ganin hakane yasa Bukar yin sauri yasa hannunshin ya tallaboshi ya ɗagoshi. Ya jingina bayan Ba'ana nan da kirjinsa. Ya zama suna fuskantar Shatu dake kuka tamkar ranta zai bar gangar jikinta gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi. Cikin wani irin rauni murya na rawa yace. "Mata!". Da sauri ta ɗago jajayen idanunta ta ɗaurasu kanshi. Wanda haka yasa ta saki wani sabon kuka, Junainah ma kukan ta saki da ƙarfi. Shi kuwa Ba'ana hawaye na kwarya yana ƙore jinin hancinsa da bakinsa murya can ƙasan maƙoshi yace. "Mata". Murya na rawa kuka na kumbe mata tace. "Na'am Yah Ba'ana". Wani irin murmushi mai rauni yayi kana a hankali yace. "Mata Ranar da nake tsoro tazo, ranar da na gaya miki zata iya ɓaci zata zo, gata yau tazo". Sai kuma ya ɗago ɗaya hannun nashi mai lafiyar ya sharce hawayensa, cikin sanyi ya jujjuya kanshi dake masifar mishi ciwo. Ido ya zuba mata ganin yadda take kuka har numfashin ta na fizga. A hankali yace. "Shatu kin san son da nake miki gsky ne?". Cikin kuka tace. "Na sani Yah Ba'ana na sani son da kake min gsky ne". Wani dogon ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah". Sai kuma ga hawaye shar-shar bisa fuskarshi. Cikin rauni yace. "Ke kuma kin taɓa sona a ranki da gsky?". Kanta ta fara ɗan bugawa da ƙafar Sheykh dake gefenta. Tare da cewa. "Eh eh eh Yah Ba'ana na soka so na gsky na soka so irin wanda naso mu gudu tare mu tsira tare nasoka irin son da nake yiwa Yah Al'ameen sabida bana son irin wannan ranar tazo mana". Kanshi ya jujjuya kana cikin rauni yace. "Shatu haka ƙaddarar rayuwata take." Sai kuma ya kalli Junainah a hankali yace. "Junnu me yasa kike kuka, bakya son a kashenine". Cikin kuka tace. "Bana son a kasheka Yah Ba'ana. Ina sonka kamar yadda nake son sun Yah Giɗi". A hankali ya sunkuyar da kanshi tare da sakin wani irin raunataccen kuka wanda saida Affan ya zubda hawaye. Cikin sanyi yace. "Mata ina ƴarmu?". Cikin wani irin rawan jiki hawaye na kwarya. A hankali tasa hannunta ta amshi Afreen dake hannun Ummi. Kana ta juyo da rarrafe tamkar ƙaramar yarinya ta iso gabanshi cikin rawan murya tace. "Gata nan Yah Ba'ana". Wani irin murmushi mai yelwa yayi wanda saida fararen haƙoranshi suka fito ras. Da idonshi ya nuna mata cinyarshi. Cikin kuka ta sunkuyo ta kwantar mishi da Afreen bisa cinyarshi. Kana ta kife kanta cikin cinyoyinta ta saki kuka. Shima kukan ya saki mai rauni. Kana yasa tafin hannunshi ya shafi kan tattausan suman gashin Afreen hawayenshi na kwarya suna ɗiga kan goshinta. A hankali yace. "Masha Allah, Allah ya raya mana ita bisa imani al'farma Annabi da al'ƙur'ani Allah yasa mahaddaciyar al'ƙur'ani ce, ya azur tata da miji na gari". Karo na forko da Sheykh ya motsa lips ɗin shi a hankali yace. "Amin ya Allah". Sabida daɗin Addu'ar da akayiwa ƴarshi. Itama Shatu cikin kuka tace. "Amin thumma Amin". Sai kuma ta ɗago kanta a hankali jin yana cewa. "Naji lbrin Ummey ta tuno baya ta gane ahlinta ance min ma wai ɗan ta ne ya aureki ko?". Ina ta kasa mgn sai kuka, Ummeyn ce ta sharce hawayenta a hankali tace. "Eh Ba'ana na tuno baya, na gano ahlina Allah ya saka da al'khairi ya biyaka da mafi kyawun sakamako". Cikin rauni yace. "Amin Amin Ummey". Sai kuma ya kalli Bappa dake ta kuka a hankali yace. "Bappa kana kukan baka cika min al'ƙawarin da kayi bane?". Da sauri Bappa ya gyaɗa kai alamar eh. Kai ya jujjuya kana a hankali yace. "Ba laifinka bane, ƙudirin ubangijine ba gashi yanzu Ɗiyar Shatu ce a cinyata, wani bazai haifi ɗan wani ba ai. Ni na yafe muku yanzu na yarda na gane komai nufin Allah ne. Sai dai kuma ina neman yafiyarku al'ummar Rugar Bani baki ɗaya busa duk wata cutarwa da nayi muku." Sai ya kuma kalli ɗaya daga cikin yaransa da suka shigo tare a hankali yace. "Koda bana da halin muku bayani, ga Droo zai muku dukkan bayanin abinda ke tafe, gaba ɗaya na mishi bayanin komai kafin mu taho". Sai kuma yayi shiru jin duk anyi shiru ana jinshi sai shessheƙan kukan Shatu dake tashi. Kalato yawun bakinshi yayi ya haɗiye sabida wata irin azabebben ƙishin da yakeji tamkar zai kashesa. A hankali ya kalli Ummey cikin rauni yace. "Ummey ƙishi nakeji ki sanmin ruwa". Yayi mgnar yana kallon Shatu data zuba mishi ido da sauri. Ya sani ta tuno bayanin daya taɓa yi matane na cewa in an bashi ruwa yasha zai ɓace zai tsiri. Haƙƙun kuwa itama abinda ta tuno ɗin kenan sai dai bata saniba ya kakkarya duk waɗan nan abubuwan. Cikin rani yace. "Shatu Insha". Yace lokacin daya amshi kofin ruwan da Ummey ta miƙo mishi. Shiru batayi mgna ba sai kukanta daya ƙaru. Sheykh kuwa zuwa yanzu Allah ne kaɗai yasan abin da yakeji a zuciyarsa sabida azabar zafin kishi. A hankali murya na rawa ido na zubda hawaye yace. "Mata ina sha, ko kada insha zaki gaya musu, ki gaya musu mana". Da sauri Jalal yace. "Adda Shatu menene wani tsafin zaiyi ne?". Da sauri ta kalli Jalal kana ta juyo ta kalli Ba'ana ta kuma juyowa ta kalli Sheykh. Cikin sanyi murya na rawa tace. "Ka." Dai-dai lokacin kuma Baroon yasa hannunshi ya bugi ruwan tare da cewa. "Idan yasha zai ɓace ne fa". Yayi mgnar sabida baisan Ba'ana ya ƙauracewa tsafi da asirce-asircen ba. A hankali ya juyo ya kalli Shatu tare da cewa. "Ƙarasa mgnarki domin itace kamar zaɓin rayuwata da mutuwa ta." A hankali tasa hannunta ta ɗauki Afreen dake kallon fuskarshi tana wasa. Cikin rauni tace. "Kada ka sha Yah Ba'ana ka bari hukuma tayi maka hukuncin daya dace da kai". Yana zubda hawaye yace. "Uhummm to shike nan Mata. Amman nasa baki san me nake aikatawa ba shiyasa kike tunanin hukuncin hukuma zai rageni da rai". Da sauri ta nufi cikin ɗaki tana kuka. Kana su Jalal kuma suka kamashi sukasa a motarsu sukayi gaba dashi. Su kuwa Bukar da Bugulu da kuka suka tafi. Yayinda duk mutane ke zubda hawaye. Bayan anyi sallan la'asar ne. Sheykh yace su fito su tafi cikin disashewar murya Shatu tace. "Jamil aini zan kwana biyu". Kai Jamil ya ɗan juya yace. "A a Yah Sheykh yace ki fito mu tafi, wai ya fasa baza ki kwana ba". Jin haka yasa Inna Amarya dasu Giɗi da Gaini da Seyo da yanzu suka dawo sukace. Tabi umarnin mijinta. Dole haka ta fito suka tafi, harda Junainah. Gaba ɗaya Rugar Bani tayi shiru tayi sanyi tamkar waɗanda akayiwa mutuwa. A can masaraur Joɗa kuwa. Cikin wani irin ƙunan rai Sheykh ya kalli A....! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 a yawan posting ne babbancinsu yake. Idan kinaso turo kuɗin ta Account 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai kiyi screenshort na Debit Alert ki turo ta WhatsApp 09097853276. Sai in saki a group, ku ƴan 300 in baki da damar biya ta Account to ki sayi katin Mtn na ɗari uku kacal ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276. Banbancin special Group da Normal group a yawan posting ne kada kizo kice in miki ƙarin bayani ɗan Allah. By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Agogon hannunsa, ƙarfe 11:30 pm na dare har yanzu Shatu bata shigo inda yakeba. Idanunsa ya rumtse da ɗan ƙarfi, tare da gyara kwanciyarsa, ya mai jin wani irin zazzafan kishi na taso mai. Allah Ya sani yana jin ciwo da zafi acikin zuciyarshi, har yanzu idan ya tuno yanayin tashin hankali da kuma tausayi da rauni’n da ya gani a fuskar Shatu, lokacin dasu Jalal ke dukan wannan taƙadirin tsohon saurayin nata. Mchewww yaja wani dogon tsaki a fili yace. "Sabida shine zata barni ni ɗaya a ɗaki kamar wani marar galihu?" Muskutawa yayi tare da fesar da zazzafar iska ta bakinsa, sosai yakejin kuna acikin zuciyarsa, wanda kuma duk akan Kishin Shatou’n da yakeji ne. A haka dai bacci b’arawo yayi awon gaba dashi bayan yayi ta juye-juye. Ita kuwa Shatu tunda suka dawo ta gaza tsaida hawayenta. Allah Ya sani bata taɓa jin son Yah Ba'ana aranta ba, bata kuma jinsa a matsayin saurayin da take buri da fatan aure, sai dai tasan tabbas tana mishi so irin na ɗan uwan taka. Tana jinshi tamkar su Yah Al'ameen dasu Yah Giɗi. Tana mishi so irin na ƴan uwa musulmai da son ya gyara rayuwarsa ko ya samu rabauta ranar gobe kiyama. Kuka sosai takeyi, rungume da Afreen damunta da yarinyar tayi ne kuma yasa ta fito da ita. A falo ta samu Ummi zaune ita da Jalal. Cikin disashewar murya tace. "Ayyah Ummi ga Afreen kaina ciwo ina so inyi bacci ta hanani". Da sauri Ummi ta miƙo hannu ta amsheta tare da cewa. "Tasha mamanta ai ko?". Kai ta gyaɗa mata alaman “Eh.” Jalal ne ya ɗan kalleta sosai fuskarta, ta kumbura tayi jazir idanunta kuwa sunyi tib tib. A hankali ya maida kanshi ga Ummi yana mai ci gaba da cewa. “Ai daga can Rugar tasu cibiyar bincike na jiha muka kaishi. Alhamdulillah kuma shida bakinshi ya amsa dukkan laifukansa tare da yin bayanin komai, ya tabbata cikekken mai laifi da ake nema ido rufe, yanzu kai tsaye ba ɓata lokaci za'a kaishi kotu ta yanke mishi hukunci ranar Monday da izinin ubangiji.” Cikin sanyi Ummi tace. "Allah sarki, Allah yasa ya samu da sauƙi". Miƙewa Jalal yayi tare da cewa. "Wani da sauƙi kuma Ummi ai yadda yayi ta kashe mutane, da sace dabbobin su shima kasheshi za'ayi a rage mugun iri a duniya". Jin hakanne kuma yasa cikin sauri Shatu ta koma ɗakinta. Bisa kan gadonta ta kwanta tare da kifa kanta kan pillow, wani irin sassanyan kuka ne ya kwace mata. Lokaci daya Komai ya fara dawo mata sabo, tun randa ta fara ganin Yah Ba'ana da kuma yau da tayi mishi kallon da take tsoron kada ya zama na ƙarshe ne. Saboda ita dai bata taɓa sanin cewa yana sata da kashe mutane ba. Haka ta dinga sak’e sak’e acikin zuciyarta, a ranar dai haka suka kwana kowa da abinda ke damunsa. Washe gari kuwa, ranar Lahadi, Sheykh yana gida wuni zur amman Allah bai sa yaga idon Shatu ta fito ba. Wannan abun ya ƙara ingiza mishi zafin kishinsa, ji yakeyi tamkar yayi ta ihu dan takaici. Bayan sallan azahar ne. Ya dawo a falon ya samu Ummi da Aunty Juwairiyya da Mamey. Wacce kuma ta shigo ne dan ta duba Shatu, da yawan kuka ya sakar mata zazzafan zazzaɓi da ciwon kai. To ta fito daga d’akin Shatou d’in kenan, suna zaune afalo ya dawo. A hankali ya ɗan sunkuyo ya shafa kan Afreen dake cinyar Mamey. Tare da cewa. "Mamey ɗazu naje kina bacci". Tana kallon yadda yake shafa kan Afreen yana cewa. "Allah ya miki al'barka". Murmushi tayi tare da cewa. "To masu ƴaƴa kaima Allah yayi maka al'barka". Cikin jin daɗi yace. "Amin Amin Mamey na". Murmushi tayi kana tace. "Muna son mgn da kai". Da sauri cike da biyayya yace. "Toh Mamey gani". Miƙewa tayi ta nufi waje, shikuwa gyara al'kyabbar dake jikinshi yayi tare da bin bayanta. Kai tsaye Part ɗin Abbanshi ta nufa yana biye da ita a baya. Da sallama suka shiga. Murmushi Abba yayi tare da miƙa hannunshi ya amshi Afreen daketa raba ido. Ita kuwa Mamey gefenshi ta zauna. Da sauri ya zauna gabansu a ƙasa bisa Austrian carpet, ya tanƙoshe sawunshi ya fuskancesu da kyau. Gyaran murya Abba yayi tare da zuba mishi ido, wanda haka yasa shi yin ƙasa da kansa. Shiru-shiru basuyi mgna ba, hakane yasa ya sake ɗago kanshi da sauri yayi ƙasa da idonshi sabida ganin daga Abban har Mameyn ido suka zuba mishi. A hankali ya fara motsa lips ɗin shi yana cewa. "Astaghfirullah!!". Ya fara tubawar ubangijin mu. Kafin ya tubarwa iyayen nasa dan hakan da sukayi ya rauna tashi sabida bai san laifinsa ba. Su kuwa sun mishi hakane dan su sa mishi rauni da kuma halarto da biyayyarsa. Karo na uku ya kuma ɗagowa ya kallesu. Kawai sai ya tankwashe kansa bisa kafad’arsa murya cike da rauni yace. “Dan Allah Abba Mamey kuyi haƙuri ku gafarceni idan wani laifi nayi muku, ku sanarmin dan in kiyaye gaba kada in maimaitashi". Sai kuma ga idanunshi sunyi rau-rau sun fara wani sheƙi alamun hawaye na tsastsafowa daga cikinsu. Cikin tsare murya da fuska da kauda wargi Abba yace. “Muhammad!” Da sauri murya na rawa yace. "Na'am Abbana". Sai kuma ya kalli Mamey da itama ta kirashi. Amsawa yayi tare da zuba musu ido. Kai titsiyewar iyaye akwai sa rawan jiki da fargaba a zuciyar ɗan adam. Cikin tsananin kausasa murya Abba yace. “Ina bukatar in baka umarni kayi wani abu, ban saniba ko zaka iya min biyayya ko bazaka iyaba". Cikin sauri ya kalli Mamey da tace. "Ni umarni nake so in baka". Da rarrafe ya ƙara matsosu cikin rawan murya yace. "Abba matuƙar dai abin da zaka sani bai saɓawa umarnin Ubangiji da tsarin Addinin Musulunci ba, in sha Allah zaka sameni mai biyayya a gareka da izinin Ubangiji." Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe cikin yanayin gamsuwa. Shi kuwa a hankali ya kamo hannun Mamey, cikin sanyi ya had’a su ya tallafe haɓarshi sai ga hawaye shar-shar suna kwaranya murya na rawa yace. “Tsawon shekaru goma sha uku ina kuka dare da rana kuka na cikin zuciya, ina so in ganki da idona ma Allah bai bani Dama ba. Nakanji wani irin daɗi na musamman in Umaymah ta bani umarnin inyi abu kai tsaye, sai inji kamar ban rasa uwar da zata tirsasani yin abinda ya dace ba. Mameyna bani umarni da izinin ubangiji zanbi zan miki biyayya". A hankali tasa hannunta tsakiyar kanshi tare da cewa. "Allah yayi maka al'barka". Da sauri yace "Amin". kana ya kallesu yace. "Menene umarninku?." Kusan a tare suka haɗa baki wurin cewa. "Umarninmu shine ka amshi mulkin Masarautar Joɗa, da Lamiɗo yake son yin murabus, ka yarda ka mulki masarautar Joɗa domin kawo gyara da tsari irin na addinin musulunci, Ni Umarnine kai tsaye nake baka". Mamey ta kare zancen. Abba kuwa cewa yayi. "Ni kuwa al'farma nake nema". Abun ya zo mishi amatuk’ar bazata amman kuma saidai umarnin iyaye ya wuce wasa. Wani irin kukane mai rauni ya kwace mishi, take hawaye ya soma kwarara akan fuskarsa, cikin raunanniyar murya yace. “Mamey zanyi na amince zan mulki masarautar Joɗa, Abba kaima kace umarnine kawai na amince zanyi muddin hakan zai saku farin ciki". Cikin tsananin jin daɗi suka ɗaura hannunsu a kanshi tare da sa mishi al'barka. Sai kawai ya kife kansa bisa cinyar Mamey murya na rawa yace. “Kuyi min addu'a da bakunanku masu al'barka, ku roƙa min Allah ya bani ikon zama adalin shugaba mai tausayin al'ummar sa, ku roƙa min Allah ya bani ƙarfin zuciyar yin mulkin, sannan ku roƙa min Allah yasa kada giyar mulki ta bugar dani, ta sani danasanin muku biyayya ranar gobe kiyama, ku roƙa min Allah yasa talakawa suyi farin ciki da alfahari dani a matsayin shugaban su". Ya ilahi ya mujibadda'awati. Su kansu su Abba tausayin shi ya rufesu, domin yanzu suka gano abinda yasa yake tsoron mulki da gudunsa. Cikin sanyi sukayi ta jero mishi addu'o'i. Yana amsawa da. "Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati". Daga nan Abba yayi ta bashi baki da bashi ƙarfin guiwa. Dole sai kiran sallan la'asar ne yasa suka fito suka nufi masallaci. Bayan kuma sun idar da Sallah’n sun fitone. Abba ya sanarwa Lamiɗo da Galadima yadda sukayi. Sujjadar godiyar Allah Lamiɗo yayi sabida baiyi zaton abun zaizo da sauƙi haka ba. Shi kuwa Sheykh Part ɗinsa ya koma. Junainah da Mimi yaran Aunty Juwairiyya ya wuce a falo, har yaje bakin ƙofar shiga falonshi ya juyo yace. "Junainah zo". Da sauri tace “To” ta biyo bayanshi. A falon ya tsaya a hankali yace. "Ina Adda Shatu ?". Cikin sanyi tace. "Tana ɗakinta". Da sauri yace. "Kuka takeyi ne?". Kai ta ɗan gyaɗa mishi alaman “Eh” Uhummm kawai yace kana yace. "Jeki". Ƙarfe tara dai-dai na dare ya fito daga Bathroom ɗinsa cikin shirin bacci. Shiru yayi jiyo muryar Afreen nata kuka a falo. Da sauri ya jawo al'kyabba ya ɗaura akan men sleeping dress d’in dake jikinsa. Direct parlor’n ya fito. "Ummi lfy kuwa meke damunta?". Yace yana zama kusa da Ummin. Cikin damuwa Ummi tace. “Wlh tun ɗazu kuka takeyi, to uwar kuma Maman ba ruwa, saboda tun shekaran jiya bata wani ci abincin kirki ba". Cikin ɓacin rai yasa hannunshi ya amshi Afreen, daketa wawure-wawuren hannunta tana kaiwa baki alamun yunwa. A kafaɗarsa ya saɓa ta tare da miƙewa ya nufi Bedroom ɗin Shatu. Ita kuwa Shatu tsananin ciwon kai da alamun zazzaɓin da take jine yasa. Take turawa Ummi Afreen ita, kuwa sai tsotsan take so. Sabida ba'a barta tasha yadda take buƙata ba. Cikin takaici ya tura ƙofar ɗakin tare da yin sallama, sounding a bit harsh yace. "Assalamu alaikum, ke ina kike?” Shiru yayi saboda hangota da yayi akan sallaya, ta fuskanci al'ƙibila da alamun salla takeyi ko tayi ta idar. Rai a haɗe ya zauna abakin gadon yana mai jijjiga Afreen daketa ƙananan kuka, tare da tsotsar yatsarta babba da ciccila ƙafa. Bisa kafaɗarshi ya sakata yana ɗan jijjigata da hura mata iska a kunnenta. A take ta fara sauƙe ajiyar zuciya don dama kukan harda rikicin yin bacci. Da sauri ya juyo kanshi yana kallon Shatu jin kamar shessheƙan kuka take sauƙewa. Ai kuwa kukan takeyi ta ɗaga hannunta sama kaɗan tana addu'o'in. A hankali ya juyo ya ƙara matsowa gareta, cikin tarin takaici ya dawo bakin gadon ya zauna, wani irin dogon numfashi mai nauyi ya sauƙe kana cikin takaici murya a daburce yace. "Kuka! Kuka!! Kuka!!! kikeyi har yau har yanzu, duk kukan da kikayi a can bai isheki ba? Duk kukan nuna mishi soyayyan da kikayi bai isheki ba, sai kin dawo min cikin gidana kina min kuka? kina tauye min haƙƙina dana ƴata akan wani can banzan ɓarawo!". Da sauri ta juyo ta kalleshi, hawaye na zubo mata ta zuba mishi ido. Wani irin maƙoƙon kishine da baƙin ciki ya tokare masa wuya, a fizge da ɗan ƙarfi yace. “In ma ni bakya sona! baki da lokaci na! Bakya buƙatar ganina! Bare ki sauƙe haƙƙina dake kanki, ai ita dai Afreen ƴar kice kuma tana da haƙƙin ta a kanki ko? In kuma kinajin duk kin tsanemu ne baza ki iya rayuwa damu da bamu haƙƙinmu ba, dan Allah ki gaya min ba sai kin zauna kina ta min kuka a cikin gida, kina cutar min da yarinya da yunwa ba, sannan kina tayar min da hankali ba, Ki faɗa min in bakya sona, In sama miki salama kije can ki auri shi wanda kike so ɗin!!!” Ya ƙare maganar da ƙarfi. Cike da fushi da zafin kishi. Wanda har Ummi dake falon ta jiyoshi. Karo na forko kenan a rayuwar aure su da Shatu da taji yana mata faɗa haka. Jin hakanne kuma yasa da sauri ta kamo hannun Junainah suka tafi ɗakinsu. Ita kuwa Shatu cikin rauni ta zuba mishi ido tana mamakin fusatarsa da kalaman da yakeyi. Shi kuwa Sheykh cikin takaici yace. "Na sani ai dama ni na sani bawai sona kikeyi ba, dole akayi miki ko? dama shi kikeso! Wannan abun shi nake gudu da tsoron auren matar da ba sonka takeyi ba. Amman ba matsala kiyi ta sonshi. Nima ina da masu sona, kuma zan aurosu, su kuma kular min da ƴata". Idanunta da ta zuba masa tad’an lumshe, cikin rawar murya tace. "Yah Sheyk...". Da sauri cikin fushi da zafin kishin ganin son Ba'ana ne yasata wannan kukan. A faɗa ce ya daga mata hannu cikin tsawa yace. "Da Allah rufe min baki". Yana faɗin hakan ya juya ya fita daga d’akin, still rungume da Afreen akan shoulder dinshi. Kai tsaye bedroom ɗinsa ya wuce. Cikin tafasan zuciya ya kwantar da ita can ƙarshen gadon nasa. Kana a hankali ya miƙe ya zauna sabida azaban tafasar da zuciyarsa keyi. Ita kuwa Shatu wasu hawayene, masu sanyi suka zubo mata. Musamman da ta fahimci cewar, zafin kishine ya birkita mata salihin mijinta. A hankali ta miƙe tsaye, tare da soma takawa ta shige Bathroom. Ruwan ɗumi kawai ta watsa tare da yin Brush kana ta fito daga cikin toilet ɗin. Turaren Oud mai daɗin ƙamshi ta shafa ajikinta. Tare da zura wata royal blue sleeping gown ajikinta mai adon net. Yayinda kuma har yanzu ta kasa tsaida hawayen dake kwance acikin idanunta. Wasu lallausan sleeping shoe ta zura a ƙafarta, tare kuma da tubke long hair ɗin kanta, da bluesy ribbon. Tana gama kimtsa kanta kuwa, ahankali ta fito daga ɗakin, tare da jawo ƙofar ta rufe. kaitsaye ta nufi Side ɗinsa. Cikin sanyi ta tura ƙofar Bedroom ɗin nasa tare da yin sallama can ƙasan maƙoshinta. Ganinsa atsaye da tayi ne kuma yasa, ahankali ta jingina da jikin ƙofar tana kallon yadda yake zirya a tsakiyar ɗakin, shi kadai sai ya kai mari ya kau gouro. Ga wani irin numfashi mai ɗumi da yake fitarwa. Idanunshi kuwa sun kaɗa sunyi jazir. A hankali ta nufo tsakiyar ɗakin. Cikin sanyi da kuma rauni ta nufi inda yake. Dai-dai lokacin shi kuma ya juyo. Yana juyowa kuwa ta faɗa jikinshi ta rungumeshi tsam a jikinta. Ashagwaɓe ta saki wani irin raunataccen kuka mai kashe jiki da zuciya. Murya na rawa cike da rauni tace. “Kayi haƙuri Yah Sheykh ka gafarceni, na tuba please, kukana bawai inayi dan na ɓata ranka bane, banason fushinka, Dan Allah kada ka kwana kana fushi dani, I’m very scared dan bazan iya jurewa ba...” Kasa ƙarasa maganan nata tayi, lokaci ɗaya kuma ta ci gaba da sakin Shessheƙan kuka, tare dasa hannayenta akan chest ɗinsa. Shi kuwa Sheykh har yanzu fushi yakeji, saboda haka ma gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi dan tsananin takaici kukan da takeyi. Hannunshi yasa ya soma ƙoƙarin ɓanbareta daga jikinsa, murya adaƙile yace. "Ni Sakeni! ki barni!! kuma ki fita harkana!!! Kije can ki gama kukan naki a can ɗakinki, badai kinfi sonshi ba? maza fice min a ɗaki ni ɗakina ba wurin zubda hawayen soyayyar wani ƙato bane." Jin hakanne yasa, cikin sauri tasa hannayenta ta saƙalo wuyanshi, tare da cusa kanta a ƙirji shi, murya a raunace tace. "Ni banason shi, da gaske Yah Sheykh ka yarda dani bana sonshi, aduniya waye zanso sama da kai? kaine fa Mijina, mahaifin ƴata, sannan kuma Garkuwa ta, tayaya zan so wani bayan kai?” Da sauri yace. "Eh mahaifin ƴarki ko? Bama mahaifin ƴaƴan kiba, wato irin daga ita shike nan ko?". Baby face d’inta ta shag’wabe, cikin kasala da kuma son sauk’ar masa da fushinsa tace. "I’m very sorry Zawj mahaifin yaƴana." Idanunsa yaɗan lumshe, cikin kuma yanayin fara jin sanyi arashin ya tureta ya koma bakin gado ya zauna tare da cewa. "In dai bazaki bar kukan nanba fice min a ɗaki sanida kukanki yana ƙona min rai". Da sauri tasa tafin hannunta ta share hawayenta. Kana ta matsoshi Ahankali ta kwanta a jikinshi tayi lib, laɓɓan bakinta taɗan tattauna kana a raunace tace. “Please Yah Sheykh nabar kukan, amma ka yafe min, bazan sakeba dan Allah kayi haƙuri". Ajiyar zuciya mai sanyi, ya sauƙe dan ta haɗashi da Allah ta gama zance. Juyowa yayi asanyaye ya fuskanceta, tare dasa hannunsa ya ɗan tallafo kanta, shiru yayi batare daya ce komae ba, sai tsurawa fuskarta ido da yayi. Ganin hakanne kuma yasa ahankali ta sake matsowa jikinsa, wani sassanyan hugging tayi masa, tare da fara sauƙe tagwayen ajiyan zuciya cikin sanyi da taushin murya a hankali tace. "Nifa Bana sonshi, so irin wanda nakeyi maka, nadai soshi matsayin wana jinina, sannan kuma nayi kukane saboda rauni na. Musamman ganin yadda ake dukanshi, da kuma yadda iyayenshi ke kuka. Yah Sheykh Yah Ba'ana shine wanda yayiwa Ummey magani tsawon shekaru biyu ba dare ba rana kafun ta fara magana ta dawo haiyacinta. Naje gidansu dare da rana cikin ruwa da iska na amsowa Ummey na magani, Bai taɓa cutar da niba, Ya soni tamkar ransa, Nikuma na soshi matsayin ɗan uwa musulmi, Shekaran jiya tausayin dukan da akayi mishine ya sani kuka. Jiya kuma tunda Jalal yace min za'a yanke masa hukuncin kisa raunina yasa na kasa tsaida hawayena. Amman bawai dan ina sonsa so na aureba, kawai dai akullum Ina tuna al'khairinsa garemu ne, domin koba komae shid’in yayi taimako agaremu”. Wani sassayan numfashi ya sauƙe tare da, sa hannunshi ya ruggumeta gam-gam a jikinshi. Haka nan yaji duk jikinsa yayi sanyi. Jin yanda yayi hugging d’inta ne kuma yasa ahankali tace. "Nida Allah ya azurtani da miji kamarka, miji na gari! Mumini! Salihi! Mai tausayina! Mai riƙo da ibada! Mai cikakkiyar nagarta! Ta yaya idona zai iya ganin wani ɗa namiji da wata suffar, har in soshi? Nida nake da kai, na shaida Allah yamin kyakkyawan zaɓi! Ina sonka sosai Yah Sheykh nah, Hamma Jabeer, kuma Malam d’ina, ina sonka, zan kuma ci gaba da sonka iya rai da mutuwa, sannan please ka yafe min zuwan da banyi gareka ba, ka d’aukeshi amatsayin ajizanci da kowani d’an Adam keyi, then maganan Afreen kuma kaina ke ciwo shiyasa na barta dasu Junainah, ka yafe min ni bani da sama daku kaida Afreeen kune farin cikina. Kune silar dawowata Nigeria'n rankune ke ajiye dani a masarautar Joɗa". Wani irin sasayyan kiss ya manna mata a goshinta. Cikin kuma yanayi jin sanyi da daɗin kalamanta yace. “I Love you Aysh, I always Love you, I love you so much, Tabbas nayi farin ciki da samun aurenki farin ciki marar misaltuwa, Kece cikon farin cikina My Wife, kece sanyin zuciya da idanuna! sannan kuma har lau kece GARKUWA ta! Duk wani farincikin da zan samu yana tare dake ne, hakika ke HASKE ce acikin rayuwar Jabeer, zan rayu dake har abada!!” Yakai ƙarshen maganan nasa cikin wani irin murya, mai sauƙar da kasala, tare kuma da zame jikinsa, ahankali ya kwanta kana ya jawota ya kwantar da ita ajikinsa. Idanunta ta zubawa kyakkyawar fuskarsa, Cikin kuma yanayin sanyi tace. "Please Yah Sheykh, idan da hali kayi wa ya Ba'ana wata al'farma mana". Kallonta shid’inma yayi kana hankali yace. "Wacce irin alfarma kikeso ayi masa?” Cikin zubda hawaye tace. "Dan Allah kasa a meda case ɗinsa kotun musulunci, a yanke masa hukuncin Musulunci dan Allah". Kansa yaɗan jinjina, cikin yanayin jin rauni da tsananin tausayi kuma yace. “I’m understand My Shatu, but amma kiyi haƙuri kinji, ki daina kuka domin dama tuntuni kotun musulunci aka kai ƙarar, kotun su Abban Yusuf (HUKUNCIN ALLAH) za'a yanke masa Insha Allah" Wani sassayan numfashi ta fesar tare dasa hannu ta share hawayen ta. Kana anutse tace. "Alhamdulillah!” Shiru ta ɗanyi sakamakon jin yanda ya soma yawo da hannnunsa akan waist dinta, akasalance ta ɗago kanta ta kalleshi, wanda shi ɗinma kuma kallonta yake da lumsassun idanuwansa. Ahankali ta matso da fuskarta gab da nasa, tare da zaro harshen ta ta ɗaura akan lips ɗinsa, domin ta fahimci a irin wannan yanayin sam ba buƙatar ace, sai ta jira shi ya fara kissing ɗinta. Idanunsa da suka ɗan sauya kala lokaci daya ya lumshe, musamman alokacin da yaji sauƙan harshenta akan laɓɓansa. Wani irin sha’awa da shauƙinta yakeji, hakanne ko yasa shi buɗe bakinsa, ahankali ta zura harshenta acikin bakin nasa. Wani irin dogon numfashi dukansu suka Sauƙe alokacin da tongues ɗinsu suka had’e waje ɗaya. Azafefe suka shiga kissing din juna, Yayinda kowannensu ke transferring yawun bakinsa wa ɗan uwansa. Kissing ɗin juna sukeyi sosai, Yayinda Aysha’n ke neman zautar masa da lissafi, hakan kuwa shiya sanya azafafe ya zare vail ɗin da ta rufe jikinta dashi. Ganinta da yayi acikin royal blue sleeping gown ɗin da yayi ne kuma, yasa shi jin wani hot feeling ɗin ta. Lokaci guda ya soma sakar mata kiss tako ta Ina. Yayinda daga gefe guda kuwa daddaɗan kamshin Oud dinta ke sake kunna sa. Aninayen dake jere agaban rigar nata ya ɓalle, tare da zare rigar daga jikinta gaba ɗaya, haɗadɗiyar surar jiki dana kirjinta ya zubawa ido, yana me sakejin sonta acikin zuciyarsa. Jikinsa na rawa tamkar wanda bai taɓayin sex da ita ba, haka ya mannata da jikinsa bayan ya zama naked. Atare suka soma fitar da wani irin numfarfashi, saboda yanda duk suka ruɗa juna da salonsu. Zama yayi akan gadon tare da ɗorata asaman jikinsa, lokaci daya kuma yaji numfashinsa na kokarin daukewa saboda yanda yaji Manhood ɗinsa ta samu kekkyawan masauƙi, dumi da kuma daddaɗan sweet da ya samu kansa acikine kuma yasa tunkafun aje ko ina yasoma yi mata wasu kalan sambatun dake nuna yana matuk’ar enjoying mood din. Domin kuwa harji yake kaman zai shiɗe. kaman kuma yanda yake azauce haka itama Shatu’n... After 58minute Bayan kuma komai ya lafa sunyi wanka sun fitone. Ya kalleta da kyau ganin yadda ta lafe ta kwanta lib, da’alama ta ɗan gaji ne. Murmushi yayi sannan ya fice daga cikin dakin, Dinning area yaje. Tea mai kwauri ya haɗa da zafi ya cika ɗan babban kofi kana ya dowa daƙin. Hannunshi ya miƙa mata, ganin haka yasa ta kama hannun, Ɗagota yayi ta zauna, kana shi kuma ya zauna agefenta. Cup ɗin tea din ya kai bakinta. Babu musu kuwa ta buɗe bakin sabida wani irin masifeffen yunwa da takeji, shikansa yasan dole ne ma, taji yunwa, sabida yanda yayi heaven sex da ita yau din, is so special. Tasha tea din sosai, saida ta kusan shanyewa ne kuma ta janye kanta ahankali, tare dayin gyatsa asanyaye tace. "Alhamdulillah". Hannunshi yasa bisa cikinta a hankali ya shafa cikin kula yace. "Shanye shi ko mangana". Ya ƙare maganar yana sa mata cup ɗin tea din abaki. Shanyewa tayi kana ya aje cup ɗin bisa bedside. Sannan yazo ya kwanta ya jawota jikinshi. Washe gari ranar Monday kotu ta yanke wa Ba'ana hukuncin kisa ta Hanyar rataya. Sabida hujja da shaidar daya bayar a kan kanshi. Kana yayi bayanin duk shanayen da yake sacewa daga wannan ƙasar zuwa waccar ƙasar. Ya bada tabbacin duk suna nan. Ya kuma sa yaranshi sun medawa kowa nashi. Domin suma sun musulunta. Bayan kwana biyu aka shirya rataye shi. Bayan anyi komai an fito da shine. Ya kalli taron fulanin Rugar Bani. Cikin zubda hawaye yace. "Dan Allah ku yafe min". Wani irin raunine ya rufesu mai sa zubda hawaye. Kusan a tare sukace sun yafe mishi. Cikin sanyi yace. "Ngd". kana ya juyo ya kalli Sheykh dake gefensa, murya na rawa yace. “Ga dai ƙarshena ni kam, Allah bai nufa zan rayu da Shatu ba. Allah ya ƙaddara matarka ce. Dan Allah ka kula da ita Shatu mace mai rauni da tausayi." Cikin zubda hawaye Sheykh yace. "In sha Allah". Sai kuma ya kalli Bugulu cikin rauni yace. "Mama kin tuna kin min al'ƙawarin zaki musulunta kuma zaki bar sata". Cikin kuka tace. "Nayi al'ƙawari". Da sauri ya kalli Sheykh a hankali yace. "Dan Allah bawa mahaifiyata ƙalmar shahada, a gaban idona in samu in mutu da farin ciki". Cikin zubda hawaye Sheykh yace. "Toh". A nan ya musuluntar da Bugulu. Nan aka rataye shi gaba ɗaya mutane na kuka. Sosai Sheykh da kanshi yayi ta kuka sabida. Amanar kula da Shatu da Ba'ana ya bashi amana. Bayan an rataye shi ne. Droo yayi musu bayanin cewa fa. Ya musulunta tun da dadewa. Hakane yasa Sheykh da kansa yayi masa wonka kana ya limanci sallan gawanshi kana aka kaishi gidansa na gsky. Rayuwa kenan. Shatu kuwa sai dai ta buya tayi kuka, Ummey da kanta tayi tashan kuka. Alhamdulillah bayan rasuwarsa da wata ɗaya. Lamiɗo da kanshi ya shiryawa Sheykh da Shatu da Ummey da Dr Aliyu da Baba Basiru da Galadima su tafi ƙasar Cameroon dan yiwa iyayen Shatu godiya da kuma nemawa Jamil auren Khadijah, dan yana son ranar auren a kuma naɗa Sheykh a matsayin Sarkin Masarautar Joɗa. Alhamdulillah sun gama shirinsu, Washe gari zasu tafine. Batool ta kira Sheykh. Suna zaune da Shatu kiran ya shigo bayan ya ɗagane ta mishi bayani ta ƙara da cewa. "Affan ne ya bani number ka. Alhamdulillah aurena next week Ina gayyatarku ɗaurin aure". Cikin ɗan sake fuska yace. "Masha Allah, Allah ya kaimu in Sha Allah zanzo nida Affan". Cikin jin daɗi tace. "Toh ngd matuƙa Hamma Jabeer". Daga nan sukayi sallama. Da sauri ya sauƙe numfashi ganin Shatu bata kallonshi ma. Ranar litin da yamma jirginsu ya sauƙa cikin ƙasar Cameroon birnin Yahunde. Wasu irin motoci masu tsadar gaskene sukazo suka ɗauke su zuwa gidan Abboi. Suna isa bayan sunyi parking sun firfito gaba dayansu Jamil ne ya ɗan juya....! By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: *Lamiɗon Adamawa, Dr Aliyu Mustapha jama'ar Adamawa duk suna a gaisheka.😭😭😭 Allah ya jiƙanka da Rahama Lamiɗon Adamawa Dr Aliyu Mustapha. Wannan shafi gaba ɗayan shi sadaukar wane gareka. Jinjina da godiya ga Sarki mai ci Muhammad Barkinɗon Aliyu Mustapha. Allah ya taya riƙe!.!.. Ya juyo ya kalli Shatu dake sauƙe numfashi tare da yin murmushi mai cike da jin daɗin ganin gida. Yah Al'ameen ne ya matso gabansu Sheykh da sauri tare da cewa. "Bismillah mu isa ciki". “Masha Allah” Galadima yace tare da bin bayanshi kai tsaye parlon Abboi na musamman suka nufa. Kana suma saura duk suka bi bayansu. Shatu da Mamey da Ummi da Sara kuwa cikin gida sukayi. Tarba mai cike da mutuntaka akayi musu tare da Kekkyawar mu'amala. Kwana su biyu rak. Suka juyo suka dawo Nigeria, bayan sun gama tsaida batun auren Khadijah da Jamil. Hafsi da Salmanu. Rafi'a da Yah Al'ameen Jalal da Hibba. Bisa mutuntakan da kimar Lamiɗo da tsarin su, na son a ranar za'a naɗa Sheykh a sarautar Sarki Joɗa, yasa duk aka tsara batun ɗaurin auren a Masarautar Joɗa za'ayi shi. Sosai angwayen keta rawar ƙafa abun. Bayan sun dawo da wata biyu. Sosai Afreen ta girma dan yanzu watanta biyar, in ka ganta kace ƴar wata bakwai ce. Rarrafenta ya nuna ko ina zataje, tayi kuɓul-ƙubul gwanin burgewa da ban sha'awa. Kuma yanzu aurensu Jalal saura watanni shida cus da izinin ubangiji. Yau asabar ne, tun safe Sheykh yana gida. Kiran sallan azahar ne yasa ya ɗan miƙe zaune bisa kujerar 3 str da yake kwance. Cikin lumshe ido ya kalli Afreen dake wasanta a tsakiyar falon. Shatu kuwa nata binta zata kamota, ta tubke mata gashin kanta. A hankali ta zauna tare da cewa. "Allah na gaji in biki, nan ki zille can in biki can ki zille nan, na lura sam bakya son a taɓa miki kanki". Murmushi yayi tare da cewa. "Waya sani ko ke ta gado". Da sauri tace. "Sai dai in Junainah ta gado". Miƙewa tsaye yayi yana murmushi. Sai kuwa yayi sauri ya koma ya zauna Kamar wanda aka ture ya faɗi. Da sauri ta miƙe tare da matsoshi cikin kula tace. "Subahanallahi Yah Sheykh lfy kuwa?". Hannun yasa ya dafe kanshi da kai, tare da rumtse idanunshi. Da sauri ta zauna ta jawoshi jikinta, kanshi tasa bisa ƙirjinta cikin sanyi murya tace. "Yah Sheykh baka da lfy ne". Manna kanshi yayi da ƙirjinta murya can kasa, kana ido a lumshe yace. “Ba komai fa Aish kontar da hankali ki". Cikin rau-rau da ido tace. "Ta yaya zan kwantar da hankalina kuma, in ka tsaya kai ɗaya kana shirin faɗuwa na lura da hakan da daɗewa". Ajiyan zuciya ya sauƙe kana a hankali yace. "Lfya ta lau Aish bakiga ma, yadda nake yawan cin abinci ba, bini-bini naci abinci, toh amman kuma wannan karon laulayin da jiri yazo min, musamman in na daɗe a zaune, toh in na tashi tsaye sai inga har duhu yana rufe min ido". Cike da mamaki tace. "Laulayi kuma?". Ta ƙare mgnar cikin zaro ido. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. "Eh mana". Da sauri tace. "Waye mai cikin?” Tashi zaune yayi tare da cewa. "Kece mai cikin mana nine kuma mai laulayin". Da sauri tace. "Na shiga uku Yah Sheykh ciki kuma?nifa tun jinin biƙi ban sake yin jiniba". Kiss ya sakar mata a goshi kana a hankali yace. "Toh kafin wani jinin yazone kuma ciki ya shiga". Cike da al'hini tace. "Yah Sheykh ban ganeba". Cikin tsananin jin daɗi yace. "Allah kuwa Aish kinada ciki, na kimanin watanni uku har ya shiga na huɗu, yana ma gab da fara motsi". Da sauri ta ɗan ja da baya ɗage rigarta sama kaɗan tayi tare da zubawa cikinta ido, ya ilahi ya mujibadda'awati ta faɗa hawaye na kwaranyo mata murya na rawa tace. "Innalillahi Dr. Afreen na da watanta biyar kacal kuma ace ina da ciki, yarinyata zata sha wuya, na shiga uku". Da sauri ya jawota jikinshi ya ruggumeta tsam cikin kwantar mata da hankali yace. “Baki shiga uku ba Aish, al'janna zaki shiga da izinin Ubangiji, aihuwa rahamace Shatu, wasu suna nema ido a rufema Allah bai basuba mu kuma ya bamu. Kuma Alhamdulillah batun Afreen nima da fari hankalina ya tashi so da naga. Ba abinda nonon yayi mata sai ban damuba, ni yamin ma ko kin sani kawai kina ɓoye min ne, sabida kada in sani in nuna farin cikina har Magauta su gane shiyasa baƙi in gaya miki na gane". Cikin zubda hawaye tace. “Yah Sheykh daga haihuwa da kwana arba'in fa kenan na samu ciki". Dariya mai sauti yayi tare da cewa. "Ance miki ni ɗin wasane, bugu ɗaya nakeyi ƙollo ke shiga raga. Gashi kema ɗin ma zalamemmiyace da an baki saiki karɓa. Toh mu godewa Allah kinji ko Mar'atussaliha, muyi farin ciki da abinda Allah ya azurtamu dashi, kiyi Sujjadar godiyar Allah kiyi hamdala sai mu roƙi Allah yasa tagwaye ne, ina kina son ƴan biyu?” Cikin jin sanyi da daɗi tace. "Uhumm sosai ma kuwa Yah Sheykh". Kai ya ɗan ronƙofa ya sumbaci lips ɗin ta kana yace. "Toh Allah ya bamu". Amin Amin tace. Kana yaje yayi al'wala ya wuce masallaci. Ita kuma ta ɗauki Afreen ta wuce da ita. A falo ta samu Junainah ta miƙa mata ita kana ta wuce. Bayan kusan wata biyu kenan lokacin cikin ya cika wata biyar. Sosai ya ɗan fito cas sai kuma tayi yar ƙiba. Afreen kuwa yanzu tana dafa abu ta miƙe tsaye. Aurensu Jalal saura wata 4. Alhamdulillah tana fama da karatunta, kuma wanda yanzu suke shekarar ƙarshe ita da Rafi'a shiyasa ma aka kai bikin da nisa dan Rafi'a ta ida. Tana ruggume da Afreen ta shiga Part ɗin Mamey, dawowarta daga makaranta kenan. Da sauri Mamey tasa hannu. Ta amshe Afreen sai kuma ta kalli Sara dake biye da ita a baya tace. “A'a Sara ya haka, kin barta da jaka da wannan lukutar ƴar tasu". Cikin sauƙe numfashi tace. "Wlh Mamey Afreen na min son inna a soka asha jinin jikinka, wai sai taƙi Sara ta amsheta dole sai ni zan riƙeta". Ta ƙare mgnar tana dungure kanta. Dariya ta karketa kanar tasan abinda akace..ita kuwa Mamey da sauri tace. "Toh Sara ɗauko mata abinci." To tace kana taje ta ɗauko mata. Bayan ta ɗauko ta ɗauki nata ta tafi. Ita kuwa Mamey serilac ɗin Afreen ta dama kana ta fara bata. Tana bata tana kallon Shatu. Sai kuma ta ɗan yi gyaran murya tare da cewa. "Da sauƙi ma ai duk da wahalan karatun da rainon bai sa kin rameba". Kanta ta ɗan sunkuyar ta kalli cikinta cikin yin ƙasa da murya tace. "Toh ba cewa yayi wai inada cikiba". Da sauri Mamey ta danne dariyarta tare da cewa. "Wai ne ma Shatu? Har yanzu a wai yake?". Cikin ɗan jin kunya tace. "Uhum". Nan dai sukayi ta hira daga bisani ta miƙe ta koma Part ɗin ta. Alhamdulillah shirye-shiryen aure nata kan-kama. Tare da shirin naɗin sarauta. Tako ina tako wani lungun da saƙon masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria da kudancin, dama maƙotan mu kamarsu Niger, Cameroon, Chadi. Da dai sauransu duk takardar gayyatar naɗin sarautar sabon sarkin masarautar Joɗa ya riskesu. Shiri iya shiri akewa bikin da yake haɗe da ɗaurin auren mutane shida. Cikin Shatu kuwa ya girma ya fito ras, sabida yayi watanni takwas. Afreen kuwa Alhamdulillah tana gudu ko ina yanzu ga gwarancinta ras. Watanninta goma sha ɗaya amman in ka ganta zakayi zaton Yar watanni goma sha biyar ne. Alhamdulillah su Shatu sun kammala karatun su lfy, komai yayi yadda ake buƙata. Hajia Mama kuwa duniya tayi mata atishawar tsaki. Sabida kuturta ya kuma shiga yatsunta na tsuntsayen. A hankali take tafiya Afreen na riƙe da yatsarta. Tana ta gwaranci. "Abba! Abba! Abba!". Murmushi yayi tare da buɗe mata hannunshi da sauri ta tsaki yatsar Shatu ta nufi inda Sheykh ke tsaye, cikin tarin farin ciki yace. "Oyoyo Mamina". Kana ya ɗagata sama. Murmushi Affan yayi tare da cewa. "Afreen sarkin wayo ita kowa natane". Jamil ne yace. "Hmmmm ai ni jiya ta bani mmki. Wai Ance Abbanmu na kiranta zai bata sweet wai sai tace. “Bata so Abbanta a kawo mata". Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Kuma daga baya ta bishi da gudu tana Abba cha ciwiut". Murmushi Sheykh yayi kana ya sauƙeta, tare da kallon Shatu dake zaune ta tasa cikinta gaba. Cikin wasa ya kalli Jalal daya shigo yanzu yace. "Jalal ko dai zamu ɗaga bikin kun nanne sai Aish ta haihu zatafi sakewa". Da sauri ya katse wayar da yakeyi da Hibba tare da cewa. “A'a me yayi zafi, tasha zamanta a ɗakinta mun hutasshe ta zuwa bikin". Jamil kuwa kwaɓe fuska yayi tare da cewa. "Uhumm wai a ɗaga". Dariya Affan yayi tare da kallon Sheykh dake musu murmushin wasa nan dai sukaci gaba da tattaunawa kan bikin. Alhamdulillah yau bikinsu Jalal saura mako ɗaya rak. Komai ya kankama. Tuni baƙi sun fara cika masarautar Joɗa tako wani yanki. Hotels din Ɓadamaya Lamiɗo da Sheykh sun kama fiye da rabinsu sabida, sauƙar baƙin da suke tsastsafowa tako wani yanki. Yau jumma'a wanda ya kama sauran kwana bakwai cin a nawa Sheykh rawani jumma'a mai zuwa kenan. Wanda ya kama kuma ranar za'a ɗaura aurensu Jalal tuni su Umaymah da tawagarta sun iso. Tun da safe kuwa yau Shatu ta tashi da ciwon mara, kaɗan-kaɗan. A haka take ta sabgoginta, sabida tana tare da amare duka uku. Sha ɗaya dai-dai na safe Allah ya sauƙeta lfy ta haifi ɗanta na miji santalele. Farincikin a ahlin Sitti ba'a mgn. Bayan an gama kimtsa mai jego da jaririnta kato fari ƙal dashi. Suna kwance Sheykh ya shigo. Cikin tarin farin ciki dan yana gidan Malam Abubakar ne Yah Jafar ya kirashi ya masa al'bishir. Cikin jin daɗi ya zauna gefen Shatu. Tare da miƙawa Safiyyah hannu ta miƙa mishi jaririn murya cike da zallan farin ciki yace. "Alhamdulillah masha Allah. Allah na gode maka, da wannan kyauta da kaimin. Ya Allah kasa baɗi iwar haka mu samu tagwaye". Dariya sukayi baki ɗayansu ganin yadda Shatu ta zaro idonta cikin alamun tsoron tace. "Wayyoooooooo Allah na. Yah Sheykh sai kace wata inji". Aunty Rahma ce tace. "Ato ai da alamar hakan zakuyi tunda gashi a shekara ɗaya an samo irin tagwayen Nana Faɗima". Ummi ce dake gefe tana fifitawa Shatu tea tace. "Ko ƴan ukune Allah ya kawosu akwai masu tayaki rainon su. Inji gashi yanzu Afreen tunda aka yayate, sai dai tazo ta leƙaki tayi gaba abinta". Da sauri yace. "Uhumm yauwa Ummi na gaya mata dai". Ya ƙare mgnar yana sumbatar goshin yaron cikin tsananin farin cikin da son yaron. Sai kuma ya kalli Mamey dake shigowa yace. "Mamey da waye yake kamane?". Matsowa gabanshi tayi ta kalli fuskar jaririn kana tasa hannunta ta tallabo tashi fuskar. Cikin jin daɗi tace. "Da kai yake kama". Cike da jin daɗi yace. "Alhamdulillah". Nanfa akaci gaba da hidima. Yau kwana biyu da haihuwar Shatu. Zaune yake agaban Mamey da Abbanshi, kai ya ɗan ɗago ya kalli Abbanshi tare da cewa. "Ummm Abba nace wanne suna za'a sawa yaron?". Murmushi mai cike da jin daɗi Abba yayi tare da cewa. "Na baka zaɓi zaɓawa ɗanka sunan da kafi so". Murmushi mai cike da jin daɗi yayi tare da cewa. "Mamey kefa, ko Jadda kikeso inyi mai suna". Yayi mgnar cikin raha. Da sauri tace. "Mutun da ɗan shi mun baka damarka a matsayinka na uba". Kanshi ya sunkuyar tare da cewa. "Ngd matuƙa da wannan damar". Daga nan ya sallamesu ya miƙe ya fita. Bedroom ɗinsa ya wuce. Yana shiga ya kira Shatu a waya, ta kawo mishi ɗan. Yayi mishi huɗu ba. Ido ta ɗan zuba mishi tare da cewa. "Me sunanshi?." Murmushi yayi tare da kashe mata ido a hankali yace. "Sai ranar suna zakiji". "Abinma sirrine kenan". Ta faɗi tana murmushi. "Ina da wani sirrine bayan ke, Y.M.D.G na". Ido ta zuba mishi tana mai nazartar baƙaƙen da yake yawan faɗi wasu lokutan. Kiranshi da akayi a wayane yasa ta bar zancen. Ranar jumma'a, da safe bayan an fito sallan asabu, aka raɗa sunan yaron kana suka nufi cikin gida kowa na mamakin sunan da Sheykh ya sawa ɗansa. A tare suka shiga falon shida ƙannensa. Da sauri Mamma tace. "Affan me sunan ɗan naku?". Murmushi Affan yayi tare da nuna Sheykh dake wucewa Side ɗinsa Haroon da Ibrahim na biye dashi a baya. Da sauri Umaymah tace. "Affan me sunan ana tambayarka kayi shiru". Cikin dariya yace. "Uhumm Yah Sheykh da abun mmki sunanshi fa ya sawa ɗan, duk zuriyar mun nan ya rasa wanda zaiwa takwara sai yayiwa kanshi". Cike da mamaki su Ummi sukayi salati, shi kuwa Sheykh murmushi yayi tare da juyowa jin yadda suke salati yana dariya yace. "Yoh duk zuriyar mu, nuni wanda sunanshi ya kai nawa daɗi Muhammad Jabeer, kuma kafin in burge wani gwara in burge kaina da kaina. Kuna ina son yaron yaji daɗin da nakeji a duk sanda naji an kirani da sunan sabida iyayena sunmin kekkyawan zaɓi". Murmushi Mameyn tayi tare da cewa. "Allah ya raya Muhammad Jabeer ƙarami yasa ya gaji halayyar mahaifinshi". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Ita kam Shatu murmushi takeyi tana shafa kan jaririn. Tare da kallon Afreen dake zaune gefenta. Oh Allah mai iko wai itace dai Shatu da yara har biyu. Nan dai sukaci abinci. Kana duk mazan suka fara shirin fita ɗan sha biyu dai-dai za'a naɗa Sheykh. Ƙarfe ɗaya saura. Duk illahirin manyan Masarautar Joɗa, da baƙin sarakuna. Da duk maza ahlin masarautar Joɗa, hatta Jabeer da yau aka fita sunansa. Jalal yazo dashi. Gaba ɗaya ɗakin rantsawar ya cika maƙil da bani Adam. Babu abunda ke tashi sai sarewa da tambura da al'gaita da kakafi. A hankali Lamiɗo ya tashi bisa kujerar, kana ya matsa. Sarkin naɗi, ya kamo hannun Sheykh dake cikin shiga ta al'farma shigar limancin. Ya matso dashi gaban kujerar, kana a hankali yasa hannunshin ya zare hiramin kansa. Sannan ya sunkuyo ya amshi. Rawanin da Lamiɗo ke miƙa mishi. Yana daga tsayen ya naɗa mishi. Kana ya juyo bayanshi da niyar zare al'kyabbar jikinshi. Da sauri Lamiɗo yace. “A'a barshi da shirgarsa ta limancin, shigar sarauta bazata kori ta limancin ba.". A hankali Sheykh ya lumshe idonshi yana mai jin wani irin masifeffen nauyi dake ratsa kanshi nauyin rawanin mulkin Masarautar Joɗa. Shi kuwa Sarkin naɗi kai ya gyaɗa kana ya zaunar da Sheykh bisa asalin kujerar masarautar Joɗa da sunan Allah a bakinsa. Kana aka miƙa mishi sandan ya amsa ya riƙe, sarkin fada ya matso kusa dashi. Hakama ɗan zagi. Sauran fadawa kuwa duk sai suka matsa suka janye labulen da sukayi musu da manyan garunan su. Lokacin ɗaya gaba ɗaya mutanen cikin hall ɗin duk suka zauna Tare da jinjina kai, dan ko kai sarkine in kazo Masarautar wani sarkin to shine a sama. Sabida kalmar nan ta bahaushe. (Kare ma a gidansa zaki ne) Bare kuma sarki. Nanfa makaɗa da mabusa duk suka ɗauki amo. Cikin wani irin rauni Sheykh ya lumshe idanunshi tare da ci gaba da tasbihin da yake abokin rayuwarsa. Sabida wani irin tashi da tsikar jikinshi keyi. Sarautar tana ratsashi. Bayan an gama naɗa shi ne, aka naɗa Baba Basiru a matsayin Galadima. Wanda dama anfi son Galadima yafi sarki shekaru. Nan kuma aka naɗa Affan Chiroma. Kana Jalal Wambai, Jamil Durbi. Yah Jafar kuwa Majidaɗin Masarautar Joɗa. Masha Allah komai dai ya tafi yadda ya kamata. Nan aka naɗa duk sauran hakimai. Kiran sallan Jumma'a ne ya tadasu a taron. Nan kuma aka raka'a. Inda Sarki Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa ya kasance limamin kamar kullum. Bayan ya tsaya ya dai-dai-ta tsayuwarsa bisa mimbari. Ya fuskanci taron al'ummar Annabi dake cike maƙil a masallacin da harabar. Gyaran murya yayi cike da rauni dan fara hudbar jumma'a kamar kullum. Cikin taushin murya da lafazi. Murya na rawa yace. "Mulki, da sarauta". Sai kuma muryarsa ya fara rawa, sabida nauyin abinda yake jin tsoro daya ratsa kanshi. Hawaye na zuba yace. “Da ace ɗan Adam yasan nauyin dake cikin kalmar mulki ko sarauta da bai ɗauke ta ƙaramar kalmaba. Da daga cikinmu mun dena sha'awarta sabida nauyi da haƙƙin wanda kake matsayin shugaban su, da zai rataya akanka". Sai kuma ya sunkuyar da kansa. Cikin rauni da zubda hawaye ya fara zazzafan hudba kan sarakuna da kuma shugabannin. Wanda gaba ɗaya aka nitsu akayi cib. Mafi akasarin mutane rauni da tsoro ya sasu zubda hawaye. Bayan ya idane, akayi salla aka idar. Sannan dubban al'ummar Annabi Sallallahu alaihi Wasallam suka shaida ɗaurin auren. Jalaluddin da Muhibbar, (Jalal and Hibba) Khadijah da Jamil. Rafi'a da Al'ameen. Al'amarin yayi armashi matuƙa gaya. Nan aka fito, mafi akasarin manyan sarakuna da shugabanni da baƙi a take Airport suka fara wucewa, sabida komawa. Jirage kuma a ranar tamkar a jidda Airport a lokacin aikin Hajji. Haka jirage ke tashi. A Ɓadamaya International Airport. Tuni mutanen Cameroon sun tafi da amryarsu. Da duk mutane su. Hakama su Aunty Rahma sun kai Hibba part ɗin ta. Mutanen Cameroon kafin su tafi sun kai. Khadijah Part ɗinta. Sosai mutanen gidan suka ɗan rarragu. Sheykh kuwa hada-dadar jama'a ta hanashi shiga gida. Sabida zaman fada. Sai bayan sallan isha'i ya samu shiga gida. Kai tsaye Part ɗin Mameynshi ya wuce. A can kuwa ya samu su Umaymah gaba dayansu. Sai Shatu da Junainah dake Part ɗinsu suna gyarawa sabida mutanen sun tafi. Cikin jin daɗi Mamey da yan uwanta sukayi ta sanya mishi albarka da mishi addu'o'in Allah ya bashi ikon mulki kan gsky. Ga mamakinsu yana kuka. "Amin Amin". Daga nan ya fito ya nufi Part ɗinsa. Ita kuwa Shatu tuni sun gama kimtsa komai. Har tayi wonka, ta kimtsa cikin wata tattausar doguwar riga mai ɗan karen kyau. Afreen da Jabeer kuwa dama Ummi tayi musu wonka kafin ta tafi. Tana ruggume da Jabeer Afreen na biye da ita a baya ta nufi Side ɗinsa. Jin Junainah na ce mata. Adda Shatu Hamma Jabeer na kira. A hankali ta tura ƙofar tare da sallama a bakinta. Cikin sauri ya juyo dan dama bai ƙarasa shiga tsakiyar ɗakin ba. Wata iriyar sassayar ajiyar zuciya mai sauƙi Shatu ta sauƙe. Sabida ganinsa cikin shigar sarakuna yayi masifar ratsata kwarjininsa ya ninku ɗari bisa ɗari. Afreen kuwa da gudu ta nufoshi. Ta isa ya sunkuyo ya ɗagata sama, ya ruggume ta tsam a jikinshi da hannu ɗaya. Kana ya buɗewa Shatu hannun ɗaya. Da sauri ta iso ta faɗa jikinshi. Ruggume ta yayi tsam a jikinshi. Cikin sanyi murya na rawa yace. "Aish bayan nauyinku. Ke Afreen Jabeer da kai tsaye in ance iyalaina ku ake nufi. Kana Abbana Mamey dasu Jalal da in ance ahlina su ake nufi. An sake ƙara min nauyin da duk Ɓadamaya nine shugaba a garesu kuma abin dubawarsu". Tasan mijinta tasan rauni sa. Tabbas tasan baison mulkin nan, tamkar dolene. A hankali ta kuma ruggume shi gam jin yana cewa. "Mulkin nan yana ɗaya daga cikin manyan abubuwan da Lamiɗo ke tirsasani inyi a rayuwata. Sai dai na yarda da batun mulkin ne bisa Kekkyawar niyar yin gyara da kauda al'adun da ba tsarin shariya ba, da kuma kauda wasu abun da suke kamanceceniya da asiri". Cikin jin daɗi tace. "Allah ya baka ikon gyara ya kuma kare mana kai da kariyarsa. Ya baka rai da lfy da damar gyara al'farmar Annabi da al'ƙur'ani". Amin Amin yace cikin rauni. Alhamdulillah komai ya dai-dai-ta. Kab baƙin sun koma. Lamiɗo kuwa tunda aka naɗa Jabeer dole ya bar masarautar Joɗa domin ba'a sarki biyu a gari ɗaya. Dole ya koma Mubi da zama, sai dai Sheykh na yawan kai musu ziyara. Yana ɗaya daga cikin abinda yasa yaji baison Lamiɗo yayi murabus ya bashi mulki sabida yasan za'a nesan tasu. Junainah taci gaba da karatunta, nan cikin Joɗa. Junaidu ma yayi nisa da karatunsa. Alhamdulillah anyi auren Yah Salmanu da Hafsi ma, kana Yah Gaini da Binto. Yah Seyi da Mari. Sai Yah Giɗi kuma da yar Jamila ƙanwar Junaidu mai binshi. Rayuwa na juyawa, lokacin na tafiya, wuni zuwa kwana. Kwana zuwa mako. Mako zuwa wata. Wata zuwa shekara. Alhamdulillah an yaye Jabeer lfy lau Afreen nada shekara biyu da rabi shi yanada shekara ɗaya da rabi. A cikin haka ne Sheykh ya Haɗe kan ahlinsa suka tafi aikin hajji. Sosai sukaji daɗin zuwan domin kab ahlin Sitti sunje. Bayan sun dawone Shatu ta fahimci tanada shigar wani cikin. To Alhamdulillah wannan laulayinsa son sex ne Sheykh ya zama ba sauƙin. Yana fada ma in ta ciyosa zai gudo yadawo. Alhamdulillah Kuma haka dai sauke tafiya, wasu lokutan Shatu kan gudu ta koma Part ɗin Mamey. Yanzu cikin ya fara girma. Yauma kamar mafi akasarin lokuta. Suna zaune a falonta. Ita da Khadijah da Hibba wanda suma sunyi haihuwar farinsu. Kuma yawanci yanzu Afreen tana Part ɗin Hibba da Jamil. Shi kuwa Sheykh da sauri ya wuce Side ɗinsa yana cewa. "Mitcwww a wani saka tafiya a hankali kamar Wahainiya wai kai sarki. A riƙeka a fada a hanaka ganin iyalinka a duk sanda kake so. Mulki ko jaraba". Ya ƙare mgnar yana kiran Shatu a waya. Cikin kwaɓe fuska tace. "Na'am Hamma". Koikoyan muryar ta yayi tare da cewa. "Na'am Hamma. Dan Allah kizo kinji ko Shatu na. Kizo miyi wata mgnar dan Allah kada kice a a". Cikin sanyi tace to. Kana ta miƙa ta fita. Tana shiga ya juyo yana zare al'kyabbar jikinshi tare da cilla rawaninshi gefe ruggume ta yau tare da cewa. "Itta wannan harka da kike gani, babu ruwanta da rawanin sarki ko matsayinshi dole yayi ƙasa da ita yayi mubaya'a". Ya ƙare mgnar yana longoɓar da kai bisa kafaɗa. Murmushi tayi tare da cewa. "To me kuma kakeso?". Kanta ya nuna mata da ƴar tsarshi tare da cewa. "Abun daɗi na, nakeso". Ya ƙare mgnar yana zuge zip ɗin rigarta yayi ƙasa dashi. Murmushi tayi tare da kamo hannunsa ta daura akan mararta, cikin yanayin sanyi da shagwab’a tace. “To naji amma saidai kamin alk’awarin cewa bazakayi sosai yanda zaka takurawa unborn dinmu ba.” “Eh na amince.” Yafada yana me hade goshinsu waje daya, tare da daura lips d’insa akan nata ya shiga tsotsa, wani irin dadi yakeji sosai aduk lokacin daya gansa atare da Shatun. Kasa yayi da rigar jikinta tareda zame kansa ya daura bakinsa akan tsayayyun breast dinta. Cikin wani irin salo na musamman yake sucking nipples dinta, hakanne kuwa yasa duk ta rude masa, azafafe ta shiga aika masa wasu salo na musamman daya sa ƙafafunsu kasa ɗaukarsu, cikin zakuwa da kuma tarin sha’awarta dake damunsa, ya ɗagota caɗak suka ƙarasa kan makeken royal bed ɗinsu, daya sha zanin gado na alfarma. Shumfudeta yayi asaman gadon tare da zare mata duk wani kaya dake jikinta, cikin yanayin dake nuna tsananin shaukinta da yakeji, ya soma kissing din kowani gaɓa dake jikinta, more especially saman mararta da kuma kan breast dinta, saboda ya fahimci cewa aduk lokacin da yake kissing dinta awajen tanajin dadi sosai. Wani irin numfashi mai haɗe da nishi taja alokacin da taji saukan harshensa acikin privet part ɗinta, Idanunta ta lumshe tare da sake turo masa jikinta, saboda yanayin yanda yake tura harshensa garets yasa duk ta kara zaucewa. Haka shidinma gaba daya jikinsa rawa yake, musamman ma ayanzu da yaji yanda Shatun nasa ke leaking abun ba’a cewa komai. Wani irin sautin nishi na musamman suka sake atare, a dai-dai lokacin da taji manhood ɗinsa ya ziyarceta. Rungumeta yayi sosai tare da soma yi mata sambatu kala kala, wanda kuma tasan duk pleasure din da enjoying ya sasane. Domin ta fahimaci yanda ayanzu Sheykh din ke masifar enjoying mood Dinsu idan suna sex. Tabbas ayau wata duniya suka fada ta musamman, duniyar da daɗinta ya kusan zautar da Sarki kuma Sheykh Jabeer, domin wasu kalan sambatu da godiya ya dinga yiwa Shatun nasa, saboda dadin da tajiyar dashi ayau din na musamman ne. Domin kuwa bayan sex harda blowjob ta haɗa mishi, wanda dadinsa ya kusan gusar masa da tunani. Bayan komai ya lafane kuma, sun fito wonka. A hankali ta kalli wayarshi dake gefenta wanda kira ya shigo cikinta yanzu. Leƙowa yayi ya kalli wayar da sauri kuma ya juyo ya kalleta ganin taga wacce ke kiran nashi, Da sauri yasa hannunshin zai dauki wayar. Cikin sauri ta...! By *GARKUWAR FULANI* 4/6/21, 4:15 PM - &: Ta juya kanta, ganin kamar baya son taga wayake kiranshi. A hankali ta miƙe tsaye tare da juyawa ta fita. Shi kuwa Sheykh, a hankali ya sauƙe ajiyan zuciya mai nauyi. Murya a daƙile yace. "Assalamu alaikum". Cikin yanayin tarin so bege ƙauna mai tsanani Jazrah ta saki wani irin sassanyan kuka murya na rawa fuska na zubda hawaye tace. "I love you Jabeer I love you so much in sha Allah bazan taɓa yin aureba in dai bazaka aureni ba." Cikin sanyi da tausayin yadda take kuka muryarta na rawa. Ya sani ya shaida Jazrah na mishi wani irin masifeffen so. Tunda a kanshi taƙi tayi aure. Babu yadda ba,ayi da itaba taƙiya. Cikin daƙilewa yace. "Thanks". Murmushi tayi cike da jin daɗin yadda yanzu yana amsa kiranta har ya saurareta, yau kuma ga ƙarin godiya. Ta buɗe baki zatayi mgn kenan taji yana cewa. "Please ki dena kirana ba tare da izinina ba. Ki gaya min ta text in na gani na baki lokaci sai ki kirani." Da sauri tace. "La ba'as". Daga nan ya katse kiran Yana mai ta ajjudin kafiyar Jazrah. A hankali a haka dai rayuwa tai ta juyawa. Lokacin na tafiya kwanaki na shiɗewa makkonni na juyawa zuwa watanni na gangarawa zuwa shekaru. ***** Bayan shekaru shida. Tuni yanzu Junainah ta zama cikekkiyar budurwa ƴar shekaru ashirin da ɗan ɗori. Tuni Junaidu ya kammala karatunsa har ya kama aikinsa da taimakon Sheykh. Soyayyarsa da Junainah kuwa ta kankama ta haɓaka manya sun saka baki. An gama komai na al'adar aure kamar tambaya da kai kayan aure. Daga bisani ansa rana nanda wata ɗaya rak. Alhamdulillah Shatu kuwa yanzu yaranta shida. Afreen. Jabeer. Muhammad. Abdulkarim. Habib. Khausar. Afreen, Jabeer, Muhammad takwaran bappanta, suna kiranshi da Bappan. Abdulkarim takwaran baban Sitti wanda randa tsohon ya rasu ranar aka haifeshi. Sai Habibullah takwaran Daddy kausar. A cikin shekarun shidan nan abubuwa da yawa sun faru, a ciki harda rasuwar. Jadda da Galadima. Yanzu Shatu ta zama cikekkiyar matar sarki mai iko. Gimbiya Saudatu kuwa ta haɗe da Mamey gwanin burgewa. Hajia Mama kuwa tana nan ita ba mutunba ita ba dabba ba. Gaba ɗaya matansu Jalal sunada ƴaƴa uku uku. Sosai aketa hidimar bikin ƴar auta. Yau tun da safe Sheykh bai fita fada ba. A cewarsa yau ranar Shatu ce. Dan yau suka cika shekara goma biyu ɗaya da aure. Suna cikin yaransu. Afreen da yanzu takeda shekaru goma da ƴan watanni a duniya tayi caras da ita gwanin kyau. Jabeer kuwa tuni ya kerera tsawo da girman jiki sau tari in waɗanda basu sansuba suka gansh akanyi zaton shine babban. Gashi shi halittar mahaifinshi Allah ya bashi kwarjini da kamala. Shiyasa tsama sosai ke tsakaninsu. Yanzuma tsaye take a gabanshi yana zaune bisa kujera yana lumshe da ido yana bitar addu'arsa cikin suratul Anfal. Cikin tsiwa da mamyancen son girma tace. "Daddy ba Kai nakewa mgna ba". Da yake haka suke kiransa kasan cewar sunan babansu gareshi. Tsaki taja tare da cewa. "Ina maka mgn ka manna min hauka ina ka ajiye min System na". A hankali ya buɗe idonshi ya kalleta, kasan cewar yaje ƙarshen surar. Murya can ƙasa yace. "Kifa dena min ihu a kaina, nace miki ban ɗauka ba, bana da shine da zan ɗauki taki argar ma". Cikin hatsala tace. "Ni kake cewa ina ihu Daddy ni mahaukaciyace da zakace ina maka ihu a kai. Wlh ka fito min da abuna". Bakinshi ya taɓe tare da cewa. "Masifeffiya ba sai kiyi ta yiba". Yana faɗin haka ya meda kanshi ya jingine ya lumshe ido alamun zaici gaba da bitar sa. Aifa ina wuta ta faɗa ciki. Cikin son girma da tsiwa tasa hannu ta dungure mishi kai cikin ɗaga murya tace. "Nice ma masifeffiyar ko Daddy, sabida raini". Murmushi mai yalwa Sheykh yayi jiyo yadda taketa masifan. Shi kuwa Jabeer sai yayi mgn kona kusa dashi bai jiba. Cikin dariya yace. "Wai Afreen kam meyasa takeda neman rigimane?". Da sauri Shatu dake gabanshi tana rage mishi kayan jikinshi tayi kwaffa tare da cewa. "J baya fa jin mgn wlh shike tsokanarta ƙasa-ƙasa". Murmushi Sheykh yayi sabida yana matuƙar jin daɗin sunan da take kiran Jabeer ɗin. In ba ya ƙureta ba da wuya ta kirashi da cikekkin sunanshi sai dai tace (J) ko kuma Mahmoud. Cikin ɗan ɗaga murya yace. "Afreen wai me nene kam?". Ya ƙare mgnar yana juyowa ya fito falo. Da sauri itama Shatu ta biyo bayanshi. Ita kuwa Afreen dake ta sababi ita ɗaya da sauri ta nufi falon Side ɗinsa da yanzu an bunkasa masa shi akwai ƙofar shigama ta gefe. Murya na rawa ido na zubda hawaye tace. Assalamu alaikum. Cikin nitsuwa ya zauna bisa kujera tare da ɗaura ƙafarsa ɗaya bisa ɗaya. Tare da cewa. "Wa alaikassalam shigo". Ya ƙare mgnar da sanin in ba yace ta shigoba nan zata tsaya. A hankali ta shigo gefenshi kusa da Shatu ta durƙusa tare da fara mgnar murya na rawa tace. "Abeey ai Daddy ne ya ɓoye min System ɗina, na tambayeshi kuma yace wai ina mishi ihu a kai, wai ni mahaukaciyace fitsarerriya wai." Danne murmushin sa yayi tare da cewa. "Jabeeer!". Da sauri ya miƙe cikin tsananin biyayya ya shigo bayan yayi sallama an bashi izinin shiga. Gefen Afreen ya tsuguna tare da yin ƙasa da kansa a hankali yace. "Na'am Abeey". Cikin tarin son yaron yace. "Me yasa zakace mata fitsarerriya?". Cikin tanƙwashe wuya yace. "Abeey ihu take min a kai kuma bitar hadda nakeyi". Da sauri yace. "Na'am wato dai ka gaya mata hakan?". A hankali yace. "Eh". Cikin danne dariyarsa yace. "Bata haƙuri". Da sauri ya ɗan juyo ya kalli Afreen cikin sanyi da ladab yace. "Kiyi Aunty Afreen bazan ƙaraba". Cikin yanayin son ɗan uwantaka tace. "Na yafe". Wani irin murmushi yayi tare da cewa. "Ina system ɗin nata?". Cikin sanyi yace. " Bappa nefa ya ɗauka ya tafi Part ɗin. Mamey dashi. Shine Khausar kuma tace mata nine na ɗauka". Murmushi Sheykh yayi tare da cewa. "Toh kinji ko Mamina a rinƙa bincike kafin ayi masifa ko!." Daga nan ya sallamesu suka fita. Jawo Shatu yayi ya ruggumeta gam-gam a jikinshi cikin tarin farin ciki yace. "Nafi jin daɗi da al'faharin in ganni tsakiyar yaranmu suna rigima ina sasantasu. Da yanke hukunci nan nake jina a cikekken sarki mai iko da dama da matsayi. Fiye da in ganni a fada in mulkar masararutar Joɗa dattawa na zama a ƙasa na." Cikin jin daɗi tace. "Na lura ai kana jin daɗin hakan". Yatsarshi yasa ya ɗan lakace hancinta tare da cewa. "Eh mana, sabida su ƴaƴa farin cikinsu nada yawa a rayuwar iyaye. Duk yawansu bazaka banbance sonsu ba. Kamar dai tsakanin mata in kana dasu sama da ɗaya." Shiru tayi tana kallonshi sabida taji ya saki layin zancen kuma, ta dade da fahimtar akwai abinda yake jimamin sanar mata. Shi kuwa ganin yadda ta tsareshi da idone ya sashi. Sauƙe numfashin sa tare da gyara zamanta a jikinshi. Murya cike da nagarta, kamala, nitsuwa, da tausasawa, yace. "Kin san meyasa nace miki haka". Kai ta jujjuya mishi alamun a'a sabida wani irin tsinkewa da zuciyarta ya fara. Shi kuwa a hankali yace. "Bari in miki kekkyawan misali. Kinga dai Afreen ita muka fara gani muka fara haifa ko. Ita Allah ya fara nuna mana matsayin ƴarmu ta cikinmu ko?". A hankali tace. "Eh". Cikin nitsuwa yace. "Gud to kinga dole ita muka fara so da sabo da ita da jin farin ciki da ita da buri da fata, da komai a kanta kawai mukayishi tsawon watannin da mukayi kafin ki haifo mana Jabeer ko?". Stiil kai ta gyaɗa mishi zuciya na tsinkewa. Shi kuwa hannunshi yasa cikin rigarta tare da cewa. "To kuma Alhamdulillah da muka samu Jabeer. Sai shima muka fara sonshi da begenshi da al'faharin samunshi. Ba tare da kuma mun dena don ita Afreen ɗin ba ko?". A hankali tace. "Eh." Kiss ya ɗan manna mata a saman breast ɗinta kana yaci gaba da cewa. "Kuma son da mukewa Afreen na forko bamu rageshi ba, saima ƙaruwar da yakeyi sabida tana girma muna ƙara shaƙuwa da ita, son kuma da muke mata bai hana muso shi Jabeer da yazo daga baya ba, har kuma muke jinshi matsayinsu dai-dai da nata. Sai dai mun san ta fishi girma dole mu nuna mishi ya bata girmanta". Cikin sauƙe numfashi tace. "Eh". A hankali yace. "Kuma gashi bayan Afreen da Jabeer ɗin yara huɗu Allah ya sake bamu, kuma duk muna sonsu, son sabbin bai ƙori na tsoffinba ma'ana sonsu Khausar bai kori na Afreen ba. Ita kuma Afreen sonta bai hana sonsu Khausar ba. Duk muna sonsu muna ji dasu, sai dai dole babba babbene kuma dole mu sosu tunda Allah ya bamu su." A tare suka sauƙe ajiyan zuciya. Harshensa ya ɗan zaro yana lasar saman breast ɗinta. Saida yaga ta ɗan nitsu kana a hankali yace. "Toh wannan itace cikekkiyar misali tsakanin miji da matasan son uwar gidan bazai taɓa hana na amrya ba. Haka kuma son amrya da take sabuwa bazai taɓa hana son uwar gidan da take sun dade tareba. Asalima tanada. Tata kimar da darajar a matsayinta na babba, wannan shine misalin daya kamata duk matan duniya ku gamsu dashi. Ki dena zaton wai in an auro amarya za'a dena sonki. Wlh sam ba haka bane uwar gidana. Ke kuma amarya ki daina gigi da zaton wai ba'a son uwar gidane ko an gaji da ita ko yayinta ya wucene aka auroki. Wlh sam ba haka bane." (Wannan itace falsafa mai kyau, in dai ke ba jaka bace ya za'ayi kiyi zaton dan ya auroki zai daina son uwar gidansa. Ke kuma uwar gida in banda kishi me zaisa kiyi zaton ke kece sama dake aka fara to ai uwarsa ma na nan kuma bare ke daya sameki rana tsaka da haƙora talatin cas a baki nai. Dan zai auro wata sai kiyi zaton ai dai nice uwar yayanshi. To babu ruwan soyayya da uwar yaya. Ke dai dage ki iya allonki ki wonke. Da kekkyawan mu'alama amrayar kanta zatafi girmamaki da ganin darajarki.) Cikin wani irin masifeffen maƙoƙon kishi kumallon mata da kuma tsantsar karantar miji da fahimtarsa murya na rawa hawaye na zuba cike da rauni Shatu tace. "Allah ya bamu zaman lfy Yah Sheykh, ƙarin aure ba laifi bane. Allah fa da kanshi ya baku wannan damar". Cikin rawan jiki da tausayin rauninta wanda yasan dole taji kishi. Cikin sanyi yasa harshensa bisa haɓarta a hankali ya fara lasar hawayenta cikin tsananin son da ganin darajarta da yabawa da kulawarta da fahimtar abinda yake son sanar mata. Shiru tayi tana jin ɗumin harshensa shi kuwa cikin sake mata kiss tako ina yace. "In bakya so ki gaya min Aish sai in fasa auren." (Toh sokuwa kada kiji mijinki yace wai in bakya so zan fasa, kice zakice bakya so. Yaseen farfaganda ce kawai, da son kwantar miki da hankali da irin su nuna miki kin isa dasu ɗinanne, kada kiyi zaton zasu tozar taki. To da kinyi wautar cewa eh. Ni bana so ban aminceba kada kayi aure. To kallon sokuwa zai fara yi miki yoh to ke uwarsace da zaki hanashi yin auren da Allah ya bashi damar yayi. Ke kuwa amrya uwar kaɗi firi ki shigo rana tsaka ki nunawa uwar gida kin fita sanin mijinta. Wawuya to wayayyu basa haka, wai ke irin ke ake so ɗinnan irin anai miki zaƙin bakin nan, to wlh kada ki kuskura kiyi zaton uwar gidanshi bata gabanshi maza bakin gangane duk ta inda yafi zaƙi ta nan suke bugawa. Domin dolene ya miki wannan zaƙin bakin. Sabida ai duk ɗan siyasa dole yayi kamfen yayin neman a zabesh to, hakama neman aure, kisa a ranki yana son matarsa. Kema mada kisa a ranki amryafa ana sonta sannan uwar gida kiyi haƙuri domin amarya ko ta buzuzuce za'ayi mata marmari, in kinga yana rawa da ƙafa ɗaya tattara ki watsarsu, basu lokaci zai dawo har kataryarki ya nemeki. Cikin tsananin zafin kishi Shatu tayi ajiyan zuciya data samu ya danne mata malolon da takejin yana gab da kasheta tace. "A'a Yah Sheykh na amince Allah ya bamu zaman lfy". Cikin tarin jin daɗi da gamsuwa da wayewarta yace. "Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati, Shatu my happiness my everything my life Mar'atussaliha". Ya fara jero mata sunaye, wani sunanma ranar ta taɓa jinshi. Da sauri ta miƙe ta fita. Tana cewa. "Laa na manta na ɗaura tukunya". Ta faɗi hakan tana fita dan kada ya gane halin da take cikin ( Sabida in mijinki ya gane miki kinada mahaukacin kishi to kallon zarerriya zai rinƙa miki, hattara mata). Tana fitowa bedroom ɗinta ta wuce. Tana shiga ta meda ƙofar ta rufe, kana ta faɗa bisa gado ta saki wani irin masifeffen kuka mai cike da kishin mijinta abin sonta. Da sauri Junainah dake Bathroom ɗin ta tanayiwa Khausar wonka ta fito. Gefenta ta zauna jiki na rawa tace. "Innalillahi Adda Shatu meya sameki meya faru?". Kawai sai ta mirgina ta ɗaura kanta bisa cinyar Junainah ta saki kuka mai rauni tare da cewa. "Ba komai Junainah na tuno su Yah Lado da Inna ne". Cikin rashin gamsuwa Junainah tace. "Adda Shatu wai yaushe kika fara ɗaukana a matsayin ƙanwar Hamma Jabeer? Kin mance tare muka tashi muka rayu bani da wani ɗan uwa ko ƴar uwa sama dake, gaya min gsky meya sameki?". Cikin yin ƙasa da murya tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa. "Yah Sheykh zai ƙara aure Junainah na kasa hana kaina kuka!". Murmushi Junainah tayi tare da cewa. "Shine zaki ɓoye min, to sa a ranki ni nan Junainah ko Ishman Aunty Rahma ya auro ni mai tayaki kishine. Kuma wlh auren a dole yazo mishi kana kada kiyi kokonton soyayyarshu gareki. Allah dole Abba ya sashi amsar auren Mamey ma har kuka tayi ita da Ummi wai kuna zamanku lfy kada a birkita muku zama sai dai naji sunce itama Aunty Jazrah Bata faɗa". Cikin jin daɗi tace. "Toh dan Allah kada ki cewa su Mamey nayi kuka hankalinsu zai tashi." Cikin gamsuwa da hakan tace. "Toh". Gyara zamanta tayi tare da cewa. "Wai yaushe kika dawo?". Cikin lumshe ido tace. "Yah Junaidu ne ya ɗaukoni wai rana tayi kada in sha rana ya kodar masa sani". Dariya sukayi baki ɗayansu. Kana sukaci gaba da hira. Haka dai aka fara shirin auren Jabeer da Jazrah, Junainah da Junaidu aure haiƙan ƙadaran. Alhamdulillah anyi aure lfy an watse lfy, amare sun tare. Kowa ya kama gidansa. Bayan shekaru goma sha ɗaya. Abubuwan da yawa sun faru cikin shekarun. Yusuf ɗan Affan ya auri Afreen sai dai basa ƙasar suna India. Jabeer ƙarami kuwa yana karatu a jami'ar Madina Bappa yana nashi karatun a India. Habibullah kuwa yana karatu a nan cikin jami'ar Ɓadamaya. Jazrah ma ta haifi yara uku Aliyu takwaran Dr Aliyu, sai Ruƙaya da Aminatu takwarar Gimbiya Aminatu wacce itama ta rasu. Shatu kuwa ta ƙara biyu Khadijah takwarar Umaymah sai autanta Sultan. Rayuwa fa ta miƙa komai yana tafiya. Hajia Mama ta rasu babinta ya ƙare a masarautar Joɗa. Yau kimanin mako biyu kenan da tafiyar Shatu Cameroon. Sai yau da hantsi jirginsu ya dawo. Habib ne ya ɗaukota da Jabeer ƙarami wanda yazo hutu. Sai Bappa wanda tare suka zo da Afreen da ƴan tagwayenta. Mu'azzatu da mu'azzam dan da tagwaye tayi haihuwar farinta. Suna zaune a falon Jazrah Aminatu na goye da Mu'azzam wanda takwaran Yah Sheykh ne. Tanata juyi tana cewa. "Sorry Mu'azzam Adda Afreen kizo ki bashi nono mana". Tura baki tayi tare da naɗewa bisa kujera, taci gaba da bawa Jazrah labarin littafin *Ba Kason ɗauka bane* na Aysha Aliyu Garkuwa. Da sauri Jazrah da yanzu take jin hausa ras tace. "Afreen kamar muryar Mamanku nakeji fa". Da sauri suka miƙa baki ɗayansu suka nufi. Side ɗin Shatu. Da gudu Afreen ta iso ta bayanta ta ruggume ta tare da cewa. "Oyoyo Mommy". Cikin sarkuri ta juyo don bayan ta tafi Cameroon Suka zo. Cikin jin daɗi tace. "Oyoyo Adda Afreen". Jabeer ƙarami ne ya ɗan harareta tare da cewa. "Toh ki barta ta shiga ciki mana, kin tsare mana ita a woje." Ya ƙare mgnar yana amsar. Mu'azzatu dake hannun Jazrah tare da cewa. "Aunty yunwa nakeji fa". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh Yah J Jabeer ɗan Jabeer". Murmushi sukayi duka kana kab suka wuce falon Shatu. Bayan sun gaggaisa ne, sunci sun sha, Shatu ta wuce ɗakinta. Tayi wonka tare da al'wala tana fitowa tayi salla kana ta kimtsa cikin wani tattausan yadi Royal blue mai ɗan karen kyau riga da zani. Ta cancaɗa daurinta ras. Ta fesa turare, da shafe humra mai sanyin ƙamshi, Da sauri ta jawo wayarta jin text ya shigo mata a waya. Murmushi tayi ganin Habibi Da'iman. Sheykh kenan. Buɗe saƙon tayi. "Alhamdulillah barka da isa lfy Gimbiya Aysha, hasken Masarautar Joɗa, kina shigowa ƙamshinki har fada yazo ya gaidani. Yanzu zamuyi salla, Please dan Allah ki gama da yaranki da jikokinki kafin in dawo in sameki a ɗakina, kinji ko Aish na". Cikin jin daɗi ta maida mishi amsa "Uhummmm toh Yah Sheykh me zaka bani?". Murmushi yayi tare da rubuta mata. "Kayan daɗin ki". Murmushi tayi tana mai lumshe ido. Ai kuwa ana idar da salla ya nufo gida. Kai tsaye ta ƙofar falon Shatu ya shiga. Su Jabeer, Bappa, Habib, Aliyu, Sultan autanshi na biye dashi a baya. A falon suka samu Afreen, da yaranta da Amina da Khausar Ruƙayya da Khadija suna cin abinci. Suna ganinshi suka gaisa. Kan Mu'azzatu dake hannun Jazrah da yanzu ta fito ɗakin Shatu dan mata sannu da hanya da kyau. Shafa kanta yayi tare da cewa. "Jika wahal da kaka ko?". Murmushi Jazrah tayi tare da cewa. "Gata ƴar lukuta". Cikin jin daɗi yace. "Haka Mamanta take tana ƙarama. Kamar yau ina tunowa haka Abbanmu ke kiranta ƴar luku". Murmushi Afreen tayi cike da jin daɗi. Jabeer kuwa baki ya taɓe tare da cewa. "Abeey nifa". Cikin son ɗan nashi Yarima Jabeer kenan motsusu yayi tare da cewa. "Kai ai na musamman ne". Duk suma sauran sai suka zuba mishi ido. Ɗaya bayan ɗaya ya yabasu. To Sheykh kuwa da tsuntsaye ma sai ya yabawa ko wacce taji bata kishin ƴar uwarta ko ganin tafi ƴar uwarta bare yaranshi. A haka dai ya wuce ya tafi Side ɗinsa. Ita kuwa Jazrah ta wuce Part ɗinta dan tasan. Shatu ce dashi yanzu. Ita kuwa Shatu a hankali ta fito tana mai baza ƙamshi. Ganin kab yaranta suna sabgogin gabansu ne yasa ta shafa kan Mu'azzam dake zaune kusa da ƙofar ta wuce Side ɗin Yah Sheykh da ɗan sauri jin yana ɗan kiran Jabeer tare da cewa. "Kira min Mommynku. Da sauri ta ƙarasa cikin falon nashi tare da cewa. "Assalamu alaikum Yah Sheykh gani da kusa". Da sauri yace. "Wa alaikassalam *(Y!.M!.D!.G!.)* na! Nooryat Noor ƙalbi My love my happiness". Cikin jin daɗi tace. "Yah Sheykh kenan kamar wasu yara". Da sauri yasa hannunshin ya kamo nata ya jawota jikinshi tare da ruggumeta ajiyan zuciya ya sauƙe tare da sa kanshi tsakanin wuyanta da kafaɗarta yana sunsunan wuyanta yace. "Aish waya ce miki soyayya tana tsufa? Ai sai dai masu ita su tsufa. Mu kuma bamu tsufan ba tukun". Ya ƙarashe mgnar tare da wucewa bedroom ɗinsa da ita. A hankali ya meda ƙofar ya rufe kirib. Tare da sauƙe nufamshi kana ya sunkuyo ya ɗagata ciɗak yayi kan gado da ita. Cikin lumshe ido ta ƙanƙameshi gam a cikinshi. Haka yasa suka kwanta a tare. Da sauri yasa hannunshin ya ture rawaanin kanshi tare da cewa. "Hegen nauyi da takura". Murmushi tayi tana mai kunce igiyoyin dake sarƙafe gaban al'kyabbar jikinshi. Tare da cewa. Ash Yah Sheykh nauyi". Mirgina wa yayi gefe ya kwanta kana ya jawota jikinshi ya zama sunan fuskantar juna. A hankali ya kai lips ɗinshi kan mata wani ɗan sasayyan kiss ya manna mata kana a hankali yace. "I missing You so much my love". Sai kuma taga ya ɗan juya da sauri ya kalli windows ɗinsa. Fahimtar yana dubawa ko a buɗene yasata cewa. "Yauwa Hamma Jabeer niko inda da wata tambaya data daɗe min a rai." Da sauri yace. "Wacce tambayace haka faɗeta miji". Ya ƙare mgnar yana tura hannunshi cikin rigarta. Hannunta tasa ta ɗan shafa sajenshi tare da cewa. "Akwai lokuta da dama ina wani dalili yasa munje HOTEL duk ɗakin da ka kama in mun shiga sai ka bibbincika ka dudduba lungu da saƙo, wani lokacin ma kace in fita mu sauya ɗaki. Koma sauya HOTEL ɗin baki ɗaya, meyasa? Me kake dubawa?." Ronƙofawa yayi kanta yana zare zip ɗin rigarta yace. "Ok ban taɓa yi miki bayani bako?." Da sauri ta gyaɗa kai. Cikin nitsuwa yace. "Wato shi HOTEL wani wurine mai cike da ƙalubale ga duk wani mutumin kirki, Especially in a cikin ƙasar ka ta haihuwa kake, domin da yawa har yanzu mutane basu fahimci cewa larura zata iya kaika hotel, ba lallai dole sai ɗan iskaba kamar yadda wasu ke zato. Sai dai abin lura a nan abinda ya kamata ga duk ko wani musulmi, muddin larura ta kaika HOTEL, to ka tabbatar ka binciki duk ɗakin daka kama ciki da woje kama Daga jikin ƙofa, wurin kunna fanka, wurin ajiye Rimot ɗin AC, Jikin AC, tsakiyar jikin fanka, saman silin, jikin ƙarfen labule, jikin TV Especially in suna fuskantar gado, da kuma jikin kan gado kofar Bathroom dama cikin Bathroom ɗin". Da sauri Shatu tace. "Me yasa? Sabida me mutun zai tsaya wannan dube-duben duka!?". Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Sabida mafi akasarin HOTEL'S wasu ƴan iskan kajeme kawai dan su dasa na'urar Camera a jikin duk waɗannan wuraren da na faɗa miki. Ya ɗauka musu duk mu'amalar mata da miji ko ɗan iska da ƴar isa, daga nan sai su sarrafashi ya zama blue Film, da yawa waɗanda suke ciki basa sanin ana ɗaukar su. Na'urar Camera da suke amfani da ita ƴar ƙanƙanuwace kamar botur ɗin rigar maza, in sun liƙata sai ta ɗauki komai. Su kansu masu hotel basa sani. Wasu lokutan kuma su ɗin ne da kansu ke dasata. In baki mantaba akwai ranar da na samu camara ɗin ma liƙe a cikin abin AC. Har muka canza ɗaki masu hotel ɗin sukayi ta bani haƙuri suda kansu suka binciki ɗakin da muka sake shiga kin tuna." Cikin jan dogon numfashi tace. "Eh tabbas na tuna Hamma, eh to lallai kuwa in hakane dole musulmai muyi taka tsantsan". Kai ya jinjina tare da cewa. "Shiyasa shi musulunci yana da daɗi kinga koda mutun baya bincika in yana amfanin da hadisin nan da manzon Allah ya hanemu da yin jima'i tsirara har sai an rufu. Kinga mutun zai tsira. To amman dai mafi sauƙi ka bincika kawai. Dan in kayi garaje wata ran za'a yaɗaka a bazaka a duniya kana jima'i da iyalinka ace BF ka fara yi. Kaga anci zarafin ka anci zarafin addinin ka". Ya ƙare mgnar da fara yin ƙasa da rigarta. Ita kuwa Shatu kai ta jinjina tare da cewa. "Masha Allah da kamilin miji mai cikekkiyar kamala da Nagarta. Sai kuma wata tambayar". Da sauri ya kwaɓe fuskarsa tare da cewa. "Bazaki bari sai na nitsuwa ba dan in baki amsa mai kyau". Cikin narke mishi a jiki tace. "Afwan kada in mance ne ai, kuma tambayar ba tsawo". Hannunshi yasa yana jan zariyar wondonsa tare da cewa. "Toh ina jinki". Cikin maida nitsuwarta gareshi tace. "Menene ma'anar *(Y.M.D.G?)*". Wani irin kekkyawan murmushi yayi mai cike da shauƙi yace. "Sirri nane kalmar". Cikin fara murzashi tace. "Dan Allah ka gaya min". Wani sassayan numfashi yaja jin salon da ta fara yi mishi. Murya a narke yace. "Sai in kinyi al'ƙawarin bazaki gayawa kowa ba". Da sauri tace. "Nayi". Murmushi yayi tare da zare rigarta ya ture gefa. Cikin raɗa yace. "Zan gaya miki harufa ukun na huɗun na ƙarshe ki ƙarasa da kanki". Cikin zaƙuwa tace. "Toh ina jinka menene ma'anar Y.M.D.G. Please bani amsa da sauri na zaƙu?". "Matso da bakinshi yayi kusa da kunnenta a hankali murya can ƙasan maƙoshi yace. "Y. Yana nufin *Yarinya* M yana nufin *Mai* D yana nufin *Daɗin* G ɗin kuma ki gane kinga ukun dai suna nufin (Ƴarinya mai Daɗin...".) Narkewa jikinshi tayi tare da cewa. "Please na tuba gaya min". Murmushi yayi tare da kai bakinshi bisa kunnenta a hankali cikin raɗa yace. "Ƴarinya mai daɗin G..." Da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen kunyan kalmar da ya rufeta. Haka nan taji kanta na huruwa yana sama tana jinta a saman gajimare ashe waɗannan harufan abinda kenan suke nufi, iya wannan sunan da yake kiranta ya isheta gane matsayin yadda Yah Sheykh ɗinta ke gamsuwa da ita ɗari bisa ɗari. Shi kuwa ya Sheykh cikin tsananin so, bege, shauƙi, kauna, yace. "Allah sarki *ƳAR FULANI* mai kunya Alhamdulillah da Na samu sa'ar samunki dan da na rasaki to tabbas da *NAYI NADAMA (MI WASMITI)* kinga ko lallai na yarda shi *NAMIJI BAYA KAƊAN* dan da shawarar Affan na fara gano magautan mu. Gashi a hankali muka samu Kekkyawan shaƙuwa da *TAUSAYAWA JUNA* sai daga baya na gano ashema ke *BANDIRAWO* ce a gareni tunda uwa ɗaya ce ta bamu tarbiya. Gashi cikin ikon Allah *RUBUTACCEN AL'AMARI* ya ƙaddara saduwarmu da aurenmu cikin *HUKUNCIN ALLAH* harda yara. GASHI MUN ZAMO tamkar hanta da jini. Tsorona ɗaya a duniya kada *RIGAR KOWA* ta fara ɗaukanki ta barni." Wani sassayan numfashi ta fesar a hankali tana maijin tattausan kalamansa gareta. Shi kuwa Sheykh cikin gsky da gsky yaci gaba da cewa. "Gwara ta ɗaukeni ta barki. Domin duk da nasan cewa *NAKASA BA KASAWA BACE* tofa in ta ɗauke min ke ta barni zan rabu da rayuwar farin ciki domin Shatu kece *GARKUWA* a gareni sabida sam Rashin ki *BA KASON ƊAUKA BANE* Agareni. Ya karashe mgnar tare da yujowa yayi mata rumfa da ƙirjinsa tare da jawo tattausan blanket ya rufesu yana mai cewa. "Mu ɓuya Shatu na kada wannan ƴar darun Hammanta AYSHA ALIYU GARKUWA, ta hangomu ta samu abin rubutawa makarantanta. iyayen son ganin ƙoƙob sai kuma ya fara tasbihai tamkar yadda ya saba. Subahanallahi Alhamdulillah wa la'ilahaillahu, Allahu Akbar Astagafirullaha..............................! Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Allah na gode maka da ka bani aron rai da lfy da nitsuwa da kwanciyar hankali ka bani iko da dama na kare wannan littafina mai suna GARKUWA lfy kamar yadda na farashi lfy dani da makaranta shi baki ɗayansu. Yah ka jiƙaina ka gafarta min al'farma Annabi da al'ƙur'ani a duk abinda nai kuskure, ka tsare min al'ƙalamina a karo na gaba. Abinda nayi dai-dai ya Allah ka taramu bisa ladan nida masoyan Manzon Allah waɗanda in an haɗa su da Allah da manzo kan kada suyi abu bazasuyi shiba. Afwan! Afwan!! Afwan!!! Masoya na makarantana, na nesa dana kusa waɗanda na sani da waɗanda ban saniba waɗanda suka biya da masu karanta na sata, wanda na taɓa mgn dasu da waɗanda ban taɓa mgn da suba. Dan Allah ku gafarceni in akwai wani abu da nayi miki/ka bisa rashin sani da ajizanci na ɗan adam ko kuma gajiya da yawan jama'a da rashin hutu yasa kinyi mgn ban kulaba kuyi haƙuri ku yafe min abubuwan ne suna min yawa. Ina mai fatan Allah ya ƙaddara saduwarmu a wani littafina lfy al'farmar Annabi da al'ƙur'ani. Godiya ta musamman gareku wadanda suka biya kuɗin littafin suka karanta da kuɗinsu ba na sataba yan na sata ba sai na ƙarasa ba yaseen doguwa bullulutu baƙar mutuwa🤣🤣🤣. *Alhamdulillah na godewa Allah da ya bani ikon cika alƙawarin da nayi ko ince yarjejeniya da nayi daku ƴan special Group, na posting PAGE bibbiyun kullum Alhamdulillah ina al'fahari yadda ko rana ɗaya rak rana ɗaya kacal dai cikin rakun littafin ban taɓa tsallakewa ko ƙetarewa banyi muku posting ba Alhamdulillah nayi al'ƙawari kuma na, cika wannan ma yana ɗaya daga cikin manyan nasarorin da na samu a littafin GARKUWA. Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah zanyi bacci hankali konce in tashi sanda nakeso* Littafin GARKUWA na kuɗine idan kinaso ki karanta wa, bada haƙƙin na a kankiba, ki sai katin Mtn na ɗari uku kacal, ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp number na 09097853276. Sai in saki a group kota ac no 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI*